Skip to content

Chapter 35

Chapter 35

Juyin Kwado Book One Complete Hausa Novels 1 507 words 0 views Progress saved
Download Book

Hatta da wannan tafiyar da muka yi ta samo asali ne daga gujewa karɓar shugabancin kamfanin!” “Abin tausayi!” Cewar Uwais. “Me ya sa yake saka wani abu a saman idonsa?” Sana ta tambaya. Adam da Ivana suka yi dariya. “Glasses ake kiransu, kuma su ne suke taimaka masa wurin gani, ba tare da su ba ba zai iya ganin ko da tafin hannunsa ba!” “Na gane!” Cewarta tana waigawa tare da kallon hanyar da ya bi. “Adam taimaka min na miƙe!” Cewar Ivana, Adam ya taimaka ya ɗagata. “Ina za ki je?” Ya tambaya ganin ta yi hanyar kogin dake gefe da su, Ivana na ɗingisa ƙafa tace. “Zan wanke fuskata ne” Da haka ta ƙarasa bakin kogin, ta tsugguna ta fara wanke fuskarta, sai da ta gama ta miƙe, tana shirin komawa inda su Uwais suke ta ga wani abu ya faɗo gabanta tim!. Razana ta yi ta ja baya tana ƙarewa budurwar da ta faɗo gabanta kallo. Kafin ta yi wani yunƙuri budurwar ta ruƙo wuyanta, sannan ta buɗe fuska-fukanta ta tashi sama da ita, hakan yasa ta ƙwala ihu domin naiman ɗaukin abokanta. Lokacin da Su Adam suka iso bakin kogin har budurwar ta yi nisa da ita a sama. “Ivana!” Cewar Adam cikin matsanancin tashin hankali. “Me ya samu Ivana?” Cewar Adam da ya ƙaraso wurin da gudu, shi ma kuma sai a lokacin ya lura da Ivana dake sama. “Wace ce waccan?” Arman ɗin ya tambaya yana kallon budurwar dake tare da Ivana. Kafin wani ya amsa masa Uwais ya buɗe nasa fukafukan zai tashi sama, Arman ya dakatar da shi. “Uwais! Zan tafi tare da kai!” “Zo mu je!” Kawai Uwais yace, sannan ya riƙe hannun Arman ɗaya, ya tashi sama da shi, suka bi bayan budurwar da ta ɗauke Ivana. ...End of book 1... ____________________ _Humm! Shin wacece wannan wadda ta sace Ivana?_ _Shin kuna ganin cewa Uwais da Arman za su iya cetonta?_ _Wata ƙiyayya ce tsakanin Eid da Malik Cangaz?_ _Wani abu ne ya samu matar Eid da ahalinsa da har ta kai ga yana son ɗaukar fansa!_ _Me Malik Safraz yake shiryawa?_ _Wani ƙudiri ne ya sa Sana matar Malik Wasimudeen shigowa cikin ADVENTURERS?_ _Shin kuna ganin dakarun Malik Cangaz za su iya riskar ADVENTURERS?_ _Mece ce makomar auren da Malik Cangaz yake shiryawa?_ _Yaushe ADVENTURERS ɗinmu za su riske ƙofar Malik Cangaz?. Shin za su iya samun nasarar buɗe ƙofar? Shin za su koma gida ko a'a?_ Domin ci gaba da karanta book 2 za ku biya ₦400 for regular group. ₦800 for VIP to. 5487270431 Salma Isah Monie point Shaidar biya kuma ta 08130172702. Sannan za ku samu complete book one and 2 on Arewabooks, kada ku manta ku yi following ɗina domin samun notification da zarar na yi update. Ina me tabbatar muku da book 2 is giving 🔥🔥🔥. A har kullum, godiya ta musamman zuwa ga masoyana a duk inda kuke. I ❤️ like WUJIGA-WUJIGA 💋. See you in book 2. Best regards Salma Ahmad Isah ✍️ A.k.a Candy🦋 A.k.a Bahaɗejia🐎 2024...

Table of Contents

Chapters

35 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35