Chapter 26
Chapter 26
na ABDOUL-MALEEK AK tuni ya baza ko INA. Har wasu na mai dashi rubutu ta hanyar copy suna dorawa irinsu Facebook, Twitter, Instagram, telegram dadai saurinsu haka gidajen radio suma suka ringa maimaichin abun kamar ba gobe. Sai yanxu hankalin mutane ya fara dawowa jikinsu. Tuni hankalin jami'ai kuma ya tashi da wannan ballo ruwa da AK yayi Wanda suka rasa ta inda zasu toshe hakan. Hankalin duk wani Dan siyasar dake Nigeria a tashe yake da ganin wannan video, tuni jamaar dake kiran AK da criminal suka dawo girmama koda jin sunan shine. Saidai amsa daya da ko wanne mutum ke dokon jira a jirace shine bayyanar ak a zahirance. Da kuma asalin kasar shi da inda yake zaune domin kuwa kallo daya mutum zai yi masa yasan cewar shiba mutumin NJ bane, ko daga yanayin zancenshi da baya idasa fita duka. Wannan Abu shine yayi sanadiyar takawar shugaban kasa har xuwa Lagos. Inda suka tattauna da manyan Jami'ai da kuma wasu kuso shin gwommanatin dake mulkarmu ta karkashin kasa...... Meeting din gaggawa suka shirya tsakanin masu ruwa da tsaki a cikin tafiyar. After like 50 minutes haka suka shirya meeting ɗin gaggawa cikin wani haɗaɗɗan building mai haɗe da wani ƙaton hall acikinsa, coutions ne acikin sa na alfarma wanda hall ɗin yaji kayan mo re rayuwa, ko ina stainding A/C ne manner a wurin sai sanyayyar ƙamshi da kuma fitar numfarfashin jama'ar da wurin ya tara ne ke tashi. meeting sukayi me sunan meeting Dan sai dab da magrib suka tashi suna ta faman kulli da warwara, ahaka har suka sami mafita kana kowa ya kama gabansa bayan zaida mafitar da suke ga itane kadai mafitarsu. Kwanan Armstrong hudu AK yayi dirar miki a boyayyen wurin da suka boye shi ta hanyar footage din dake cikin karkashin harshensa. Tsaro sosae akama wurin duk don kaicema samin kuskure,amma hakan bai hana ak bayyana a gabansu ba. A lokacin su Mr President, Ajmaal, Isa manu, dadai sauran manyan kawunan suna a cikin setrest din ne don sun fitar dashi a station din ma baki daya. Suna kan azabtar da Armstrong Woyar dco ne yayi kara hakan ya sanya shi dakatawa da bugun Arms din. ”What AK kuma?” Ya fada a zabure har yana kokarin hantsilawa saida Ajmaal yayi saurin taro shi tu kuna ya daidaita tsaiwarsa. Wani matsiyacin kallo Ajmaal ya jefawa arms. ”Ta Yaya yasan kana a wannan boyayyen wajen?” Ya fada yana shakar arms din. Wata shegiyar dariya arms ya saki tare da furta. ”Ku a dakikin tunaninku da kunyi haka ne don boye ni daga BOSS?” Ya fada cikin wannan dangerous voice din nashi. ”ANSWER MEE ARMS!” Ajmaal ya sake maimaitama arms tambayarsa. Dariya ya shiga yi kafin ya furta ”footage” ”Karya kake arms babu camera a jikinka nida kaina nayi check out naka!, don haka ka bani amsana a karo na karshe” ”Shi yasa na CE duk cikin Ku babu Wanda Zan kira da *JAN WUYA, duk kaninku ”KOLAYE NE” Ya fada yana daga harshen Sa tare da sanya shi tsakanin seen da tongue nashi ya turo musu Yar karamar camerar. Duk cikin su babu Wanda be razana da wannan basirar tasu ak ba. Ehhhh dole suce basira mana amma sai suka waske abinsu.... Few minutes Zaune yake zama irin na harde kafar nan. Akan kujerar da Isa manu ke kanta a da a yanxu kuma ta dawo da ak din. Fuskarnan tamkar tayi aman Wuta tsabar tsananin fusata,A fusace Ajmaal yayo kan ak duk kuwa da yadda Mr President ke kokarin hana shi amma be hanu ba. ”Kaida kazo da sunan kwatar yaronka to kasani kazo nan da sunan mutuwarka ne!,, A wannan rana a kuma nan wurin idan har ban dagarzaga kasusuwanka to na rantse ni ba namijine” Wani Dan iskan kallo da ak ya watsawa Ajmaal ne ya sanya jikin Isa manu ya soma karkarwa,shi da ba shi aka ma kallonba. Wani irin gyara zamansa yayi ya sakko da kafarsa daya dayar kuma ta na kan kujerar da yake kai. Ya dora hannunsa saman kafar like irin kasaitaccen basaraken nan. ”Ko wane mafarauci gwarzone har sai sanda ya fuskanci ingarman zaki. Ba kamar kai da rundunar jami'anku ba!, bana da runduna bana da tsoro a jikina bare naji tsoron mutuwa. *TUN A HAIHUWATA NACI GALABA AKAN MUTUWATA_*” Ak ya furta kalaman tare da wani iriin doka hannunsa akan kujerar da yake zaune a kai. Kalaman da suka kusan zauta yar karamar kwanyar duka jama'ar dake setrest din..... A zuciye wani da suke kira da tonfal babban yaron su Isa manu yayo kan ak, da wani irin salon daukar hankali ak dake zaune ya sanya kafarsa tun kafin mutumin ya karasa ya sarke kafarsa. Ji kake rigifff mutumin ya zube kasa ba tare da ya ko motsa ba. Cikin kankanin lokaci ak ya sissince arms dake daddaure ya tafi dashi a gaban idonsu ba tare da sun Iya dakatar dashi ba haka suna ji suna gani ya sabi arms a kan shoulder nashi yabar wurin dashi.cikin wannan takun NASA me cike da bajinta,hadi da mazan taka Wanda kallo daya idan kai masa sai hantar cikin ka ta kada..... ”Kai wannan yaro anyi dan tsinanne, kasa sai kace ta uwarka kazo ka zame mana fitina tare da hana mu rawar gaban hantsi” Isa manu ya fada bayan daya tabbatar ak dade da barin wurin. Ajmaal da gefen kunnansa ke digar jini ne Wanda ak ya bashi rabon shi. Cikin tsanin bacin ran ya furta. ”Stoppp” Da karfin masifa ”Na gaji dajin koda me irin sunan sane” Sai kuma ya dago ya kalli Mr President ya furta. ”Sorry sir. Duk ba laifinka bane da alokacin da na d'ana kunamar bindigata baka tsayar dani ba ai da tuni saida wani bashi ba!, amma ka dakatar dani” ”Babu dai kai ba shiba!” Tonfal ya fada Wanda babu jimawa ya farfado daga mutuwar wucin gadin da yayi. ”More bit never get one choice but if we take a maximum change we get a big choice” Mr President ya fada yana gama fadar hakan ya fice a wurin... A lokacin da akai wannan darbarwar salman yana kasar India yawan shakatawa tare da wayayyun yan matansa. ★★★ ”Mommy Wllh duk inda yake a fadin duniyar nan saina dau fansar Jinin mahaifina da yayi, sai nayi sanadiyar barin numfashinsa da gangar jikinsa kamar yadda yaso raba nawa mahaifin da nashi!” *FAROUQ AUDU BASHASHA* kenan da ga audu bashasha shi kadai ya haifa a duniya.Shi yasa yaron ya taso cikin wani irin sangarta da tabara, Duk inda ake neman wani teteros to in akace maka Farouq fakat kenan. A yanxu haka Audu bashasha yana kasar India wurin kwararrun likitoci don kula dashi. Ashe be mutu ba da sauran ranshi lokacin da ak ya fasha kansa, Sun boye hakan ne domain gudun bacin sunan Sa, shi da kansa shine ya dauke RIYYA, ya mata wani irin mugun boye mahaifiyarsa kuma irin muta nan ne da sammmm babu ruwansu da duniya. Itace ma dalilin daya sanya ta hana. Cikin muryar da yake cike da tsantsan sarauta Hajiya Khadija suraj sunusu shureim ta dubi Dan nata Tare da furta. „Idan har Jinin dake gudana a cikin naka Jinin nawa to ban amince maka ba” Ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54