Chapter 35
Chapter 35
tace Aisha me Zan gani ba dai an sakeki ba? Aisha ta fashe da kuka,Umma tace ba kece da kuka ba nice da kuka Aisha,yanzu Zaki zo ki addabeni ki buwayeni ki damu rayuwata,ki dinga wulakantani nayi nadamar rabaki da gidan mijinki Farooq,Nice na zugaki laifina nane dama ance Indai yarinya ta wuce zaman gaban iyayenta to idan ta dawo sai ta kusa dukan uwarta,Aisha tace ai kece Kika jawo min yanzu gashi nice a wahala kalli yanda na koma sai kace Jimina,wa yace ki yarda da shawara ta,ai da kina da hankali tunda ni Kika ga na kauce Hanya sai ki gyara min ai Nima ban wuce ayi min fada ba tunda na Fara manyanta kullum kwakwalwata sake kwancewa takeyi Saura kadan Aisha tayi dariya yanda Umma tace kwakwalwarta ta kwance, Aisha ta kwashi kayanta ta koma ciki wani sanyi taji a rayuwarta. Farooq Kuwa da Nabeela amarci suke Sha amma zuciyar Nabeela Babu dadi tunanin Affan takeyi Ina zata ganshi ta nemi yafiyarsa sanna son Affan take kamar hauka ko sex sukeyi da Farooq sai ta tuna Affan take gamsuwa sunayi tana ganin Farooq kamar Affan ne ke Mata sai tayi ya jin Dadi,Indai bata tuna Affan ba to baza ta gamsu ba ranar, gashi kunyar Affan take tunda yazo ya samu an daura Aurenta da dan Uwansa bata sake farin ciki ba a rayuwarta wannan yasa ta tsani Yusuf gaba daya basu zauna lafiya ba,ta dinga nunawa Yusuf halin ko in kula tun Yana binta har ya gaji Suka Fara fada kullum basu da kwanciyar hankali har ya koma wulakantata karshe ma ya saketa hakki ne ya Kama su kwata kwata Allah bai bari sunji dadin auren ba,Farooq Kuwa zuciyarsa tana ga Aisha Kawai gangar jikinsa ce a wajen Nabeela nan ma dai Nabeela bata Yi dace ba. Kamar yanda Raudat tace Affan ya shirya suje garinsu ranar na zuwa wani wanka Affan ya dauka da jakarsa ta kaya me kyan gaske in ka ganshi ka rantse turai zai tafi,Raudat kuwa wata doguwar Riga tasa na leshi dinkin manyan Mata masu ji da kansu ta Sha dogon takalmi da Jakarta ta kayan sawa sai hand bag komai coffee and white,tana Fitowa ta mikawa Affan flight ticket,wani yaron Affan ne yazo a motar Affan ya kaisu airport suka shiga jirgi ranar farko kenan da Affan ya Shiga jirgi tsabar gayu sai kace Wanda ya shekara dari Yana shiga yanda yake tafiya Yana gabatar da komai nasa,ga sit dinsa ga na Raudat suna zaune idan ya saci kallonta sau daya sai ya dauke Kai itama sai ta juyo ta saci kallonsa haka suke faman Yi har suka sauka lafiya,suna zuwa wani driver ne da mota me tsada Yana jiranta,suka Shiga mota da Affan ta Fadi sunan wani Hotel a garin ta rigada ta Masa booking Bai kashe kwandala ba,suna zuwa Hotel ne me tsada da kyau har room dinsa sannan tace Zan tafi zan dinga kawo maka abinci daga gida idan Kuma kaci a nan baka bukata ka fada min a waya tana kallonsa tana Murmushi,yace to sai ki ta min abu da kudinki karfa Watarana a min gori ni bana so nasan halin Mata bana Jin Dadi ki dinga kyaleni Ina biya Mana please bana so idan ba Haka ba Zan koma gida Kawai kin maidani yaro,Dariya tayi tace afwan to ka huta ,yace karki kawo min abinci nifa ba yaro bane ba Kuma duhun Kaine dani ba sannan Ina Jin turanci,tace to sorry na daina tace zanzo da dare muje yawo ta Kai hannu zata ja Masa gemu ya goce yace wannan fa raini ne ke ba matata ba sannan ba budurwata ba Zaki lalatani ya juya tare da rufe kofarsa,ta tafi tana Murmushi dama tsokanarsa tayi tasan fadin ransa. Yau Kawu yana dawowa Siyama ta masa Sannu da zuwa ya amsa ta karbi kayansa ta Kai daki sai tsarabar Kauye lafiyayyen nonon shanu kindirmo cikin katon wani bowl,Kwan zabi,etc Aunty tace Sannu da zuwa Suka shiga daki Siyama kuma ta Kira Aslam,kashewa yayi tare da kiranta back sallama tayi ya lumshe Ido yanda muryarta ke tafiya da Imaninsa,inyini yaya ya aikin,lfy Alhmdllh ya furta Yana gyara kwanciyarsa saman kujera tace Kawu ya dawo yanzu,yace Allah mun gode maka tunda ya dawo lafiya daga nan Suka fada hirarsu ta masoya har Kawu ya fito yayi wanka tare da gabatar da Sallar Isha Yana Jin Siyama ta makale murya tana ta yiwa bawan Allah shagwaba,bata San yana jinta ba,tana kwance a tsakar gida suna Palo shi da Aunty ita Aunty ma bata ji me take cewa ba amma Kawu hankalinsa na kanta,karaf yaji tana cewa kasan Ina sonka nima amma sai kayi ta cewa Kai kadai kake so na gobe zaka Zo da Yamma,yace bayan kin daina zuwa layin mu ma,tace zanzo ne ,Kawu ya zaci Siyama gidan Farooq take shiga bai san ko taje unguwar ba a waje suke Zama Kuma tunda Nusaiba ta bar gidan sau daya taje,Kawu a ransa yace wato Siyama ba Wasa take ba zuwa zatayi ya Mata cikin shegen amma gobe zai gani idan zata fita, gajiya yayi da ji ya fito,Siyama tana ganin ya fito da Fushi tace Zan kiraka Yaya ta kashe wayar amma sai tayi kamar bata kashe ba taci ga da cewa ka jirani gobe zanzo gidanka da Yamma,Dariya tayi tace hmmm sai dai na zo,kawu yace Siyama zo magana tayi Aslam Kawu na kirana ka kirani anjima Kawu ne ya daka Mata tsawa Allah yasa dama ta kashe wayar, yazo ya fisge Wayar tunaninsa wayar suke da Aslam ya Kara Wayar a kunne Yana masifa yace duk abinda ya samu yata Kaine wallahi Matukar aka lalata min yarinya Kaine ya Danna wajen red ya kashe bai kula ba dama a kashe take,yace ke Kuma Siyama duk abinda zaku yi kuyi bazan bashi ke ba ya juya ya koma daki. Siyama ta fashe da kuka kasa kasa karshe ma ta koma dakinta ta kwanta,washe gari Kawu ya kafa ya tsare Yana jira yaga ta Ina Siyama zata fita,4pm yaga tayi wanka ta shirya ta saka hijab tace Aunty zanje karbo Miki Humrar, Kawu yace gidan ubanwa Zaki je,Ashe da gaske kike Siyama gidan Namiji Zaki je,tace nife ba can Zan je ba jiya ma kawai fada nayi amma na kashe wayar,Ni kike tsokana sabo da ni sa'anki ne ya taso zai sharara Mata Mari tace a'a bada Kai nake ba da Kaina nake tsokana,yace to daga yau ba inda Zaki je na hanaki fita ko kofar gida Kuma ki fadawa Aslam din Kar ya sake zuwa min gida tunda ba alheri kuke shukawa ba,ke Zaki iya sani inyi abinda banyi niyya ba. Siyama bata ce komai ba tace kayi hakuri kawu ta koma ta zauna a dakinta,Aunty ta fito tace wallahi abinda kakeyi ba tsari gaskiya duk abinda yaron nan yayi maka idan yaji ka hanashi zuwa gidan nan ai mutuncinka zai zube dan Allah karka Yi haka ai da kunya,Siyama baza ta aikata ba wlh ba abinda zai faru me yasa kake haka wai,Kawu ne ya mike ya fice,Yana fita ya hadu da Maman Nusaiba ta dawo daga unguwa ta Masa kallon banza tace oh Mallam Dauda sai muka ji Kuma wannan matsiyacin zaka aurawa Yar rikon
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71