Skip to content

Chapter 25

Chapter 25

Zuciyar Masoyi Book One Complete Hausa Novels 1 1,179 words 0 views Progress saved
Download Book

mata gaisuwa ta tarar da wannan mummunar labarin kusan ma hankali mama hafsa har yafi na mami kololuwar tashi, ita mama hafsa a yadda suke ji ayanzu ita da faiza da su rasa Abdullah gwara su rasa mahaifin faiza .to duk dai yadda mami ta kai ga bincikenta akan Aisha bata samu komai ba mama hafsa ce ta fara kawo shawara suje inda iyayen Aisha suke su samesu , haka kuwa akayi da yamma ranar lahadi mami tasa musa ya tuka su dan tasan duk munafukanta ne" sun san inda Abdullah ke neman aure har gidan mlm abu tun daga inda suka sauka suka Tako lungun gidan komai yafara tsinkewa mami kmr ta zubda kwalla haka takeji , tama yaya Abdullah me kamkyame yake iya shigowa wannan kazamin lungunan . Aisha na tsakar gida tagama daka kayan Miya tana gyara zogale da zata musu Miya kmr wadda akace ta tashi kawai tashiga dakinta ita kanta ta rasa me ta shigo dauka ta jiyo sallama daga kan da zatayi ta window tagar tayi arba dasu mami Amman su basu ganta ba ,idan aka cire shekaru za'aiya cewa Abdullah na biyu ne yazo gidansu Amman sai dai wannan macce sabanin shi" Aisha ta fadi haka aranta tunda take a rayuwa bata taba ganin halitta da sukai kama sak ba irin Abdullah da wannan bawair Allah da batasan kowace ce ba,tabbas Abdullah balarabe ne akamaninsa da yanayin shigarsa zaka gane haka ko bai sanar ba, murya mama hafsa ce ta doki kunneta tana cewa A'a mu ba zama muka zo Yi ba ........... MMN SUDAIS CE [3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗 ZUCIYAR MASOYI 💖💖💖 💗💗💗💗💗 AISHA A BAGUDO Page 14 Murya mama hafsa ce ta doki kunneta tana cewa A'a mu ba zama muka zoYi ba" mama hafsa tadan juya ta kalli sashin gidan duk ba kowa sai yaya umar dayashigo zai dibi ruwa a botiki sannan ta juya takalli Inna tace ke kadai ce a gidan kece uwar yarinyar kennan to ina uban nata yake ? Gaban inna ya fadi ita bata fahimce ta ba sosai domin idanunta nakan dayar matar dake tsaye wacce tun shigowasu suke bin juna da kallon sani "sai da tace iyayen Abdullah ne wanda kuke son manna masa yarku ita kuwa mami karewa gidan kallo take tun daga sama har kasa tana girgiza kai tana gudun Kar ma wani abu yafado mata aka. Mlm abu yana titi inda suke zama inna tasa yaya umar yaje ya kirawo sa suka taho atare ,tunshigowarsu shima da kalmomin mami yagane daga inda bakin suke da saurin jiki mlm abu yakaraso Amman daga kallon da mami tai masa yasa jikinsa ya danyi sanyi ,zai Yi magana mama hafsa tace dakata malam ba maganar ka muka zo ji ba ,kasan ko daga ina muke ? Mlm abu ya tsareta da Ido shima duk da tarin talaucinsa bai san wulakancin , tacigaba mu iyayen Abdullah ne wanda tsiya tasa kuka masa kiranye mlm abu yace tsaya kiyi magana da kyau ki fuskanci abunda kike fada "mami ce tayi magana ba tsari ne yakawo mu ba Abdullah ya taka ya burma an kulle shi saboda haka nake son dan Allah abar mana dashi , ma'ana karaba banzar yarinyar ka da dana zan mallaka maka duk abunda kake so tun daga kan naira daya zuwa million goma nasan bakasan ni ko wacce ba Amman ita wannan tasanni ta nuna inna da yatsanta ,ke kuma kin xubamin idananu kmr zaki cinye ni ki masa bayanin ko Wace ce ok saboda kinkasa shawo kan ishaq da asiri shine zaki bi takan " dana" to wlh bazai yuwa ba ,mlm abu tsaye ke yana bin inna da wannan matar wato mahaifiyar Abdullah da kallon saboda maganganun ta suyi masa kama da mai tabin hankali , mami tace ka tsare ni da Ido ka tambayi matarka zata maka bayanin koni wacce ,mama hafsa ta karba idan karaba atsakaninsu yarka da Abdullah kaga kunyi hannu riga da talaucin kennan. Yaya umar ya dago zai mayar mata mlm abu ya hanashi cikin matsanancin bacin rai yake dubanta shi kam ba girmansa bane ya tsaya yana sainsa da mata ,ya dubi mami tana da wani nasibi atare da ita tamkar yadda Abdullah din nata yake uwa uba daraja da kimar da mijin nata yake dashi wato mahaifin Abdullah ,taci albarkacin hakan da ya mayar mata da wacce tafi nata na zafi, yace duk abunda aka fara shi cikin arziki ya kamata a kareshi a hakan saboda haka za'a barmu ku danku , koma ince an bar muku , Amman ku bakuda abunda da zaku bamu wanda zai wadatamu da mutunci a idanunmu ,"mama hafsa tayi sauri ta cafe ai magana takare in dai kun rabar mana da Abdullah , Amman banda haka uhmm taja numfashi , kuje kutako daidai ku mana ko wanda yadan gota ku Amman dan tsiya sai ku tabo kuloluwarku . Anan inna zatayi magana mlm abu ya sake hanata mami tana kallonta tana girgiza kai ita duk yadda ta tsani abu sai taga bai kai iyanzu da take tsakar gidan ba, ta dubi zogale dake gaban inna ita dai wlh sun gama da ita yanzu haka irin abinda suke bugawa Abdullah kennan a cikinsa ta fada a ranta ,. Mlm abu ya numfasa yace ina fatan idan kun koma zaku sanar da kafar data zo neman diyata tazo ta karbi duk wani abu da aka kawo da sunan neman aure domin yanzu bama bukata . Mami tace shiyasa nace idan kuna bukatar Kari kuzo zan kara muku duk wani abu da aka kawo muku na Abdullah ko ninkinsu ku tattara kurike abarmuku Abdullah din kawai muke so ku rabu dashi. Mama hafsa tace kun samawa kanku lfy idan kuka rabu da Abdullah haba to da angaya muku tsiya ko talauci hauka ne ,da zai sa duk ku rufe idanuwanku ku kasa duba abunda zai yuwu kuyi ta hauka tamkar masu karfi . Maganar tayi tsaye a ZUCIYAR duk wanda yake gurin hatta mami da suka zo tare tana ganin kamar maman na nema kauce hanya Amman da yake itama zuciya na zugata nan da nan Kuma abin ya mata dadi ,mlm abu yayi sai da ransa yana yimata kallon wanda ta fisu hauka da talauci ,Killa ita ce dukiyar ta ruda take neman haukacewa dan da ganinta ko kadan ba jinin arziki bace . Inna kuwa bakin ciki ne kawai ya turnuketa har bata sanda take zubda hawaye ba ,gashi mlm abu ya hanata yin magana ,yaya umar dake tsaye shima ganin inna na hawaye kawai shima yasoma kuka yanaji aransa da Ali ne daya fi kowa zuciya haka tafaru a gabansa baba ya hanashi magana Killa da tuni zuciyarsa tayi bindiga . Mami tace magana ta karshe kuma ina fatan zaku hanzarta aurar da diyarka ga gajeyaye irinku . Mlm abu yace wannan abunda ya shafemu ne gargadi kuma ki koma kiyiwa danki ,domin duk randa ya kara tako harabar gidana hukumace zata raba mu dashi.. Mama hafsa tace idan har ba tune abinda aka binne masa ba ai kuwa dole zaku ganshi .ta dubi inna hade da mata kallon banza tace dan Allah akoma riga a tone sirkulle da akayiwa yaro ko yasamu ya huta

Table of Contents

Chapters

62 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62