Chapter 10
Chapter 10
mutafi Hospital saitace mun bazatajeba inkaita wajen "Imhal wai tayi mafarkin anbige Imhal da mota tanata kuka tana neman tai makon ta...... Kafun nayi wani yun'kuri tana cewa inkaita wajenta inkaita, saita suma... Dana so kafun tasuma ingaya mata tana nan lpy saita suma kuma. Soyayyace mai 'karfi tsakanin su sosai itada Imhal ko makaranta bata iya tafiya saida ita hakama bacci, ni wani lokacin ma har tsoro abun nasu yake bani.... Dan ina tunanin idan ta tashi aure ta tafi tabarta yaza'ai ko ciwo Imhal takeyi itama saitayi, haka itama Imhal idan Nafisat naciwo itama sai tayi... Abunda yafara sata tasamu hawan jini accident d'in Imhal nafarko wanda tai takwana 18 bata farkaba danta bugu sosai,akanta to lokacin ne itama tasuma anan tasamu hawan jini... Idan naga wani abun nasu sai naga kamar uwa d'aya ta haifesu wlh... "Yarahaman,Fawass ya fad'a yana lumshe idansa, zasu warke insha Allah Amman ita tayi suman ne mai 'karfi dan da'alama kafun zuwanka tayi wani an watsa mata ruwan sanyine yadawo da ita hayyacin ta. Ita kuma Imhal allurar da aka mata ne sbd tasamu bacci sosai dan jinin yashiga anutse. Itama da jininta bai hau ba sosai da zata farka nan kusa amman zata iya kai zuwa sallar isha'i kafun tafarka. Karka damu dad jikin nasu ai alhmdllh da sau'ki sosai zasu warke, bi'izinillahi ta'alaa.... To shikenan, yanzu ina Imhal take, tana nan kusa da ita muje kaganta... Futowa sukai daga office d'in Fawass Dad mans ne agaba, Fawass abaya, tafiya sukai d'akin da aka kwantar da Imhal sosai yaji tausayinta dan ta'kara ramewa sosai dama ita ba jiki ba.... Yaji tausayinta sosai, kallon Fawass yay yace "Tarasa jini ne..? " Eyy dad shine ai maganar danake maka d'azu.. "Hmm wlh kan nan nawa yayi chaji sosai wasu maganar ba banjin su sosai. Murmurshi Fawass yay yace idan nace kun tsufa kuce a'a "Kaci gidan ku, mune muka tsufan.... "Ey mana kun tsufa wlh... "Haka Abbie ma yake dakace ya tsufa saiyace Allah yakiyaye.... "Ey mana kaga laifunsa.. "Dariya yay kawai dad mans yace amman babu matsala dai ko...? "Insha Allah babu dan data farka zataji dai². "Yanzu nawa aka kashe mata, ina aka samu jinin ma...? "Haba dad aiko bansan kaba Imhal nasani bazan amshi komai ba bare kuma dukanku nasanku kuma kud'in family na ne... Kodai kamanta wanene agaban ka ninefa d'an Hassan d'inka ABDULLAHI fa wanda mahaifiya d'ayace ta haifeku, mahaifi d'aya kuma.. Idan sane yaciko da kwalla amman saiya danne, yace "to yanzu waye yabata jinin...? "Nine nabata jini.... "Kaine kabata jini kuma....? "Sau nawa kenan kana bata jini Fawassss, mai makon asiya mata... "Haba saikace wanda muke ya'ki dajuna, menene dalilin da inadashi sai an siya... "Rungumesa yay yana tuna baya.... Allah sarki kamar bai goya Fawass ba abayansa ba.... WANENE DADDY MANS.....??? WANENE FAWASSSS......??? FLASH BACK 🔙 MANY YEAR'S BACK 🔙 Ashekarun dasuka wuce baya.. """""""""ALHAJI MANSUR MANSUR MAI KOMAI DA RUWANKA.. DA ALHAJI ABDULLAHI MANSUR ORDER KODAGA DUBAI NE AKWAITA. YARAN ALHAJI MANSUR MANSUR ABDULLAHI NE... Ashekarun dasuka wuce Alhaji Mansur mansur Abdullahi wani babban mutum ne wanda yay gadon noma da kiwo kuma yakasance mutum mai zuciyar kasuwanci baya tsayawa sai anyi masa. Duk da kasancewar bai taso da mahaifiyar saba wajen matar uba yataso yasha azaba awajenta dakuma tsangwama dan har yamallaki girman sa bata daina basa wahala ba. Yasha kwana awaje komai ruwa komai sanyi, idan lokacin zafine kuma tasakasa arumbu. Saitai sati batai masa wankaba yanada shekara 4 yafarayiwa kansa wanka kuma idan zaiyi matu'kar lokacin sanyine ko damuna to dana randa zaiyi. Amman idan lokacin zafine saidai tazuba masa na d'anwaken da takeyi tace yayi wankan dashi, ita tazubawa 'kaninsa ruwan d'anwake da zafinsa, haka yay ta jinya harya rasu. Duk da wannan azabar datake basu bai fasa gaishetaba da kuma bata girman taba. Kuma koda wasa mahaifinsu ABDULLAHI baisan Menene yake faruwaba dan idan yana nan riritasu take, harya dawo shi kad'ai ma. Wannan dalilin ne yasa baya wasa da neman kud'i dakuma noma da kiwo dan yanasan yagina kansa shima Itakam Baba laure tana wad'annan abubuwan ne danta kashe MANSUR wanda takasa dan dataga ta kashe ABDULLAHI 'kaninsa taji dad'i, tunda ita babban ba'kin cikinta shine rashin haihuwar dabatayi, gashi kuma Allah yay wa mahaifin su arzi'kin noma da kiwo ga gonaki kota ina... Haka rayuwa taci gaba, inda wajen yawon neman asiri tane tayi hatsarin da idan baka san taba bazaka ta6a gane taba, inda anan take fad'awa mahaifinsa gaskiya dan lokacin data futama shibai saniba.. Anan ne yay kukan ba'kin ciki narashin d'ansa wanda takashe lokacinda yatafi birni, dan lokacin daya dawo har'an binnesa, tunda lokacin ba wayaba bare akirasa... Tunda bai dad'e da tafiyaba yarasu kuma idan yaje saiyayi sati biyu sannan yake dawowa.. Lokacin kuwa da sako yaje masa harya kwana 3 da rasuwa. Babu ko motsawa yay mata saki d'aya inda da'kar dasaka bakin manya yadawo da ita bata dad'eba kuma tamutu.. Inda shima mahaifinsa Allah yay masa rasuwa, nan ne ya'kara dagewa dan ganin ya amfani wanann gonakin da mahaifinsa yabar masa.. Dan haka yadage babu safiya babu rana noma yakeyi da kiwo, har Allah yasa yaginu yazama wani.. MANSUR ABDULLAHI mutum ne mai tsayawa kan yaransa baya barin su suna rayuwa sakaka.... Matarsa guda d'aya ce inda yakeda gonaki sama da guda 20 na gadon mahaifinsa kuma kowacce ana noma acikinta.. JAN NAMIJI, shine sunan da 'yan 'kauyen su suke fad'a masa, sbd kasan cewarsa idan yashiga gona awuni duk girmanta saiya nometa tasss.... Yana shuka dukkan abunda kasani nafannin noma kuma yana kiwo, gashi abun duniya bai rufe masa idoba sam... YANA SHUKA. SHINKAFA, ALKAMA, GERO, DAWA, MASARA, WAKE, DOYA, DAN KALIN TURAWA DANA HAUSA KUMA YANA DA MANYAN LAMBUNA GUDA BIYU DAYA LAMBUN ANA SHUKA KAYAN MIYA NE DA VEGETABLES. DAYAN KUMA ANA SHUKA DUKKAN ABUNDA YADANGANCI FRUIT'S NE... INDA KUMA FANNIN KIWO YAKEDA RA'KUMA, SANU, TINKIYOYIN NAN MASU KAMAR SHANU, DA AKUYOYI DA KAJI DA ZABI, DA TALO TALO, 'DAWISU, JUMUNA, AGWA GWA TANTABARU DA AKU, DA TSUNTSAYE MASU KYAU WA'DANDA YAKE KIWON SU... Akoda yaushe idan yayi noma yakan futar da wadda saiya bawa dukkan "yan 'kauyen JANIKI abuncin dazasuyi sama da wata 3 suna ci ya ajiye wanda zaici nashekara sanann yafutar dashi yasiyar aburni cikin garin kano... Hakama kuma kiwon yana futar dana jama'a sannan kuma yafutar dana siyarwa, idan yasiyar yakan siyi gonakine da kud'in ribar noma kota kiwo. Matar sa d'aya Binta sunan ta Hjy fatima dan tare sukaje aikin Hajji.. "Yan 'kauyen nan suna matu'kar girmama wannan ahali kuma anajin maganarsu sosai... Dan saboda karamcin mahaifinsa, dakuma kunya ta mahaifiyarsu... Hjy Binta marainiyace ta taso bata da uwa bare uba dan duk sun mutu mahaifinta yarasu tun tana ciki, inda mahaifiyarta itama tarasu lokacin data haifeta, ta tasone awajen...... ✍🏻✍🏻✍🏻 *Keep waiting my fan's*🤗🤭 *Mrs Hallsad ce*🤩🤩 *Gamasu san fara biya dawuri saisu tuntu6i wannan number 08032762588_ 08162889618* *Gamasu san sufara biya da wuri saiku tun tu6i wannan number 08032762588* *_Idan kuma ta account ne_* *_Acc 0110015052_* *_SADIYA ABDULLAHI UMAR_* *_ECOBANK_* ```Idan kuma katin wayane na #400 ne kachal``` ```Comment section kuma #200 ne kachal wannan sau'kine agareku My special group kuma Da``` *'Dan shaye shaye ne* 🍾 *Am 16 years old*
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40