Skip to content

Chapter 14

Chapter 14

Zuciyar Masoyi Book One Complete Hausa Novels 1 1,190 words 0 views Progress saved
Download Book

tasan da zamanki ya bude idonsa a hankali yaga hoton zanenta wanda yayi shi da hannusa ya kafawa hoton ido shi kam kusan komai ya nema gurin Allah yana samu , Amman yarasa me zaiyi wa Aisha ta soshi ,duk wata dabararsa na neman karewa a wannan bangaren ,a fili yace mami nasan Idan kika ga Aisha zaki so ta sosai nasan duk abunda nike so kema zaki so shi .to cikin satin daya gabadaya wanda shine mami ke sa ran tafiyar Abdullah sokoto kamar yadda suka yi da mama hafsa sai gashi tafiyar tasamu Abdullah zuwa kasar Dubai domin nemo wasu sinadari da kamafaninsu ke bukata ,su biyu sukayi tafiyar shi da RK ,sai salis kwanansu hudu suka juyo tun ranar juma a ,sai talata don haka shima satin cikin aiki yake dole bbu maganar tafiya sokoto .duka karfe goma na safiyar juma'a cikin kamfanin nasu dike yake da maaikata kowa ya maida hankali akan aikinsa yayin da ba a fi mintina goma da shigowar MD Abdullah ba, yayin da Secretary dinshi yashigo ya gaisheshi sannan ajiye files akan makeken table din dake gaban Abdullah yadan rankwafa sannan ya juya ya fita ,salis yashigo da coffee cikin karamin cup ya ajiye a gabansa ya fita yadda yake neet haka komai na office din yake haka Kuma yake gudanar da aikin nasa ,bai fi mintina talatin da fara bincike files din dake kan table din wayar sa da ke ajiye agefe ta hau sauti mai ratsa jiki Abdullah ya dago ido yana duban system din wanda zanen hoton Aisha ne a bayyane ya furta ahankali Aisha kennan wasu na shekaru talatin da tara zuwa casain wasu sun gama shekarunsu sun tafi ke sai yau kikai 18 ya fada tare da kashe komai ahankali ya Mike zuwa kofar shigowa ,ta tsakanin glass din da ya ratsa kofa yake hange mutane dake bukatar ganinsa har sun Karu akan sanda ya iso hakan yasa yaji bai iya tsallalakewa yabarsu ya dubi agogon dake manne da hannushi goma da talatin da biyar uhummmmmm yaja numfashi Aisha wata abace mai mahimmanci a gareshi don haka akwai bukatar yaje yaganta koda na minti ashirin ne ya matsa intercom secretary yashigo , Abdullah yace zanyi off zuwa na da wani lokaci yana son komai yacigaba sannan adakatar da masu San ganinsa haka duk wanda yasake zuwa yayi hakuri sai zuwa Monday wanda suka riga suka zo sudan Jira shi,sannan yace yaturo masa salis , secretary yace Ok sir ,ya juya ya fita bai jima ba sai ga salis yashigo. Yasanar dashi bukatarsa nason fita Amman dole sai ta kofar baya domin masu jiransa bazasuji dadi ba idan suka ga fitarsa, kofar baya salis ya bude suka fita salis ya kwaso wasu ledoji guda biyu yabiyo dashi yana mai jinjinawa Abdullah da irin wannan halin nasa nason kyautatawa mutane da sauri musa yataso yayi da Abdullah ya daga masa hannu yace ya zauna zasu je da salis yanzu zasu dawo musa ya girgiza kai hade da hanzarin bude musu murfin mota suka shiga sai suka biya yakara mata siyyaya har dasu greeting cards "kai tsaye gidan su Aisha suka wuce basufi minti uku da tsayawa a kofar gidan mlm abu ba wata yarinya da bata fi shekaru bakwai ba zuwa takwas ta fito daga gidan cikin sauri abdulla ya kirawo ya tambaye sunanta tace hadiza yace yauwa hadiza Maza jeki ki gayawa inna Abdullah ne yazo yana son ganin Aisha yarinya tace ai inna bata nan tun jiya Abdullah yadan ciza leban sa , sannan yace usman fa. Hadiza tace duka suma basa nan usman yaje makaranta ba kowa agidan sai yaya Aisha Abdullah yadanyi shiru sannan yace salis ajiye kayan yaje mota ya jirashi , salis yayi yadda yace tun bai wuce ba yaji yana cewa yarinya ta dinga daukar kayan da daya da daya tana shiga da su , sannan idan tashiga ta turo Aisha yarinya ta kwashi Leda biyu da karfinta tashiga dasu ta ajiye cikin zumudi ko Aisha batayiwa magana ba tadawo ta kwashi ragowar ta shige ,sai byn ta tara kayan guri guda take gayawa Aisha taje inji Abdullah . AISHA dake kusa da famfo tana wanke wanke ta dalla mata harara tace shine ya hanaki kisiyomin Omo dana aikeki . hadiza tace A'a sannan cikin sanyi jiki ta Kuma fita ,aiko sai gashi tasake dawowa wai yace dan Allah kije yanzu zaki dawo Aisha ta kalleta tace kice masa aiki nake Kuma ke nake jira da omon fa . hadiza ta fice haka ta gayawa Abdullah sannan ita Kuma tashige dan gaba da su ta siyo Omo tana yi tana waigensa Abdullah ya dafe kai game da duba agogonsa yana mai sauke hadiyar zuciya ,kai tsaye zuciyarsa ta raya masa ya shiga da kansa dan haka ya shige soron farko yashiga na biyu shima a gyare yake kmr na farko yana karasawa tsakar gidan zai shiga dan haka yadan tsaya daf da ciki ya leka Aisha ce zaune abunta hankalinta kwance akan kujera tana wanke kwanuka a gaban famfo ta gama sauran tukane har yashigo bata sani ba Kuma bata ji motsen komai ba shi Kuma bbu akan abunda idanunshi ya sauka a cikin gidan sai kan damuwarsa bbu ruwansa da wani yanayin na cikin gidan shi sam bai lura da komai ba sai Aisharsa ,tayi masa kyau sosai bai taba ganinta a daidai irin wannan lokacin ba, dan hasken ranar da ya haskata yasake fito mata da sirrin kyan da take da shi. kananan kayan dake jikinta ya dada taimakawa wajen fito masa da kyawunta da bai tabaSani tana dashi ba , hakan yasa tasake daukar hankali matuka, bai taba tsammani ta iya dressing irin haka ba" ya zuba mata idanunshi da sukarigada suka gama rikecewa ko kiftasu bayason Yi, yakarasa sannu ahankali yadan tsugunna daidai inda take zaune motsen tsugunawarsa ne yasanya ta dago a tsorace sukayi 4 eyes dashi ido cikin ido suke kallon juna sai ayau ya kara tantance sexy eyes dinta kullun idanunta a lumshe kmr maijin bacci. yayin da Aisha numfashi ya tsaya cak na wani lokaci kafin daga baya yasoma circulating zuciyarta ke dokawa da sauri da sauri sai da ta saita kanta da kyau sannan ta iya bude baki tayi magana tace manene haka abun naka yawuce waje har cikin gidan iyayena. Abdullah yayi murmushin nan nasa mai mai daukar hankali har dimple point dinsa ya fito yace today is 14 that's your birthday Aisha ta fiddo idanu waje tana zaresu dan tsoro Anya Abdullah ba aljanini bane " ji wani sabon balai har ranar haihuwar ta yasani ta fada akasan ranta wanda a fili ta sake daure fuska sosai tace kayi kuskure idan kana tunanin zan taba fahimtar ne ,ok kasamu labarin bakowa shine kashigo domin kasamu abunda kadade kake so, to kayi babban kuskure domin ni din bairin ka bace kaje can ka nemi irinka ba ni Aisha ba Abdullah ko kallonta kawai yake ,tace tun farko daman nagane nufin ka shiyasa bazan taba amincewa da kai ba kaje kanemi irin wayan da zaka yaudara in yaso daga baya sai ka gudu kabarsu ,kan Abdullah ya daure yaji maganar kmr ba daga bakinta take fitowa ba tace Abdullah kabar mana gida kadama

Table of Contents

Chapters

62 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62