Skip to content

Chapter 43

Chapter 43

Mikiya Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

mata tare da fadin. "Saidai kuma kinyi kuskure domin dishan tazo nemanki itama tama jima anan din, don haka ina kikaje DIDI!?" Anne ta sake jeho mata wata tambayar. "Zamu fita wani aiki ne dama shine da bata zo na tafi" "Kuma ita karyar ta miye da kai tsaye kika gaza fadamin?" Wasu hawaye ta share amma kuma sake zubowa suke yadda annen ta tsareta da ido ma shi kadai firgitata yake. Haka dama anne take zakayi wasa da ita amma kuma bata karbar no nonsense,sai kuma annen ta sake dubanta a nutse cikin tsantsar kulawa domin ba ta lura ba iyaka tsoron tuhamar da tay mata take gani dangane da Didinta ba. "Ki dauke tamkar babbar aminiyarki, yayarki kan uwarki kana ki dube ni a matsayin mahaifiyar da baki da kamarta, ki fadamin meke damunki?, domin na lura tunda wancan abun ya faru mood naki ya sanja sosae. Idan har bakiji tausayina a matsayina na mahaifiyarki kin fada min damuwarki ba wanne hali kike tunanin nizan shiga? Karkiji tsoron komai ki fadamin komai din da yake faruwa da rayuwarki MARYAMA" Kife kanta tayi akan kafafun annen domin ta yarda kafff duniya bata da ya mahaifiyarta. Komai na labarinta da Ak bata boye mata har dauketan da yayi da irin yadda take ganinsa ya kwamushe mutane. Har zuwa yau data sake cin karo dashi wanda ita ko a ranta bata taba kawoma ranta cewar shi ne ba.... Kuri Anne tayi da ido tana kallon didin nata kawai tama rasa ta yadda ya kamata ta fara, cannn taja wani numfashi kadan tare da duban meerah din ta fara jeho mata tambayoyi tana bata amsa ita kuma. Haka harta ta bata shawarwarin dasuka kamata duk da ma ita nata ya kusan xuwa karshe domin suna cikin satin biki ne tsulum tsulum. Dama kuma daga yau din Anne'n tayi niyar hana abarta fita domin killace ta bata gatan da ake bama ko wacce ya idan za'ai aurenta. Duk wasu hidinduminta suna a gidan hajiya ummah na a gidan kuwa yadda Kasan ba biki za'aiba haka gidan yake domin ko tada zancen ba'ayi. Ba danma wannan rikitacciyar tsohuwar kakar tasu tazo ba da itama kanta har mantawa take da wani zancen aurernta. Amma itama da biyu tazo yau kwanaki uku kenan domin bata kaunar Annenta sammmm acikin duka matan baffanta ita kadai tafi takura mata sa'ar annen ma daya da take da tsare gida bata daukar wargi ko wanne iri ne kuwa daga wurin ko wanne mutum. Shi yasa sau da yawa matan gidan ke shakkarta yadda kasan irin jinjn saurartar nanne ke yawo a jikinta haka take. Ita kanta meerah din wani sa'in kawai kallon annen nata take. Nan anne ta bata shawarwari sosea kuma taji dadinsu tare dajin nutsuwa ta musamman. Don duk wannan tsoron saita nemasa ta rasa Lallai sai yanzu ta yarda da wannan karin maganar ta bature Na *_A problem shared is a problem solved*_ Sai gashi tun ba'aje ko inaba komi yazo mata da sauki. "ALHAMDULILLAH!" Meerah ta fadi incheerfully. ★★KANO★★ Yau kwanakin su baffafofin kamal hudu a kuma yaune suke shirin komawa. Amma sai baban mariya yazo da batun kawai su tsaya a daura Auren dansu a gabansu, da sunso kin tsayawar saida kamal din yayi magana kana suka yarda zasu tsaya a daura auren. Bayan sun sake kiran dangi sun sanar musu wohoho zokaga yadda ake bidiri a dangi nan fa mata da maza suka ringa yowa tururuwa suna dannowa kano gidan kamal. Sunce shima sai sunyi may auren gata irin na ko wanne da, Wasu a gidan kamal din suke wasu kuma a gidan baban mariya aka sauke su. Da yamma kamar yadda baban mariya ya bukata aka daura auren KAMAAL SURAJ RANO da amaryarsa MARIYA USMAN SHEKA akan sadaki dubu dari da hamsin. Akwatuna kuma daga baya zaiyi kwasam saiga abinda ya kusan gigita duniyar kamal domin ga sanarma Ak a kurarren lokacine don besha ma zaiga sakon shiba. Amma sai gashi ya niko gari tun daga lagos zuwa kano dake dama ya taba zuwa sau daya bayan Shi kamal din ak din ya kirashi abujan nan da yaje.. Shi da kansa ya amsawa kamal auren mariyan ya kuma hada musu party dinner a wani katon holll. Ya kuma turama kamal din zunzurutun kudi har million biyu. A daren yabi girjin dare ya koma wajen sha daya da wani abu yabar kano shida arms, Washe gari aka sake sabon biki kana mazan suka tafi sauran maran kuma sai an gama shagulgulan bikim kafin su tafi. A wata sabuwar anguwa kamal yasai gida yabar wannan baban mariya ya aika a gano gidan don su gane girman gidan saidai abin mamaki kamal ya zuba komai babu abinda bai zuba musu ba. Dade da kayan kitchen ya zuba musu wasu sai yan tsitstsinen da ba'a rasa ba. Umayma harda kukan ta a lokacin da danjinta dana malam ke sanar dasu abinda kamal din ya musu. Dama yar gudun mawar da yan uwa da aboka nan arziki suka hada musu zasuje su mata kayan dakin, kayan kitchen kuwa dama basa lissafi dashj lallali kamal ya zo busu da wani babban al'amarin da bazasu taba mantawa dashi ba, zuwa yamma aka shiga jibje musu wasu shegun akwatuna masu shegen kyau da tsada. Wannan aikin nabban abokinsa ne ZAYD suraj. Wanda wani aikine ya taba hadasu a wata cout akan shariyar wata yarinya da akayi raping nata kuma kamal ne dan sandan daya jagoranci case din har zuwa sanda yayj winning ta hanyar mikasu ga cout din da anan ne suka hadu da Zayd din wanna shine wanda ga karasa aikin ta hanyar jajircewarsa harka aka yaron senetor na garin kano a prison. Kunsan magana ake ta sarauta a wurin. Akwatuna saida aka sauke musu set uku ko wacce da kolonta. Yaufa ake yinta dan fulani yaje asibiti dubiya an bashi lemo da kaji akace kado fito yace ahhhhhhh ai nikam naga makwanci. To hakace ta kasance da iyayen mariya Hakika duk wanda yayi hakurin dafa dutsi to asannu zaisha romansa. Sunci wuyar sun shanye dakan da dukan sai gashi sama taka allah ya basu dami a kala. Duk wasu abubuwan al'ada suma saida sukama kamal suka mika a hannun danginsa. Dare nayi aka mika amarya mariya wa gidan mijinta a yanzu kamaal suraj rano. Sosae tasha amarya mariya tasha kukanta kasancewarta mutum bame hayaniya bane ya sanya sammm babu wani batun tada hankali akan maganar auren. Haka dai al'amura ke wakana cikin kwanciyar hankali komai yaci gana da tafiya. ★★Lagos★★ Gidansu salman kuwa mahaifiyarsa da yayar mahaifiyarsa ganin dai tabbas auren na shirin tabbata ya sanya hankalinsh tashi matuka, yanzuma zaune suke itada yayarta me suna Aunty mariya sai kuma yarta sury idon nan yay hulu hulu dashi nashan kuka. Ran kowa a wurin a bace yake, cikin kuka sury ta rarrafa gaban mom salman ta kama kafafunta fadi take. "Mom don allah ki taimaki rayuwana wllh ni salman nake so shi kadai nake kauna a matsayin abokin rayuwata! Mom taya kuka min haka bayan kunsan cewar ni shi kadai nake so" Ta fadi tana sake rushewa da wani kukan Salman da shigowarsa kenan yaja tsaki "Mtsss ni kuma uban wa yace miki zanso mace kamarki babu baya babu

Table of Contents

Chapters

54 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54