Chapter 55
Chapter 55
aure . kafin na aureki sai naji ashe ma, da ba sonki nake ba sai yanzu ina mutuwar kaunarki tunda a da zan iya hakuri da rashinki Amman yanzu Allah yasani bana ji zan zama cikakken mutun muddin na rasaki. kullum sake jin kaunar nake musamman idan kika faranta min rai a duk dare . lokuta da dama na lura ke bame damuwa da sex bace .shi yasa ma wani lokacin nakan cinye kwadayina "a kanki in ragwanta miki. kuma nasan dan baki damu dani bane shiyasa duk rashin bakya sona ne ko.. ya fadi haka yana sake matseta da jikinsa . please Aisha me zan miki ne ki soni ko dan mu samu ni,imar juna tare . bani kadai ba,. nasan irin dadin danake yayin saduwarmu inda kina sona ne dadin da zanji tare da ke sai ya ninka wanda nake ji a yanzu. wlh Aisha muddin mami da dady suna farinciki da rayuwar aurena dake to na gode wa Allah . banki narasa komai nawa da na mallaka ba. akanki ya dan dagota suna kallon cikin idanun junansu cike da tsantsar kaunar juna". ahankali yace Aisha zan iya rayuwa a dokar daji ni dake a hakan koda yayan itatuwa kawai zamurinka ci . muyafa ganye in dai ina tare da ke bazan damu ba.. Aisha ta dinga kallonsa yayinda kallon nata ke sake tsumawa Abdullah tsansar jiki ya koma lip's dinta na kasa yabata light kiss , lumshe Idanunta tayi maganganunsa suna ts ratsa mata jiki ta dade da gane Abdullah mai kaunarta ne . ita dai wasu al'amura nasa ne suke bata tsoro yasa taji ta kasa sakin jikinta sosai dashi. ya hada goshinsa da nata cikin wata irin murya da bata sanshi dashi ba. yace please Aisha Tell me do you love me ... Tayi shr taki cewa komai dan jikinta a tsanyaye yake yace kice min wani abu mana murya tamkar mai shirin yin kuka zan iya yi komai ciki har da zama bawanki . zan iya miki kowani irin bauta ne" kuma komai wahalarsa ... muddin zaki soni bazan damu ba nasan in kina sona bazaki iya rabuwa dani ba . Nan da nan kwalla tacika mata Ido dama yarigada yasan haka ce zata kasance " ita Kuma ba kukan komai take ba tsabar tautsayinsa taji har cikin jininta . tana kuma mamakinsa. Kafin tagama jimami ya sake jeho mata wata tambayar data frigitata. yace Aisha ko zaki iya rabuwa dani sannan kiyi rayuwaki batare dani ? Ta dan kalleshi ahankali cikin sanyi jiki tace Abdullah ko ba dan wani abu ba . daman can na dasawa Raina tun kafin muyi aure muddin na aureka to zanyi hakuri da komai in zauna dakai . ,bazan iya rabuwa da kai ba ,sai dai idan daga gareka ne "tunda daman auren ba hannun a yake ba ,wannan sai dai in daga gareka ya faru to ba yadda zanyi zan iya barinka na har abada .... Abdullah ya zuba mata idanunshi yana nazari akanta sannan yace Aisha meyasa kike ce idan kika aureni baza ki iya rabuwa dani ba? Ta Lumshe tsumammu idanunta tayi kmr baza tayi magana ba daga can Kuma tace saboda ayanzu dana aureka kai kadai ka taba sanina Diya macce nima kai kadai na fara sani. to idan har na tada hankalina na rabu da kai dole nasan gaba ma zanyi wani aure Kuma sai wani ya kuma sanina shiyasa naga da Yi hakan kawai gara in zauna da kai komai zai faru zanyi hakuri tunda na gane kai ma me kaunarta ne . Kwata kwata Abdullah bai dauka tana da hankali irin haka ba a wani lokaci idan yayi tunanin irin haka a kanta da matsayin shekarunta sai yaji tsoro ya kamashi kada gaba takara shekaru da kaifin hankali daya fi wannan har tazo tadinga kallon Bai dace daita ba. yayi shr yana cinza lip's dinshi ahankali. yana jinta ya dauke kansa dan wani lokaci idan tana magana taga yana kallonta sai ta daina Dan haka tunda suke daita bata taba yin doguwar magana data wuce kalma ashirin ba. sai a yanzu muryata na sake ratsa tsansar jikinsa . cikin sanyi murya tace dan haka zan iya hakuri da komai mami zatayi akaina nasan itama ba wai sona ne batayi ba. fushi kawai take yi dani tunda bani take son ka aura ba kai kuma ka nace takarasa fadin maganar cike da shagwaba yasa yatsansa ya lakace mata hanci dashi yace ok ni ne ma nanace ko . ta daga masa kai. jawota ya sake jikinsa ya mata wata irin runguma hade da busa mata iskar bakinshi a fuskarta soyayya wani lokaci takansa duk girman mutum ya zama tamkar wawa na wucin gadi. haka yasa Abdullah yace idan mun koma gida mutaru muyi tabawa mami hakuri har sai ta huce ko. Aisha daga masa kai, ita Kuwa ta fadi haka ne kawai dan tagane yadda yake damuwa da maganar mami akan yadda take nunawa. sannan ya lalubo hannuta cikin nasa yasoma shafa cikin tafin hannuta yana mammatsa mata yatsu. yace kanwata na gode sosai tunda kin amince zaki zauna dani. dan Allah ki taimaki ZUCIYAR MASOYINKI komai runtsi karki bari wani abu yarabamu dake kinji cikin murya ta tausaya masa. batace komai ba illa dai sake daga masa kai datayi. to a dare sun sake kasance cikin wani irin farinciki fiyye da kowani lokaci. abinda bai tabayi mata ba ma yayi aranar dan wanje auratayyarsu har kukan dadi sai da Abdullah yasa Aisha tayi tarinka jin da gaske bazata iya rabuwa dashi ba wanda shima Abdullah yasake ji ajikinsa tabbas Aisha ta dan fara sonshi .π MMN SUDAIS CE [3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: πππππ ZUCIYAR MASOYI πππ πππππ AISHA A BAGUDO Wow tawan nagode kwarai da yadda kike matukar son novel din nan ,ina kike my khadeey pinkyπ£π£π£ this page belongs to you Only ,kiyi duk yadda kike so dashi kina Raina yaruwa love you so much dear muna mugun tare π€π€π€π€πππ Page 36-37 Washegari sai karfe biyar na yamma agogon Nigeria a sannan suka sauka a Abuja wanda tun karfe uku direban da zai kai su kebbi . yake zaune zaman jiransu saboda rashin isowarsu da wuri daga can mami ta roki dady da yace su bari sai da safe su taho saboda tafiyar dare ga hazo anayi a ranar . Shima dady yaga dacewar haka . dan haka tafiya zuwa kebbi dole ta tashi sai washegari Amman dady yace su taho da wuri saboda shima jibi zai tashi sai da suka gama naganarsu dashi sukai sallama Abdullah ya'ajiye waya. A tsohon gidan su na Abuja byn Abdullah ya fito wanka duk sanyi da ake tsulawa basasa Abdullah sanya kaya ajikinsa ba . daga shi sai short niker zuwa cinya kana kallon Yadda gashin jikinsa ke kwance ya dauko system ya daura kan table yana karkadewa ya zube sannan ya kunna yashiga neman sakonni da dady ke son ya tura England . Har Aisha zata shiga wanka itama ta dubi agogo karfe takwas dan haka tafasa ta koma kicin ta hado masa fresh miki a cup ta nufe falo inda yake . ya dukufa a internet jikinta nannade da towel iya cinyarta ta karoso . ta ajiye masa a gefe
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62