Skip to content

Chapter 36

Chapter 36

AURENMU Book One Complete Hausa Novel 1,273 words 0 views Progress saved
Download Book

ka sabo da ba yarka bace za a zalunci yarinya a bata me karayar arziki,da yarka ce ai da baka yarda ba,Kai Kam juya marar amfani,ai Kai hoto ne a duniya mutum mutumi tunda baka haihuwa mene amfaninka baka San ciwon haihuwa ba baka San zafin da ba,in Banda Kai kwangiri ne kana gani 'yata ta fito sai da muka sa ya saketa sabo da bakin talauci shine Kai zaka Kai Yar wani sabo da zalunci me za aci da Aslam,ka duba Nusaiba yanzu ta shiga daula fantamawa takeyi yanda take so, tsohon banza ta juya ta wuce,Mamaki ya Kama Dauda ya bude baki haka Kawai shi ba kulata yake Yi ba ta bude baki taci mutuncinsa haka ta tafi,yace irin wannan annoba ne ga al'ummar duniya wannan matar Shehu Yana fama ai fasa fitar yayi ya koma gida,Yana zuwa ya fara bawa Aunty labari kaf har gwadawa yake yanda Mama tayi Masa,Siyama ta kyalkyale da dariya ta dinga dariya tace hakkin marainiya ne,hakkina ne wlh a guji batawa maraya rai gashi Allah ya saukar da aya,wlh Kawu Ina jiye maka Kar rabo ya kasheka lokacinka baiyi ba,rabo kisa yake watakil sai baka raye za ayi,gwara ka hakura Kar lokacin zuwan 'ya'yana duniya ya matso kazo ka hana zaka iya mutuwa,Kawu tunawa yayi yanda akace rabo na kisa tsoro ya kamashi Kar ya mutu,Shuru yayi tare da lulawa tunanin duniya,Siyama ta dinga dariya ta mike ta ebo kindirmo ta zuba sugar tana juyawa tana cewa rai ,Kawu yayi Shuru Aunty tace ayi bawa da kafiya haba Dauda. AsmaBaffa [4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️ 56-60 Official By AsmaBaffa Page naku ne UMMY M MARYAM BASHIR MBELLO Dauda Yana zaune bai ce komai ba,Siyama tana kallonsa ko zata ji zai ce ya yarda amma sai ji tayi yace idan na mutu ma kwana na ne ya kare dama Allah yayi kwanana ya kare sabo da haka Ina Kan bakana Kuma karki sake yazo min gida,kwana uku Kawu ya hanata fita Kuma ya hana Aslam zuwa zance,Siyama duk ta Shiga duwa,Aslam ma Sai dai suyi waya a boye kasancewar yace sai ya kwace Wayar in ya sake ji suna waya,ai Kuwa Watarana Kawu ya Kama Siyama tana waya da Aslam,tana tsaka da waya sai ga Kawu Katsam ya Miko Hannu yace bani Wayar,Siyama tace Yaya Aslam karka kirani idan kaji Shuru Kawu yazo zai kwace Wayar,Aslam yace alright bashi I love you karki yarda a raba mu please,tace Inshaallah Muna tare har abada,Wayar Kawu ya fisge ya kashe ta gaba Daya ya juya ya tafi da wayar, Kawu Yana Fitowa ya fice daga gidan,Siyama ya bari tana kuka Aunty ce ta shigo ta zauna a gefen katifar Siyama tace kiyi hakuri Siyama,duk aure da Kika gani idan aka Yi sak ba wani kalubale to bai ma fiye Danko ba ko Mene zaka Nema idan da nasara sai an samu matsaltsalu sai an Sha wahala,abinda nake so dake kici gaba da addua idan Aslam ne Alkhairi Allah ya baki shi idan Kuma ba Alkhairi ne bane Allah ya zaba miki mafi Alkha....ba wani mafi Alkhairi Aslam ne Alkhairi na Kawai idan ana son zaman lafiya a bashi ni tun kafin na kangare na daina Jin magana gwara ma ki fadawa mijinki tun kafin na Fara fetsara a gidan nan,Aunty tace to fa ku Yara idan kuka tsunduma bakwa Jin Kira ai sai kiyi tunda bakya Jin magana.. Siyama ranar haka ta yini sukuku ko aiki bata taya Aunty ba,Aslam kuwa gidan da Mum take yaje ya sameta a Palo ita Daya,bayan ya gaida ta,Mum tace Aslam kamar kana cikin damuwa kwana biyu Naga Kuma kamar ka Dan rame lafiya? Marairaicewa yayi sannan ya Fara bawa Mum labarin komai,ita Mum Murna takeyi danta ya samu mace,yace Mum kina murna baki ji me nace ba Kawunta yace bazai bani ita ba Kuma ya kwace Wayarta sannan yace Kar na sake zuwar Masa gida,Mum ta kalli Aslam tace Inshaallah zai hakura karka damu ka kwantar da hankalinka,Mum taya hankalina zai kwanta idan ban sameta ba fa ya zanyi,Ni ban taba son wata haka ba,ka kwantar da hankalinka nace Inshaallah zai hakura Kuma ko waye haka zaiyi a matsayinsa na uba babbar kawar yarsa dole ya hana,Addua zaka Yi sosai,Aslam yace yanzu Mum baza kije min ba? Wannan yakin naka ne Aslam ka dage kawai,Shuru yayi Kawai ya zuba tagumi ya tsinci muryar Mum tana cewa Amma na maka sha'awar Siyama,Ki daina sha'awar min Mata Ni kadai nake son abata Wai yaji haushi tace baza taje Masa ba, Mum ta dinga dariya tace to aci gaba da sonta lafiya,tashi ma yayi ya bar gidan. Bayan kwana uku Aslam duk ya wani fututtuke ya tashi hankalinsa ya rasa inda zai sa Kansa rashin Jin Siyama,itama bangaren Siyama haka. Zuwa Yamma Siyama da Aunty Suna tsakar gida saman katuwar tabarma suna Jin radio Kawu Yana zaune saman kujera aka sako wakar soyayya Siyama ta mike zaune tana saurar wakar Mawakiyar tace kaine tunanina,Siyama tana bada amsa uhmmm Aslam ne wannan wakar sak tamu, mawakiyar ta sake furta Kaine ruwan Sha na,Siyama tace me gardi ma ruwan, kaunarka tayi girma a zuciya tace tabbas haka ne Aslam dina,Zo ka kula Dani me so na inji me wakar, Siyama harda hawaye tana Jin wakar Kawu ya tsaya kawai Yana kallon ikon Allah shi da Aunty, kuka ta saki sosai tasa tafukan hannayenta tare da rufe fuskarta,Aunty tausayin Siyama ya kamata,tana shesheka tace amma Aunty ke da Kawu ba auren soyayya kuka Yi ba da alama baku San mene so ba,Kawu ta kalla tace Kawu kasan Kuwa me nake ji a raina ka tausayawa yarka Kawu ,shi kuwa ko kulata baiyi ba. Zuwa dare Aslam ya kasa daurewa yazo da Kansa gidan ya Samu Kawu ya tafi wajen abokansa Bayan Sallar Isha,Aunty tana daki sai Siyama a tsakar gidan zaune ta hada Kai da gwiwa,Aslam da Kansa ya shigo gidan ba Sako ba,tana Jin taku da kamshi ta dago da sauri,Siyama ta mike Zumbur tana kallonsa,tsoro take ji Kar Kawu ya shigo ya samu Aslam hannunsa ta ja da sauri tayi maza ta turashi dakinta,tana turashi ciki Kawu ya shigo gidan Aunty ma ta fito tayiwa Kawu shimfida a tsakar gidan Sabo da ana zafi a waje suke kwana,Siyama ta dora Hannu a Kai tana kallo Kawu ya kwanta,Aunty ma tayi nata shimfidar gefen Kawu ta kwanta,Siyama ta Fara tunani ta ya Aslam zai bar gidan oho,Aunty tace kin tsaya Mana a kai ke baza kiyi shimfidar ba? tace sai can anjima,Kawu yace bar algunguma ita ga Yar soyayya,Siyama dakinta ta Shige ta kulle kofa harda sa key sun zaci duk fushin soyayyar ne. Ta samu Aslam a katifarta a zaune,a kasa ta zauna shi Yana katifar tana Murmushi wani sanyi take ji Yana ratsa ta,kallonta yake sanye take Riga da skert na Atamfa masu kyau,Ina yini tace tana Jin kunya amsawa yayi kasa kasa,ya furta ya kike kwana biyu naga ma kalau kike ai ko missing Dina baki yi kawai cin abincin ki kike Yi kina koshi Ina can hankalina a tashe,Siyama tace ka taho min da wata Wayar? yace no Kawu ya hana muyi hakuri yanzu idan na baki wata zai ce mun raina shi bai kamata ba,Siyama tace

Table of Contents

Chapters

71 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71