Chapter 25
Chapter 25
wanne irin laifi ta musu da suka zaɓi su jefar da ita? Tana son ta tambayi wanne irin mutane ne su masu son zuciya?_ _Ita kaɗai tasan abubuwan da suke cunshe a cikin Rai da ruhinta, wanda suka kusa tarwatsa zuciyarta ta buga ta dena aiki, domin tasan tana dab da bugawar. Badon Allah yayi ta mace me tsananin haƙuri da danne abu komi girman sa a cikin zuciyarta da tuni numfashinta ya jima da barin gangar jikinta..... A bayyane ta sauƙe wata nannauyar ijiyar zuciya cikin muryan da yayi low sosae ya furta. "Me yake damun DIDINA haka?" Kanta ta ɗago tare da kallon mahaifiyar nata cikin raunatacciyar murya ta shiga faɗin. ”Nima bansan abinda ke damuna ba Anne! Kawai dai inajin yanayin cinkushewar zuciya ne, da rashin jin dadin yanayin rayuwar ma baki ɗaya” ”Ce ALHAMDULILLAH domin Allah shine abin godiya a koda yaushe!” ALHAMDULILLAH ɗin kuwa ta furta tare da duk sauran adda'oin da suka zo mata. Ƙiran sallar asuba da aka ƙirane ya fitar da Anne a ɗakin bayan taci kukanta harta gode Allah. Ko Washegarin ranar Meerah kasa fita ko ina tayi, kayan karin tama har ɗaki Raiha ta kawo mata..........ita kuma ta wuce makaranta. Tana zaune a ɗaki Sai wajajen sha biyun rana kana ta fito verander inda ƴan uwanta aurarru suke zaune. Gaisar dasu tayi wasu sama sama suka amsa wasu kuwa arziƙin kallo bata samu daga gare su ba. Kwanciya tayi ba tare data nuna damuwarta akan rashin amsanta ba basu yi ba. Babbar yayarsu da suke ƙira aunty Zaheedah ce tace. ”guys na manta ban baku wani latest story ba" Shewa suka sanya a tare kusan su biyar kana aunty Sumayya ta furta. ”Bamu musha ƴer uwa” Saida tayi ƴar dariya kaɗan irin ta rashin mutuncin nan kan furta. “Kai Wllh na daɗe banga mara zuciyar mace irin zulaiha ba, Ata zaluntar mutum amma saiya nuna baimasan ana yimay ba. Kunsan a wayewar garinda Affan ya rasu sai dana sake banka musu ɗaki ita da Belle" ”Kai Wllh na daɗe ko'a littafin Hausa Novels banji me hali irin na matar nan, ayi yarinya sai kace me zuciyar takarda ko ma wacce bata da zuciyar a tsakiyar ƙirjinta” Aunty labiba ta faɗi tana gyara zama "Nake baku labari shegen kamar kullum ranar ma kasa tanka min yay saima rawar jikin daya fara min...... Ita kuwa shegiyar Wllh ko kallo na kasa yi tayi kamar dai ko yaushe” Aunty Maryam da tunda suka fara maganganunsu ce dama kuma bata ce musu komi ta furta. ”Innalillahi! Yanxu dama har yanzu Zaheedah baki dena wannan banzan halin naki ba?, Na cutar yarinyar mutane ta shigar mata ɗaki kina gane mata sirrin aurenta......Wllh kiji tsoron Allah domin ɗaurin talala ya miki duk randa Ubangiji ya tashi nuna miki ikonsa a kanta Wllh daga ranar zaki gane Allah ɗaya yake” "Huyummmmmmm me zuciya irinta marasa kan gado, ke dai kici gaba da zama a cikin duhun kai da bar abada bazaki waye ba" Cewar aunty labiba, shewa suka sanya mata nan fa suka koma kanta suna mata cin mutuncin da suka ga dama. Ni kuwa dake kwance a wurin tsammmm na miƙe domin kunnuwa ba rasuji gaba da jin zunufi ba. A cikin zuciyata kuma ina musu fatan shiriya duniya da lahira. ★★★ *ABUJA* Zaune take akan caution ɗin da yama ƙatataccen parloun ƙawanya, tayi zurfi sosae a duniyar tunanin halin da rayuwarta take ciki. Tana zaune cikin ƙunci na rayuwa da azabtar War kishiya. ”Zulaiha! Zulaiha!!" Shiru alamun tayi nisan kiwo a cikin kogin tunanin data faɗa. ”Zulaiha kodai kin sanya wata damuwar ne a cikin ranki?” Matashin mutumin dake kanta tsaye ya tambaya wanda a shekaru zai iya kaiwa irin Talatin da bakwai ɗin nan ko da shida. zamanta ta gyara tare da fuskantar sa sai kuma idonta suka ciko da kwalla. ”Yanxu Bello tambayana ma kake ko damuwar woni abu nasa a raina? Duk irin ƙalubalen da nake fuskanta a cikin gidan nan? Haƙuri na yana dab da ƙarewa Wllh na gaji- na gaji *NA GAJI BELLO!* Duk irin abubuwan da ake min woni a gaban idonka woni a bayan idonka amma kanzil ba zaka iya furtawa akan anyi min ba daidai ba” Ta furta cikin muryan kuka sosai da sosae. Kafaɗunta ya dafa cikin kwantar da murya ya shiga furta. ”Har abada ba zan gaji da cewa kiyi haƙuri ba zulaiha, ita rayuwar duniya ƴar haƙuri ce kuma duk wanda yayi haƙuri baya taɓa faɗuwa ƙasa....Ƙarshen ko wanne haƙuri nasarace, ƙarshen tsanani darajace, ƙarshen wahala ɗaukakace, ƙarshen jarabawa kuma Alkhari ne ciki gaba da zaman haƙuri dakai kukanki wurin Allah domin shi maji ƙan bayinsa ne" Daga haka ya saki kafaɗunta yay taku ɗaya ana biyu ta riƙo hannuwansa, Sai kuma kawai ta faɗa jikinsa tare da cusa kanta cikin ƙirjinsa rana fashewa da wani irin kuka me cin Rai. Tsammmm ya rungumata ya fara lallashinta,Saman sa ya nufa da ita tana cikin jikinsa. ★★★ Ayau wayar garin litinin zazzafan martani ya fito daga bangaren *AK* Wanda indai mutum masoyin media me to da wannan zazzafan latest news din ya karya. Ga abinda martanin ya kunsha na farko a cikin tiktok. Yana zaune a wani kayataccen palo ne wanda Wanda ya wadatu da komi na mo re rayuwa, sanye yake cikin shigar bakaken Riga da wando yayi covering duka jikinsa ko kwayar idonsa babu me Iya gani. Shi kanshi video'n don ka tabbatar dana musamman ne idan ka shiga kafin ka fara ganin komai said kamar 5 minute haka xuwa 7. Kafafun nan a harde kamar kullum cikin nutsatstsen sautin da yake fita cikin wani irin low voice nd sweet ya shi fara mayar da martaninsa kai tsaye. _Fusata ya kamata ace kunyi bawai nuna fushinku a kaina ba!. Kasancewar kun gane wannan shugaban da kuka zaba ha'intarku yake yi, akanshi ya kamata ace kun nuna fushinku sakamakon zabarshi da kayi_ _A yayinda fitilun titi suka dauke hanya ta cika shara da kuma tarkace, A yayinda ake wulakanta talakawa tamkar dabbobi a asibitin gwammanati!, cin hanci ya wanzu a kowanne ofishin ma'aikacin gwammanati anan zaku nuna fushinku. Me yasa ba baku nuna fushinku fusatarku a ire-iren wadan nan abubuwan?, amma a yayin da gurbataccen shugaba ya shigo hannu shine kuka harda fitowa wata zanga zanga? Kukayi kone-kone kuka har gitsa komai da komai a cikin ko wanne lunguna na wannan gari dama wajen garin?. Idan har wani iftilati ya faru daku ya kasance kuma kuna bukatar taimakonsu to amfani Duke wannan hatta shi wannan taimakon Right?. A wannan kasar shima talakan ba wani salihin bawa bane, shine ma hanya mafi gurbata a wannan fannin. Rashawar dake tattare da kuri'a itace ke bama shugabanni wannan ikon. A yayinda da suka zo suka raba muku wasu yan tsirarun abubuwan amfanin yauda kullum da bazasu wuce wuni daya ba. Shine kawai kuke zabarsu ba tare da tunanin menene abinda gobenku zata haifar muku ba. Sabo da rashin sanin yanci zarmammun cikinku suke dauraku akan ra'ayin da ba naku ba, domin kasa ta sanja dole sai talakan gari ya fara sanjawa domain kawar da rashawa da kuma son zuciya. *DON HAKA MU FARA SANJAWA.....*_ Kafin kace mene tuni media ta dauki hayakin bala'i domin wannan zazzafan martani
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54