Chapter 45
Chapter 45
masa wani irin suya . itama tajima zaune anan daga baya ta Mike ta shige bedroom dinta ta kwanta. ita kadai tasan abinda take sakawa a ranta dan kukan ma kin zuwa mata yayi alokaci. Abdullah kuwa ya kasa tsaye ya kasa zaune a daki ya dinga kallon hannun daya mareta dashi . ya dunkule ya buga a bango har zuwa wani lokacin a karshe ya sake fitowa ya dan saci kallon inda yabarta bata nan yasan bbu wata walwala a tare daita yanzu . dan haka ya wuce gurin mami da taufik can ya yini yana gaya mata Amman ya gyara zance sosai yadda bazata ga laifin Aisha ba . to sai a lokacin ma yake jin wani abu daban na bangaren iyayen Aisha wanda ya faru a lokacin dasu mami sukaje gidan ita da mama hafsa ,kafin ayi musu aure . Abdullah ya kara jin zafin kansa akan marukan da yayi mata har dare yana tare da mami tun rana jikinsa a sanyaye ya baro London ya barwa mami taufik da nufin zasu zo gidan washegari. Ya kasa bacci ,ya rasa duk wata natsuwatsa saboda sun sabarwa kansu bacci da dumin juna. dan haka ya daure ya Mike ya nufi dakinta yace kome zata yi masa shi dai ta barshi ya rabi dumin jikinta . yaje ya lalubi kofarta ya jita agarkame. ita kuwa bayan ta kulle kofar ma barin key tayi a jiki gudun kada yayi amfani da extra key. tana jinsa yazo yafi sau biyar yana murda hannun kofar har da knocking a hankali taki kulashi har ya gaji ya hakura . Washegari da safe ya isketa a kitchen bata fasa yi masa duk abinda zai ci ba . saboda dukkansu basu amincewa masu aiki suyi musu abinci ba . sai dai suyi iya nasu . sadik yana kusa daita yana zuba mata surutu. Abdullah ya shigo ya dan saci kallon fuskarta tam take a daure kmr dai asalin Aishar da ya sani . ya kasa magana ya sunkuya yana yiwa sadik magana yace morning my dear . Shima sadik din yace morning dad . yace masa shine jiya ka kulle min kofa ko kana jina ina ta bugawa ka kyaleni to ni dai ayi hakuri dan Allah . ta gane daita yake yacigaba da maganar sa sadik kuwa sai tambayar sa yake dan bai gane kan maganar ba . Aisha kuwa da sauri ta dan hada abinda take ta shige ta barsu a gurin . Ya Mike yabi bayanta da kallo yasa hannu ya tallabe fuskarsa daidai barin daya mareta. ya langwabar da kai yana jin zafin gurin har yanzu. hannushi duka yasa ya dafe tsaitin ZUCIYARSA dashi ahankali ya furta ya Allah..... yana daya sanin aikata abinda yayi . Mami bata zo gidan ba sai kusan azahar. ya fito ya dawo falo saboda zuwan nata . a gidan tayi sallah Aisha ta sauke da bata duk wata kulawa da tasaba yi mata ,. wanda azahiri kuma bata so zuwan mami ba alokaci suna falo duka har Abdullah ko magana bai yi ba. yaji intercom na kara ya Mike ya fita ya duba ya dan jima a wajen sai kuma gashi ya shigo a fusace yayi bedroom din ummu affan din . dan jim sai gashi ya fito da handbag dinta yakaraso yana zazzagewa a rude yace kingani ko mami kalli kalli ya fito da passport dinta da komai na cikin jakar . yace duba mami wai dan bata da hankali .....Nigeria take shirin tafiya ita kadai yana yi yana kallonta yana nunawa mami . A fusace itama take kallonsa, Amman batace komai ba Abdullah yace direban da tasa yazo yakaita airport ne ya zo yanzu . ya sake mikewa a fusace ya fice ya dawo yana watsamata wani irin mugun kallo . Aisha ta Mike tsaye tana son tayi kuka. tace ni kabarni na tafi abuna. ya zaburo zai sake dauketa da wani Marin dan jin haushin abinda tace. mami ta dakatar dashi ya dinga harararta yana kwafa ran maza ya baci . Mami ce tasa baki tace ta zauna shima ya zauna ta fara bata hakuri jin da tayi ba zasu barta ta tafi ba . Yasa ta kifa kanta kan kujera ta fara kuka Sosai Abdullah ya gane irin yadda take kukan komeye ya taba zuciyarta kwarai . ya ji ba zai jure jin kukanta ba. kawai ya Mike ya bar gurin . sai wajen dare sannan mami ta fara shawo kan al'amarin sai da ta nuna musu bacin ranta sosai wato zuwanta bashi da wani amfani kennan. sannan fa jikinsu yayi sanyi Abdullah ta farawa fada sosai ta nuna bai kyauta ba . sannan ta dinga yiwa Aisha maganar data shiga jikinta sosai. tace kinga a kalla yanzu idan bbu ni bbu ke dole yaran nan zasu shiga wani hali . tunda daga jikina sai nake ayanzu anan saboda haka komai rintsi ki daure ki zauna da ya'yanki sune abin alfaharinki wata rana. anan ta juya kan Abdullah take gaya masa bata raba dayan biyu wuyar da Aisha tasha a farkon haihuwar su affan da akace ta tsorata har cikin ya juye . Hadi da maganar datayi mata a waya ne . dan ko awa biyu basuyi ba da yin waya dady Allah ya jikansa yace ga halin da take ciki Abdullah ya dinga kallonta yana kallon mami shi bai taba jin haka ba . sai da yayi tunanin sosai ko shi yasa ta dinga tambayarsa mami alokaci . har ya zata ko dan mami bata zo duba jikinta bane ya dinga jin tausayinta aransa. tana da zurcin ciki da yawa . har wani sanyi sanyi ya dinga ji akinsa alokaci,. a karshe mami ta hade su gabadaya tayi musu nasiha dole su tsaya su rike kansu da ya'yansu. tunda ita ayanzu jiran irin ta dady take har tasa su hawaye . To kwanan mami uku a gidan nan su . har ta fahimci halin da Aisha take ciki . ta kawo mata abinci taga Aisha ta fice da sauri ta barta da Abdullah. ta kalleshi sosai tayi murmushi tace ai ciki ne ma daita ake ta wannan rikincin. ya tashi da sauri ya bi bayanta ya tarar tana toilet ta rufo kofar daga ciki tana Kwara amai . ya dawo gurin mami yana nuna murnarsa a fili tamkar cikin farko zata haifa masa. Sun shirya sai dai ba kmr da ba. dan Aisha taki kula shi ballanantana taje ga shimfidarsa . Shi kuma abinda ba zai lamunta ba kennan. kuma ko a gurin mami suke idan ana hira yayi ta janta da magana tayi banza dashi . kawai tayi shr ta kyaleshi . mami ma ta lura da hakan kuma tana rigashi kwanciya shi yana gurin mami kafin yazo tasawa kofar key gashi ba damar ya buga saboda mami zata jiyo . har daren ranar da mami zata koma London ya rasa yadda zai yi dan haka suna zaune sau uku suna hira tun dare bai fara ba dan sadik tuni har yayi bacci akan kafar mami. mai kula dashi tazo ta dauke shi. wani tunani ne yazo masa take yayi murmushi ya dan ciza gefen lips dinsa . ya kalli Aisha yace dan Allah ummu affan taimaka min da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46