Chapter 13
Chapter 13
su za a karo mata. To sai ga sabani ga tunaninsu, ina ruwan Allah Mai azurta bawa. Mairo dai jeren kayanta ta ke a loka, ba ta kula su ba. Nabilah ta kasa shiru ta ce, "Kausar yau billager ta shigo gari". Kausar ta ce "Ke ina jin 'charity' ne daga (MSS), ba ki san ta shiga MSS ba? Kungiyar 'yan a bamu saboda Allah?" Ita yaran sai suka koma ba ta dariya sabida yadda suka sa mata ido babu gaira babu dalili, ko mai ya yi masu zafi da ita? Allahu A'alam. Bayan bisiting da sati biyu, rannan Mairo ta fito domin yin fitsari da daddare a lokacin Kausar ma ta fito ta tsugunna a bakin rariyar hostel tana goge bakinta domin ta kwanta. Mairo na daga bandaki ta hangi wani mulmulallen abu mai sheki da tsayi na sanda ya nufi Kausar. Ta ware idanunta gabadaya sai ta gane katon maciji ne wanda ake rade-radin akwai a makarantar. Ta yar da butarta ta sheko da gudu dai-dai sanda macijin ya fasa kai, ta angije Kausar tun karfinta ta wulwula ta fada kwatami da baka, abin tsautsayi, sai kulbar (macijiyar) nan ta huce fushinta a kafar Mairo, wato ta sare ta. Kausar ta mike cike da bala'i a lokacin idanunta suka gane mata abin da ke faruwa, dai-dai lokacin kulbar ta sulale tana komawa inda ta fito, ga kuma Mairon da ta angije ta kwance a kasa ba yadda ta ke. Ta daura hannuwa aka ta rafsa ihu, wanda ya ratsa gaba dayan hostel din, student da metron suka fito. Kausar ta ce “macijiya ce ta sare ta.” Ai jin haka captain ta suri Mairo, sauran yara suka bi ta yuuu! Har da su Kausar sai gidan principal ana buga mata kofa. Ta fito a gigice ita ma nan take ta bugawa school doctor waya, nan da nan sai ga ta, aka wuce da Mairo asibitin makaranta, Doctor ta dukufa ga son ceto ranta. Kausar da Nabilah suka kasa komawa hostel ko babu komai akwai tausayin rai a zukatansu, balle ita Kausar da tasan hakikanin yadda abinda ya faru. Nadamar abubuwan da ta ringa yi wa Maryam Bedi, suka shige ta. Ta ji tausayin Maryam matuka, ta kuma tambayi kanta, shin ko wace irin zuciya ce da ita? Irin su Maryam ne masu rama sharran da hairan, babu shakkah ta yi nadama. Nabilah ta yi mamakin damuwar Kausar akan Maryam ta yi yawa, ta kasa ko magana. Ta ce "Kausar kowa ya koma hostel sai mu, ni fa tsoro nake ji". A salube Kausar ta sa kafa cikin dan karamin asibitin ta samu benci ta zauna, ba ta da niyyar tashi. Nabilah ta biyota cikin mamaki, ta ce "Wai me ya faru ne? Ba zaki zo mu tafi ba?" Ta ce "Je ki abinki Nabilah. Amma ni a nan zan kwana". Nabilah ta kama baki, dai-dai lokacin da Mummy Dukku wato principal ta fito zata koma gidanta. Ta hango su Nabilah ta ce, "Ku kuma me kuke a nan ba ku koma hostel ba?" Kausar sai ta sa kuka. Ta matso ta dafa kanta domin ta santa farin sani sabida mahaifinta, ta ce "kawarku ce ince ko?" Nabilah ta yi saurin cewa "A'ah, dakinmu ne kawai daya". Mummy ta lura da kukan da Kausar ta ke sosai ta ce, "Ke kuwa tausayinki ya yi yawa Kausar, alhamdu lillahi dafin bai shiga cikinta ba, kuma Doctor ta zuke shi. Insha Allah zuwa safiya za ta warware, tashi ku tafi dare ya yi sosai". Sai da suka je daki ne Kausar ta ke gayawa Nabilah hakikanin yadda akai maciji ya sari Maryam. Ta ce "Yanzu ni tashin hankalina shi ne, idan ta mutu ban nemi gafararta ba ina zan sa kaina?" Jikin Nabilah ma ya yi sanyi, ta ce, "Allah Sarki, irin su ne ake cewa masu halin 'yan aljannah". Suka yi jugum-jugum har wayewar gari ba su runtsa ba, nadama ta ishe su, sai kuma kaunar Maryam farat daya ta bi zuciyoyinsu. Washegari Uncle ya zo kiran suna kamar yadda ya saba, cike da mamakin rashin ganin Maryama a class don kullum ya shigo idanuwanshi akan wurin zamanta yake. Duk da haka bai fasa kiran sunan ba, har ya zo No. 40, shiru ba ta amsa ba. Ya dago manyan idanunsa ya zubawa Kausar cike da zargi kamar ita ce ta boye Maryaman. Ya ce "dakin ku daya, tana ina ban ganta ba?" Kirjinsa har wani harbawa yake da sauri-da-sauri. Fargabarsa kada ace da shi iyayenta sun cire ta daga makarantar sabida su Kausar. Bakin-cikinsa shi ne yau ace Maryama ta bar makarantar nan. Tashin hankalinsa shine ko sunan kauyensu bai sani ba, alhalin yanzu yadda yake kaunar Ilham haka yake kaunar Maryama. Idan zai iya rabuwa da ita, to hakika zai iya rabuwa da Ilham. Cikin in-ina Kausar ta ce "Maciji ne ya sare ta, tana kwance a maternity..." Tun kamin ta kai karshe Uncle ya fita. Ya doshi maternity cikin matsanancin tashin hankali, ko gani ba ya yi sosai. Ya banka kofar da kafarsa babu neman izini. A kwance ta ke, idanunta a rufe, rana daya kacal ta zabge, ta yi wani irin fari fat kamar babu jini a jikinta, sannan ta kumbura kamar an hura balam-balam. Nurse din da ke kokarin daura mata 'drip' ta juyo a razane ta dube shi, bai kula ta ba ya karisa gaban gadon da Maryam ke kwance ya tsaya kurum yana kallonta. Kamar an ce da ita bude idonki, ko kuma alamar tsayuwar mutum ta ji a kanta oho, ta bude fararen idanunta a hankali wadanda suka kumbura suka yi mata nauyin budewa, a hankali ta ce "Uncle…….." Sai hawaye suka zubo ta gefen idonta. Ya yi saurin kama hannun damanta, ya ce "Sannu Maryama, sannu kin ji. Allah Ya ba ki sauki". Ya juya ga nurse din ya ce "Edcuse me madam Serah, na yi miki shisshigi cikin aikin ki. Maryam na daga cikin dalibai na masu muhimmanci a gare ni. Ki yi hakuri". Ta yi murmushi ta ce "Ai na ga alama, wannan patient din taka akwai raki da saurin kuka. Na dauka dadi zaki ji da kika ga Uncle sai kuma ki kama kuka?" Mairo ta maida idanunta ta rufe tana murmushi. Ta nemi ciwon da jikinta ke yi ta rasa, sabida kasancewar Uncle Junaidu tare da ita. Suna magana a kanta shi da Madam Serah ta gaya mishi wannan macijiya ta dade tana sarar dalibai, anyi duk iya kokarin da za a yi don ganin an fitar da ita daga makarantar an rasa. Wani zubin sai a yi tsammanin ma ta mutu don sai a yi shekaru biyu ba a ji duriyarta ba. Amma yanzu kam za a daukaka zancen zuwa federal da yardar Allah za a fitar da ita. Ya ce "Maryama ta kumbura, ta yi biyun yadda ta ke". Ta yi murmushi ta ce "Jini ne babu isashshe a jikinta, wanda aka zuke tare da dafin amma already an tafi a sayo wanda za a sanya mata a asibitin Aminu Kano". Hankalin Uncle ya tashi, ya ce yana son ganin Doctor Nanah, ta ce tana ofis ka karisa. Ya samu Dr. Nanah a ofis cikin tashin hankali. Ta ce "Yaya dai Uncle Junaidu?" Ya ce "So
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66