Chapter 32
Chapter 32
ta fadi cikin kwarin gwiwwarta. girgiza kai kawai meerah tayi wato kudi masifane kuma daudar duniya. ta furta a cikin ranta tare da duban fatiman ta furta. ”Karuwanci yanzu shine sana'ar? dan Allah fatima ki dawo madaidaiciyar hanya duk wani mutum indai masoyinki ne na gaskiya fatan shiryar ubangiji zai nemar miki, bawai ya famfa kiba wllh zina masifa ce fatima, Annabi bafa cewa yai muyi zina ba cewa yayi karmuyi zina mu kuma nesanta kanmu daga duk hanyar da zata hada mu da zina!. ma'ana karmu kusanceta mezesa ki kira wannan da sana'a?” yatsine fuskarta tayi alamun gajiyawa da qosawa da zancen ta furta ”Meerah banida wani zabin daya wuce wannan idan na dena neman kudi da jikina ke zaki ciyar damu nida mahaifiyata da yan uwana? Ki sani wllh meerah ina sane sosai da haramcin aikata zina amma wllh bazan bari mu rayu da yunwa ba nida yan uwana” Dan lumshe idonta tai tana me qoqarin hana qwallan idonta zubowa. "Fatima ki barwa haramcin nan don Allah na rokeki, Kuma fa karki manta na gari basa taba karewa a cikin duniya duk kuwa irin lalacewar da zamani yayi” ”Fatima muje wata maganar kinga ma wani ana kirana wani alhaji ne yake son tear leather a ledar ta, da zaki yarda ai dana jonaku Wllh ki kwashi rabonki kema” Shiru kawai meerah tayi domin fatima tayi nisan da batajin kira,wannan ya sanya ta Jan hannun Raiha sukayi gaba abinsu. Ganin lokaci na tafiya har Isha'i na shirin kawo kai. Tafiya suke amma gaba daya cikin kunan rai take tana mamakin wannan rayuwar da wasu suke ganin hanyarsuce madaidaiciya.Tasan a yanzu haka da za'a kasa Mata kashi dari da kyar a samu kwararan talatin na gari, towai meye matsalar? Daga kuma ina abun ya samo tushe?, Rashin hakurinmu?, Rashin kai zuciya nesa da kuma son zuciyoyinmu. A fili ta furta ”Ya Allah ka mana maganin dukkan matsalolin da suke kewaye da rayuwarmu, ka Zama gatan Mara gata, ka sanyaya zukatan bayinka ya Allah ka kuma nesan tamu daga cikin gurbatattun bayinka” Haka da taci gaba da tafiya cikin wani irin sanyin da jikinta yayi. Haka sukayi tafiyan babu armashin komai, Ko a gidan hajiya umman ma sama sama suka gaisa suka bata sakon suka dawo gida. *🦅 MIKIYA 🦅* *~We want an end to oppression💪~* https://chat.whatsapp.com/GiLzmY90dz17bRbw5yMYBg ____________________ *MARYAM NASEER* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* Page 33&34 Bayan dawowansu dake lokacin anyi isha'i sallar tayi kana daga baya kuma tayi wanka. Shirin bacci tayi bayan tayi nafilanta kamar ko yaushe,kwanciya tayi tare da daukar wayanta Deta'nta ta kunna ta shiga WhatsApp nata, sama sama tadan galli status na mutane, sai itama ta koma wurin status din tare da rubuta. *_BEAUTY IS NOTHING WHEN BRAIN IS EMPTY_* Tare da sanya emoji na hamma. Har zata sauka sai kuma taga anyi tagged nata a group nasu na *Jonalist empire's* Shiga tayi hayatudden taga yana tuna mata da fitan da zasuyi gobe da hantsi zuwa wani park. Da _OKay don't worry Allah ya kaimu_ Ta bashi amsa tana sauka. *district Abuja* Yana kwance akan irin wannan doguwar kujerar me kama da gadon nan. Lallai sai yau na sake tabbatar da kamannin AK da dirin jikinsa da wannan actor'n Indian film din suke tasananin kama wato *PRABHAS* Sai naga fuskan shin ma kusan nace a ga nina ma yafi *PRABHAS* din ma haduwa da hasken fata the guy is faultless and flawlesss and very cleaning skin. Sanye yake cikin wata Riga Latvia Lithuania Luxembourg da wando na kamfanin dior hormes white shirt and a very soft white, masu tsananin taushi da kuma laushi. Suman kanshi is silky black and shining gashin nan kwance har keyarsa inda ya masa wani dan iskan aski. A hankali ya shiga ware lumsassun idonsa dogayen eye lashes dinsa me suka shiga motsawa, harya samu ya bude idon a kasalance. He loves keeping straight face din na a matse kamar kullum, Nikam zan iya rantsewa ban taba ganin mutun mai son bata rai kamar AK ba. well pampered yatsun hannun shi da suka ji gyaran manicure ya lankwasa su suka bada sautin *BASSs* kai Wllh duk inda ake Neman cikakken namiji Ak shine katt kuma babansu, don he's goddam porschy sosai yaji wankan aji da Hutu hadi da haduwa. Door bell daga taba ne ya sanya shi dakatawa daga niyan nufan bedroom da yake, cikin muryan nan kasa sosai ya furta ”come here" Arms ne ya shigo shima cikin nashi shigan na bakaken suit, zama yayi tare da kaida ak din a takaice. Shima zaunen ya koma tare da daukar woyansa yana latsawa. ”Already flight namu zai tashi ne da 4:00pm” ”okay alright” Ya fada tare barin palon zuwa bedroom, shower ya sakarma kansa. After 45 minutes sai gashi ya fito Sanye da bathrobe sky blue a jikinsa, daya soft hannunsa kuma dauke da wani towel yana sharce gashin kansa. Soft fatar Jikinsa sai digar ruwa take, jikin nan yadda kasan kwai da madara don santsi da daukar I do. Cikin be ko wanne lokaci lokacinsa ya soma shirya kansa, babu jimawa ya fito zuwa harabar hotel din kai tsaye parking space ya nufa. Domin yana da wata fitane kafin jirginsu yabar Abuja. *Meerah POV* Dake yau suna ta fita baccinta tasha sai sha biyu saura kana ta fito sanye cikin Arabian jallabiya ta mata. Anne tama sallama 1k ta bata tunda tasan inda suka nufa yau. Adda'ar samun nasara ta data da kuma binta da fatan alkhairi. Haka ma saida ta shiga wurin baffanta shima sallamar tamay. 1k ya kuma bata sai ta fada masa anne ta bata. Shima adda'ar ya mata ta fito kai tsaye gidan jaridarsu ta nufa. A bakin gate din gidan jaridar suka hadu da disha da hayatudden sai mardiyya, wacce take faman banka mata harara. Ita kuwa disha tama manda da batun woni fada da suka yi jiya, da gudu ta karasa suna rungume juna. ”kai masha Allah dear yau kinyi kyau sosae" Murmushin gefen baki meerah ta saki tana furta ”zaki farako” ”Kar dai Ku sanya mu yi leet oya Ku shiga muje” Hayatudden ya fadi yana bude musu motar. Da sauri mardiyya ta bude gidan gaba ta shige. Oho itakam ma merrah batasan abinda take ba. 12:00 suka Isa park din da zasuy aikin ranar akan wani kusa. Shiga ciki sukayi bayin sun nuna I d card nasu. A inda ake faka motoci suka ajje nasu, kai tsaye A cafeteria suka yada zango order juice sukayi tamkar a gaske. juyar da kanta tayi tana kallon reception din park din yanda iska ke kadawa kaman za'ayi ruwan sama, flowers din reception din sai kadawa suke suna making sounds, wani iri taji zuciyarta namata da bazata iya cewa exactly ga yanda yake mataba. wani iri iri dai haka takeji kamar ana kallonta hakan yasa ta juyo dakanta adan hankali Duk da yadda take da dakakkiyar zuciya hakan be hana gabanta faduwa ba. Wai me wannan mutumin yake nema da itane da yake ta faman bibiyar rayuwarta haka. ”Naga kinata kallon waje meerah ko wani abune yake damunki, gashi ko juice din baki shaba” Hayatudden ya katse mata tunani. Saurin dawo da nutsuwanta tayi tana furta ”babu komi kawai banajin sha ne”
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54