Skip to content

Chapter 30

Chapter 30

Zuciyar Masoyi Book One Complete Hausa Novels 1 1,186 words 0 views Progress saved
Download Book

idanuwansa sunkada sunyi jawur yace mami ta wuce ko.....? yadda ya fadan yasa minal taji tausayinsa yakamata ,yayi murmushin karfin hali dan wani dokawa zuciyarsa keyi a hankali yace minal a wasu lokunta sai ki ga abubuwa suna faruwa irin haka Allah yana kaddarawa bawansa wani abu yasame shi domin gwada imaninsa ,ciki muryar tausayi yace mami tayi fushi dani saboda ina son Aisha ,ta tafi tabarni bata San cewa nayi shr ne ina bawa zuciyata hakuri Aka rashin Aisha dazanyi ,zan auri duk wacce mami ke so batare da tawa soyayyar ba... Abdullah ya runtse idanunshi ya daga kansa sama hannushi daya ya daura tsaitin ZUCIYARSA kwallar dake idon minal ce ta karasa zubowa tasa bayan hannunta ta goge tana kallon danuwanta cikin halin tashi hankali bata da halin taimaka masa ...... MMN SUDAIS CE [3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗 ZUCIYAR MASOYI 💖💖💖 💗💗💗💗💗 AISHA A BAGUDO Page 18 Ran dady yayi matukar bacci sosai game da bayanin da mami keyi masa ,shi duk bai san abinda ya faru ba Amman shi duk ba wannan ya Dame shi ba, lafiyar dan nasa ,kansa a caji yake ga rashin lafiyar Abdullah ga zirga zirga ta sha'anini kafa company dinsu da suka samu nasara a Denmark ga rashin Abdullah da gurbinsa daya bari domin wani abun dole sai Abdullah hakan bai hana dady tsallalakewa ya dubo lafiyar Abdullah din nasa ba bayan kwana biyu da dawowar mami... A sa'a dady ya sauka a Germany domin a ranar ake warwarewa Abdullah bandejin karayar dake kafadar Abdullah din hakan ne yasa dady ya sawa ransa Abdullah yana samun cigaba a lafiyarsa har ma yaji dadi sosai da yadda ake kula da shi dan haka kwanansa uku ya juyo tare da minal bayan ya kara sakin kudi sosai akan maaikatan asibiti akan lura da Abdullah ,dama dai bbu wani mai jiyya dake zama dan Abdullah kadai sai securities guda biyu RK da salis... Washegarin da dady yadawo daga Germany mama hafsa ta iso ita da faiza tare da shiryayen shirinsu duk akan Abdullah a rashin sa'a suka tarar Abdullah din ma na can gadon asibiti a wata uwa duniya .. To duk yadda mami tayi da dady akan tana san sake komawa dubo Abdullah dady yaki , Mama hafsa kawai ya sanyawa hannu akan taje duboshi , Amman faiza ta zauna ,faiza kuwa a yadda tazo a shiryenta taci alwashi bata kara komawa sokoto sai tare da auren Abdullah a kanta ,dan haka ko ba dade tana nan tana jiran warkewar Abdullah da dawowar sa.... Tun bayan gaisawa da Abdullah yayi wa mama hafsa bai sake tanka mata ba tun zuwanta ,komai tace sai dai yayi shiru koda maganar ta na bukatar amsa , saboda a ganin shi kamar yadda yaji daga bakin mami ita mama hafsa tana daya daga cikin wadan da suka haifar da rikicen dake kwalkwalwarsa ,dan haka tana barin gurin yabada umarnin bai san sake ganin wani yashigo dakin da yake idan kacire maaikatan sai dai ko daga cikin mahaifansa .... Bbu yadda mama hafsa batayi na san ganinsa Amman fur aka hanata ance yana bukatar hutu ta ciza yatsa na ba adadi. daganin wautarta tun farkon xuwanta saboda a yadda taga Abdullah laga laga a kwance shi yasa take son ta fara aiwatar da shirinsu , kmr yadda sukayi da faiza , Amman sai gashi daga gani daya tun bata fara aiwatar da komai ba ,an datse sake ganin Abdullah din ta buga ta buga Amman sam aka hanata ganin Abdullah" haka ta hakura domin visa dinta ya cika na dawowa dole ta taho batare da tayi komai ba daga cikin abunda taje da niyyar Yi..... Watan Abdullah biyu da kwanaki dady yasake biyo jirgi ya ganshi yadda yaga Abdullah yayi matukar razanashi ya tsorata tamkar ba'a asibiti yake ba , Abdullah ya rame sosai ta yadda har kwayar Idanunshi sun nuna haka , sannan ga wata muguwar kasunba daya tara ,dan ya hana a gyara masa tamkar ba Abdullah din dayasani ba mai matukar son tsafta da kyamkyami... Aranar dady ya gana da babban likitan dake kula da lafiyar Abdullah a office din doctor jack suke a zaune dady ke tambayar yadda yaga jikin Abdullah yakasance doctor jack kwararen likita ne da ya nakalci cututtuka da dama ,yayi gyaran murya yace shi duk wata cuta da Abdullah yazo da ita iya bincikensu ya samu saukinta koma ya warke musamman daakayi saa Abdullah din bai da kyan jiki to abinda yake damunsa a yanxun kirjinsa Amman akwai magunguna a yanxun daake son Yi masa amfani da su. Sai dai Abdullah ya hana zuciyarsa sakat da yawan tunane tunane,wanda iya bincikenmu Abdullah yana tattare da damuwa aransa wanda sakamakon yawan damuwar da zuciyarsa take har yasa ZUCIYAR ke barazanar kamuwa da wani ciwon na daban .,kirjin dady ya buga da karfi doctor jack yacigaba munyi kokarin ganin ya'ajiye duk wani damuwa saboda ganin yadda lafiyar sa take yin kasa ni kaina na zauna dashi ya kai sai hudu Amman har yanzu bbu wani canji ,shi yasa muka dakatar da shan maganinsa mai karfi dan gudun faruwar wani abu. doctor ya numfasa yace Amman yanzu abinda naga za'afarayi wanda zai ceto shi daga hakan a binciki abunda ke damunsa a kawar masa da damuwarsa dake damun zuciyarsa , Allah sarki dady kasa ko motse kasayi yayi akan kujera yace to doctor kmr yaya kake ganin za',ayi ciki harshe turancin duka suke magana doctor yace abunda yafi a bincika idan wani abu yake bukata ayi masa idan Kuma damuwa ce yake tare da ita a kawar masa da ita yin haka kadai zaisa yacigaba da karfan magani na karasa samun lafiyar sa ,domin duk kan masu yi masa hidima na bincike su bayani guda daya ne , kawai yake cewa abinda ya dame shi, ko yake bukata wanda Kuma bbu naganin sa asibiti .. Hankali dady a tashe yabaro office din doctor Abdullah ciwon zuciya INA..... yana ta nanata hakan a ransa to a dare sai da Abdullah yadawo tsaf da shi komai yayi neet a jikinsa , dady yana kallonsa yana cin abinci yana sake nazari akansa yana Jin tautsayi dansa har washegari suna manne tare duk wani zirga zirga ta sha'anini aiki bai kai mahimmanci zama da Abdullah ba a wajen dady ,Abdullah yasamu natsuwa kadan yaji dadin zuwan dady ,wanda har da kansa dady ya fahimci hakan ba kamar farkon da yasame shi ba ahankali dady ke bincikawa me ya sawa ransa har da yake son jefa shi cikin wani hali,ka tausayawa dadynka kasanar dani damuwarka bakada sama dani duk duniyar nan nima haka na jure abubuwan da dayawa game da rayuwa Amman bazan iya jurar rashinka atare dani ba ya kamo hannushi cikin nasa yana masa duban ina sauraronka Abdullah dai yasan dady yana da fahimta abu yana da Kuma saurin ganewa dan haka baiyi shakkan komai ba yadda yagayawa maminsa haka ya gayawa dady har zuwa jenyewar da yayi na auren Aisha dan ba yadda ya iya ....da kuma fushin da mami tayi dashi ... Dady ya zubawa dan nasa Ido sosai yake kallonsa ya damu da fushin da mahaifiyarsa tayi dashi , Amman bai sani ba itama mami tana can hankalinta da ranta suna kan

Table of Contents

Chapters

62 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62