Chapter 42
Chapter 42
MMN SUDAIS CE [3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗 ZUCIYAR MASOYI 💖💖💖 💗💗💗💗💗 AISHA A BAGUDO Page 26 A hankali ya shiga dakin ya dan jima tsaye yana binta da kallo kmr wanda yarasa abinyi daga bisani ya tura wayarsa cikin aljihun wandonsa na baya "yasa hannu ya kamo nata ya dago ta kai tsaye gaban madubin dake manne cikin dakin ya kaita ,a tsorace take binsa wanda har mayafin dake lullube a kanta ya zame daga jikinta ya fadi kasa yasa hannunsa ya cire yayi cilli dashi gefe ya matso da ita gabansa cikin sanyi murya yace Aisha see ur face tsawon watanni biyu da kwanaki rabon da su ga juna" tun daren da zai tafi Denmark sai yau din da idanuwansa suka hadu ta cikin madubi "sunyi shiru suna kallon juna daga bisani ta janye idanunta ta sunkuyar da kanta "ya juyo da ita suna fuskantar juna ya rike duka kafadunta a hankali yake magana yace Aisha kuka kuka har yanzu dai please ...stop crying ya kamo hannuta cikin nasa yana murzawa daga can kasa yace haba Aisha ki tausayawa Abdullah yana cikin wani hali na barazana gaf yake da rasa numfashinsa ya maida hannushi ya dago habarta ya zuba mata narkakun idanunshi cikin nata suna fuskantar juna take . idanuwansu suka sarke waje daya wasu abubuwa masu wuyar fassara ke fitowa daga idanunshi suna shiga nata " tayi saurin rufe idonta ahankali wayyo meyye wannan Kuma ? yayin da hawaye suka cigaba da biyo fuskarta. gabadaya jikinta ya dauki kirma lokacin daya wani tsoro yayi barazanar neman kai ta kasa '" tun kafin takai ga zubewa kasa ya taro abarsa ya manta da jikinsa "Abdullah ya sake zuba mata manya idanunsa dasuka gama rikicewa . akasan ransa ya iya furta rayuwa! rayuwa!! rayuwa!!! AISHA itace rayuwarsa Kuma Mafi soyuwa halitta acikin zuciyarsa" duk tsowan lokacin daya dauka batare da sanyata a idanunshi babu wani abu da yaragu game daita. sai ma kyaun data kara yi masa Sosai.. hancina yakai gefen wuyanta ya manna mata rikitattaccen kiss wanda wanda gabadaya ya susutawa Aisha tunani. tarinkajin tsigar jikinta natashi kadan kadan har suka Mike tsaye cak . , tana jin wani yanayi daban ajikinta ,wanda dabasan da zamansa ba, yahade jikinsu waje daya ya fara mata fushin bakinsa kamshin jikinta yana ta ratsa jikinsa yasa hannushi duka biyu yana share mata hawayen sannan ya janyo ta suka dawo kan gado ya zaunar daita yayinda shi ya zame ya dan tsgunno gabanta ya kai nasa hannayen akan nata dake zube kan cinyoyinta. ya kira sunanta ta dago ta kalli cikin idonsa ya runtse idonshi ,kallon da take masa yarinka rudashi daman can haka idanunta suke tsumashi duk lokacin da ta kalleshi ballanantana a yanzu da ya hadu da tsabar gajiya bacci ga kukan da tasha" tsigar jikinsa suka Mike yarinka jin wani sanyi nabin ajikinsa yayi saurin dauke idanunshi daga kanta "dan bai son hakan ya rude shi har ya rikita masa lisafin da zai manta da yanayin daya baro maminsa a dazu kafin su taho "ya jima bai ce komai ba ,sai da ya saisaita kansa sannan yasake kiran sunanta batare da ya kalleta ba yace Aisha ba kuka yakamata kiyi ba yanzu. duk kan wani abu daya faru ya wuce ina so dan Allah ki manta dashi a yanzu" gabanmu kawai zamu duba , abinda ya faru yarigada ya faru sai dai mu tsaya mu rungumi rayuwarmu ta gaba Allah ya nufemu da zama maaurata sai murike juna da amana. yana magana yana kara matse hannayenta cikin nasa nufi shi su rike hakan sosai ,ya koma ya zauna kusa da ita akan gado jikinsu manne da juna, yana son nuna mata yadda matsayin yake cikin zuciyarsa Amman bazai iyayin haka yanzu ba ,sake tuni maminsa dayayi ya aiyana aransa ko tasamu runtsawa " yasan daidai wannan lokacin indai bawani tashin hankali take ciki ba yakamata tayi bacci"ya runtse idonsa yana Jin yadda zuciyarsa ke dogawa dum...dum..kusan minti goma sannan ya bude su ya kalli agogo dake daure da tsintsiyar hannunsa Shabiyu ke neman wucewa" yace Aisha mugabatar da nafila sai mu kwanta ko batayi musu tare suka Mike yayi gaba tabisa kamar yadda yaja hannuta zuwa toilet din dake manne da dakin .. Sun idar da sallar nafila yayi musu addu'oi sosai kmr yadda dady yace suyi ko kadan yaki yarda su sake hada Ido da ita 'dan kallonta nasake riketashi ya maida ita kan gado ya jawo hannuta ya sumbata yace Aisha zanje in kwanta kiyi baccinki anan "kar ki sake yin kuka idan kika sake zandawo mu kwana tare .. Ya Mike har ya juya zai tafi ya sake juyowa ya kalleta yana Jin kmr ba zai iya barinta ta kwana ita kadai ba ",Amman yasan ko ya zauna yadda take yi dina bazata taba sakewa dashi ba" koda kuwa bbu abunda zai mata . a falon yayi zamansa ya kunna sigariinsa ya kuna yasoma suka yana tuna kallon da mami tayi masa dazu,k komai yarinka dawo masa a kansa" hankali yake aiyana muddin mami bata saki ranta tabbas bazai iya moran sansar jikin Aisharsa ba yadda ya dauki lokacin mai tsawo yana tanadin wannan ranar akanta ga dai Aisha can a daki Kuma tazo a matsayin mallakinsa abinda yafi kauna kennan fiyye da komai" yau ranar farinciki ce gareshi da zai kwana gida daya tare da ita. Amman ga maminsa abin bacin rai ya juye mata tayaya zai iya kasancewa da ita cikin wannan halin shan ya furta zan zan jure har sanda zan samu natsuwa " yanzu haka ko sun haifi ya'ya da Aisha killa mami bazata so su ba ya fada a ransa wanda a filli ya rufe idanunshi yace mami mami dan Allah kiyi hakuri ki sawa auren Abdullahnki da Aisha albarka shine kadai zai jiyar dani farinciki dake tattare da Aisha" hakan ya dinga yi yana busar da hayakin sigarinsa lokacin lokacin yakan tashi ya dubu Aisha sai ya hangeta kan gado kwance sai ya dawo ",ya kwanciyarsa yayi akan doguwar kujerar dake falon har sanda akafara kiraye kirayen sallah asuba yakarasa kashe sigariinsa cikin kauli guda daya Sha sannan akayi kiran asalatu .. Karfe bakwai da mintina ya leka dakinta har kan gadon ya haura kusa da ita ,tana kwance abunta Amman da dukkannin alamun itama ta tashi tayi sallah "ta takure sosai a gado ta rufe duk jikinta sai fuskarta da tabari. dan haka ya xuba fuskar dake tattare da sanyi idanunshi yasa hannunsa ya shafi gefen fuskarta , har kan jajayen lips dinta bakinsa yakai yakamo yadan tsotsa sannan mike ya fito ya janyo mata kofar yana fita tana bude idonta tana sauke ajiye zuciya itama yadda bai samu bacci ba haka ta kwana tana murkususu .. .. takwas da mintina part din dady tayi masa " mamakin ganinsa dady yayi Amman ya danne mamakinsa ..Abdullah yakaraso yana gaishi. dady ya dan nakalceshi kadan sannan yacigaba da abinda yake yace har ka fito ina Aishar?. Abdullah ya dan sunkuyar da kai yace na barota gida ,sannan ya dan yiJim yace jiya na bar mamina kmr ranta a bace ,na shigo yanzu nashiga bata tashi ba, ya fada yana dan murmushi dan boyewa dady damuwarsa bai san wanda ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62