Chapter 37
Chapter 37
mata katin tace lallai mun tabbata dakikai a cikin gidan nan duba nan ki gani katin auren Abdullah ne a hannuki zubewa faiza tayi tare da fixge dan kwalin dake kanta "minal ta rinka aika mata da harara wanda tun zagin da mama hafsa tayi ,ya shigo da ita falon ita dama zaman su bai kwanta mata ba dan dai mami ce kawai ta zube su a gidan ..duk da hankalin Abdullah a tashe yake bai hanashi tasowa ya bar falon ba,domin kallon abinda faiza da mahaifiyar ta keyi Karin Bakin ciki ne kawai . Dr sagir ya samu yana jiransa tare suka shiga part dinsa Abdullah na tsaye jikin window falon wanda ya bulla ta baya. hannushi duka cikin aljihun wandonsa ya zubawa waje Ido a hankali cikin raunanniyyar murya yace doctor ...doctor na hakura da Aisha mami bata sonta tace inje na zauna da Aisha bani ba ita" ita tayafeni tabarwa Aisha ni ...kana ganin zan Yi nasara kuwa bayan bbu yarda mami ciki ya fada yana kallon doctor sagir ...., Dr sagir yataso ya kara so kusa dashi ya dafa shi relax Abdullah kasan halin da kake ciki ba ishashiyar lafiya ce da kai ba ,dan Allah ka natsu bai kamata kana tada hankalin haka ba , Dr sagir yayi shr yana Jin zafin halin da Abdullah ya tsinci kansa ciki sannan ya janyo shi suka zauna tare yace ka kwantar da hankalika alamun nasarar aure kennan asha wuya a farko mami ta fadi haka ne saboda ranta ya baci musamman daya kasance taji abin late Kuma a matsayinta na mahaifiya kaga dole tayi fushi "Abdullah yarinka kallon doctor yana Jin sa kawai ba dan zuciyarsa ta amince masa ba.. Dr sagir ne ya ja shi suka fice waje sukai break fast duk wani Shiri Dr sagir ya zo masa dashi akan bikin sai barinshi yayi yanason yaga hankalinsa ya kwanta tukun Abdullah ya gane hakan dan ko zuwan da yayi Germany dubo shi haka ya dinga masa .. Duk wani barbade barbade da karunwanci yakare a gurin faiza Kat kennan yau sauran kwana biyu daurin auren Abdullah da wata ba ita ba kamar yadda suka ci alwashin hankalinsu yayi mugun tashi karfe goma dai dai Amman bbu wanda yabi takan abincin da ita faiza ta tashi tun asuba ta girkawa Abdullah ta barbade shi tas da garin magani "to duk wannan ma ta kau sai neman cima ruwa kuma yanzu domin ganin Abdullah a yanzu ya dada sawa wata kusan a cikin ta subuce ta cire daga ita har mama hafsa tamkar wasu masu dan kanoma haka suka dawo sun kasa tsugunne ,duk da mami tasan dalilin faruwa haka Amman sai abubuwan nasu suka rinka rikide mata kmr masu aljanu aljanu.faiza tana huci tace ni kudi kawai nike bukata yanzu in tafi sokoto idan ba'a maida kwanakin nan kaina ba dole a gaba mu zama daya ni dashi dan wlh bbu Yar iskar data dace dashi idan bani ba a gaban mama hafsa take magana "maman sam kasa magana tayi ta Kuma cewa kudi nike so....mama kinyi banza dani ai idan boka mai gani har hanji na doron kasa koda asiri dole na mallaki Abdullah hakan bai Dame ba, idan yafarko wata rana ai dai na lasa na dana", mama hafsa ta rage murya sosai tace kin dai fi kowa sanin yadda muka ta tike kan wannan yaron me dan banza daurin kai tsiya gashi ba wata nasara da aka samu sai ma dada kwabewa da abubuwan sukayi 'faiza tayi wani tunanin ta girgiza kai tace dole ne na koma sokoto a yau ta kowace hanya"Sam bata yarda sai burin ta ya cika akan Abdullah tayi wuf ta fakin ido ta fada dakin mami daman can Kuma ita mami koina ajiyar kudi take a bedroom dinta wani ma har ta manta faiza ta harhado kudin ta cuccusa a jikinta, ta fito kennan suka ci karo da teemah faiza tashiga yi mata yanke ba gaira ba dalili ta shige ta, haka kawai teema jikinta ya bata wani abun tayi Amman ko da tashiga dakin bata ga alamun wani abu ba kawai sai ta share tacigaba da abinda ya shigo da ita . Aranar faiza ta bar kebbi kmr mama hafsa ta bita haka taji, domin tana ganin mami tayi sakaci Kuma ta boye mata akan auren Abdullah. bayan ta latsa mata zuma a baki faiza tace ta zauna tajirata zuwa gobe zata dawo sannan ta hakura ta zauna zaman jiran wata sa'ar... Dady zaune afalonsa su teema zagaye dashi kowacce na zuba shagwaba iri iri musamman minal dan itace karama yakan biye masu wasu lokuta da dama musamman idan yayi tafiya ya dawo ko Kuma zai yi tafiya ,daga can dady ya natsu yace abinda yasa nace kuxo kunsan kmr yadda kuka ji jibi jumma'a za'a daura auren yayanku kunsan Kuma da akwai Yar matsala daga maminku dan haka nake so ku tsaya akan gida kada wani abu ya fito ku canji maminku har sai ta huce. abi komai yadda ya kamata ko bakomai bazaku so a tafi da maminku a baki ba "Kuma ita wannan yarinyar yar'uwace a gareku ..suka amsa masa da to sannan ya nuna musu set din akwatina kayan da siyo musu daga Germany har da na mami sannan yakara musu da kudi yace idan sun duba in akwai abinda suke bukata kowace ta masa magana su duka suka tashi suna murna har suka fita dady yana addu'a Allah yara shi tare da ya'yansa ya bude Ido ya ganshi cikin jikokinsa. Duk a wannan ranar ne mahaifiyar mami ta sauka a Nigeria kakar Abdullah kennan sanin yadda zata iya kasancewa da mami yasa dady yasa a taho da ita domin ita din babbar jigo ce gurin tausar mami ,da yamma ta iso. washegari da safe dangin mahaifiyar dady suka karaso daga ka'oje dan tun kafin bikin yaje yace sai dai a raba kai wasu suje can gidan maimuna wasu suzo gidan sa ,dan shima yana bukatar su cikin wannan bikin . Tun safe dady ya tura aka kafa musu tantuna na Runfa kusa guda shida acan gidan alhj aminu "har dare dady na can tare da bakinsa a gidan dake kallon gidan nasa dan haka ko sau daya Abdullah bai samu ganin dadynsa ba ,mami itama mata sunyi yawa a part dinta bai samu shiga ba ,tunda safe da shiga gaishe ta shima bai samu kallon arziki ba sosai dan haka duk wanin ranar jikinsa a sanyaye yake yana part dinshi saboda in ya fito ma marokan kofar gidan damunsa suke yi, Dr sagir ma yazo can bedroom din sa yasame sa tare suka yini har yamma Dr sagir yace yaje can gurin su Aisha su tun ranar talata suka fara bikin su gobe daurin auren Kuma a goben za'a kawo ma Aisharka Abdullah yarinka kallonsa Amman bai Yi magana ba Dr sagir yace banga Aisha ba sakina dai tace tana ciki tana kuka Abdullah ya sake dagowa ya na kallonsa sai yanzin yayi magana yace me ya sameta .Dr sagir yayi murmushin yace sakina tace saboda gobe daurin aurenta... Abdullah yayi shr yana rayawa a ransa shi da ma a kawo masa abarsa akayi yasa ta a daki ya kulle yayi ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62