Skip to content

Chapter 7

Chapter 7

Zuciyar Masoyi Book Two Complete Hausa Novels 1,156 words 0 views Progress saved
Download Book

zuwa hudu ina ganin itama Aisha ai haka ne malam Abdullah dole sai tayi idda kafin suyi mata aure dan haka a tunani sai tayi idda itama ko ba haka ba ne . Abdullah yadan sotsa keya kmr dady tamkar dady yana kallonsa yace haka ne . dady ya sake yin murmushi to kaga kuwa har na dawo .. Abdullah yadan janye wayar yayi . yana murmushi dan gabadaya yagama rudewa gashi har yasa dady ya fahimceshi ya fada aransa . Shima bangaren dady dariya yayitawa Abdullah . MMN SUDAIS CE [3/12, 3:02 PM] Kaunace Sila: 💗💗💗💗💗 ZUCIYAR MASOYI 💖💖💖 💗💗💗💗💗 AISHA A BAGUDO Page 51-52 Aunty Maryam na can bangaren aikinta ,inna ke sanarwa zance ciki da abinda ya kawo ciwon yayi tsanani , ta bar abunda take ta zubawa inna ido sosai , ahankali cikin mamaki tace innarmu cikin me Kuma har gabanta yana faduwa . Inna bata bi takan tambayar da Aisha tayi mata ba tacigaba dayi mata bayanin yadda ake samun lalura iri iri na laulayin idan macce ta samu ciki , tayi shr tana ji Amman ba abinda inna take fada take fahimta ba , tunanin ta yana can wani guri. tashiga uku Kar dai Abdullah ciki ya bankamata ,sannan ya sakota. tasan inna bata fadar abinda bata da tabbacin a kansa aunty ce tashigo tana surutai kai nima fa yau dole a daga min kafa nima mara lafiya ce dani . Aisha ta kalli aunty Maryam ,inna tasan maganar zata mata dan Allah ta kwashe kwanuka ta fita wankewa har aunty ta zauna Aisha nabinta da idanu ahankali murya adashe tace aunty wai ciki dani ? Aunty ta kalli yadda tayi maganar tace au ke tun jiya baki sani ba. cewa nake kinji ne shiya bangaya miki ba. to ciki ne dake bai kai wata daya ba . nace ke Kuma irin naki laulayin kennan ciwon ciki da zazzabi ". Kwalla ta cika a idanunta kafin kace me sai hawaye shar ...shar... aunt tace to mayye haka Kuma ke me son kananan yara. gashi Allah ya kawo miki shine zakiyi kuka Aisha kuwa da zaune tamkar an dasata , bata sake cewa komai sai cigaba da kukanta take ita kadai tasan abinda ta tuna . aunty ta matso kusa daita sosai tace A'a ai yanzu ba kuka zakiyi ba abinda ya faru yarigada ya faru,. ta lafiyarki zakiyi da dan dake cikinki tunda ....Dr salim ne yashigo ya katse su ganin Aisha na kuka yasa ya ja ya tsaya yana kallonta can Kuma ya matso kusa da su yace yaya jikin ne ? Aunty Maryam tayi dariya tana girgiza masa kai tace ko daya . wai dan an gaya mata ciki ne daita ,shine take kukan dadi . Dr salim ya kura mata Ido baya son har baya so daukewa daga kanta ,dama takasance matarsa aka Kuma sanar masa tana dauke da cikinsa da bai san irin gatan da zai nuna mata. ba har sai shagwaba ta isheta," har sai da aunty takira shi sannan ya dauke idanunshi daga gareta". da sauri ya kalli aunty yace ina tunanin irin su abinda dariya ne dasu. haka nake da wata kanwa itama ko bacci zatayi yara suka hanata duk girmanta sai kiga hawaye. aunty tasake kwashewa da dariya tace kusan duk jirgi daya ya kwasosu kmr wasu kawaye shima dariya yayi sannan yace excuse me sister inason na dan ganki na mintina kadan " aunty tace ba komai ta tashi tabishi sanda inna ta dawo itama. Dr salim yace mijin Aisha ya jima da tafiya ne ko kuwa daman tafiye tafiye yake aunty tace A'a ai... Daman ba tafiye tafiye yake ba ..sai Kuma tayi shr . Dr salim ya dan nakalci wani abu ,. yace sorry ina son nasani ne saboda irinsu da yanayin da take ciki yanzu tana bukatar kulawa ma'ana dole takasance tana da wani a kusa daita da zai dinga lura da ita sosai. musamman ita da cikin yazo mata a haka. duk lokacin dataji ciwon ciki tana iya shan duk wani abu datasan zataji ya daina. ya numfasa sannan yace to idan kuwa mijinta yana kusa shi zamu bawa matakan da zata kiyaye da irin abin dazata dinga Sha. har zuwa lokacin dazata daina jin ciwon cikin . Aunty Maryam tace ai da yake yanzu ma tana gida ne Amman ko ni ko inna duk wanda ka yiwa bayani ma za'a san abinda za'a dinga yi . dr salim ya furzar da iska hade kurawa aunty Maryam ido dan ba abunda yaso ji ba kennan Kuma maganisa a kawai alamomin tambaya sosai a tare da bayaninta ,Amman bai son ya fiyye shishigi da binkice akan komai. yana son yabi komai cikin tsari dan haka ya sake numfasawa yace shikenan . Har byn kwana biyu bata saki ranta ba kullum sai tayi kukanta . Itama haka kawai tarasa dalili yin kukanta . mlm abu yashigo inna ke sanar dashi gabadaya yau taki ma cin komai. tasa damuwa aranta shi kansa mlm abu lallabata yake wannan lokacin. ya dauko ledar yalon da yashigo dashi ya wanke ya ajiye mata. yace yaya zakiyi da kaddara Aisha duk yadda mutun yaso sai ki ga Allah ne kawai zai tsara masa yadda yaso. inda mlm abu ya godewa Allah ma . allah ya nufa cikin ta hanyar aure zaa same shi . gashi anyi auren ba a dade ba. Allah yakawo rabuwar an rabu da rabo atsakanin . Ahankali ya furta ba komai haka Allah yaso . yana jinjina kai . Usman ne ya matso kusa da inna ya zabga tagumi yana ji abinda mlm abu kecewa gabadaya tausayin yaruwarsa yake . gobe in Allah yakaimu sati guda kennan da sakin . Amman har yanzu bbu wani bayani daga garesu abinda mlm abu yace kennan yana tsare inna da idanu. inna tace muma kada a nemesu in dai basu suka nema ba. abar abun haka komai daren dadewa ai shi cikin zai nemi ubanshi . Dr salim ya kalli aunty Maryam da suke zaune a wani ward su biyu yace abinda yasa na sameki anan sister domin na fayyace miki bala'in dana afka ,hakika Maryam kanwar nan taki nake maseefar so kai tsaye. dan haka na kagu komai zai faru dani gara ma ya faru akan narasa . Aunty Maryam ta zazzaro ido "wa kennan kake nufi ?ya gimtse fuska yace wace kike daita. aunty ta sake kallonsa sosai, . tace wai Aisha kake nufi ?yace yes ita fa sister bbu yadda zanyi shiyasa na sanar dake ki taimakmin dan Allah. "aunty Maryam tashiga rudani da frigice dan haka ta soma girgiza kai tana cewa doctor kasan abinda kake fada kuwa . kai ya kada mata ,. Amman ai Nace maka Aisha matar aure ce . gama ciki nan ya nuna maka hujja. Dr salim ya dubeta dakyau yace sister Maryam tunda kanwarki ta Tako asibiti nan naganta nake addu'a r idan har ba alkharina bace Allah ya fidda min ita daga Raina . Amman wlh kullum kmr ziga zuciyata ake akan soyayyarta . addu'ar dana dage dayi ne da Kuma hujjojin dana samu sune suka sa na tunkare ki kai tsaye da maganar . Ban taba jin wani tashin hankalin daya sameni na farat daya

Table of Contents

Chapters

46 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46