Chapter 28
Chapter 28
da Ramatou nasan kunso kuji salon Manane ko?to anki a fad'i kwalelen kudeππ se ameda idanun) Palon saman muka zauna da ganan muke jin kukan Rid da irin sa albarkar da yake kwararowa Manane... (Yau fa yarinya tayi aikin manya...dama munce MACE BATA KAD'AN) Bari mu leko Halima ... Zaune suke ita da kawarta gaban Boka tana zayyana mishi iri bak'in aikin da take so amata... Wata mahaukaciyar dariya ya kece da ita se kuma ya d'aure fuska yace daman na fad'a miki tun abaya a had'a miki dana mallaka dan soyyaya shi da *Zuri'ar* a cikin jininshi take bare k'anwar nan tashi akwai shakuwa me karfi tsakaninsu amman in kin kiyaye abunda zamu baki to za'a dace.... Gyara zama tayi tace yo mize hana ide buk'atata zata biya Wani kulli magani ya bata yace ungo wannan zaki had'ashi da Jinin hailarki se asaka mishi a abinci yaci ko abin sha ..yanaci to ina tabbatar miki ko uwar data haifeshi se ya tambayi izinin ki sanan ze iya gaisheta ma ...batun rabashi da *Zuri'ar* kuwa wanan Aljani dan kundaloπΉ zamu tura mishi... Note:wa iyazubilla.Mata kuji tsoran Allah kudena zuwa wurin bokaye ..ina anfani zuwa wurin boka...wani magani da ansa ko ke akace kici baza ki iya ba saboda kazantar dake cike amma dan tsabar cuta da rashin imani ki zubawa wani yaci....Allah ya qara kare mu daga sharri mutum da aljani.Ameen) Se washe baki take cike da murna suka aje mishi kudi masu yawa wanda basu man nawa bane.... A hanya tace gobe2 nan zan zuba mishi yaci . .k'awarta ta kuwa kuwa se zugata take..... Bata dawo gidan ba se kusan isha'i...dede dakin Rid tayi kwafa ta shige dakinta.... Mintina kad'an ya konkwa sa kofar d'akin kan ta fito zuwa gidan papy.... Kulolin ma shiya dauke su yayi gaba abinshi se fara'a yake dan yau Manane ta shayar dashi mamaki se wani nishad'i yake ji yana shigarshi Gidan papy ma kuwa seda ya lura da irin fara'ar dayake da kuma kallon dayake bin Manane dashi ita abun kunya ma yake bata. shi kuwz inya tuno iri abunda tamishi besan sanda yake sakin wani lalausan murmushi ba yana qara mamakin wai Manane yar yarinyar daya rena ace yau ta gusar mishi da sha'awarshi a ranshi yace ashe de ta girma.... Halima ma duk tana lura dasu a ranta tace kuyi ku gama daga yaune ..gobe warhaka baza ma ku ganshi nan ba..... Karfe ukku na dare Firgit ta tashi daga munmunan mafarkin da tayi da kalmar innalilahi wa inna.... abakinta wanda yayi sanadiyar tashin Rid duk tabi ta tsurΓ© se zarΓ© ido take shim ganinta haka se duk yabi ya rude sai tambayar ta yake da kyar ta iya ce mishi mumunan mafarki ne tayi se kawai ta fashe da kuka .. Rungumeta yayi a kirjinshi yana bata magana daga baya yace tashi ki d'auro alwala kizo ki ja tazbaha kiyi addu'oi ki roki Allah koda wani abune yazo miki cikin sauki...... Dede times d'in Mom ma ta tashi daga munmunan mafarkin da tayi tun lokacin taso kiran su Dad ya hana yace tabari har gari yakara waye wa dan kada ta d'aga musu hankali dole ta hakura ta tashi ta d'auro alwala ta ringa jero nafilfili har zuwa lokacin da aka fara kiran assalatu Ana idar da sallah tafara kiran Rid seda tayi mishi kira ukku bai d'aukaba hankalin ta ya dada tashi sai takirayi Manane ita kanta sai da hankalinta ya tashi ganin kiran Mom a wannan lokacin ta daure ta dauka bayan sun gaisa take tambayarta Rid sai tace mata yana masallaci bai dawo ba Lafiryar ku de ko ? Lafiya lau Mom dawani abune? Aa bawani abu dama wani mafarki ne nayi sai na tsorata shiya sa nakiraya naji ko lafiyarku .. Dam gaban Manane ya bada tace wani irin mafarki? Don nima jiya nayi wani mafarkin da tsoratar dani Way fa wata mata ba'ka lut da bakak'en kaya ta na jan yaya Rid zata sakashi cikin wani katon rami ina janshi tana ja itama daga karshe tazaro wata sharb'eb'iyar wuka ta daba min a ciki ta jashi yana waywaye na har tana sakashi cikin ramin...... sai ta fashe da kuka Mom seta d'an lalasheta tana fadin haba Manane ai ba kowani mafarki ke zama gaskiya ba tunda kin ro'ki Allah insha Allahu shi zai k'ara kiyaye mu amma cikin ranta tsoro ne fal dan irin mafarkin ne itama tayi nanta qara rok'on Allah ya qara karesu duka *Zuri'ar* suna cikin haka Rid ya shigo dakin rungumeta yayi ta baya yana sharema ta hawayan yana ce wa relax mana baby Daga can tsit Mom taka she kiran Manane ma kauda wayar tace Mom ce fa tayi kira to mine ciki? Taraba jikin ta dana shi tana famar guduwa tana fadin ni har kasa na fara jin kunyar ta ma Yana dariya ya kamota yace bari to nasaki kiji kunyarta sosai tunda yanzune kika fara yana ko'karin hade bakinsu ta zille tayi k'ofa da gudu tace yaya yau fa akwai school tayi fice warta Lafiyenyen break tayi musu dan harda farfesun kayan ciki tayi musu ta dibi nata taci tayi ficewarta school Fitarta keda wuya Halima ta fito tana d'an dube dube kulolin ta bude duka taga farfesun kayan ciki tayi hamdalah ta debi nata sanan ta fiddo maganin ta zuba a ciki tasa spoon ta jujuya tarufe ta zauna ta fara ci bata jima ba Rid yafito ya zauna ko kalan ta beyiba zai fara zuba wa carab tarike hannunshi tace haba honey inanan zaka zubawa kanka abunci be ce mata komi ba yakoma ya zauna Cike damugunta ta qara motsa miyar ta zuba mishi a plat ta tura gaban shi ya dauki spoon zai kay bakin shi Halima na jin dady sai kawai wayar shi tayi kara sai ya meda ya aje sunan Haidar yagani da sauri yadaga wayar tsaye yayi yana fadin ganinan zuwa yadauki wayoyin shi da brefcase din shi yayi hanyar fita da sauri ta sha gabanshi tana fadin yaya zaka fita bakaci komi ba kabari ko spoon biyu ne kayi banza yayi da ita yayi ficewar shi a mota Haidar ke sanar mishi an kawo wata mata urgently haiwuwa ce ta taso mata kuma baby yakoma bayan mahaifa so dole ayi mata aiki dan ceto rayuwarsu su biyun(Allah yasoka da kaci guba yau) A bangaren Halima ko yana fita tayi jifa da plat din tana huci tace ai gobe ma rana ce. ... Ya kuke ganin zata kaya fand ? Shin asirin nan zai kama Rid kuwa? For coments99951593 Fasma & AΓ―cha [3/2 14:05] πππͺπ¨βπ©βπ§βπ¦π¨βπ§βπ¦ *Zuri'ar* *mu* ( *Notre* *Famille* ) π¨βπ©βπ§π¨βπ©βπ§βπ§π©βπ§βπ¦ππ Story&written by π³πͺ ~AΓ―cha~ and ~Fasma~ π³πͺ _Dedicated_ _to_ _Ramatou_ *Aisha A...Asiya..Ramatou..Fanta..Momyn Mami Fatchima ..and so one dan kuna yawa munga comment din ku mun gode Allah ya saka da alheri..ya bar zumunciπππ*love you all irin sosai din nanπβ€ 120__125 ```Manzon Allah (SAW)ya ce:''Duk al'ummata zasu shiga aljanna sai wanda ya ki. sahabbai suka ce :waye zai ki ya Manzon Allah, ? Sai ya ce :wanda duk ya bini zai shiga Aljanna .wanda ya ki bina to ya ki shiga Aljanna kenan'' Bukhari ne ya rawaito``` Yau ta kama dimanche tun safe tayi aikace2n da yake ba ita ce
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41