Chapter 65
Chapter 65
shi. Ya amsa yana duban ta sosai, ganin yadda ta ramar da kanta cikin ‘yan kwanaki kalilan saboda damuwa. Bai nuna mata komi game da zuwan Junaid da Amir ba, tambaya ta farko da ya watso mata ita ce. “Mairo maza biyu za ki aura ne???” Ta cira kai da sauri ta dubi Baffanta, ya girgiza kai ya ce, “Yo maza biyu mana? Kin amshi maganar Junaidu, an gama komi sai shafa fatiha kadai ya rage, sai kuma ki turo min Alh. Abdurrahaman da kansa ya zo bikon ki? Sannan shima Amiru ya zo, dukkanninsu da rokon a maida aure. To dukkansu akwai mutunci da ganin girman juna tsakanina dasu. Don haka bana bayan kowa, zabi yana gare ki, kamar yadda shari’a ta baki dama. Ina so ki gaya min wanda kika fitar ni kuma ranar da na sanya ba zan daga ba zan daura aure”. Kanta a sunkuye ba ta yi magana ba, har sai da Baffa ya gama yana sauraron ta. Ganin ta ki yin magana ya ce, “Kefa nake saurare Mairo”. Daga can kasan makoshinta ta ce, “Baffa ni bani da zabi a cikinsu, kamar yadda ka ce sharia ta bani damar in zaba, ni kuma na baka wannan damar, ka daura da duk wanda ka ga ya dace. Duka ina son su ina kaunar su, don haka ba zan iya zaben daya a cikin su ba”. Baffa ya girgiza kai yana murmushi. Autar Inna Hure, bai san sanda zata daina yarinta ba!. Ya ce, “To shi kenan, tunda haka kika ce, na kuma gode da wannan GIRMA da kika bani, ya nuna min cewa kin amince ba zan yi miki zaben tumun dare ba. Da fatan duk wanda na zaba miki a cikinsu za ki yi min biyayya shima ki yi masa, ba tare da an tsaya yin wasu tone-tone da kwakulo laifin da ya riga ya shige ba, za ki zauna lafiya dashi har karshen rayuwarmu”. Kanta a kasa ta ce, “Na yi wannan alkawarin Baffa”. Ya ce, “To tashi ki koma kan aikin ki, Allah ya yi miki albarka”. Cikin zuciyarta ta ce, “Amin”. Ta taso ta fito kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki. Daga Amiru har Junaid ba ta kara jin duriyar kowa ba. Ta bi shawarar Nabilah, da ta ce dukkansu kar ta neme su ta rabu dasu. Sai ana i gobe daurin auren da ba ta san da wa Baffa zai daura ba a cikinsu. Text din Uncle Junaid ya shigo cikin wayarta da misalin karfe uku na sulusin dare. Ta zaro wayar daga karkashin filonta, hannunta na rawa ta duba, ga abin da ke rubuce. SAKON UNCLE JUNAID GA MAIRO! “Marriage is much more important than mere relationship. It’s the root of all family tree. Any mistake in sowing the seed will be disastrous.... a mature seed has better chances for germinating than an immature one.... A garden close to one’s home has to be watered and tendered than that which is very far away................... -Mai son ki. (wato aure yafi muhimmanci fiye da dangantaka kawai. Domin shine jijiyar bishiyar iyali gaba daya, don haka hadari ne babba asamu kuskure wajen dasa wannan bishiya.... kosashshen iri zai fi saurin yado fiye da talalabuwa.... lambun da yake kusa da gidan ka zaka fi bashi ruwa da kulawa, fiye da wanda yake nesa.............). Ta karanta ya fi cikin carbi, kafin ta fahimci me sakon Uncle yake nufi. Yanzu ne ta fahimci ashe duk sakonnin nan da ake turo mata tana Michigan da ‘logo’ na hular ilmi, ashe Uncle Junaidu ne. Ta kifa kai cikin filon ta, tana kuka mara sauti. Kukan tausayin Uncle Junaidu! A lokacinda ta fahimci Uncle Junaid ya sadaukar da soyayyarshi ga aurenta da ‘ya’yanta..... Ta yadda har ya kira alakarsu da ‘mere relationship’. Ita ma ta yarda ta amince AMIRU SHI NE ZABIN ALLAH, ba zabin zuciyarta ba......!!! [8/20/2019, 06:30] Meema: Daga kowanne bangare ba su samu matsala ba, sun samu kwarin gwiwa daga Baffa, Yaya Habibu da Alh. Abdurrahman Gaya. Wadanda burinsu kenan. Hatta Hanan wadda ke da 'ya'ya biyu a lokacin da mijinta Ramadan ta samu halartar walimar maida auren Dr. Mairo da Amirunta, Amina da Uncle Junaidu, wadda aka gabatar a ranar asabar, juma'a, ashirin ga watan maris, daruruwan jama'a suka shaida daurin auren Mairo da Amiru a karo na biyu, a kofar gidan Alh. Abbas mai goro. Wannan aure ya ga kusoshin ilmi, daga Kano da wajenta, da daukacin jami'o'in Najeriya. Furofesoshi, kwamishinoni da daktocin ilmi, abin ba a cewa komi. Daga Mairo har Ameeru babu mai ra'ayin bidi'o'i, dokance suke da a sake mallaka musu juna. Tsohuwar soyayya ce ke aiki tare da taimakon sabuwar soyayya. Ta dankawa Alh. Abdurrahman da Hajiya Aisha jikokinsu kamar yadda suka nemi alfarmarta, sai fatan Allah Ya ba ta wasu masu albarka. Tana nan zaune a bakin gadonta, tana jiran angon wanda ke can yana ganawa da bakinshi, tare da duba agogon hannunta. Rabin awa kenan da fitar Dina, ta fada bayi ta sake sheko wanka mai suna wanka, tunda kuwa ba ta taba yin irinshi a rayuwarta ba. Ta feshe jikinta da 'fehrenheit' da 'cerruti' dinta kamar yadda ya ke a al'adarta. Tana kokarin sanya kayan barci ya turo kofar ya shigo cikin bulalen 'pyjamas' yana rike da wani dan fulas mai tsananin kyau. Kunya ta kama Mairo, kamar bata taba sanin Amirun nata ba, wanda hakan ya janyo ta sanya rigar a bai-bai. Amir ya yi murmushi, ya rausayar da kai ya iso gare ta, ya ajiye filas din hannunshi a gefe, ya dora kanshi a dogon wuyanta. At last! Sa’ar tashi ce a karo na biyu. Gashi ga Maironsa, bayan gushewar shekaru uku kwarara, cikin duniyar kuntatacciyar soyayya. Shikuwa me zai yiwa Uncle Junaidu, ya biya shi a wannan duniyar? Babu, sai adduar Alheri. Kyawawan fuskokinsu suka zahhara cikin mudubin. Dukkansu suka saki sassanyar ajiyar zuciya mai nauyi. Wadda ke cike da godiya ga Allah! Cancarakas! Ya dagata ita da filas din da ya shigo da shi sai 'bed-room' dinsu. Ya zaunar da ita a bakin gado, ya mika mata filas din, ya ce. "Sako ne daga Nabilah, ta ce hannu-da-hannu na baki. Ya zama shi ne cimarmu a wannan daren, sai dai ban san ko mene ne a ciki ba". Ta soma kicin-kicin bude filas din, da kyar ta samu ta bude. Suka bi cikin filas din da kallo dukkanninsu. “Kwadon Rama” ne wanda ya ji kuli-kuli, tumatur da albasa sai kamshi ya ke. Dariya ta kama Mairo, don ta lura Nabilah dai na son a TUNA BAYA…..... ne. Mairo ta soma cin kwadon ramarta sosai, kunnenta kamar ya tsinke don dadi. Ta kusa cinyewa ya rike fulas din, ya rausayar da ido yana yi mata kallon nan nasa da shanyayyun idanun nan nasa, wanda ya kassara kuzarin jikinta. Ya tada wani tsohon al'amari, wanda ya riga ya shude a tsammaninta. Amir da Mairo, suka ce “Takori kauce a nan, yau bama bukatarki”. *** Washegari Daddy yayi kiransu, ya danka musu ‘passport’ dinsu, mai dauke da visar kasashen duniya guda uku; Athens, Amsterdam da Pretoria. Yace da Amir yayi amfani da hutun sa na karshen shekara suje su huta tsayin watanni uku. Mairo bata tashi dawowa ba, sai da guzurin ciki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66