Chapter 38
Chapter 38
hankali,, nasoyi na gaskiyane kadai zei yasani cikin addu'oinsa,, nagode🙆🤦♀😥* 5⃣6⃣&5⃣7⃣ A hankali nijlah tafara girgiza Kai hawaye na qoqarin bin fuskanta' ki hadiye kukan nan Kona barki cikin wannan kazantan. Dasauri nijlah ta tasa hannu ta rufe Baki tana cewa' Allah nadena Dan Allah kayi hakuri Ka wankemin. Kai ni mashkur na hadu da aiki' anya kuwa Zan iya wanke wannan abun, yafada Yana kallan yadda jinin ya daskare a qasa gefensa yafara bushewa. Ganin bashida yadda zeyi yasashi yin ta Maza ya miqe tsaye da nijlah a jikinsa. Tana hannunsa ya cika ahun wanka da ruwa me zafi bayan ya Gama ya yafara cire Mata kayan jikinta' nan ya sata cikin ruwan zafin Yana cewa' kinga kiyi hakuri ki zauna ciki nasan maranki Yana ciwo ko? Daga masa Kai tayi tana tashi tsaye a cikin ruwan tace' bazan iya Zama ba da zafi' Beyi magana ba ya qara ruwan sanyi ciki Amma duk da haka nijlah taqi Shiga tana masa kuka. Banza yayi da ita ya qarasa gurin data bata yafara sharewa da tsintsiyan kwakwa' bayan jinin ya Ragu ya barbada omo da jik,, Saida ya Gama ya tattara kayanta ya zuba cikin warshing machine. Nan ya dawo inda nijlah ke tsaye ta zuba masa ido,cikin tsawa yace' Wallahi kika Bari naqaraso nan Baki gyara jikinki ba Saina sa bulala na Zane Miki jiki' kazama kawai' ke ko San rabuwa da wannan jinin bakiso gashinan ruwan haryayi sanyi. Nijlah na kuka ta Shiga ciki tana wanke jikinta' kimin Shiru anan' dukanki nayi ko zagi dazaki sani gaba kina kuka' maraji kawai.. Shiru nijlah tayi tana wanke jikinta' harta Gama be qara yimata magana ba ya chanza Mata saban ruwa ya Mata wanka da kanshi' Saida yayimata Sabi 5 kafin ya kyaleta, hakan ma danta fara bashi hakuri ne tana ciwa da ciwo . Towel ya dauko yasata ciki tare da bude Mata kofa yace' jeki shafa Mai' Maqale kafata nijlah tayi tana kallan shi' kije nace Nima yanzu Zan fito wanka zanyi naqarasa dauraye Miki kayan. Tabe Baki nijlah tayi tana magana a shagwabe' ni dai saika daukeni Ka kaini can' ta fada tana Nuna dakin. Besan lokacin da murmushi ya subuce masa ba' kallanta yayi yaga bata da niyyan tafiya Dan haka yasa hannu biyu ya dauketa' Kan gado ya ajiyeta tana dariya nan ya dungure Mata Kai Yana cewa' Kifa nutsu kisan kinyi aure' nan ba a gaban Kaka kikeba. Turo Baki nijlah tayi tace' toba kace zaka yimin komai ba aidai naji lokacin da kake gayama Kaka da malam. Zaro Ido yayi Yana kallanta kafin ya bude baki da kyar Yana cewa' au shiyasa kikemin yadda kikeso ko? Girgiza Kai tayi tana boye fuska' nan ya Barta ya koma toilet, bayan ya Gama wanke kayan ya yi wanka me kyau ya gyara jikinshi,,nan ya fito ya dauka air freshener ya feshe dakin.. Kallanta yayi yaga yadda ta kwanta Kan gadon bacci harya dauketa' kallan bedsheet yayi yaga yadda tafara batashi da jini' kansa ya dafe Yana ambata sunan Allah tare da saurin daukan jallabiyanshi yasa. Da sauri ya fita Yana kwala Kiran maryam' Maryam ke maryam' da gudu Maryam ta ajiye yanka alayyahun hannunta ta qaraso inda yake' gani auta ta fada kanta a qasa. Amsa wannan da Allah kiyi sauri ki siyomin pant anan shagon bakin layi' har Maryam ta fara tafiya yace' kinga kiyi sauri ina jiranki anan' To tace tana tsoran tambayanshi jikin nijlah duk da tasan mashkur bame yawan fada bane kuma bashida zafi haka ta fita tana tausan nijlah. Bata Jima da fitaba ta dawo da baqar Leda a hannunta' da sauri ya amsa Yana Mata godiya ya koma daki. Tashinta ya riqayi Amma nijlah taqi tashi sabida bacci yamata dadi ba kadan ba' ganin tana bata masa lokaci yasashi daukanta be direta ko inaba sai cikin toilet' saban wanka ya sake Mata tana kuka tana komai ahaka harya Gama ya dasa Mata pant nan fa nijlah tace bazata Saba sai ya cire shiko Dan haushi be iya magana ba ya dagata Sama yasamata' qoqarin cirewa nijlah take ya bude baki cikin zafi Yana magana' Wallahi kika sake kika cire wannan abun Saina daukeki da mari, shashasha kawai'wai ya ina Miki Abu kina Neman maidani bawanki ya qare maganar muryanshi na rawa Dan harga Allah yafara gajiya da wannan wahalan Dan be Saba ba... Ganin yadda ranshi ya baci yasa nijlah Shiga hankalinta nan ta bude baki tana magana a hankali' kayi hakuri honey bazan qaraba' Wani irin sanyi mashkur yaji ya ratsa zuciyarsa har besan lokacin daya rungumota jikinshi ba Yana cewa' Keda Baki manta sunan Dana gayamiki ba shine Baki taba gayamin ba sai yau? Itama murmushi tayi tana boye fuska.. To fita muje nidai Dan Allah kidemin gaddama inba sokike aji kanmu ba Dama gashi masoyanki basa ganin qoqarina. Tare suka suka fito Yana riqe da hannunta,,nan ya cire bedsheet ya shinfida Mata wani' zoki kwanta anan ki huta kafin na samamiki magani ko' eh nijlah tace tana kwanciya Kan gadon.. Cikin sauri mashkur ya qarasa shiryawa ya dauka mukullin motanshi ya fita' Pharmacy ya Samu me kyau anan ya tsaya yayi musu bayanin abinda ke damun nijlah' murmushi Dr yayi Yana cewa' ok first period dinta ne shiyasa yazo Mata da wannan yanayin na ciwo Amma idan Ka bata wannan maganin Zata Samu sauqi da yardar Allah. Godiya mashkur yay ya amsa maganin tare da biyanshi kudin ya fita cikin sauri Yana tsoran Kada ta tashi taga bayanan ta cire pant din jikinta... Yana dawowa ya sameta zaune takasa bacci Banda ciwo babu abinda ke damunta' nijlah na ganin shigowansa ta tashi da gudu ta fada jikinshi tana cewa' Dan Allah honey Ka ciremin wannan abun ciwo yasamin a cikina ta qare maganar cikin kuka da tashin hankali. Sosai Mashkur ya tausaya Mata Dan likitan yayimasa bayanin irin ciwon da Mata ke Samu a wannan lokaci' hannu yasa ya rungume tsam a jikinshi Yana cewa' kiyi hakuri zai dena kinji.. Daga masa Kai tayi sabida tsabar ciwan dake damunta nan ya dauko ruwa ya ballo maganin ya kaimata Baki Amma saitaqi amsa ta rufe bakin. Be iyamata fadaba ya sa maganin a bakinshi ya zuba ruwa cikin' kallanshi kawai nijlah take taji yasa hannu ya daukota ya Dora Kan cinyarshi' bakinsa yasa yafara lakubar nata bakinta tare da qoqarin budeshi da hannunsa' Tureshi tafara tana kuka shiko ya yasa kafa ya matseta sosai ya kuma bude bakinta ya hade da nasa' anan ne ya riqa Dura Mata ganin har Saida ta hadiye kafin ya janye bakinsa a nata ya bata ruwa ta sha,, Shi kuma ya zuba ya kuskure bakinsa' sai yanzu yakejin dacin maganin a bakinsa sedai be damu da hakan ba tinda yayi nasara akanta ta shanye gaba daya.. Janyota yayi a jikinsa a hankali Yana shafa bayanta tare da manneta da qirjinsa, ta bayanta yasa hannu ya shafa maranta Yana lumshe ido,lokaci guda shauqinta dasan kasancewa tare da ita' nan ya maida kallansa gareta. Murya a kasalce yace' ina sanki nijlah' inasan wannan shagwaban naki sedai banisan taurin kai' inaso kidena kinji amaryata? Shiru tayi masa kama bada ita yake ba daga Baya tafara tinanin wayar dataji yanayi da Yasmeen jiya da dare
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46