Skip to content

Chapter 66

Chapter 66

Abari Ya Huce Book One Complete Hausa Novel 619 words 0 views Progress saved
Download Book

watanni biyu dan Pretoria. Bayan sun dawo ta nemi chanjin wajen aiki zuwa jami’ar Abuja, ba da son ranta ba, sai don ta samu kasancewa full-time da mijin ta. Abin son ta. Uban ‘ya’yanta kuma abin kaunarta; Dan Abdurrahman Gaya. A shekarar ne kuma akayi bikin kaddamar da Amiru Abdurrahman matsayin gwamnan CBN, bayan gwamna mai ci a lokacin yayi ritaya. Ba don shekarun shi sun kai ba, sai don kwarewa da sanin makamar aiki da dimbin tagomashin cigaba da ya kawowa Central Bank of Nigeria a matsayinsa na tsohon ma’aikacin World Bank. Shima Uncle Junaidu ya samu ‘promotion’ zuwa ‘chancellor’ na jami’ar Bayero bakidaya. Zumunci da aminci bai taba yankewa tsakanin su ba. Shekara na zagayowa Mairo ta direwa Hajiyar Amiru wani saitin 'twins' din data zabi a bawa sunan (Ilham da Sagir) kannen Uncle, don bazata taba mantawa da kaunar da Ilham ta nuna mata ba. Uncle yaji dadi kwarai kuma ya kawo Ilham daga Wales don kawai taga takwararta. Farin cikin Hajiya Aisha abin ba a cewa komai. Dina ma ta sake samun Hurairah (Hure) bayan fidda rai. Amina ta samu Atiku, Ikhlas ma matar Uncle ta sake haihuwa. To haka Nabilah duka hayayyafa suke kamar kaji, sai mu ce Allah Ya raya, kuma Allah Ya kara dankon zumunci. MASHA ALLAHU LA-KUWWATA ILLA BILLAH... Maman Safah da Marwah ce....ke cewa. Sai mun hadu a sabon littafin YAKANAH cikin yardar Maiduka. Dandano Daga Yakanah Karfe goma sha dayan dare garin kano yayi tsit, sai iskar hunturu dake kadawa. Malam Ja’afar ya dauko tabarmar sa ya shigo cikin gida daga soron kofar gida. Zai gitta ta dakin Fati ya jiyo sheshshekar kukanta. Ya dakata, ya dago labulen yana kallonta. Tana zaune akan darduma ta kunshe fuskarta cikin hijabi sai kuka take. ya karashe shigowa cikin dakin yace “Fadimatu kukan me kike yi? A razane ta cira kai ta dube shi idanunta jawur sun yi luhu-luhu alamar tayi kuka har ta gode Allah. Malam Ja’afar ya zauna a wata ‘yar kujera dake dakin yana fuskantar diyarsa. Ta share idonta da hankici, ta ja shashsheka kafin tace “Baba babu komai” ya jima yana kallonta sannan yayi murmushi yace “kina tuhumar mu dayi miki auren da baki so, auren mijin ‘yar uwar ki. Ki yi hakuri, alheri muke nufin ku da shi, ba zaki gane ba sai nan gaba. Idan kun gano gatan da muka yiwa rayuwarku” Fati tayi shiru tana sauraron babansu. Taga wannan itace damarta ta karshe. Daga gobe za’a zarga mata igiyoyin wanda baya sonta. Ta kai kanta kasa tana kuka sosai tace “ku yi min alfarma Baba. Baba baka taba sa ni in yi wani abu na shallake maganarka ba. Amma a wannan karon ina so ka dubi hujjoji na. Baba. Dr Sulaiman baya so na, baba Dr. Sulaiman yafi karfi na. bani da ilimin da zan jera da shi a matsayin matarsa. Baba sulaiman bazai taba son wata ba bayan son da yake yiwa yaya Hadiza. Baba kune baku sani ba, amma Dr. sulaiman ya tsaneni ban san laifin da nayi masa ba. Ban taba gaishe shi ya amsa ba, haka bai taba kallona a matsayini jinin Hadiza ba balle yayi la’akari da wannan ya kaunace ni. In dai don ‘ya’yanshi ne, ai nima ‘ya’yana ne…zan cigaba da rike su ba sai na zama matarsa ba……” Ya ce “Amma zaki zama matar wani ko? Kuma babu wanda zai aureki da zugar ‘ya’yan yayar ki. naji hujjojin ki Fati, amma nima ina so in tambayeki “wane abu ne Hadiza take da shi wanda ya kaita ga matakin zama matar Babban likita irin Sulaiman???? Tana ‘yar talakawa kamar ki??? Mu biyo Fati da Babanta a littafin YAKANAH yana zuwa bada jimawa ba!!!! __________-_TAKORI

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66