Skip to content

Chapter 33

Chapter 33

Mikiya Book One Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
Download Book

Sai kuma kamar wadda aka tsikara ta mike tana ce dasu ”pls ina dan zuwa” Ta fadi tare da mikewa tsaye kai tsaye cikin park din ta numa, Ahankali take binsa tamkar me sanda. Woyane a kunnensa cikin yaren labarcin da tamkar a bakinsa aka ruwaito shi yake wayar. Kafin daga karshe taji ya ambaci room 0035 3rd floor. Ganin kamar zai juye ne ya sanya ta saurin komawa baya a haka ya bace mata. Rasa ma yadda zatayi takai kanta room din tayi, cennnn wota dabara ya fado mata wata maid service CE tazo zata wuce ta gefenta. Ai kuwa cikin sauri tasha gaban wannan maid service din tare da furta. ”please go to room 0035 a 3rd floor ” ”okey biyoni” Wannan maid din ta mata jagora har xuwa gaban room din. Gabanta faduwa yake sosae amma haka ta danne ta tunkari kafar room din. A hankali tamkar wota barauniya ta dan leka kanta cikin room din,Da kafafunsa ta fara cin karo Wanda suke sanye cikin wani sgegen bakin shoe Sandal's. Zara² fararen kafafunsa sunyi wani mugun kyau ta cikin takarmin. ”Boss kamar yadda ka umarta mun dauko shi yana dab da kawowa park din!, ba tare da bodyguards nashi sun ankare ba. Kana kana da zama da misalin 5:35pm da kamal Rano ya sauka shima tun 10:00 am” Ita dai keyarsa da gashin kansa ke zube kawai take Iya kalla. Dake shi komi nasa irin na muna fukai da marasa gaskiya yake samm bata ji abinda yacema dayan mugun ba. Wani irin shegen zaro ido waje tayi ganin Wanda suka zo wurin domin shine wannan mugun yayi kidnapping dinsa. Sosae jikinta ya shiga rawar tsoro domin taga wannan mutumin da gaske mugu ne, kashe mutane da sacesu kawai ya Iya. Cikin wani mugun tashin hankali ta juya tana barin word din, tsabar ma ta rikice ta rasa ta wacce hanya suka biyo haka ta ringa sanja hanyoyi amma ta gane inda suka biyo da wannan maid service din. Gafff taji tayi karo da wani Abu. A tsorace taja baya dake a mugun tsoracen take dama. Ai kuwa bisa tsautsayi kafarya ya zame tayi wani irin baya. Wani razanannen ihu ta Saki tare da rimtse idonta da karfin bala'i ganin ashe kasa tayi. Baki daya ta gama saddakar da cewar yau saidai wata ba ita ba a cikin wannan duniyar. Shikenan ashe dama sallamar karshe ne tayi da annenta tare da baffanta. Wani irin fusgota taji anyi babu zata,kai tsaye kan faffadan kirjinsa dake tashin wani irin bala'in kamshi ta fada. Ba tare da tunanin komi ba ganin ta tsirane ya sanya ta wani kankame jikin wanda ta fada da karfin gaske tana sakin wani raunataccen kuka. ”Allah Sarki Anne'na da tuni na mutu yau ba tare da nemo miki koda daya daga cikin ahalinki bane!” Ta fada tana cikin muryan kuka sosae. Wani irin fisgeta a jikinsa yayi tare da jifanta da wani shegen kallo yana Jan tsaki. Tana yin ido hudu dashi a matsayin Wanda ya temaketa ta kwallara kara tare da furta. ”Kai cho na Wllh daka temakeni!, Wllh dana San Kaine kara na fada kasan na mutu, Allah ya Isa ban yafe maka ba! Mugu! Azzalumi!!!” Tana fadar hakan ta kwasa a guje da gudun masifa tana yin kasa. Tana dira a gabansu disha da suka haukace a nemanta. Itama a haukacen ta furta. ”Nafsi Nafsi Wllh kowa yayi ta kansa ga mala'ikun duniya nan” Ta fada da karfin masifa tana kara kwasa a 449, haba tuni sai gashi sun take mata baya ganin yadda take gudu cin karfinta, domin sun San duk abinda ya tsorata MARYAM ABDULLAHI GWANI harya sata gudu to ba karamin abu bane. Da sauri hayatudden daya rigasu Isa gaban motarsu ya bude musu, su kuma suka fada yaja da mugun gudu suna barin wurin. Ai kuwa suna daf da fita a cikin park din idonta ya sauka a kanshi, alama ya mata da saina gimtse miki wannan shegen bakin. Tamakar kuwa tasan abinda ya furta din ta turo dan karamin bakin nata gaba tare da murgudawa. ”wai meerah meya faru?, dasu waye kuma kika hadu bayan mun jiyo ihunki daga can cikin park din, kafin kuma gudunki ya biyo baya?” Hayatudden ya tambayeta disha kuwa da mardiya in banda faman sauke ajiyar zuciya babu abinda suke aikin yi. ”Hmmmmm kude Ku bari da masu kidnapping mutane na hadu, ihu na kuma da kuka ji kidnapping nawa suka so yi Allah kuma ya kubutar dani” Da wata kafurar harara mardiyya ta bita tare da furta. ”Dama sun dauke kin Wllh da an rage mugun iri” Wani Dan banzan kallo meerah ta watsama mardiyya tare da fadin ”Nifa idan na Rena kasuwa ko sautu bana mata, haka idan akace mutum kwakwalwar kifi gare shi to bana tayawa bare nima na samu nawa rabon na toshewar kai!” Ta fadi tare dajan wani mugun tsaki. Fadane ya so ballewa tsakanin mardiyya da meerah amma dai Allah yaso be farun fa. Ta hanyar shiga da hayatudden yayi. *AK* Wuraren 4:30 na yamma yatashi awahale domin samma ya manta da batun ganawar da akace zaiyi da kamal Rano. addu'an tashi daga bacci yayi kafin ahankali ya sauko daga saman clean royal bed nashi. juyawa yayi ya kalli agogen dake bed side nashi yaga karfe nawa ne yanxun, ganin shida saura ne ya sanya shi tashi a hanzarce tare da nufar kofan bathroom ya shiga, wani irin hadadden babban bathroom ne mai hade da closet an raba wajen part biyu bangaren dama wani irin hadadden closet ne komi na wajen blue and white ne, ga kaya kala kala dake jikin hanga ga kuma yar stool a tsakiyar wajen sai bangaren haggun kuma koface wacce bayi ke ciki bude kofan yayi ya shige bayan ya zame kayan jikinsa ya zira bathrobe. Yay kusan 30 minutes kafin yafito daga bathroom din sanye da wasu lafiyayyun Riga da wando sai yar gadon wato pcarp daya daura gashin nan dake walkiyar kyau da baki ta zuba har kasan keyar.sai nose mark da bakin safa akafanshi sai uban kamshi yake, jinginar da kanshi yay ajikin bangon dakin kafin ya dago kai ya dunkule hannu ya daki bangon dakin da karfin bala'i yana tsaki ganin hoton fuskar wannan fitsaratun a cikin kwayar idonsa tana yimay rashin kunya. ”damn it” ya fada fuskan mace bai taba tsayamai arai kaman na yarinyar nanba but why?! Kiran sallan dayaji daga masallacin anguwar ne yasa ya mike tsaye, wasu tausasan slippers ya zira da sauri ya bude kofa yafita daga dakin, yana sakkowa arms yayi saurin mikewa sauran kuma suka rufa musu baya zuwa masjid danyin sallan magrib. Basu dawo ba saida akayi sallan isha'i dama kuma al'adan shine baya dawowa daga masallaci idan anyi sallan magrib, saida wani kwakwkwaran dalilin. Kai tsaye stairs yahau ya bude kofa ya shiga dakinshi mayar da kofan yayi ya rufe harda saka key ya jingina da kofar yana sauke ajiyan zuciya,ahankali ya daura hannunshi kan heart dinshi da duk single beat remains him of her in his arms, ahankali ya daga kai ya kalli plain sky blue chiffon curtains din dake jikin babban window dakinshi dake kadawa sosai sakamakon iskan da akeyi na hadarin da yama samaniya kawanya ta

Table of Contents

Chapters

54 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54