Chapter 5
Chapter 5
kallo hade da jin wani mummunar faduwar gaba ta dafe kirjinta tana jin yadda zuciyarta ke beating. Waye malam abu ?haifaffan garin zariyar kala kala ne, dake jihar kebbi shine da fari a gurin iyayensa tun bayan rasuwar wansa yanzu Kuma daga shi sai kanwarsa Laure mahafinsu yarasu tun lokacin Laure nada shekara goma a duniya alokacin rikonsa yakoma gun kakarsa data haifi babansa, yayin da kanwarsa ke hannu mahaifiyarsu laure tana da shekara gama shabiyu tasake wani aure, ko kadan kakarsa ba irin kakaninan bane masu sakarwa jikoki, don haka ta tsaya tsayin daka akan karatunsa da tarbiya ,sai dai ita sam ta tsani karatun boko yara tsaransa masuyin karatun bako sai ta hanasa Hulda da su, acewarta boko ko a wuta. ta Mika shi makaranta allo acan garin akaoje malam abu yakasance mai tsananin hakuri da biyayya yacigaba da karatunsa har lokacin da yakamala yana zuwa gida duka huta inda kawarsa Laure tasa muji har an tsadaaganar aure, tafiya tayi tafiya yasoma siye da siyarwa a lokacin ya hadu da maimuna suka kula soyayya atsakaninsu , byn yagama shekartunsa da dadewa ya aure maimuna itama su biyu ne agun aiyayensu ita da yayanta wanda tunda yasamu scholarship karatu zuwa kasar sin baakarajin dauriyyarshi. Daman da tazara dayawa a atsakaninsu . Kuma har zuwa lokacin da iyayensu suka koma ga Allah bai dawo . fataauci mlm abu yasoma daga kaoje zuwa cikin kebbi zuwa zariyar Kala kala, , sosai yake samun cigaba asanar dayakeyi , kafin daga baya yakoma can kebbi da zama inda yasamu mai gidan da yabude masa shagon siyar da kayan shinkafa da sabulai takarma da dai sauran su , watan su biyar acan , rasuwar mahaifiya sa ya riske su haka suka koma sai byn da akayi arbain suka dawo ,yakasance iya CE kadai ta rage masa, gidan da suke ciki daki guda daya hakanan Allah bai hanasu abun da zasu sama bakin salati ba har suka kai ga samun haihuwa . shekara yusif biyu da watanni aka haifi Umar duk da ba haihuwar fari bace Amma gida maimuna takoma tayi wanka yaransu biyu abun sha'awa ga kyau musamman yusif dazata dawo ne tazo da Aunty Maryam shekara Umar biyu aka tashe su daga gidan hanyar dasuke adai dai wannan lokacin uban gidansa ya kwanta rashin lafiya dan haka aka karbi dakan daga cikin kudin dayake juyawa duk da haka Allah bai hanasa samun wasu kudi da yakama musu haya nan kusa dasu ba ,aganin malam abu bai cancaci yakoma gida acikin wannan hali ga yara ,duk da shima daki daya ne a wannan gidan innarsu yusif tasake haihuwa da namiji akasawa yaro suna Ali watan Ali bakwai Allah yayiwa uban gidan mlm abu rasuwa dan haka aka kwaice shagon dake hannushi saboda kayan ciki yashiga cikin gado. byn share makoki mlm abu ya koma saide saiden takalma silifas da roba har da gajerun wanduna na yara wata rana asamu kasuwa wata rana Kuma sai godiyar Allah Amman dayake ZUCIYAR masu rikon iyali ne da mlm abu yana bakin kokarinsa sai dai abinda yazama dole ya Gaza idan lokacin damuna tayi yakan koma gida yayi aikin Gona tunda dama akwai guda dayar data rage musu shida kawarsa Laure duk shekara ana Yi sai a biyasu shine yanzu yakeyi idan ya girbe ya saida wasu yabi bashin da yayi aikin Gona wani yakawo gida ya kaiwa iya nata da Laure shiya abun baya wani dadewa a dalilin haka itama innarsu yusif har da saide saide takeyi anan cikin gida tana Kuma daurawa yusif da Maryam su shiga makwafta dan neman abin rufa asiri. Shekaru na dada ja komai na rayuwa na dada tsawaitawa su inna da mlm abu musamman dayake yanzu sun dan taru wani lokacin kafin mlm abu yashigo da daddare tuni inna ta bayar a siyo masu garin kwaki ta jikamusu su ci su kwanta shima idan yadawo yasamu yaci wani lokacin kum idan yasamu waraka yadan ya shigo musu da abinda zasu ci ,kasancewa wannan lokacin silifas din roba yake kasawa abakin titi wani lokacin tun safe har ya taso babu mai tayawa bare a siya ko da wari daya ne cikin wannan lokacin ga inna da karamin ciki yana matukar bata wahala da taimakon Allah ta ke iya duba yaranta a haka take daurewa tana zuwa asibiti saboda lalurar ciki tayi yawa, ita tsammaninta duk dan ta dan jima bata yi ba tunda tunda lokacin Ali shekara uku har da watanni bbu wanda ya jima kmr sa duk cikin yaranta . Cikin inna ya tsufa da Kyar take iya komai ga wani sabon tashi hankali daya samesu ,mai gidan ta basu notice nan da wata 3 zata gyara gidan danta zaiyi aure Kar kaso kaga yadda hankali mlm abu ya tashi a kullun da zance yake kwana yake tashi har rama yayi a wannan lokacin a safiyar laraba har ya fita can bakin titi inda yake zube takalma sai wajajen Tara sai ga yusif da gudu yaje yakirasawoshi yazo inna bbu lfy a gigice ya taho byn bar kayansa gun makocinsa daman tun jiya bata jin dadi ganin abun ya gagara ne yasa tani makwaciyarsu tace akirasa su wuce asibiti yana zuwa ko yace su tafi saboda yadda yaganta ita kuwa inna da taki kasancewa ita bata taba haihuwar asibiti ba sai a gida tani tarike zuwa titi a sami mota tare da mlm abu basufi mintina da tsayuwa moto ci nata wucewa Amman bbu ta haya wata mota kirar passant mai dauke da lambar sokoto har ta gota su sai km ta dawo ahankali ,ta sauke gilashin motar wani mutun mai fuskar fara'a ya tambayi su mlm abu yayi masa bayanin mutumin yace bbu laifi su shigo ya taimakesu su duka duka shiga domin a wannan lokacin bbu rashin gaskiya sosai a duniya a motar yake sanar dasu shima asibiti zai je dauko matarsa ta haihu tun jiya da daddare yau za a sallemesu . Asibiti ya zarce da dasu ya tabbatar an gama musu komai an tura ta dakin haihuwa saannan ya karasa gurin iyalinsa mlm abu kuwa bai iya tsayawa ba shima ya bishi suka shiga tare suka tarar har an basu sallama ,suna hada kayansu ita da wacce suke tare alhj yakarasa ya dauki bby yana kara mata addu'a sannan ya mikawa mlm abu ya juya yana ma matar sa bayanin sa ya karbi yarinya yayi mata addu'a sannan suka sake gaisa da matar mutumin yana kara Yi musu Godiya sosai da sosai alhj yace bbu komai nima nan jiya bananan makocina ne ya kawo su dama ai haka rayuwa take a haka suka fito yana so yaga likita domin jin dai dai da sallamar tasu, tani ce ta tare su da murna ai har ta sauka yanzu da sauri suka sake karasawa ciki lafiya ta haifi diyart mace har an fito da ita an gyara yarinya ita ma inna ana gyarata,duka basu fi minti ashirin ba da zuwa ta haihu , nurse din tace dama da an dau wani lokacin mai tsawo sai dai ta haihu a mota aka gyaro yarinya tasa siyo mata kayan bby aka turasu inda zasu huta sannan su mlm abu suka karasa ya dauki bby baki yaki rufuwa yana Yi mata addu'a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62