Chapter 49
Chapter 49
ba. Saidai masu hadiyar zuciya su hadiya in yaso ta buga su mutu" Ak ya yaboma Moh maganfanun da tunda uwarta ta haifeta ba'a yaba mata koda kwatancinsu ba. "ABDOUL-MALEEK" Muryan Oum ya katse shi daga wata maganar da yake shirin sake yanko mata. Hatsaniyace sosai ta kaure a cikin dakin kowa yaki ya rusuna kowa ji yake da nasa zafin kan. Abinda ya rusunar da rigimar nasu faduwar da Oum tayi. Wannan shine dalilin lafawar komi haka Ak yama Oum dinsa daukar jarirai ya fice da abarsa zuwa clinic din masarautar, Shine da kansa ya duba Oum nashi kasancewarsa dactor, kana pilot ne idan yaso babu inda baya ketawa a kasashen duniya. Kana gashi Babban soldiers wanda matakin farko ma da Marshal ya soma..... ⭐Washe gari ⭐ A nutse yake Sakkowa daga matakalar benen zuwa entrance din da zai sada shi da bangaren oum dinsa. yana sanye cikin wasu fitinannun lallausan farin yadi. yayin da kuma ƙkafarsa ke sanye cikin wani black combat toms mai kyau irin na yayan sarakunan nan, Sai wata mini jacket din daya dora saman kayan yar filic da ita. babu abinda ke tashi ajikinsa sai wannan fitinannen kamshin turaren nan nasa me azabar tsada da bama wanda yake shakarsa cikakkiyar nutsuwa ta musamman. Tamkar wanda akema wanka da madara haka farar fatar jikinsa ke daukar idon me kallonsa. Cikin cikakkiyar takun da kallo daya zakayi masa ka gane cewar kakkarfa ne sabo da motsa jikin da yake aduk kwanan duniya ta hanyar machine gams. Blue eyes din nan rufe cikin wani luxury sun glasses wanda ya sake bayyana taswirar karan hancinsa da yake mike ziyat tamkar da biro aka zama masa shi daram. pink lips din nan nashi sai wani kalan glowing yake tsananin taushin na bayyanuwa wa me kallonsa, kallo daya zakama Ak ka gane shi din me kyau ne kana na musamman masha Allah,domin allah ya wadatashi da komi najin dadin rayuwa. cike da kwanciyar hankali da nutsuwa yake takawa irin takun dake nuna shidin kakkarfan namiji ne kana tsayayye. Marar daukan wargi da in Manners din nan. Kai tsaye babban katafaren parlourn Oum dinsa yama tsinke wanda girmansa yake dauke da wasu tsadaddun furnitures, parlour ne mara tarkace amma yana da kyau na fita daga hayyaci. Kayatattun royal cushion din dake zagaye da parlourn sunyi may kawanya, daga tsakiya kuma akwai wani shimfiɗaɗdiyar red carpet da throw pillows akai, sai wani ƙkaramin round table daga gaban wani kebantaccen rug, sai babban plat screen plasma din da ya kusa cinye bango guda na parloirn don girman shi. iskan A/cn dake kasawa kai tsaye yake fidda wani irin daddan yanayi a cikin parlourn, dubansa ya kai ga ƙkaton agogon dake manne a bango wanda yake ƙkawace da zanen pop, tare da pisc na Oum shi tare dame martaba. ⭐10:25am agogon ya buga cire pcarp din kansa yayi yana kallon ƙyakkyawar fuskan Oummey'nshi dake zaune kan caution mug ne a hannunta me dauke da zazzafan ruwan bunu marar madara. Kallo daya zaka mata kagane ita din mahaifiyarsa ce saboda kamar dake tsakaninsu, lumshe idanunsa yayi hadi da dan sauke numfashin ganin zaune cikin koshin lafiya da yayi. Cikin amon muryansa mai dadi da nutsuwa yace "Takabbalallahu minna wamin kum alaina wa'alaiki ya Oummey! ". Shafa tulin sumar kansa tayi wanda yasha gyara mai kyau da sheki yayin da yake durkushe agabanta ya dafa hannayensa duka biyu a ƙkafarta, cike da kulawa tace "Amin barkan mu da wayewar garin Alhamis lafiya habeebty" Jesra dake tsaye hannuwanta sarke akan kirjintane ta dan turo baki gaba tare da fadin. "Aifa shikenan nikam tawa ta kare tun da nakan gaban goshin ya dawo" Cikin yanayinsa na rashin son magana yayi dan murmushi yana faɗin "Kina kishi da hakan ne jes?” ya fadi hakan yana maida kallonsa ga mahaifiyar tasa yana faɗin "Ya Oummey nah ya saukin jikin ki?". " Alhamdulillah naji sauki tun da ka dubani HABEEBT?,kaje ga Me martaba ya kamata ka sake auna yanayinsa Garga" Kansa yayi noding yana mikewa tare sa barin shahin...... *BY AMMEY LAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* *~We want an end to oppression💪~* https://chat.whatsapp.com/GiLzmY90dz17bRbw5yMYBg ____________________ *MARYAM NASEER* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* Page 47&48 # ROMANCE # BLACK MONEY # DEEP # Hope # courage # Survival # Humanity # Inspiration 🤍🔥✅✅✔ ⭐ NIGERIA ⭐ A kullum duniya canjama bawa ajin karatu take yau din kace kawai zata tabbatar maka da hakan, musamman idan kaga ta banbanta da ƙkaddarar jiyanka!. Rayuwa mataki biyu ce Acikin kowacce duniya duk wacce kaddararka ta zabar maka zata kaika ne zuwa makomarta, sabanin shine kawai dace wajen banbance nagartacciya ko gurbatacciya. A yau dai ga merrah wacce take dab da amsa sunan mrs Salma isa manu, wanda komi da komai ya gama kammala kansa daya danganci bikin aurensu wanda ya rage kwanaki biyu takkk. Kamar kullum yanzu ma zaune take a palon Annenta tana danna wayarta wajen karfe biyar da rabi na yammacin ranan alhamis. A zahiri danna wayar take amma a badinin ta ita kanta bazatace ga abinda take aikatawa a cikin wayar ba. Abinda kawai ta sani shine tana lallatsa wayar ne. Sallamar da aka yine ya sanyata dagota da kanga. Hajiya ummace ta shigo da sallama rataye da jaka a hannunta. Mikewa tayi ta nufeta tana murmushi ta amshi jakar tana fadin "Hajiya sannu da zuwa" Zama tayi akan kujerar palon kana ta amsa da cewar "Yauwa Merrah na biyo sahun kine dama kwana biyu shiru bakya zuwa. Ni na rasa wacce iriyar amaryace wannan ace gyaran jikinka ma gudunsa kake?' Kyaje gidan ne mijin ya koroki astagfiroullah Allah na tuba. Wllh tsaya kiji wannan bikin da naje Ikaja. Bayan kai amaryar da kwana biyu mijin nan ga daho kaza a dafe rigijff tasha kayan miyarta sharr. Ai wllh nake baki labari yakai gidan su amaryar nan bayan uwarta taci taji salam babu komi tace wannnan ai kunyi mantuwa babu komi a ciki na kayan hadi. Kinsan me yace ce musu yayi yanda sukaji kazar nan haka yaji yar su, to yanzu dan Allah me amfanin hakan? Wllh babban gata nake miki yar nan" Wani murmushin da baikai zuci ba meerah ta saki tana sunkuyar da kanta kasa. Acen kasar zuciyarta tana furta (Ni wllh da yamin daidai kuwa amma fa ni bama yarda zanyi wannan me kama da birin ya taba niba, bare ya hada jiki dani nevermine wllh) Fitowar Anne shine ya katse meerah daga duniyar tunanin data fada. Kallo daya Anne ta mata ta dauke kai tana karasawa inda hajiya umma ke zaune. Gaisawa sukai nan suka fada wata maganar daban ba wacce hajiya umman keta kokarin ganin ta kawota ba. Jakar kayan Anne ta turama meerah tana fadin taje tayi amfani dasu kafin ta shigo dakin itama. Hayaniyar data kaure a cikin gidan ne ya sanya su umma fita. Wata matashiyar mata ce wacce taci wani ubansun ado jikin farin leshin daya sha doguwar riga half bubu, sai farar siririyar yarinyar dake gefenta cin mutumci take zuwaba a cikin gidan tana fadin sai an nuna mata uwar data haifi amaryar da ake shirin likama dansu, dan son zuciya da bakar zalama anga gidan arziki shine za'a likema dansu... Kallo daya Anne ta watsama matar ta dauke
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54