Skip to content

Chapter 27

Chapter 27

Abari Ya Huce Book One Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
Download Book

tasan ko ta karba rabon su Ladidi ne, dama ace za su gode ne, to a'a, zagi da bakar magana ne zai biyo baya. Hajiyar ta ce "Ni ba babarki ba ce? Ba zan yi miki ihsani ki karba ba?" Ta sake kai dubanta ga Uncle Junaid da ke cikin hoto yana murmushi. Sai ta ga kamar ya turbune mata fuska, cikin rashin jin dadi. Ta maido ga dubanta ga Hajiyar, kallonta ta ke tsakaninta da Allah da matsananciyar kauna cikin kwayar idanunta. Ji ta yi kamar ta kwantar da kai a kafadunta ta yi kukan da ke cin ranta, ta gaya mata matsananciyar kaunar danta da Allah Ya dora mata. Ta ji dumin da Junaid ya ji, a jikin wannan nagartacciyar UWA, ganin hawaye na neman tona mata asiri ta yi hamzarin karba ta ce "Na gode". Har ta kai bakin kofa zata fita, Hajiyar ta kirata jikinta a sanyaye, don daga dukkan alamu akwai abin da ke damun wannan yarinya, ta ce "Har za ki tafi, ba ki gaya min sunanki ba, idan Ilham din ta yi waya in gaya mata". Mairo ta ce "Ki ce mata Maryam ce". "Maryam-Maryam!" Tana ji a bakin su Ilham, amma a wannan karon Allah bai bata ikon ganewa ba. Har yarinyar ta fita, ba ta motsa daga inda ta ke ba, ta dade tana tunanin inda tasan yarinyar. Mai yasa ba ta tambaye ta daga inda ta ke ba? To akan me zata tambaye ta? Don kwaita zo wajen Ilham? Amsar shi ne, don zuciyarta tana sonta. Ta koma falon ta zauna cike da tunani. Sai ana kiran isha'i ta iso gida, Baffa na alwalar sallah a nan kofar gida, ta tube takalminta sannan ta wuce shi, zuciyarta cike da jin haushin dadewar da ta yi. Ya ce "Ban ce kada ki kai dare ba Mairo?" Cikin matsanancin ladabi ta rausayar da kai tace "Ka yi hakuri Baffa, mota ce ban samu da wuri ba". Ya ce "Ni dai duk inda za a je aje ido na ganin ido, amma bana son ayi dare. Idan kin shiga ki turo min Lawan". Ta ce "To". Habiba na kwasar tuwon dare sanda ta shigo, ta dago kai ta dube ta a ranta ta ce, "Kai wannan yarinya da kashin arziki ta ke, kullum ta fita ba ta dawowa haka nan, sai bakin jini har yau babu wanda ya taba sallama da ita, duk kyawun nan nata. Ladidi kuwa kullum idan mutum biyu ba su yi sallama da ita ba, hudu za su yi". Ta dubi Lawan wanda ke bin ledar hannunta da kallo, ta ce "Ka je Baffa na kira". Ya ce "In an ki fa?" Ba ta yi magana ba ta wuce wajen Habiba ta durkusa ta ce "Mama Na dawo, sannunku da aiki". Lawan ya ce "Wani feleke wai 'Baffa', mu 'Baba' mu ke cewa Babanmu, ba wani Baffa ba. Wai mama yarinyar nan ta fara bin maza ne ta ke shigowa gidan nan da manyan ledoji?" Habiba ta ce "Idan ta bi sun ina ruwanka, ko mace ba don namiji aka halicceta ba? Me muka samu ne Mairo? Miko nan in gani". Ta mika mata ledar ta tusa karkashin kujerar da ta ke zaune kada Hajara ta fito ta gani, ta ce sai an raba da ita. Ta dauki tuwon da ta saka mata a wani kwano duk lamba, ta zuba miyar karkashi akai ta mika mata. Ta karba ta wuce daki cike da takaici. Ashe wani takaicin ke jiranta. Tana sanya kai dakin wani mugun karni ya dake ta. Ladidi ta kelaya amai tun daga bakin kofa har bakin katifarsu. Tana kwance a katifa tana barci kamar mushe ba abin da ya dame ta. Ta fita ta dauko tsintsiya da abin kwashewa ta soma aikin aman kamar zuciyarta ta yo waje don bakin ciki. Tuwon da ba ta iya ci ba ke nan sabida karnin da dakin ke yi, haka ta kwana da yunwa. Washegari Ladidi da kanta abin duniya ya ishe ta, ta rarrafa katifar Mairo ta tashe ta, misalin karfe bakwai na safe. Mairo ta bude ido tana kallonta, yawu ya ciko mata baki ta juya bayan kofa ta tsartar ta ce "Zo ki raka ni asibitin don Allah, na kasa gane abin da ke damuna, amma da gaske ba ni da lafiya". Sai Mairon ta ce "Ki fara zuwa ki tambayo mama tukunna, idan ta amince sai na rakaki". Ta ce "Rabu da ita kawai, zo mu fice tana daki". Mairo ta ce "A'ah, ba za a yi haka da ni ba". Ba da son ran Ladidin ba ta fita ta tambayo Habiba za su je asibiti. Habiba ta dubi diyarta ta ce "Bana so ku dinga jerawa ne kada a ga muninki". Ladidin ta kyabe baki, ta ce "Lallai ma Mama, ni ce ma mummunar?" Habiba ta ce "Sai idan ba ku jera da wannan mai kama da aljannun ba". Ladidi ta ce "Ke wannan ya dama, ni da munin nawa dai ai na fi ta farin jini, kin taba jin ko bera ya aiko yana sallama da ita?" Ta ce "Haka kuwa, ku je sai kun dawo". Suna tafe a gefen hanya har asibitin Murtala, Mairo ta yanko mata kati suka hau layi. Suna nan zaune har aka kirasu 7/30/21, 10:24 PM - Kawata: 98 Likitan yana rubuce-rubuce a file lokacin da suka shiga, Mairo ta tsaya ta harde hannuwa a kirji a bakin kofa. Ladidi ta karasa ta zauna a kujerar da marasa lafiya suke zama. Ya gama ya dube ta ta karkashin gilashinsa ya ce "Me ke damunki?" Ta ce "Ina fama da haraswa, zazzabi da ciwon kai mai tsanani, ga wani yawu da yake taruwar min a baki, bana jin dadin bakina". Likitan ya dau abin awonsu ya sanya a hannunta yana sauraro, sannan ya yi rubutu a wata 'yar takarda ya ce, su je laboratory su kawo masa result. Suka fita suka tambayi lab aka nuna musu. Nan aka bai wa Ladidi robar fitsari aka ce ta je toilet ta yi ta kawo. Nan da nan result ya fito suka koma ofishin likita. Ita dai Mairo tunda ta ga an rubuta positibe hankalinta yai matukar tashi. Likitan ya dube su bayan ya duba takardar ya ce da Ladidi, "Ina mijinki?" Ladidi ta ce "Ba ni da aure". Ya kura mata ido na 'yan sakonni ya ce, "Amma you are pragnant,(kinada juna biyu) watanni biyu cif?" Ladidi ta fiddo 'yan idanunta gaba daya suka yi kuru-kuru, wannan bai damu likitan ba ya ci gaba da aikin da ke gabansa bayan ya rubuta mata magani a wata 'yar takarda. Suka fito jikin Mairo har rawa yake, saboda dimuwa da razana, ita kuwa Ladidi in banda kuka ba abin da ta ke, wai likitan sharri yai mata, duk girman kan nan ta sauke shi tana rokon Mairo wai su je wani asibitin a sake dubawa. Mairo ta sa mata ido, ta ce "Wannan asibitin specialist ne, duk Kano daga Aminu Kano sai shi, hakikanin gaskiya suka gaya miki. Don haka ni babu inda zan kuma zuwa". Ta yi shiru hawaye na zubar mata. Ba tausayin Ladidi ta ke ji ba, tausayin Alhaji Abbas ne, bawan Allah, Baffa bai cancanci 'ya'ya irin wadannan ba.

Table of Contents

Chapters

66 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66