Chapter 14
Chapter 14
yamata rahma yasa ta huta, ya raya abinda tabari . Ku kuma Allah yabaku hakurin rashi . Allah yasa idan tamu tazo ,yasa mu cika da kyau da imani Ameen ππΌππΌ Allah sarki faiza πππππππ Page 60 Faiza tace kai mama mutane nan fa sun wuce duk yadda muke zato fa. ta koina abin arziki a jike yake . ba ga mami ba ba ga uban ba hatta shi kansa Abdullah din mai tsansar abun duniya ne . Mama hafsa Tace ke sai yanzu kika san haka kennan . ai shiyasa na tsarawa uwar duk yadda zasu bada sadakin kmr dai yadda suka bada na waccan Yar masu tatsan nono gidaje shida da motoci kinga ai an nininka kennan . Faiza tace kai mama kina wuta ina binki da fetir wlh ta Mika uwar hannu suka kashe. sannan tace ke in banda bana so abin ya wuce wannan lokacin ai da watar kasar za'a kaimu mu zabo kayan gado kinsan su masu fita ne . Sun fi sanin inda za'a samu na garari . Faiza tace dakata mama bangane maganar ki ba .. ai a hakan ma dole ne kayan kitchen lefe da sauran kayan duk a waje za'a siyo su. ai ba wani batun dan za'a yi biki wani a kurarren lokacin. tunda dai ba'ariga an soma raba AV ba. me zai faru abinda ance shi dady sai yayi kusan wata hudu kafin ya dawo. ko ana sauran sati ne ya dawo aka daura ai dai an daura. kuma komai kwakwa da nacin sa dole ya hakura . Mama hafsa Tace haka ne fa . kinibabbe banza kawai , ai ni nafi son kisamu kmr wata daya da aure Abdullah akanki kafin yadawo. sannan nasan mun dan fara tatsan abinda muka tatsa kafin yazo ya hanamu rawar gaban hantsi. akwai abubuwa na musamman dana zan tsumaki dasu. saboda Abdullah din dan haka ana daurawa ,zaki lillike masa ajikinsa sai yadda kikayi dashi . idan ya dandana zumarki kuwa. zai mannemiki har sai kindinga korarsa. Faiza ta saki shewa dan murna hade girgiza nonuwa irin dai yadda manyan yan iska keyi . tace A'a haba dai mama bawani korarsa da zanyi ai sai dai na kwashi da....... can Kuma tayi shiru jikin faiza yayi mugun tsanyi tuno halin Abdullah datayi. mama hafsa Tace karki taba damuwa naga kin wani canza kisha sha'aniki diyata . idai Abdullah ne muna nan zaki zo har nan kibani labari komai. kema ai yanzu kinzama babbar yarinya . Faiza ta mike tana dariya har zata fita kuma ta dawo tace uhm mama kigayawa mami fa ni nafi son mu zauna acikin gidan nan a part din Abdullah bazan zauna a wani guri ba Mama hafsa ta kalleta a bazance tace meyasa ke tsamiyace . ga gida can ke kadai bbu wani dan sa idon da zai dami rayuwarki da takuran yan'uwan miji. komai kuma yayi a gidan sai abinda kike so zaki canza . Faiza ta dan sake rage murya sosai tace uhmmmm ke Abdullah din nan fa da kike Gani bai da kyau fa . ni na fi son ko meza'ayi Gani ga uwarsa . mai sashi yayi mai hana shi ya hanu . yanzu kina ganin duk abinda aka sha wahalar yi a kansa idan ranar da aka kaini ma yaki zuwa fa gidan fa! . kinga tun anan ma wani abun zai karye idan kuma anan ne fa. nasan karyashi tasha karya dole mu kwana tare . Mama hafsa Tace kuma fa haka ne . faiza tace ke dai kice mata ana zamu zauna kawai naga part din nasa ma wata aljannar duniya ce . Mama tace to ni ina zan wani san hakan tunda bashiga na taba yi ba. Kinga haka ma za'a yi bari kiga na koma gunta . Kwana takwas kennan dayin maganar a maimakon ranakun bikin faiza . mama hafsa da faiza da kanwar faiza rahma suka Lula waje hado kayan amarya mami ta bude musu account dinta sosai suyi yadda suke so . Abdullah Yayi shr kansa a sunkuye byn ya gama jin abinda mami ta fada cewar ya rubuta takardun gidaje gudu shida da motoci hawa guda shida a matsayin sadakin faiza. kansa har ciwo ya farayi saboda girman al'amarin Amman ko dagowa bai yi ba yace shikenan mami za'a yi yadda kike so. Fita zai yi Amman ya kasa dole ya dawo part dinsa ya kwanta. yayi shr kullum abin ma gaba yake yi bbu wani sauki acikin al'amarin. sai randa Allah ya kawo . Kwanaki sun shude da yawa komai ya gyaru a ma'aikata. Amman banda bangaren rayuwarsa tunda ya rabu da Aisha bai kuma ganin wani mai kamanin ta ba sai a hoto. Wani lokacin har wani dan shawagi yake yi da daddare akan hanyoyin gidansu . ko gidan aunty Maryam Amman cikin ikon Allah kmr anyi ruwa an dauke ko a yan'uwanta bai taba cin karo da kowa ba . sau daya ne ma ya taba hango umar akan machine traffic ya tsayar dasu. kuma ba a hannun dayake bane kafin yayi wani yunkuri tuni sun wuce. yayi ta hange hange bai ko ga alamunsu ba. Amman ranar ko ba komai ya dan ji dadi har yayi tayiwa masu gadi da ma'akata kyautar kudi balle salis da a rana ya warke . Duk yadda mami tace haka yayi . komai kmr yadda tace haka yayi . Da yayi niyyar sanar da dady sai ya ga kmr idan ya fada tamkar ya kai karar mami ne . dan haka kawai ya kyale tunda dai abun ba gagara zaiyi ba . haka ya bude account ya fidda kudi masu dunbin yawa . kuma yadda ya siya komai na sadakin faiza haka ya kwashi makudan kudin ya zuba a account din Aisha. wanda ya bude mata hatta pin din ATM da card suna hannuta. yabata tun ana gobe zasu rabu bai dai yi mata bayani bane. haka Kuma daman yawanci yana tura mata kudade a cikin salary dinsa. dan shi tunaninsa tana can tana bukata dasu . Ya tuna wata aunty dinsa a Egypt sanda suka je ta kalleshi . cikin yarensu tace Abdullah matarka na da kyau kuma tana da shiga rai . ko zaman mitina biyar kuka yi daita kyaunta da yanayinta mai tsayawa mutun arai ne . Ya dafe kanshi da duka hannuwansa yana jin kmr ya saka kuka ballanantana shi da ya zauna tare daita ya kusanceta yasan dadinta. sannan wai Dr sagir zai ce wai ya rage tunaninta saboda ya rame da yawa ai bbu ranar daina tunaninta sai ranar da aka dawo masa da abarsa . Satin su faiza biyu mama hafsa azalzala mata akan su dawo. saboda shirye shiryen biki. Mama hafsa tayi tayi daita . Amman ina ita kuma faiza ta kafe ita lallai sai tagama abinda ya kawota . dan haka dole tasa mama ta barta . ta fara yin gaba a saboda ta dan yan shirye shirye cikin gidan kuma a fara rabon AV faiza Kuma tayi alkwarin dawowa zuwa wani sati to ba yadda mama hafsa ta iya haka ta yarda . a acewarta dai dama ce tasamu shi yasa ita faizar zata tsaya din . Kai tsaye tsaye ta sokoto mama hafsa ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46