Chapter 26
Chapter 26
,a daina mana haukan karya,sai da suka Yi rashin mutunci son ransu sannan suka tattara suka bar gidan . Ko a mata ma haka mama hafsa tayi ta tsenewa Aisha da danginta, ta juyo tadan kalli mami tace naji kmr kina wani zance ishaq da ita wacen banzar matar manene a tsakaninsu" mami tayi shr tana kallon gefen titi yayin da tashin hankalinta ka sake nun kuwa,tabbas tasan da dadyn Abdullah yasan inda yar'uwarsa take da tuni ya sauya mata rayuwa kuma tanaji ajikin baisan wacece yarinyar da Abdullah ke nema ba" Mama hafsa ta maimaita maganarta ta kai sau uku Amman shr takeji akaro na hudu ne mami ta juyo ta zuba mata Ido tace kanwar dadynsu Abdullah ne uwa daya uba daya .....daga haka bata sake cewa komai ba ta dauke kanta tamayar gefe ,banda gume bbu abunda ke fita daga jikin mama hafsa hankalinta har yafi na mami tashi surutai kawai take acikin ranta lallai zama bai ganta ba . Washegari mama hafsa tabar kebbi bbu yadda mami batayi da ita ba akan ta zauna Amman taki ita kwata-kwata hankali har yanzu a tashe yake gara taje tayi da jikinta tunda tayi da baki dole mami ta hakura ta barta , Amman tace cikin satin zata dawo . Cikin yardar Allah jirginsu Abdullah ya sauka a Nigeria karfe shabiyun rana cike da kwarin gwiwa da farinciki Abdullah din yake ,tare dimbin nasarori daya samu fiyye da yadda dadynsa ya zata ,har byn karfe hudu suna tare da dady sai karfe biyar na yamma yashiga part din mami anan ma mami rikeshi tayi da girke girkenta tana tattalinsa har zuwa dare tafi kaunar yasamu natsuwa sosai kafin tayi masa zance yarinyar dayake so ,tana kallonsa tare da yan'uwasa tana sake Jin kaunar dan nata fiyye da komai da ta mallaka kallon shi take tana tausaya masa " teema tace bros what do you buy for me? Abdullah yayi murmushin i will tell you letter bana son minal taji suka Yi dariya gabadayansu teema tace banda ni kennan yace kowa da nasa ..mami ta zuba masa Ido har yanzu ZUCIYAR ta tana damuwa da inda yaje neman aure Abdullah ya lura da yanayin kallon da mami ke Yi masa Amman bai kawo komai a ranta ba . Sai byn sallar ishai yashiga part dinsa,ya furta sunanta Aisha.....akasan ransa ita din wani part ce na rayuwar sa dan haka dukkan wani abu da yakeyi tunaninta yana makale dashi dan haka yanashiga part dinsa tasake zuwar masa daman sai dai in bai kadaita ba "har ya fito daga wanka yanajinta sosai aranshi ,ya fito da system dinsa ya bude a tsakiyar gadonshi ya danno hotonta daya dauka da school uniform a jikinta tana dariya ,ya kura mata idanunshi yana tuna murmushin da tamasa daren da zai tafi hatta dasashinta da wushiryarta sai da yagani ,kusan duk sanda ya rufe idanunshi sai yaga hakan yatafi da yanayin fatarta chocolate sosai colour dinta tadace da ita, wanda bai sani ba kai tsaye zaikirata da farar fata ,yaja numfashi black American kennan ya fada a ransa jikinsa yabashi tayi masa addu'a r da tace zata masa a daren ranar da zai yi tafiya kuma yana da yakinin Allah ya amsa gashi yayi nasara fiyye da zatonsa dan idan aka cire mami da dady itace uku da zata masa addu'a ta sameshi. shi yasa yake son itama takasance wajen raba farinciki sa , Amman hakan bai samu ba saboda shi kansa bai samu kansa ba har dare....... MMN SUDAIS CE [3/12, 3:01 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗 ZUCIYAR MASOYI 💖💖💖 💗💗💗💗💗 AISHA A BAGUDO Page 15 Washegari tun safe suna tare dady suna tura sakwanni wa sauran branch din company dinsu dake sansa daban daban "Dady sai shagwaba Abdullah yakeyi hade da ririta shi saboda namijin kokarin dayayi".Sai bayan sallar ishai sannan yashiga part din maminsa yayi dinner ya Mike hade da mata sallama mami takira yadan juyo yana karyar da kai ta tsareshi da idanuwanta ina zaka kuma yau kusan kwanaki masu yawa ban saka a idanuna ba balle muyi hira Abdullah yayi murmushin mamina ina zuwa ba koina zani ba tace A,a sam banyarda ba dawo ka zauna yadawo kmr yadda tace kallo daya ta masa tagane inda yake son zuwa, ta hadiye abinda taji ya tsaya mata a wuya.. sannan tasoma Yi masa hira tun yana gane kan zance nata har yazo bai Gabe abinda take cewa gashi sai yamike da niyyar barin falon sai dawo dashi , uhmm yauwa Abdullah sai ta kuma dauko wani zance a haka dai yasoma tunanin yasan yauma dai maminsa tana son ta rusa masa burget dinsa daga karshe yagama fuskantar mami batason fitarsa ne ya Mike yayi kwanciyarsa akan three site din falon ya runtse idanunshi yana Jin yadda zuciyarsa ke harbawa ""ya daura hannushi daya a dai dai saitin da zuciyarsa ke harbawa gabadaya ji yayi hankalinsa bai gangar jikinsa tun yanajin mami sama har yazo bai jinta yanan kwance kusan 30 minti sannan yamike zubur kmr an tsikare sa ya bar falon mami na kallon kmr zatayi kuka addu'a kawai takeyi azuciyarta Allah yasa Abdullah ba gun yarinyar nan zashi ba ... .... hankalinshi a tashe yake shi kadai yasan me yake ji a zuciyarsa yau dai komai za'ayi sai yaje yaga Aisha muddin bai je yaganta ba zuciyarsa na gaf da bugawa " ko wanka bai tsaya yi ba" har yace salis ya jirashi ya fito suwuce ,Amman suna fitowa ya sallami salis shi kadai yake tuki ,cikin kamarar benz baka yayi Parking agefen titi , ya fito ya kulle motar sannan yakarasa cikin lungun su Aisha goma batayi lokacin dan haka mlm abu yana nan a waje da kwarin gwiwa Abdullah yakarasa tare da sallama sannan har kasa ya risina yana gaishe da mlm abu... Mlm abu yakashe radiyonsa dayake ji ,cikin natsuwar yake kallon Abdullah din byn ya amsa gaisuwar sa ko kadan bbu damuwa ko bacin rai atare da yaron hakan ya kara sa mlm abu cikin wasi wasi yasoma tunanin anya yasan halin da ake ciki a game shi kuwa ?a fili mlm abu yayi gyara murya ya dubi Abdullah har yau yana da wata kima da daraja a idanunsa ,yace Abdullah ko? ALHAMDULILLAH daman kai muke Jira koda bakazo mu akwai bukatar muje ga mahaifinka "mudan jinkirta wa zuwanka ne domin ta inda aka hau tanan za'a sauka ya dan tsagaita sannan yace Abdullah mahaifiyarka tazo .....a frigice Abdullah ya dago ya kalli baban Jin sa ya tsaya dip ... yadaina ji komai nawani lokacin kmr an dura masa ruwa a kunne haka yake ji sannan ya girgiza kansa yana mai sauraron mlm abu.....hakan ya nuna wa mlm abu cewar bai san da zuwan nata ba mlm yacigaba sun zo ranar lahadi ,kuma a yadda ta nuna bada saniyyyarta akazo nema maka aure ba ...Abdullah alahakikanin gaskiya anci zarafinmu sosai dan bamu da komai wanda har hakan yasa na kudirce araina nima duk ranar da ka sake zuwa kofar gidana da niyyar neman diyata hukumace zata raba mu" Amman daga baya nayi tunanin kafin ayi haka afarayin hannun riga daga baya in yaso idan wani abu ya faru ko ma menene sai ayi .... Mlm abu ya numfasa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62