Chapter 25
Chapter 25
mata gaisuwa ta tarar da wannan mummunar labarin kusan ma hankali mama hafsa har yafi na mami kololuwar tashi, ita mama hafsa a yadda suke ji ayanzu ita da faiza da su rasa Abdullah gwara su rasa mahaifin faiza .to duk dai yadda mami ta kai ga bincikenta akan Aisha bata samu komai ba mama hafsa ce ta fara kawo shawara suje inda iyayen Aisha suke su samesu , haka kuwa akayi da yamma ranar lahadi mami tasa musa ya tuka su dan tasan duk munafukanta ne" sun san inda Abdullah ke neman aure har gidan mlm abu tun daga inda suka sauka suka Tako lungun gidan komai yafara tsinkewa mami kmr ta zubda kwalla haka takeji , tama yaya Abdullah me kamkyame yake iya shigowa wannan kazamin lungunan . Aisha na tsakar gida tagama daka kayan Miya tana gyara zogale da zata musu Miya kmr wadda akace ta tashi kawai tashiga dakinta ita kanta ta rasa me ta shigo dauka ta jiyo sallama daga kan da zatayi ta window tagar tayi arba dasu mami Amman su basu ganta ba ,idan aka cire shekaru za'aiya cewa Abdullah na biyu ne yazo gidansu Amman sai dai wannan macce sabanin shi" Aisha ta fadi haka aranta tunda take a rayuwa bata taba ganin halitta da sukai kama sak ba irin Abdullah da wannan bawair Allah da batasan kowace ce ba,tabbas Abdullah balarabe ne akamaninsa da yanayin shigarsa zaka gane haka ko bai sanar ba, murya mama hafsa ce ta doki kunneta tana cewa A'a mu ba zama muka zo Yi ba ........... MMN SUDAIS CE [3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗 ZUCIYAR MASOYI 💖💖💖 💗💗💗💗💗 AISHA A BAGUDO Page 14 Murya mama hafsa ce ta doki kunneta tana cewa A'a mu ba zama muka zoYi ba" mama hafsa tadan juya ta kalli sashin gidan duk ba kowa sai yaya umar dayashigo zai dibi ruwa a botiki sannan ta juya takalli Inna tace ke kadai ce a gidan kece uwar yarinyar kennan to ina uban nata yake ? Gaban inna ya fadi ita bata fahimce ta ba sosai domin idanunta nakan dayar matar dake tsaye wacce tun shigowasu suke bin juna da kallon sani "sai da tace iyayen Abdullah ne wanda kuke son manna masa yarku ita kuwa mami karewa gidan kallo take tun daga sama har kasa tana girgiza kai tana gudun Kar ma wani abu yafado mata aka. Mlm abu yana titi inda suke zama inna tasa yaya umar yaje ya kirawo sa suka taho atare ,tunshigowarsu shima da kalmomin mami yagane daga inda bakin suke da saurin jiki mlm abu yakaraso Amman daga kallon da mami tai masa yasa jikinsa ya danyi sanyi ,zai Yi magana mama hafsa tace dakata malam ba maganar ka muka zo ji ba ,kasan ko daga ina muke ? Mlm abu ya tsareta da Ido shima duk da tarin talaucinsa bai san wulakancin , tacigaba mu iyayen Abdullah ne wanda tsiya tasa kuka masa kiranye mlm abu yace tsaya kiyi magana da kyau ki fuskanci abunda kike fada "mami ce tayi magana ba tsari ne yakawo mu ba Abdullah ya taka ya burma an kulle shi saboda haka nake son dan Allah abar mana dashi , ma'ana karaba banzar yarinyar ka da dana zan mallaka maka duk abunda kake so tun daga kan naira daya zuwa million goma nasan bakasan ni ko wacce ba Amman ita wannan tasanni ta nuna inna da yatsanta ,ke kuma kin xubamin idananu kmr zaki cinye ni ki masa bayanin ko Wace ce ok saboda kinkasa shawo kan ishaq da asiri shine zaki bi takan " dana" to wlh bazai yuwa ba ,mlm abu tsaye ke yana bin inna da wannan matar wato mahaifiyar Abdullah da kallon saboda maganganun ta suyi masa kama da mai tabin hankali , mami tace ka tsare ni da Ido ka tambayi matarka zata maka bayanin koni wacce ,mama hafsa ta karba idan karaba atsakaninsu yarka da Abdullah kaga kunyi hannu riga da talaucin kennan. Yaya umar ya dago zai mayar mata mlm abu ya hanashi cikin matsanancin bacin rai yake dubanta shi kam ba girmansa bane ya tsaya yana sainsa da mata ,ya dubi mami tana da wani nasibi atare da ita tamkar yadda Abdullah din nata yake uwa uba daraja da kimar da mijin nata yake dashi wato mahaifin Abdullah ,taci albarkacin hakan da ya mayar mata da wacce tafi nata na zafi, yace duk abunda aka fara shi cikin arziki ya kamata a kareshi a hakan saboda haka za'a barmu ku danku , koma ince an bar muku , Amman ku bakuda abunda da zaku bamu wanda zai wadatamu da mutunci a idanunmu ,"mama hafsa tayi sauri ta cafe ai magana takare in dai kun rabar mana da Abdullah , Amman banda haka uhmm taja numfashi , kuje kutako daidai ku mana ko wanda yadan gota ku Amman dan tsiya sai ku tabo kuloluwarku . Anan inna zatayi magana mlm abu ya sake hanata mami tana kallonta tana girgiza kai ita duk yadda ta tsani abu sai taga bai kai iyanzu da take tsakar gidan ba, ta dubi zogale dake gaban inna ita dai wlh sun gama da ita yanzu haka irin abinda suke bugawa Abdullah kennan a cikinsa ta fada a ranta ,. Mlm abu ya numfasa yace ina fatan idan kun koma zaku sanar da kafar data zo neman diyata tazo ta karbi duk wani abu da aka kawo da sunan neman aure domin yanzu bama bukata . Mami tace shiyasa nace idan kuna bukatar Kari kuzo zan kara muku duk wani abu da aka kawo muku na Abdullah ko ninkinsu ku tattara kurike abarmuku Abdullah din kawai muke so ku rabu dashi. Mama hafsa tace kun samawa kanku lfy idan kuka rabu da Abdullah haba to da angaya muku tsiya ko talauci hauka ne ,da zai sa duk ku rufe idanuwanku ku kasa duba abunda zai yuwu kuyi ta hauka tamkar masu karfi . Maganar tayi tsaye a ZUCIYAR duk wanda yake gurin hatta mami da suka zo tare tana ganin kamar maman na nema kauce hanya Amman da yake itama zuciya na zugata nan da nan Kuma abin ya mata dadi ,mlm abu yayi sai da ransa yana yimata kallon wanda ta fisu hauka da talauci ,Killa ita ce dukiyar ta ruda take neman haukacewa dan da ganinta ko kadan ba jinin arziki bace . Inna kuwa bakin ciki ne kawai ya turnuketa har bata sanda take zubda hawaye ba ,gashi mlm abu ya hanata yin magana ,yaya umar dake tsaye shima ganin inna na hawaye kawai shima yasoma kuka yanaji aransa da Ali ne daya fi kowa zuciya haka tafaru a gabansa baba ya hanashi magana Killa da tuni zuciyarsa tayi bindiga . Mami tace magana ta karshe kuma ina fatan zaku hanzarta aurar da diyarka ga gajeyaye irinku . Mlm abu yace wannan abunda ya shafemu ne gargadi kuma ki koma kiyiwa danki ,domin duk randa ya kara tako harabar gidana hukumace zata raba mu dashi.. Mama hafsa tace idan har ba tune abinda aka binne masa ba ai kuwa dole zaku ganshi .ta dubi inna hade da mata kallon banza tace dan Allah akoma riga a tone sirkulle da akayiwa yaro ko yasamu ya huta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62