Chapter 28
Chapter 28
Sun kusa Yakasai Ladidi ta ce "Wallahi Mairo duk abin da kike so zan baki, ki rakani a zubar min da cikin, in Baba ya ji wallahi-wallahi kashe ni zai yi". Mairo ta ce "Ni kuwa mai za ki ba ni Ladidi in rakaki a kashe rai? Tukunna ma ni ban san inda ake zubar da ciki ba. Kin bata wayonki! Amma bana tausayinki, Baffa nake tausayawa. Iyakacin tarbiyya da ilmi ya baku, daga boko har na Arabiyyah, ya tsare muku cinku da shanku, da suttura dai-dai karfinshi. Bai cancanci wannan sakayyar daga gare ku ba….." Ta kai gefen mayafinta ta share hawaye, ta fyace majina, ta ce "Ladidi ke kuwa mai ya kai ki ga yin haka? Idan aure kike so mai yasa ba ki tsayar da daya cikin tulin samarin naki kin aura ba? Mai za ki ce da Baffa ranar da ya gane kin yi cikin shege?" Ladidi ta kufula wai Mairo ta ce ta yi cikin shege, ta ce "Kinga malama bana son wani dogon Turanci, idan ba zaki rakani ba ne mu raba hanya, wancan karon ma da aka ce na yi cikin ai nasan inda na je aka kwakule shi. Ko ance da ke kowa ma kidahumi ne, bakauye irinki? Mtsew!!!" Ta yayyaga takardar likitan da takardar maganin, ta ce "Ki je ki gayawa Baffan naki ya yi duk abin da zai yi kada ya barni da rai idan shi ne..........." Mairo ta sanya 'yan yatsu ta toshe kunnenta, ita kuma Ladidi ta tare dan A dai-daita sahu ta shige, ta ce, ya kai ta Sabon Gari. Tana shigowa gida Habiba ta ce "Ina kika baro Ladidin?" Ba tare da ta dubeta ba ta ce "Tana zuwa yanzu". Ta shige dakinsu ta danno kofa. Ta rasa inda zata sa kanta da tausayin Baffa. Ta soma kuka kamar ita ce abin ya faru a kanta. Wani sassanyan kamshi ya doki hancinta, irin wanda ba ta taba ji ba a rayuwarta. Daga nan ta jiyo muryar Baffa yana salati, yana sallamewa. Ta sake saurarawa sosai sai ta ji ya ce "HABIBU? Wa nake gani kamar Habibu?" Tamkar wadda aka cakawa mashi. Ta ji wani kululun bakin ciki ya taso ya soketa a kahon zucci. Amma hakan bai hanata mikewa ta fito ba, don gasgata kunnuwanta. Wani magidanci ne dan kimanin shekaru talatin da takwas, wankan tarwada, mai zarkadeden dogon karan hanci da yalwar idanu farare kal. Da ganin fuskarshi ka ga Malam Bedi, ta wani fannin kuma Alhaji Abbas sak! Yana sanye da kaftan na shadda Getzner kar-kar da ita, baka wul! Dinkin tazarce, sumar kansa a kwance luf baka sidik, kasancewar ba hula a kansa. Da gani babu tambaya, ka ga mutum da ya dama, ya kutsa cikin ilmummuka daban-daban. Wasu kyawawan yara guda uku, maza biyu da mace daya, sai rarraba ido suke na rashin sabo. Mairo dai tana nan rike da labule tana kallonsu, wasu irin hawaye suka zubo mata, ta yi saurin sakin labulen ganin zai juyo sashen da ta ke. Tana ji su Hajara duk suka firfito suna ta karadi da sallallami, ita kuwa ba ta kara lekowa ba. Mai ya dawo da shi cikin rayuwarsu yanzun? Bayan masu bukatarshi sun shude a doron kasa? Mai zai ce, mai zai yi, ya wanke mugun tabon da ya yi mata a zuciyarta? Mairo kuka ta ke tamkar ranta zai fita, ba ta son ganin Habibu ko kadan a rayuwarta. Gara ta bar gidan, kada ace da shi yana da 'yar uwa, mai zai yi mata wanda ALLAH da UNCLE JUNAID ba su yi mata ba? Ta soma harhada kayanta cikin jakarta da sauri-da-sauri, tana yi tana fyace hanci da hawaye duka. Ba ta ankara ba sai ji ta yi Baffa na kwala mata kira daga tsakar gida "Mairo! Mairo!! Ko Mairo ba ta nan ne?" Ta yi bakam, ta ki amsawa, ta jawo hijabinta ta zurma ta sungumi akwatinta ta yo waje, suka ci karo da Baffa a bakin kofa. Ya ce "Zo Mairo, yau ga Habibu Allah Ya dawo mana da shi". Ta sa kuka, ta ce "don Allah Baffa ka bani hanya in wuce, bana son ganinshi, ba abin da ya hada ni da shi. Idan dai zai zauna a gidan nan to ni zan koma wajen Nabilah". Baffa ya ce "Haba Mairo, waye ba ya kuskure? Ki dinga yi wa dan Adam uzuri cikin kowanne hali, uzuri sau saba'in, kafin ki kama shi da laifi. Ki saurare shi ki ji da wacce ya zo, sannan ki yanke mishi hukunci". Da haka ya lallabata suka nufi dakinshi, inda Habibu da su Habiba su ke. Habibu ya hada kai da gwiwa sai kuka ya ke, kamar karamin yaro. Ba kuma kukan komai yake ba, sai kukan jin rasuwar iyayensa daga bakin Habiba. Baffa ya fada su da fada kamar ya rufe su da duka "Ke kam Habiba ba ki ji dadin halinki ba, ko ruwa ba ki barshi ya kurba ba zaki ce Uwa da Uba sun mutu, gatsar, babu sakayawa, babu nuni da daukan hakuri da YAKANAH (Sunan Littafin TAKORI mai zuwa). Ku tashi ku fita ku ba ni waje, iyayen banza, wadanda ban san yaushe za su san Annabi Ya faku ba". Sum-sum-sum suka mike suka fita. Habibu ya dago kai yana kallon Mairo. Kyakkyawar budurwa ‘yar shekara sha takwas, wadda ya tafi ya bari tana shekaru takwas. Ita ma ta kalle shi cikin ido, sai kuma ta dauke kanta. Ta daure fuska sosai. Ya ce "Mairo Yaya Habibun?" Sai ta fada jikinsa ta sa kukan da ke cinta a zucci. Allah Ya riga ya halicci zuciyarta da kaunar Habibu, babu yadda zata yi, shi ne dolenta a rayuwa. Suka rungume juna suka yi ta kuka, Baffa ma tunanin dan uwansa ya dawo masa sabo. Ya soma share ido da habar babbar rigarsa. Sai da suka yi kukansu mai isarsu, sannan Baffan ya soma lallashinsu. Ya ce "Ni ina nan Habibu, zan zame muku uwa, uba, kuma abokin shawara. Dukkaninmu na haka ne, kowa jiran wa'adinsa ya ke". Habibu ya ce "Kaicona Baffa! Dukiyar da na zauna ina tarawa don Baba ya daina noma, Inna ta daina girki da icce, Mairo ta yi karatu mai kyau sun tashi a banza! Na kintata ne zuwa sanda zata gama sakandire sannan in dawo, ashe bazan tadda Baba da Inna ba, sannan Mairon ba ta ji dadin dawowata ba!!" Baffa ya ce "Wai haka Mairo? Ba ki ji dadin dawowarsa ba in sallame shi?" Ta yi murmushi, ta sake sunne kanta a kirjin Yaya Habibun. Ya ja karan hancinta, ya ce "Ko kallon 'ya'yanki ba ki yi ba, balle mai sunanki, mai kama da ke". Sai a lokacin hankalinta ya koma ga yaran. Cikin murmushin kaunarsu da ta mamaye zuciyarta farat daya, ta ce "Ya'yanka ne Yaya Habibu?" Ya gyada mata kai, "Ya'yana ne. Na yi aure da mamarsu tun sanda na kammala karatun digiri na farko. Ga Abbas, ga Muhammad (Bedi), sannan ga Mairo". Baffa ya yi murmushi, ya ce "Taho takwarana". Abbas ya matsa gare shi, dan kimanin shekaru hudu, Muhammad shidda, Mairo kuma 'yar shekara biyu ce. Babban wato Muhammad ya ce "Daddy wannan ne Babanka?" Ya ce "Eh, shi ne Babana". Ya kuma cewa, "Wannan ce Aunty Mairo?"
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66