Chapter 28
Chapter 28
yana sani ya miki haka,sabida yasan bashi bane yayi kisan so kekuma bakida wani hujjan dazaki iya cewa aa bayan an gama shari'ar,shawarata anan shine kije ki lallab'ashi" kallon dattijon tayi tace "Daddy dan Allah ka bashi hakuri akan ya janye wannan zancen nidai bana sansa,kuma idan su daddy sukaji nayi wannan shirmen bazanji da dad'i ba" kallon ta yayi shima yace "To hafat kije gobe zan sameshi da kaina,suna kokarin barin wurin kanwar sayyeed datazo hutu daga india ta shigo,se kallon shammaz takeyi,suna fita ta biyo bayansu da suruun ganin hafsat,a can tace da hafsat "T loojah waye wannan?" hafsa tayi sannan tace "Bros shaam my big bros kenan"murmushi tayi "hes handsome ina sansa kuwa?" zare ido hafsat tayi "Da gaske Baby?" "Ea mana da gaske wlhy" murmushi tamata tace "Idan zaki auresa shikenan sena gaya masa" dariya tayi tace "Zan aure sa mana ai yafiki kyau" haka dai suka rabu baby se matsawa take da zancen shaam,koda sukaje mota hafsat ta gaya masa dariya yayi yace "Ina ni ina ba indiya rufamun asiri" cike da zolaya tace "Kai yaa shaam banda boye boye fa,Allah ina ganinka se wani kallonta kake kana murmushi" dariya yayi yace "Ina wasa dake zan mareki wlhy" seda sukaje gidan sannan ya karbi numer din baby haka kawai yakejin yarinyar ta masa wannan zankadediyar yarinyar lolxx. Qememe muhammad ya kafe akan lallai baze janye qudirin saba kuma nanda sati daya zeyi auren danita,su daddy hankinsu ya tashi kowa gani yakeyi auren manufa ne na rama sunansa da aka nemi batawa zeyi. Waya kawai ya kira hafsat bayan magaribar ranar yace da ita ta sameshi a mota,tana zuwa ta shiga gefen me zaman banza ta gaidashi,fitilar motar ya kunna fiskarsa ba yabo ba fallasa yakai hannunshi ya daga hannunta dake ciwo,dan kara ta saki ya juyo ya kalleta itama d'in shi take kallo harta soma kwallah,dauke kanshi yayi sannan yace da ita "Har yanzu hannun nan be gama dawowa daidai bako?" batace dashi komai ba se hawaye,tausayin kanta takeji sabida sosai take tsoron muhammad,hannu ya saka ya share mata hawayen daya gangaro mata yace bayan ya dauke kanshi "Mesa kike kuka hafsa? Banasan ganin saukar tsadadden hawayenki yana zuba a banza kinji" sauke kwayar idonta tayi kasa batayi magana ba,ya sake cewa "Yanzu sanar dani me dame kike buqata,bazakiyi shagalin biki ba,ni zanyi dinner da reception sabida yanzu ne zanyi auren soyayya na kuma zab'ina" kallon shi tayi tana kuka tace "yaa muhammad dan Allah kayi hakuri" dagowa yayi a karo na farko "Hakurin me kike bani" kukan ta ne ya tsananta ta dukar da kanta taci gaba da yi,tafi minti talatin tana kuka amma bece da ita komai ba seda dan kanta tayi shiru,kanta ne ya soma sara mata ta bud'e mitar da nufin wucewa cikin gida yace cikin izzah "Nine nace dake na gaji dajin wannan zazzaqar waqar da kika sakani agaba kina reramun? Maza dawo kici gaba dayi harse ya isheni" kallonshi tayi cikeda mamaki idanta ya kad'a yayi jajir,yakuma cewa "Dawo mana nace ki rufe murfin" a hankali ta sako kafafunta ciki batare da tayi magana ba "Kalli idanki hafsat,duk yayi ja sabida bakyajin magana,nace dake kukan na menene amma kinki ji,kin zauna kina kuka sekace wacce ke rero waqa,idan ba so kike na sassab'a miki ba karna kuma ganin hawayenki wlhy,sanar dani yanzu tsakanin ki da Allah menene kikewa kukan?" sadda kanta tayi kasa tace "Auren ne bana so" kallonta yayi ya sakar mata murmushi "Banida maganin wannan gaskia,so kiyita kukan,shika d'aine damuwar kodai da wata bayan wannan?" sadda kanta tai a qasa tace "So nakeyi ka tausayawa rayuwa ta ka agazamun ka bar aurennan har nan da wata biyu na roqe ka yaa muhammad dan Allah" kura mata ido yayi na yan dakiku kan yace "sekin mun alqawari guda biyu,tsakaninki da Allah" kallonshi tayi amma batace dashi komai ba yace "Na farko sekinmun alqawarin bazaki taba kawo matsala me kamada kin fasa auren ba idan na qara miki lokaci,na biyu kuma sekin mun alqawarin bazaki sakeyin kukannan agaba naba sabida gaskia banaso yana batan rai" yawu ta had'iya tace "Abba haris ya sanar dani muhimmancin Alqwari sabida haka bazan taba fasa auren kaba,sedai idan kaine kace ka fasa,kukan ma zan kwatanta" gyada kanshi yayi yace "Nima ai alqawarin auren ki nayi,idan ko bazaki karya ba ni mezesa na karya, nasan muhimmancin alqawari ai,kije na yadda nanda watanni uku idan munada rayuwa se ayi auren" godiya ta masa ya tsare ta akan setayi dariya seda tayi dariyar kuwa sannan suka rabu,se dadi takeji...... Shaam ba kad'an ba yake jin yana san baby,sedai be sanar da kowa zancen ba se daddy kasance war shi abba haris har wannan lokacin fushi yake dashi,sedama hafsa ta saka baki yake dan sake masa kadan,cikin sirri kuwa aka shirya auren sa da baby tare da nasu hafsa,sam haleemah batasan wainar da ake toyawa ba,tunda taji hafsa zata auri wani shikenan hankalinta ya kwanta...... Hafsa gabaki daya ta rame tayi baqi,sam wani jarababben tsoron muhammad takeyi gashi abu mafi ban mamaki shine tunda ya tafi akan ya dage zancen aurensu be qara zuwa wurin taba kuma gabki daya ya dena kiranta,ita kuma duk sanda tayi yunqurin kiransa se gabanta ya fad'i, huda ce ta fad'o mata arai ta d'auki wayar ta kirata,komai da ake ciki ta sanar mata,hudan kuwa ta bata shawaran akan lallai ta kirasa,kuma ta basa kulawa as if tana matukar sanshi,wasan da yake so su buga idan ba ta wannan hanyarr ta biyo masa ba lallai akwai matsala,sabida ya shirya daukar fan sane,sosai tayi wa huda godiya koda sun dade basu hadu ba amma sosai suke hurda,huda yanzu tana germany itada mijinta. Cikin sanyin jiki kuwa tayi kiransa a waya,kamar baze daga bama,se can taji muryarsa me saukar mata da fad'uwar gaba yace "Hello" sanda ta d'anyi jimm sannan tace "Yaa muhammad Barka da yamma" gyaran murya yayi yace "Barka dai" a ta k'aice,jikinta ne ya qarayin sanyi tace "Dafatar kana lafiya" "Ina lafiya" itace amsar daya bata,runtse idonta tayi sannan ta kara budewa tace "Yaa muhammad ka gane me magana kuwa" kamar baze amsata ba yace "Na gane mana ba hafsa bace?" "Ea nice ya kwana biyu?" tafad'a cikeda jin zafin wulakancin data janyowa kanta "Lafiya lau,ya akayi ne?" dafe kanta tayi dayake barazanar rabe wa gida biyu tace "Dama naga kusan watanni biyu ban jika ba,shine nace Allah ya sanya lafiya" "Lafiya lau mana,me zan miki to? Ina auren Agreement ne zamuyi,sekace wata soyayya ke tsakaninmu dazanta damunki,kokuma daze kasance komai nawa sekin sani?" kasa hakuri tayi tace "Koda na kirak bakaji na ambaci soyayya ba ai,danni a wannan zamanin banajin ma akwai soyayya,kurin dai kamata ya sanya nayi kiranka sabida ni nasanta" sarai ya sani magana ta gaya masa,amma seya dake yace "Ni ai tun farko na sanar dake yanzu ne zanyi auren soyayah, kuma zab'ina bakijiba ne,kece bakya sona so meye zesanya na nanuqe miki?" jan dogon numfashi tayi sannan ta furzar da wani iska me zafi tace cikin wata rikitacciyar murya "Yaa muhammad" shiru ya mata tace "Why?" cikin dakakkiyar murya yace "Hafsatu manga yar sarki wacce maza ke rarrashi,koba haka taken yake ba?" ganin ze raina mata hankali ya sanya tankashe wayar ta ajiye,be kuma kiraba se
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44