Skip to content

Chapter 28

Chapter 28

Mikiya Book One Complete Hausa Novel 1,212 words 0 views Progress saved
Download Book

fito zuwa balcony na room ɗin. Hannuwansa zube jikin wandon jeans ɗin. Wurin ba hayani sai sassanyar iskan dake kaɗawa mai cike da tarin ni'ima sakamakon hadarin da yayima sararin samaniya ƙawanya.Hakan yasa garin ya yi luf ga dukkan alamu akoda yaushe a ko wanne loƙaci ruwan sama kan iya sauƙa. Yana zaune kan Chiar silinder caution ɗin dake cikin balconyn Wata ƙatuwar Toyota land cruiser Prado ta shigo harabar wurin fara ce kal sai faman kyalli da ɗaukar ido take yi.Wurin da aka tanada dan adana motoci motar ta parker,cikin slow mamallakin motar ya yi parking. Kasancewar glass ɗin motar tinted ne yasa ba'a iya hangen mai mamallakin motar har saida ya fito.An ɗauki tsawon 10 minutes kafin matashin dake draving motar ya fito. Back sit ɗin motar ya buɗe nan kuwa sai da aka kusan 20 kafin wani siririn matashin saurayi ya fito izza. Ƙafa ɗaya ya fara zirowa ƙasa sanye da halp cover shoe white color mai adon Stone a jiki irin na sarakuna.Cikin loƙaci ƙalilan ya fito da gangar jikinsa,Dogo ne sosai amma yana da ɗan kauri jikin shi a murje yake alamu na yana cikin hutu da jin daɗi,yana da hasken fata amma ba sosai ba.Farin yadin boyal ne a jikin shi mai ɗauke da ƙananun zane,wanda ya sha ɗinki irin na samarin zamani,sai Black agogo daya ɗaure a tsintsiyar hannun shi na dama dashi,a jikin siraran fararan yatsun shi kuwa ya saka white ring mai kyau a karamar yatsa.kanshi bai saka hula ba sai baƙar sumar shi data sha gyara gwanin sha'awa kamar ɗan India. kyakkyawar face na mai ɗauke da manyan dara-daran eyes balls ɗin da suke kamar madara. A hankali ya rufe manya eyes ɗin shi yana sauke ajiyar zuciya.Tare da furzar da iskar bakin shi.Manyan wayoyin shi dake riƙe a hannu ya kalla ga dukkan alamu ƙira ne ya shigo. Ɗan siririn tsaki ya ja wanda idan ba kana gaf da shi ba ba lallai ka ji ba. A kunne ya manna woyar cikin fusata murya a daƙile ya furta. "Zanci ubanka Wllh Najeeb akan takura min da kayi!, Wllh idan ka tunzirani zan fasa maka visa'n naga uban da zakay ok” Datse woyar yayi Cike da taku irin na zaratan maza ya fara taku yana nufar cikin hotels ɗin.da sauri driver'n ya mara masa biya da system nashi da dayar woyarsa. A room na daban shima ya sauƙa tare da kayayyakinsa suka zube akan lafiyayyan gado. ZAYD SURAJ kenan ɗa ga Sarkin kano mai martaba SURAJ SUNUSU SHUREIM. *AK* Cikin bacci yaji ya soma jin vebration na woyarsa, da ƙyar ya iya buɗe lumsassun idonsa. Idanu ya tsurawa screen ɗin wayar dake ta faman ruri, tamkar me nazartar wani abu haka ya tsira wa woyar kaifafan idon shi. Duk da cewar yasan ZAID bazai ƙirasa haka kawai ba, lallai dole saida wani abu haka nan ya tsinci kansa da faɗuwar gaba. Hannunsa ya miƙa da niyar ɗaukar wayar saidai kafin yakai ga ɗauka ƙiran ya katse. Ɗin Jim yayi yana me tunanin bin ƙiran saidai sanin da yayi cewar mai ƙiran nasa zai sake ƙira ne yasa shi sauƙe ajiyar zuciya tare da fesar da numfashi. Anutse ya tashi zaune yana me tunani acikin zuciyarsa, haka nan Idanunsa da suka dan ɗan tara ruwa ya lumshe saboda tunowa da PAAH tare da Momma'n shi da yayi. ”ZAID EMAAR KUWAIT” Ya furta a saman laɓɓansa woyar ya jawo tare da mannata da kunnensa. Daga cennnnn Zaid cikin yanayin sanyin jiki ya furta. ” ABDOUL-MALEEK PAPA?” Zaune ya tashi da sauri amma a zahiri ba saurin yayi ba shine a ganinsa yayi saurin. Cikin fitar sautin da yayi low sosae ya furta. ”Why? Where is my PAAH” Shiru daga cennn Zaid yayi, Ak kuma jin shirun Zaid shine ya sanya shi furta. ”Ina PAAH yake you will die ko? ka buɗe baki kamin magana Zaid” Ya ƙarashe cikin sautin tsawa “Ko ɗaya bai mutu ba anyi poisoning nashi ne agant!, wannan tafi ko wacce iriyar gubar da aka saba poisoning nashi da ita. Domin wannan da wuri zata iya zama sanadiyar rasa shi acikin loƙaci kaɗan, matuƙar akayi wasa to tabbas zamu iya rasa rayuwar PAPA gaba ɗaya” Wani irin sakur zuciyarsa maganan da Zaid ya faɗa mishi yayi, yana jin daidai yake da bugun zuciyarsa acikin kunnuwansa, haka yake jin maganganun na yankar zuciyarsa. Saurin fusgo numfashinsa dake ƙoƙarin kwacewa zuciyarsa yayi ta hanyar furta kalman. “Innalillahi Wa Inna Ilaihirraju’un!!!” da sauri saurin dake tafiya da gudun bugun zuciyarsa ya furta. ”what? My papa his under incapable survive in the world at this condition? oh god tell me the Truth I'm very dangerous twin!” Jin yadda lokaci daya yanayin dan uwansa twins dinsa jininsa ABDOU-LMALEEK AK KUWAIT ya sanja ne ya sanya. Ya shiga kontar masa da hankali, ganin kamar hankalinsan na kwanciya zai yi bane ya sanya ya shiga fada masa kalma daya takkk. Wadda bansan ko wacce kalma bace itane ta nutsar da AK da kuma lurar dashi...... *BY AMMEY LAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* *~We want an end to oppression💪~* https://chat.whatsapp.com/GiLzmY90dz17bRbw5yMYBg ____________________ *MARYAM NASEER* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* Page 29&30 # ROMANCE # BLACK MONEY # DEEP # BEST LOVE 🤍🔥✅ *KUWAIT* Zazzau ne suke a falon maza da mata kowa ran nan a haɗe wasu ido yayi ficin ficin. Mommah dake dab da ƙafafun MOH JIDDO idanunta sun kaɗa sunyi jazur tana sanye da Alkaybba hannunta rikeda tissue dakuma charbi tanaja, sai wasu daga cikin manyan fada irin su Waziri, Wambai, Makama dakuma Sarkin dawaki, chan kuma saiga wasu Manyan dattawa maza guda biyu sun shigo sun zauna suma, dan faɗuwa gaban Mommah yayi dan haduwan mutanen nan wanda bayan sarki sune masu fada aji a fadan ƙasan Kuwait kasan babban abune, ƙarasowa suka yi tsakiyan ɗakin sannan suka sami waje suka zauna Zaid ne ya ɗago rinannun eye's nashi tare da duban MOH JIDDO cikin daƙushashshayar murya yace “ JIDDO kene kika aika akirani”? Girgiza kai JIDDO tayi kafin ahankali tasa tisssue saman fuskanta tashare hawayen tasss sannan tace “Wambai ne ya aika kazo zaka ƙira musu wannan tantirin ɗan uwan naka” dasauri yadagokai yakalleta tare da sauran jama’an ɗakin dake kallonshi yace “tooh” anatse waziri ya furta “ƴan uwanka duka sun iso na kusa dana nesa” Sai kuma ya ɗan yi shiru a tare dukansu ƴan ɗakin suka zubama waziri ido duk kuwa da sunsan YARIMA MALEEK zai ambata amma hakan bai hana su binsa da ido ba. “YARIMA ABDOUL-MALEEK fa”? Ya faɗa wanda iyaka ambatar sunan shi da akayi Saida zuciyoyin wasu daga cikin su ya buga. Adan hankali Zaid ya sauƙe ƴar ɓoyayyen ijiyan zuciya yace “naƙi rashi ba adaddi bana samunshi” salati Al-hussein ya saki cikin babban sauti sosae ya shiga furta “Ban taɓa ganin gantalallen yaro irin ABDOUL-MALEEK ba ohh Allah Ace mahaifinka na ahalin Rai ko Rayuwa amma baka ma san a halin da yake ba” MOH JIDDO ce ta tare shi da faɗi ”Dama fa ba jinin MARYAM bane yake yawo a sassan jikinsa, kaima da ɓata baki kake Wllh hussein” cikin murya mai laushi wamzai ya furta "MOH JIDDO adai yi haƙuri muna a halin ciwo ne" ya faɗa yana rusunar da kansa ƙasss

Table of Contents

Chapters

54 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54