Skip to content

Chapter 40

Chapter 40

Zuciyar Masoyi Book Two Complete Hausa Novels 1,162 words 0 views Progress saved
Download Book

sakina tace sister ba zai aureni ba shi ya ma dade da yin nasa auren. har da ya'ya. Aisha ta bata rai tace kuma shine ke dan baki da zuciya kika nace da son sa ?. Tace ba haka bane kinsan sharrin so . ina ta addu'a dai . Aisha ta dan kwabe baki tace to Allah ya kyauta Amman kuwa waye wannan . tace sunansa Muhammad. Aisha ta numfasa tace suna mai girma Allah dai ya rabaki da shi ki rike wanda yake sonki . sakina tace nima haka nake fata. sunjima a ranar suna zantawa har sanda Abdullah yazo ya jima a waje sannan ta fito abinda ta kai mata kuwa maman sakina har da kuka tana godiya tana sama mata albarka. Shekarun su affan kusan goma . a lokacin suna da kanne uku . khalifa taufik sai mai sunan mlm abu sadik. duka basuyi shekara a England ba Abdullah yasamu manager a company dake England . Wata safiyar jumma'a mami tashiga gurin dady kmr yadda ta kanyi Amman sai taga dady ba motsi bata duba ba. ta dauka ko bacci ya koma duk da bai saba yin hakan ba. Amman ina...tuni ta hau salati itama ta fadi a sume gurin har aka share makokinsa mami bata wani dawo haiyacinta ba. mutuwar ta girgiza ta. ta girgiza Abdullah sosai dan har kwanciya yayi a gadon asibiti. mami kuma banda karfin addu'a da ta zauce dan har surutai ta soma a saboda ita tafi kowa zama dashi kuma ta dade tare dashi . sai dai kaji tana cewa mijinta bai mutu ba bacci yake suka binneshi saboda ya samu baiwa a nutsensa ta tarar dashi tamkar mai bacci . haka ma innarsu Aisha tayi kuka kmr ba gobe sai fadi take Shikenan dan'uwanta ya tafi ya barta ita kadai . a wannan lokacin ne komai ya daidaita atsakanin ita da mami . domin yanzu mami ta gane duniya ba a bakin komai bace. daman ita bata dauki abin da zafi ba . duk makircin da sharin ma hafsa. Allah sarki komai ya dawo kan Abdullah. shine babba shi mami ke kallo taji dadi a ranta sai ko su affan da suke shirin tafiya secondary school a lokacin. dole Abdullah ya dawo da mami London inda daman can dady yafi sha'awa su zauna. su kuma suna England komai nasu na Nigeria yusif da umar da Dr sagir ne a kai . Abdullah yasa aka fitarwa da kannensa hakkinsu kowacce aka bata nata. zuwan su London minal tayi aure ta auri ahmed wanda matarsa ta farko ta rasu . Abdullah yayi arziki sosai alokaci ya'yansa biyar duka maza duk da su affan suna gurin mami . Affan da Adnan sun girma tamkar sun fi shekarunsu . Ga kanninsu sai sake bayyana yake. kamar har ta baci da ubansu tamkar wasu kannensa idan sun tsaya. idan kuwa su biyu suke tare baza ka taba bambance affan ko Adnan a ciki ba. sai dai halaiya ce kawai data bambantasu. mami tace bata taba ganin ko jin tagwaye irinsu ba basa jituwa ko guri daya yazo yanzu dayan zai bar wajen. Amman duk wannan abinda suke ko bacci daya yayi anan kana matsawa gaba zaka ga dayan ma yayi a can. idan cikin nishadi daya yake to wlh duk inda dayan yake kana zuwa zaka ga shima dayan yana dariya ko dai wani abu ya sashi hakan . Haka ma idan bacin rai ne. wani abinda tace yana bata tsoro duk wannan abun baka isa ka taka daya ka kwana lfy a gurin daya ba . ,duk inda hargitse ya hada musamman Adnan tunda yafi affan zuciya sai kaga affan a hargetse ya shigo yana tambayar mami ina Adnan ya tafi yayi ta damunta kennan. koda kuwa sun yini basu yi magana dashi ba . har sai yaji inda ya tafi ya binciko shi. ,suna kashe wutar kuma sai kowa ya kama gabansa . hakan yana matukar tsorata mami Abdullah ma yasha lura da hakan Aisha tace dama tun suna yara basa wasa tare . Amman duk inda daya yaji kukan daya shima sai yayi ko kuma ya rarrafo ya taho gurinsa a haka mami ta dinga kallon ikon Allah . Kuma duk abun su suna shakar Abdullah yanzu nan ya shigo zasu natsu sosai har sai ya fita . haka ma mamansu sun san ita ta haifesu suna zuwa England su ganta da kannensu Amman ita tarigada ta gane hakan suna sonta sosai da kannensu suna sakewa daita suyi hira idan sunje musamman affan dan yafi Adnan sakin fuska anan london suke karatu da Abdullah yaso ya kai su new York ne Amman mami ta hana . a lokacin teema na da ya'yanta biyu. itama faiza tayi sabon aure Amman sai da aka daure mata mahaifa sannan ta samu cikin nata ya zauna . Mami ta turo daga London Aisha taje a lokacin dadin affan yaje Hong Kong tare da wasu ma'aikata. dan haka ita da yara suna England mami take sanar mata an samu labarin ahmed mijin minal fa baya haihuwa wacce matar ma data rasu ma tsawon shekaru suna tare ko bari bata tabayi ba . kuma ance daga gareshi ne dan haka dole idan Abdullah ya dawo sai dai a raba auren. a ranar minal na gidan sai faman bacin rai take da maganar mami har kuka tayi daga kallon idanunta . mami kuwa sai dada jaddada mata hakan takeyi . Shikenan ace mutun bazai ga kwansa ba a duniya Aisha tayi shr daga can tace ni ina ganin mami abin bai na raba aure ba tunda dukkansu suna son juna aure da haihuwa duka nufin ne na Allah idan Allah yayi nufin ta samu sai kiga ya kawo dalili. Koda shi din ko rabuwar sai a rabu batare da jin zafin wani ba Amman muddin yanzu aka ce haka za'a yi musu wani cikinsu zai iya kulle abin yaji zafi a ransa azo kuma daga baya ba'a samu yadda ake so ba . Mami tayi shr tana sauraronta daga baya ta jinjina kai tace Shikenan Aisha tace addu'a kawai za'a dinga yi musu mami tace Shikenan haka za'ayi. Minal kuwa da taci kukanta tagaji jin yadda Aisha sukayi da mami da murnarta ta rungume Aisha tana godiya. Abdullah yashigo falon mami a dalilin wayar da tasa aka yi masa bata da lfy . byn dawowar daga Hong Kong ya tarar hawan jininta ne ya tashi dan ma da taimakon doctor a kusa mai kula da lafiyar ta . mami ta Mike zaune tasa aka kirawo mata affan da Adnan tacewa Abdullah gasu nan jiya ko abinci bbu wanda yaci acikinsu . saboda rigima akan abinda bai kai yakawo ba ,. wai har Adnan yana dauko wuka a kitchen zai cakawa affan. Muryar Mami a raunane tace tun jiya bani da lafiya akan haka wai Adnan har yana son ya illata dan'uwansa . Amman idan wani ne yayi masa da bai barshi yasha ruwa ba . Abdullah ya zuba musu idanu yana kallonsu , kowane acikinsu ya kasa kwakkwarar motsi , saboda basu taba tsammani abin zai je kunnensa ba . ya jima yana kallonsu sannan ahankali yace takardar zama a kasar nan tashin hankali ne samunta sai da aka

Table of Contents

Chapters

46 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46