Chapter 51
Chapter 51
har da kai masa kiss a fuskar,d a sauri Aisha ta dauke idanunta daga kansu . ta fara karanto addu'a aranta" tana nan zaune bata motsa ba dan bata da kuzarin ajikinta , har suka nufo inda take bata kuma sake kallonsu inda suke ba ya kiran sunanta sai lokacin ta juyo hade da Mikewa tsaye tana kakabe jikinta duk da ba wani datti bane a kayanta nan ba. suna karasowa ya kalleta yana nuna mata budurwar . yace this is lovely my class mate sannan ya dubi lovely yace and she is my wife Aisha . Cikin mamaki ta sake shi hannushi tana kallon Aisha sosai ,tace your wife ....ur wife..?is truth yace yes yana dariya ta Miko 'hannu ta rike na Aisha cikin kwarewar harsheeta tace Nice to meet you" Aisha ta girgiza mata kai tana sakin murmushin karfin hali . Aisha ta zuba musu idanun suna ta magana da Abdullah baturiya ce Sosai bbu wani miss duk jan fatan Abdullah . da suka tsaya tare sai ta ga tadan gota shi ,ta gaji da kallonsu dan haka tayi gaba gurin ice cream din. Abdullah ya Maida kallonsa kanta sosai Amman da ya fahimci inda ta nufa sai ya kyaleta" ta jima tana jiranshi Amman shr suna ta maganarsu ,tana kallonsu tana dan harararsu ,a karshe ta juya tayi tafiyarta dama bbu wani nisa da hotel din da suka sauka sai dai bbu key a hannuta . dan haka ko step bata hau ba tayi zamanta anan kasa kusa da step tana kallon mutane dake kai kawo ta dan jima zaune can sai gashi har yaje sama ya sauko da sauri sauri yana tunanin hanyar da zai bi kmr ance yakalli barin hagunsa ya hangeta zaune a rakube tana wasa da wani abu a hannuta "yadda ya hangota haka yasa ya dan bbu a dadi aransa . ya saki numfashi sannan ya karaso inda take yana kiran sunanta ta dago tana kallonsa yadda yaga fuskarta yasa gabansa faduwa har ya tuna da farko farkon haduwarsu da ita kullum a haka fuskarta take,. ba bata rai tayi ba. Amman kuma fuskarta bbu wata walwala. Yasan bata fiyye son idan sun fita ya dinga rungumarta ba" a saboda yanayin al'ada . hakan yasa daya ga fuskarta a yanzu yasa ya kiyaye ,dan haka ahankali yace Aisha taso mu shiga ,. Bbu wani mutsu ko jayayya daman ta gaji da zaman ta yarda da abinda ke hannuta ta Mike . Suna shiga room din su yasa key ya juyo zai rukota ta zame jikinta tayi gaba. Tasamu waje gefen gado tayi zamanta tana tana jin yadda duhu ya mamaye zuciyarta har wani juwa.. juwa.. take Gani , ta runtse idanunta tana jin radadi mafi muni . Ahankali ya karaso yana murmushi yace baki ga yadda nazama ba a rashin ganinki . yasake sa 'hannu zai janyo ta gareshi ta dan matsa ahankali cikin sarkewar murya tace ple..ase ...Ni Ni karka tabani .ya tsaya cak yana kallonta hannun ma tsayar dashi yayi. yadda yake kusa daita ya dan yi shiru yana kallonta sannan ya janye hannushi ya zuba su duka cikin aljihun wandonsa. ya zuba mata idanunshi sosai yaje nazarinta yanayinta " a ransa yace Aisha tana kishin shi dan ta ganshi da lovely. wannan ai wani cigaba ne a gareshi. zuciyarsa ta dan masa dadi , duk da ba muhalin haka bane. da alamun tunda ta fara nuna haka ta soma damuwa dashi kennan numfashi yake saukewa ahankali ahankali. ko ba komai ya fara gane matsayinsa a wajen.ta ya sauke ajiye zuciya yace OK ina zuwa ya juya ya. shige bathroom har ya fito daga wanka tana nan inda take zaune inda barta , daga shi sai mini casual wanda ya dameshi har kana hango yadda jijiyarsa ke kwance ta dauke idanunta tana yamutsa fuska. ya karaso inda take zaune ya dan tsugunna kusa daita yace ayimin hakurin na cire kayan da lovely ta tabani dasu .... ahankali cikin sarkewar muryata da yafi so tace ni ina ruwana da abinda tayi maka . yadda ta fada din ne har tasa dariyarsa ta fito fili ya rufe bakinsa da hannushi duka yana kokarin hana dariyar fitowa,dan kar ya kara bata haushi, shi kuma kallonta yake Yi sosai yarinya daita zatayi masa wayo byn ga idanunta da maganar duk sun nuna kishi lovely takeyi karara. Ta kara bata fuska ganin haka yasa ya daina dariyar ya Mike ya zauna kusa daita ya kamo tafin hannuta ta fizge yace please...4give me .... tasake dauke fuskarta, aransa yace kishi yarinyar nan zatayi sosai da ganinta zai sake tabata ta Mike. da hanzarinsa ya fizgota ta fado kan lafiyayen jikinsa da suke cike da gashi ya matseta tsam dan kar ma tayi kokarin kwacewa yace wlh gara kiyi min kowani irin punishment Amman banda wannan. na hanani taba jikinki Allah bazan dauki wannan ba shima ya narke mata . Tanan kwance a kirjinsa har tayi kukanta ta gaji tayi shiru yana kallonta. ya jingina bayansa da jikin gadon yana share mata hawayen yasa'hannu ya cire band din da ta daure gashinta dashi. ya fara shafa gashin kanta ahankali yayinda kansa ke kallon sama. yace Aisha a baya nataba baki labarin wani bangaren da ya shafeni". a karshe nace miki sauran bayanin inda muna tare zaki sani. yasake matseta ajikinsa yana busa mata iskar bakinshi , har sai da yaji ta saki kara mara sauti sannan ya sausauta mata . Ya danyi shiru sannan yacigaba tabbas lovely itama tasoni a lokacin muna school . sai dai ina tabbatar miki har nabar oxford bantaba sonta ba. ko ince ni ban taba ma son wata ba saboda lokacin haduwata daita banshirya yin soyayya da wata Diya mace ba . yace Aisha ke kadai zuciyata ta taba so irin son da ban san yadda zan kwatanta miki soyayyarki gare ni daga Allah ne kuma har yanzu zuciyata akan kaunarki ta amincewa . zuciyata tana kara tabbatar min zanci gaba da sonki ne har karshe numfashi na . AISHA ta Mike saboda ta gane lokacin sallah yayi Abdullah ya ruko hannuta ta dan juyo tana kallonsa baki ce min komai ba . tayi shiru ya janyota jikinsa" tana fadowa ya riketa gam ya dora bakinsa kan nata duk mutsu mutsunta yaki sakinta da harshensa ya bude bakin yasoma tsosa cikin kwarewa . sai da yagaji dan kasa sannan ya kyaleta . tuni idanunshi sun soma sauya kala. Aisha kuwa da sauri ta Mike ta shige bathroom tana kuka. tare suka yi sallah sannan suka ci abinci dare .ya fada wanka suna shirin kwanciya takaraso da freshmilk a hannuta ta Mika masa gabadaya har hannuta ya hada ya rike gam . ta kalleshi shima kallonta yayi" ya jawo hannuta suka zauna a gefen gado dukkansu suna rike da cup din Abdullah ya zuba mata mayun idanunshi masu rikitata ya kira sunanta yace dan Allah Aisha menene abin wahala a magana wanda rashin yinta yake miki walaha ke komai bai dameki ba hatta bude bakinki . Kanta a sunkuye yacigaba . can cikin ransa kuwa rashin maganarta na daya daga cikin abinda ke kara birgeshi . saboda duk bakin daya cika magana sosai wata rana zai yi karya. A filli kuma yace ple..ase
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62