Skip to content

Chapter 69

Chapter 69

AURENMU Book One Complete Hausa Novel 1,267 words 0 views Progress saved
Download Book

baza ka iya cin abinci ba babu kyan gani,suna ta kokawa yayi dariya yace baki Isa ba sai na tabbatar ba komai,ya dauketa cak ya hau cire Mata kaya yaganta ras ba komai yace au abin haka ne Baby? yaji haushi sosai yace haka Allah yace? Ya tsareta da Ido tace kayi hakuri ka yafe min ni tsoron ciki nake yi dan Allah na siyo maganin planning na dinga Sha ka yarda I promise Ina yaye Muhammad sai na daina sha,yace to naji karki sake min haka bana so kin San irin hakurin da nakeyi,to ai nace kayi hakuri ta furta tare da rungume shi ta baya,shanmatarsa tayi ta tura shi saman bed ya fada,tace baka da karfi dama na fada sai na kayar da Kai watarana,dariya yayi ya dauketa ya jefa ta saman bed da karfi sai da kashinta yayi kara ta saki kara,yace sorry ya Kika ji to? tace da dana da komai ka dinga jefar da me Da harfa Da ne dani,Muhammad yana Dan bed dinsa a gefe ya saki kuka ta dauke shi tana cewa Kai kaci Uwaka Nusaiba,Aslam yace Allah kiyaye ta Zama uwarsa wannan muguwar, Naga kayanki a jikinta da na hanaki ki bata shine Kika bata ai gashi ta min kyau,Siyama tayi dariya tace baza ka bani haushi ba Mallam ta zauna tana bawa danta Nono,Aslam so yayi taji haushi tunda ta bada kyautar kayan nan abun yana ransa, ya dawo ya zauna a kusa da ita,tana bashi kadan tace ka koshi,yace mene haka wannan ai rowa ce,katon ciki zaiyi haka Kawai,Aslam yace nono ne yake sa katon ciki ke baki Isa ba dama muguntar da kike Masa kenan ki ba yaro abu ya koshi harda bata rai ba shiri ta bashi ya koshi,Yana Sha harda yo aman nono a jikinta,Aslam yace kazama sai karni dole na fara tunanin kishiya,Siyama sai ta Fara kuka tace shi yasa nace maka bana son haihuwar nan ka nace yanzu ga irinta nan kana ce min kazama,yi hakuri to ni da yau ma zanbi sahun jaririn ki bani nima na kora,ba wani nan cewar Siyama,ta tashi ta cire kayan ta zuba a washing machine ta wanke sannan tayi wanka ta fito,yaron ta kaiwa Nanny ta gyara shi,tana dawowa Aslam ya sunkuceta sai saman bed daga Nan suka Fara soyewa. Bayan wata biyu Nusaiba sabo da tunanin rashin miji duk ta rame gashi Ihsan har an kawo kudin aurenta za ayi bikinta ita Kam shuru,Mama haka take aikin lallashin Nusaiba tana cewa ta ci gaba da addua,Nusaiba har gidan Siyama take zuwa sabo da Jaririn nan burinta taje ta goya shi,kaunarsa take yi har ranta,yau Aslam yana gida sai ga Nusaiba ta shigo da sallama,Siyama ta amsa tace ba wajenki nazo ba wajen Dana nazo na kwana biyu ban ganshi ba,Ina yini Aslam,yace lafiya da kyar Yana hade rai,Siyama ta kalleshi bata ji dadi ba mutum me kaunar danka, Siyama ta Mika mata shi tace bari na kawo Miki Pampers a saka Masa yanzu na Masa wanka,kayan shafe shafen jaririn ta kawowa Nusaiba,ta Fara Shafa Masa mai yayi Mata Kashi a jiki,Siyama tace ki cire shi a jikinki da sauri,Nusaiba ko a jikinta tace kyaleshi ya gama na wanke sai da ya Gama ta Shige toilet dake wani bedroom a palon ta sake wanke yaron tas Siyama ta karbo shi ta maza ta shirya shi da kanta,Nusaiba ta tube kayanta ta wanke tayi wanka,Charity ta bata wata Atamfa riga da skert kusan sabuwa ce ma tace ta barwa Nusaiba,Nusaiba ta shanya kayanta ta dawo Palo ta dauki Muhammad yayi bulbul dashi yayi wayo fari tas da shi, dalilin haka Aslam yace na yafe miki duk abinda Kika min kinci darajar Dana Muhammad,Nusaiba tace na gode taji sanyi a ranta bata son irin bata ran da yake mata. Sai Yamma likis ta koma gida, Siyama kuwa ganin Nusaiba ta tafi tace dan Allah wannan abinda kakewa Nusaiba ka daina Sweetheart,ba dadi tana son danka ka dinga Mata haka Indai tazo kana nan bata sakewa, kin San fa me ta min Yarinyar nan bai kamata ma ki dinga kulata ba tunda wani abin a gabanki akayi,ya Ilahi ta gane kurenta ta nemi yafiya me yayi saura gaskiya ni ka daina Mata haka ba dadi,to nan fada kike min ko umarni kike bani ko kuwa shawara? tunda kina sonta haka sai aje a maida aure ta dawo ku Zama kishiyoyi sai kuci gaba da zumunci,Siyama ta bude baki tare da furta haka nace maka? Kawai kace sonta kakeyi har yanzu zaka dawo da ita shine magana kawai,dansa ta Mika Masa ungo danka ko na fatalar da shi,ya karbi abinsa ya haura sama Yana dariya a ransa,tace ka dawo muyi magana akwai wani abu kasa a ranka wannan Maganar bata mutu ba,bai kulata ba tun daga ranar Siyama bata sake zancen Nusaiba ba, bakinta kanin kafarta har Bata so ma Nusaiba tazo su hadu da Aslam. Tana zuwa kofar gidansu taga Machine din Salahu masoyinta Wanda ya fece,ko kallonsa bata Yi ba zata wuce ya dakatar da ita yace Nusaiba dan Allah kiyi Hakuri ki yafe min nayi kuskure,Kiyi hakuri dan Allah,tunawa tayi yanda itama tayiwa wasu laifi Kuma aka yafe mata tace ba komai na yafe maka,Yace dan Allah ki bani dama na dawo da Maganar auren mu,dama gwadaki nayi na gani da gaske kina sona tsakani da Allah Kuma na tabbatar naji labari,Nusaiba tace waye ya baka labarin? Yace Aslam tsohon mijinku shi yace kin canja yanzu Kar na dauki zugar mutane idan Ina sonki tsakani da Allah na dawo na aureki ya fada min kinyi nadama ke yanzu sabuwar Nusaiba ce,Nusaiba Murmushi tayi jin Wai Aslam da Kansa yasa baki a aureta shi da ya tsane su,juyowa tayi tace in ka shirya ka turo manya bani bukatar yin sabuwar hirar soyayya da kai ka azabtar da zuciyata,Salahu yace kiyi hakuri na gode Kuma Inshaallah Jibi za a turo ki fadawa Abba,Nusaiba Kamar bata murna ta fada gidansu sai Murna tana cewa Mama Allah ya amsa ta bawa Mama Labari,Mama tace Kai duniya shi yasa akace ka taka a sannu. Bayan wata daya aka Sha bikin Nusaiba da angonta,Ihsan da nata itama ma'aikacin banki,Mijin Nusaiba gida ne Wanda iyayensa Suka mutu suka bar Masa gado ya gyara shi sosai ya maida shi na zamani yayi kyau dan madaidaici harda gate dinsa ko Ina tiles tsakar gida broken tiles ne dagwas, Landlady ita tayi kayan kitchen na Nusaiba da Ihsan sauran Kuma Shehu ne yayi Kamar yanda uba ke yiwa yarsa,Affan ne da Raudah Suka hada lefe Akwatu hudu kasancewar Angon yaron Affan ne na hannun dama,machine din ma Lifan Affan ne ya siya Masa,Siyama ce ta tasa Aslam a gaba da kuka sai ya bata kudi tayi gudunmuwa dan Dansa da Nusaiba ke so yace me za ayiwa Nusaiba me ya dace, Siyama tana share hawaye tace a bata jari tunda mijinta baida hali sosai sai rufin asiri idan aka bata sai ta dinga sana'a a gidanta ko irin dan siyar da su Maggi,omo etc,Nawa za a bata? dubu dari ? Yace to Zan Miki transfer ki tura Mata kice gudunmuwarki ba ruwana a ciki,Siyama tace hakan ma yayi na gode,haka ta turawa Nusaiba Suka Yi shawarar kayan da zata

Table of Contents

Chapters

71 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71