Skip to content

Chapter 5

Chapter 5

Bakin Rijiya Book One Complete Hausa Novel 1,253 words 0 views Progress saved
Download Book

snacks ba" shi mamakin wani shagwaba da take masa ma yakeyi,san yan kwanakinnan ya kasa gane kan kanwar tasa se kallonta yayi yace "jeki ki kawo mun koma meye da aka gika kuma kizo ki tayani zaben kalan decoration da zamuyi gun dinner" batayi magana ta juya tanajin wani zafi a ranta,abincinma kasa dawowa kawo masa tayi shikuwa dama hankalinshi na online yana neman decor na bugawa a jarida sabida yaci burin wannan auren.....koda taje daki ta kwanta kasa yin komai tayi a haka huda ta kirata "Huda yadai?" "lapiya lau lil friend,zanzo gidanku da mijina da zan saura zuwa 4 na yamma seku gaisa,jiya jiyannan ya dawo daga uk ya matsamun yanaso yaga wannan poojah din danafi santa dashi" murmushi kurun tayi tace "toh" har yamma bata fitoba gashi mommy tana abuja, a haka har Huda tazo gidan,kallonta tayi bayan ta shigo bedroom din ta ganta a zaune tace "Poojah lapiyanki kuwa?? Tunda na kiraki naji muryanki wani iri" dan guntun tsaki taja tace "Huda wlhy na tsani inji ana zancen aurennan na yaa shaam gaba daya dena riqa ji jikina yana mutuwa,kuma banajin dadin rayuwata" kallon nutsuwa huda ta mata sannan tace " Hafsat lapiyanki kuwa?? Meye hadinki da auren yayanki keda ya dace ace kina masa murna ma kinmaga yanda kika dawo kuwa,waini yau dinnan ma kinci abinci?" lumshe idonta tayi sannan ta bude su a hankali zuwa yanzu har sun cicciko tace "Huda wlhy banida lapiya wataqila aljanaine suka shafeni,bana iyacin abinci tun bikinnan saura wata d'aya sannan kuma bana iya zama banga yaa shaam daga zaran na wuni ban ganshiba sena ringa jin zazzabi na damuna kuma idan muna tare banaso mu rabu,huda anya kuwa ba aljanai bane suka shafeni??" sosai huda ke nazarin kalaman hafsat,secan ta nisa tace "Poojah da gaske uwarku d'aya kuma ubanku d'aya da yaa shaam?" d'an tab'e fuska tayi sannan tace "wannan wane irin tambaya ne huda,wlhy uwarmu daya ubanmu d'aya dashi wannan bako tantama,bayan haihuwarshi kuwa ancire rai za'a kara samun haihuwa Allah ya kawoni" jinjina kai huda tayi jikinta duk yayi sanyi,tabbas hafsat abin tausayice domin kuwa wannan ba tantama san yayan nata takeyi kuma ta sani sarai koma menene akwai wata a qasa,ubangiji baya taba jarabtar bawansa da abinda baze iya d'aukaba,tayaya ma kanwa zata so yayanta har haka,amma a sarari se wayancewa tayi tace "Hafsat kiyayyar dakikewa matar da yayanki ze aura tayi yawa hadda kasa cin abinci har haka"murmushi kurun tayi domin kuwa ita kanta batasan cewar soyayya bace aranta!!!!!!!!! [1/10, 9:57 PM] Billy Galadanci: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi Vote me on whattpad@chi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 05 Da dare bayan isha malaminsu na islamiyyah yazo,sam hankalinta baya jikinta haka tafito tafiya takeyi tamkar wacce k'wai ya fashewa a ciki gaba d'aya hankalinta baya jikinta,motsi d'aya idan tayi da tunanin yayan nata take yinshi, A farfajiyar gidan ta hangoshi yana waya se raha yakeyi kallo d'aya zaka masa ka tabbatar cewar yana cikin farin ciki,haka kawai lokaci d'aya ta tsinci kanta dajin wani haushi mara misaltuwa ta tabbatar da Aunty leemah yake waya,kan tayi aune hawaye ya fara sintiri akan fuskarta,juyawa tayi sam bazata iya zuwa makarantar ba,karo tayi da mero tana kukan,kallon mamaki mero ta mata tace " kulele lapiya dai?? Meyake damunki?" batace komai ba tayi sama abinta rufe kofar tayi tana rusar uban kuka tarasa meke damunta...Allah sarki hafsat ga quruciya yarinya yar shekaru goma sha biyar na neman shiga damuwa akan abinda ta kasa gane meye shi,haka hafsa ta dawo sukuku dukta rame tayi baqi sam bakace ita bace,a haka har lokacin bikin yayan nata yazo..... A parlo zaune ta tarar da Daddy da momy suna hira,zuwa tayi ta zauna kusa da momy batace komai ba,kallonta baban yayi yace "Hafsatu kulele na meyake damunki ne wai kwana biyu?" murmushi tayi kurin batace komai ba momy tace "Girmane fa yatasowa Hafsat ai Alhj baka ganin wani sabuwar nutsuwa daya tasowa kulelen taka" dariya yayi yace "yar daddy gashi kinyi qanqanta da zuwa jami'a wane skul zaki je ko computer school zan sakaki?" murmushi takumayi sannan tace "Daddy naci jamb fa,kusan 240 kumama ai yanzu na girma banwa jami'a qanqantaba dan Allah idan na samu admtn ka barni naje" "ba damuwa yar daddy Allah ya sa ki samu admtn din,wane couse kikeso?" "Education English nacika dakuma pure Elhglish duk wanda na samu zanyi ne" adua ya mata kanwani yayi magana sega yaa Shaam ya shigo durkusawa yayi ya miqawa daddynshi envelope,wasu invitation cards ne masu kyau aka ciro daga ciki,daddy se washe baki yakeyi yana ya kalli yaronshi yace "Allah ya sanya Alkhairi my son,ranar da akayi reception ranar zamuyi tarin bude clinic dinka,sabida yafi" haka kawai hafsat ta kasa controling kanta ganin invitation card na d'aurin auren ta saka kuka wiwi,kowa hankalinshi ya dawo kanta se tambayarta suke lapiya? Amma i a da gudunta ta ruga dakinta,ta fad'a kan gado se kuka me karfi ya subuce mata hannu ta saka ta dafe inda takejin wani azababben radad'i a haka Shammaz ya shigo ya sameta hannu yasaka ya d'agota ya d'aurata a jikinshi yana mejin tausayinta a hankali ya furta "Little sister meya sameki har haka? Waye ya tab'aki kike wannan uban kukan haka?" acikin kuka tace "nima ban sani ba yaa shaam ko wane lokaci idan akayi zancen aurenka sena riqa ji tamkar zan mutu nabar duniya gaba daya,idan na wuni ban gankaba banajin dadin Rayuwata idan naga kana murna kana farin ciki indai akan zancen aurenkane sena riqajin zuciya na yana tafarfasa yaa shaam wlhy banasan kayi aurennan kaga nan? Ta nuna zuciyar ta da hannunta "zafi yakemun zogi nakeji tamkar zan mutu,tun saura wata daya aurenka na rasa nutsuwata duk sanda na tuna ko abinci bana iya ci bansan meyake damuna ba anya yaa shaam baka ganin aljanaine suka shafeni?? Mesa ada ba ruwana dakai? Mesa ban damu da rashinka ba akusa dani? Mesa ada bana leqen shige da ficenka ta window? Meyasa ko maima yaa shaam,a yanda nakeji gameda zancen aurennan idn akayishi mutuwa zanyi" k'ura mata ido kurin yayi harta kai aya,mamakin kalamanta ne yake shirin birkita masa k'walwa sam yakasa saisaita tunanin shi idan har abinda zuciyar ke sanar masa gaskiya ne lallai kuwa da babbar matsala a gaba,sabida sam shi wannan yarinyar kallon qanwa yake mata uwa daya uba daya,kai koda ba haka ba shisam idan ba leeman shiba se rijiya,gaba daya hankalinshi ya tashi cikeda dabara ya kalleta yace mata "Lallai kam hafsat se aljanai sabida kin taba ganin inda qanwar mutum uwa daya uba daya tayi kishi kotaji haushi akan zeyi aure,ki sani su e sukeso su shiga a tsakaninmu sam basa san suga muna qaunar junanmu,kuma ta Allah ba tasu ba sabida haka kiyi hakuri ki dinga adua kinji,inshaa Allah zasu rabu dake,kuma karki sake ki fadawa kowa wannan maganar" kai kurun ta gyad'a masa yayi da mero dake jikin k'ofa a lab'e ta dafe qirji tana salallami domin kuwa tun ba yauba ta fahimci sarai hafsat san shaam takeyi,inkuwa hakane iska tana wahalar dame kayan kara domin kodajin wannan zancen dayaa shaam yayi ta kula baya ma buqa tar ta sanarwa wani atilastashi aurenta yafi

Table of Contents

Chapters

44 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44