Skip to content

Chapter 6

Chapter 6

Canjin Rayuwa Book Four Complete Hausa Novel 1,208 words 0 views Progress saved
Download Book

Ni ko cikin novels din da nake karantawa na turanci, labarai irin na turawa masu yin wata irin rayuwa da tasha bambam ta tamu, amma ban ta6a cin karo da labarin masu hali irin na iyaye na ba. Ismail yace, khadija inkin duba tsaf, zakiga cewa, kema fa baki kyauta musu ba. Yadda na samu labarin gatan da mahaifinki yayi miki, bai dace ki watsa musu qasa a ido ba. Amma shikenan duk abinda zai faru ya riga da ya faru. Bari in miki wani alqawari, na sani cewa arziki na Allah ne, amma inya bani, zan miki duk abinda kkso. In ya kai arzikina kamar na mahaifinki, zanyi miki fiye da abinda mahaifinki yayi miki. Inason ki rubuta wannan ki ajiye ko don sheda. Amma ynxun inason ki daina kukan nan, ki kuma yi haquri da yadda kk sameni. Ta runtse idanunta. Ina matuqar da na sanin dawowa ta hutu daga Dubai, na rantse da na san cewa duk wadannan abubuwa zasu faru dani, da na zauna can nayi hutuna. Daddy ya matsamin wai in dawo, ya kuma sake matsamin inje katsina. Ashe yamin hakane sbd ya daina sona. Ismail ya sake yin qasa da murya, "ki daina fadin haka khadija. Ki sani bawa baya iya gujema qaddararsa. Sannan bana zaton akwai iyayen da zasu daina son dansu. Kuma na tabbata inda iyayenki suke, ynxun suna tare da takaicin rabuwa dake. Hankalinsu yana kanki. Tace a'a ban yarda da batunka ba. Hankalinsu yana kaina ne zasu watsar dani bayan sun samu labarin halin da nake ciki? A dan qaramin tunani na kome nayi musu bai dace su banzatar dani ba acikin halin ciwo. Shiyasa nima nakeso ka nesantani dasu kamar yadda kayi min alqawari. Ta soma wani irin kuka mai shiga rai. Baisan lokacin da ya rungume taba ajikinsa. Kiyi shiru. Zanyi miki duk yadda kk so khadija. Saidai ina sake neman hadin kanki. Yadda kk sameni talaka, ki qara haquri. Kinji khadija? Kimin alqawarin zama na har abada. Ko na tafi makaranta ki zauna da yaya kinji. Haka dai Ismail yayi ta lallashin Mimi da kalamai. Kasancewarsa mai hikimar magana, har tayi shiru, ta kuma amince, tare da alqawarin ko baya nan kar ya damu babu inda zataje. [17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa 1⃣7⃣Ismail ne ya girka musu abinci, taliya ce yayi dafa duka, ya zabga kifi. Kuma Mimi taci sosai. Matsalarsa ban daki, amma tunda ga 'FO' din daya siyo mata, sai yace, tayi amfani dashi, zai dinga zubarwa. Cikin kwana ukun da sukayi, Mimi har nauyin Ismail takeji, domin ko cikin dare ta farka fitsari ko ba haya zaisa ta a 'FO' in ta gama, ta wanke sai yazo ya zubar, kuma ta lura yanada matuqar tsafta sosai sbd yadda yake gyaran dakin, ya wanke komai na girki, sannan yayi musu wanki. Wanka ne dai matsalarta ynxun, don acikin kwanaki ukun nan batayi wanka ba, sannan yana sata su danyi tattaki a cikin layin ya sagale ta a kafadarsa don tadan taka qafarsa. Sai dai damuwarta yana matsa mata sai ta saka hijabi, ita kuma bata saba da yawo dashi ba. Da ma shi ya sai mata sbd sallah. Yakan lallasheta da cewa, kinga duk kayanki matsattsu ne, khadija ki saka, in mun dawo daki, sai ki cire. A ranar ne Ismail ya daga katifa yayi share-share, har ya ciro ma Mimi Jakarta. Daya gama share-sharensa, sai ya taimakawa Mimi, ta koma kan katifar dama cikin zaure ya zaunar da ita. Sannan ya dauko Jakarta ya ajiye a gabanta. Har ta dauki littafin daya bata na tarihin Annabi Muhammad (SAW) ta bude tana cewa, ina page na ashirin da uku. Sai yace ga jakarki. Tace jefa ta can kan akwatunan can. "yace da kudinki a ciki fa." Ta dago ta dubeshi, sannan ta kalli jakar, "kudi?" yace duba mana. Ta ajiye littafin, sannan ta dauki jakar, ta zazzago kudin. Cikin mamaki ta kalleshi, "dama ba dasu ka biyamin kudin asibiti ba? Yace a'a. Tayi shiru tana kallonsa, ta sake cewa kodai bakasan dasu bane? Yace na gansu. Sai taga ya qara qima a idonta. Sai tace, nagode sosai, amma ka amshi wannan kudin kayi duk abinda kkso dasu, na baka. Yace, kudin da yawa khadija, ki riqe abinki. Tace babu abinda zanyi dasu. Amfanin dana debo kudin don inyi dasu basu min ba. Komai ya zama tarihi. In ma bakada buqatarsu, to zaka iya ba wasu masu buqata. Kuka ya kufce mata. Ismail yace, shikenan kiyi shiru, na amsa kuma nagode. Ya tattara kudin guri daya, yana tunanin me zaiyi dasu? Cikin baqar leda ya zuba su. A zuciyarsa yana Jindadi, domin ko babu komai, zai samu tarin buqatun dake gabansa. 1⃣8⃣Waje ya fita ya kira Mahmud cikin waya ya sanar dashi komai, Mahmud yace, Ismail ka gode ma Allah. Duk lokacin da wata matsala ta taso maka, sai kuma Allah ya kawo maka mafita. Kaga kana cikin matsalar abinda zaka bar musu in zamu tafi da wanda kai kanka zaka riqe don amfaninka, sai kuma ga wadannan kudin. Ismail yace, Allah shine abin godiya. Ni kaina nayi tunanin sassauci ne Allah ya turomin. Kuma fa kasan harda darajar aure ko? Inji Ismail. Mahmud yace, tabbas! Kasan aure daraja gareshi. Albarkacinsa sai kaga budi ko ta ina. Shiyasa ko yaushe nake baka haquri, ina tausarka a kanta. Kuma duk runtsi kar kace, zaka saketa. Ismail yace, insha Allahu zan kula. Amma fa karka manta ba sona takeyi ba, kuma nima harga Allah banajin sonta a zuciyata, tausayinta kurum nakeyi. Mahmud yace, "Allah yayi mana za6i mafi alkhairi. Ismail yace, Ameen. Sannan sukayi sallama. Ummin yaya Amina ce tazo ta kawoma Mimi faten wake hade da kifi. Sai Ismail yace, ummi zauna da aunty khadija inje gurin mamanki in dawo. Tace, to kawu. Amma ka fada mata inanan. Yace zan fada mata. Ya kalli Mimi, sai na dawo. Kai kurum ta daga masa. Sun tattauna da yaya Amina, inda sukayi shawarar a gyara ma Mimi dakin kakarsu saddam. Babansu saddam da ma ya Amince ta dawo nan. Yace, ai Ismail dansu ne tunda ance babbar ya uwa. Yaya Amina tace, ka ba Salisu aikin,, qanin babansu saddam. An kira Salisu yaga dakin, kuma Ismail ya fada masa yanason asa masa tayals a qasa, sannan a saka silin na zamani na roba, kuma a yi masu fenti duka Gidan, ya canke kudin da Salisu ya fada ya bashi harda na aiki. Sannan ban dakinsu yasa shima a duba, aka duba, yace abin tsugunno na zamani asa tayals a qasa ayi fenti asa wuta. Dama tsakar gidansu mulmule yake da siminti. Sannan ya ware wasu kudi ya ba baban su saddam yace, su siyo kayan abinci sbd halin yau da gobe. Bayan fitarsa itama yaya Amina ya bata 'yan wasu kudin ahannunta, sbd yasan Mimi ba zata amshi kudi daga wannan kudinba. Yace ta riqe do zuwa asibiti ko wata buqatar. Bayan ya koma ya tarar Mimi tana varci, ummi kuma tana zaune a tsakiyar dakin tana wasa. Yace, a'a varci tayi antin taki? Ummi tace, eh tana cikin karanta littafi, sai naga tayi varci. Ya kalli littafin, sai yaga littafin tarihin nan ne daya bata. Ya dauka ya duba yayi mata alama a inda ta tsaya ta

Table of Contents

Chapters

37 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37