Skip to content

Chapter 24

Chapter 24

Bakin Rijiya Book One Complete Hausa Novel 1,251 words 0 views Progress saved
Download Book

cikin kuka sosai, girgiza kanshi yayi cikeda damuwa yace bayan ya zare madubin dake fuskarsa ya shafi idonsa "Bazan yadda cewar idon baze bude ba sedai idan basu san kan aikinsu ba,akwai likitana dake a china,a can zamu da ita,idan mahaifanta zasu yarda zan dauki nauyin komai na aikin da tafiyar" shiru momy tayi hafsa ce tace "Niba inda zani,ku barni anan kawai Allah ze bani lapiya" kallonta yayi yace cikin fada "Hafsat idan kika kuma saka bakinki amaganar manya sena sassa b'a miki wlhy" tsoronsa ne ya darsu aranta lokaci daya,tanajin tsoron ayi tafiyar aje garin gyara ayi barna,tunda lapiya ta qalau,amma dai bata kuma cewa komai ba" sallama ya musu akan zece wurin su daddy da kanshi,yana fito wa ya hadu da shammaz,kallon kallo suka tsaya yiwa juna sannan ba tare da sunwa juna magana ba suka raba kowa ya wuce Hmmmmm toophaa ga oga muhammad ya iso Mom Nu'aiym [2/8, 8:47 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅 Love story 2018 Billy galadanchi *HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.) Wattpadd@ 68billygaladanchi *Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha* 22 Tunda hafsat taji zancen zuwa china se tafara tsoron tafiyar,lallai idan har ta kuskura akayi tafiyar nan tofa se an ce za'a yi mata aikin,kuma lallai garin neman gira rashin idone ze biyo baya,tana kwance tayi shiru uncle say ya turo kofar dakin ya shigo da sallamar sa,yunkurawa tayi ta tashi zaune sabida yanayin hannunta da har yanzu da sauransa ta tashi zaune,kura mata ido yayi yana murmushi sun dad'e sosai suna hirar su ta masoya kan ya mata sallama harya kai kofa ya juyo ya kalleta,murmushi ta sakar masa tace "Uncle say yau nakula ka nacewa kallona lafiya dai?" girgiza mata kanshi yayi "Ai dama can kinsan ni sam bana gajiyawa da kallon kyakyawar fuskar nan taki" lumshe idanta tayi cikin sanyin murya tace "Nima haka baby say" batare dayayi magana ba ya juya sanye da murmushi a fuskarsa, gabaki d'aya wani tsoro ne yakeji da yawaitar fad'uwar gaba yarasa dalili seyakeji gabaki daya duniyar tana juya masa.... Shaam zaune yana dannan wayanshi a farfajiyar shan iska dake cikin gidansa haleemah tazo ta sameshi,cikeda rashin mutunci tace dashi "Wai kaikam me kake nufi dani tunda qanwar ka ta qara zama naqashashiya kake wani shamun mur sekace nice nan na nakasata?" dagowa yayi ya kalleta yace "Me kuma ya kawo maganar hafsat anan?kuma ban sanar miki cewar kidena ce mata naqasashiya ba?" tsaki taja "Meye laifina danna kirata da sunan dayafi dacewa da ita? Wlhy akan hafsat zan baka mamaki" "Kya daiji dashi,amma ki sani wlhy sena aureta a nakashen,ni tazo ma ta haifamun yara tunda kin zama juya,narasa me kika dauki duniya dabazaki haihu ba hakanan,shasha kawai me bakin hali" a fusace ta furta "Kafi kowa sanin cewar niba juya bace tunda na haifa maka ya qanwarka ta kashe,kuma ka sani wlhy koba hafsa ba indai banice zan haifa maka yara ba kaida haihuwa har gaban abada kuwa" tsaki yaja ya miqe yabarta gun a tsaye...... Tunda haleema taji zancen auren hafsat da say zeyi seta tashi hankalinta ta sani sarai boka ya sanar mata ba ita ba haihuwa har abada sannan kuma gashi yanzu sam asiri ya dena tasiri akan sa,bokansu ya sanar musu sun sanar mata cewar lallai ya riqe addininsa yafi karfinsu ko kusantar sa ma gaba daya bazasu iyaba, wurin ummansu taje ta zayyane mata komai atake kuwa aka shirya cewan ayi airin akan hafsat gaba daya tunda itace banza.....hmmmmm Say yana zaune tare da hafsat suna hira muhammad ya shigo cikeda taqama yaud'inma acikin shigarsa ta shadda fara amma ba babbar riga bace, yau dinkine dai na zamani me kyau komai nasa fari,hannu ya miqa masa suka gaisa sannan ya mayarda dubansa akan hafsat da alokaci daya qirjinta ya soma dokawa "Hafsat ya jikin ki?" kallon sa tayi tace "Naji sauqi Alhamdulillah" shiru sukayi dukansu su uku can muhammad yace "Ke baki iya gaisuwa bane,ko bakisan girman manya bane?" idon tane ya ciciko sannan tace "Kayi hakuri yaa muhammad" dan guntun tsaki yaja sannan yace "Mesa zakiyi karyan bakya gani kuma bayan sarai idanki lapiyanshi qalau,bayan yanzu gashinan kina kallo na kuma kallo daya na miki na tabbatar kina gani kema kuma kina kallo na ido cikin ido duk sanda nayi magana" shiru tayi yayinda say ya miqe tsaye yace "Amma yallabai anya bakayi shishigi da yawa ba kuwa,baka ganin cewar mu doctors mune mukeda haqqin komai nata bawai kaiba,kuma mun tabbatar cewar idan nata bashida lapiya kai miye naka aciki? Kuma idan taimakonta zakayi mu bawai mun kasa bane ka barshi kawai mune family nata zamu mata komai ma har fita wajen" shiru ne ya ratsa wurin dukkansu sun bata dakiku suna kallon juna kafin muhammad yace "mesa arayuwa zaka kalli girma na kace zaka kirb'a mun k'arya,zanyi magana a d'aga licence dinka na zama likita idan dai har tsabar hauka wannan idan ne zaka ce baya gani" jin ankira hauka ya sanya say ya dago da fuskarsa gaba daya cikeda fusata "Kai waye? Mekake taqama dashi? Me kuma kakejin ka isa kayi da zaka kalli tsabar idona kace dani mahaukaci,dakake iqirarin cewar zaka sanya akarbe license dina mesa kai bazaka qwace ba idan ka isa,tunda nake ganin mahaukata bantaba ganin mara hankali irin kaba,tayaya zaka kalli idan mutum kace masa mahaukaci beside waye ma ya baka damar yi mana iko anan?" wani murmushin qasaita yayi sannan ya shafi gemunsa yace "Ba license d'inka ba har abu mafi muhimmanci arayuwarka zan iya kwace wa shine rayuwarka,kuma wlhy kaf fadin Nigeria ba wanda ya isa yamun komai,kuma zaka gani wlhy,ke kuma karna dawo asibitin baki gayawa doctors masu hankali kina gani dakyau ba" yana gama fad'ar hakan ya juya ya fita hafsat ta kasa koda motsi dakyar ta hadiye wasu yawu sannan ta furta "kayi hakuri uncle say ka rabu dashi,wannan mutumin na tsaneshi wlhy" matsowa yayi kusa da ita yace "Mesa nakejin matukar tsoro da yawaitar fad'uwar gaba hafsat? Gabaki daya banjin dadin tawa rayuwar sekace nine nake ciwo,wlhy hafsat hankalina baya kwance,bawai wannan muhammad dinba da kalamansa aa, komai ma senake ga kamar mutuwa zanyi ayanda nakejin duniyar tanamun qunci" zare idanta tayi waje "Haba Uncle sayyeed? Ya kake magana haka? Inshaa Allah atare zamu rayu babu abunda ze sameka,kuma inshaa Allah atare zamu mutu" murmushi ya sakar mata yace "Zanje gida na dawo nanba jimawa inshaa Allah" batayi magana ba haka yaja kofar ya fita, ita dinma dai haka kawai takejin tsananin faduwar gaba me tsanani,hankalinta sam baya jikinta,koda momy tazo bayan isha abinci kurin tabata sukayi sallah seta kwanta,say yazo sun dan taba hira,wuraren karfe tara yamata sallama akan seda safe ze dawo,har kuma ze fita ya dawo ya kalketa yace "Hafsat idan har Allah yasanya wani abun yafaru dani kimin adu'a ita kadaice nake buqata agareki" kura masa ido tayi dukta rude murya na rawa ta furta " mesa kake irin wannan tunanin wai? Sabida kawai wannan muhammad din yayi wannan furucin seka damu,inshaa Allah ba abunda ze iya yi maka" murmushi ya sakar mata "Hafsa nafasan waye muhammad,sam yayi furucin dayayi ne sabida kawai ransa ya b'aci amma mutum ne me nagarta sosai,matsalar sa d'aya kafirar zuciya da rashin human relation amma hes

Table of Contents

Chapters

44 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44