Skip to content

Chapter 26

Chapter 26

Garkuwa Book One Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

ƙanwar tata suka nufi gida. Su kuwa Bappa da yaranshi da makiyayanshi anan sukayi al'wala, kana suka juya suka nufi cikin Rugar tasu dan zuwa masallaci. Yayinda ko wanne garke an bar mutun ɗaya sabida tsaro... Bayan sallan isha sunci abinci sun ɗan taɓa hira, kaɗan kana Bappa ya tarasu yana karantar dasu kamar yadda ya saba duk dare, da kuma safiya kafin a tafi kiwo shiyasa sam ahlin wannan Rugar Bani ba jahilai bane. Suna zaune, yaro yayi sallama, yace. "Wai ana kiran Shatu a woje". Ummey ce ta ɗan juyo ta kalli yaron tare da cewa. "Wake kiranta?". "Wai yace ince mata inji Ya Salmanu ne". Yaron ya faɗi. Da sauri Ummey tace. "A a Salmanu ne ya zobe? To maza kace ya iso mana ya zai tsaya a waje kamar baƙo". To yaron yace kana ya juya ya fita. Jim kaɗan sai gashi ya dawo gefen Ummey ya rusuna tare da cewa. "Yace wai ince mata, ta fito woje". "Da mamaki Ummey tace to gata nan zuwa". Sai kuma Inna ta ɗan kalli Shatu tace. "Tashi kije ai mun gama aikin ma". Ita kuwa Aysha dake zaune gaban Inna suna gasa tattabarun da aka yanka tunda yamma, kwano ta ɗauko a konɗonsu kana tasa gasassun tattabarun guda biyu. Tasa yaji a gefe, ta rufe, kana ta gyara wuyan hijabinta sannan ta miƙowa Junainah kwanon. A hankali ta ratsa gefen su Ya Giɗi ta wuce. Ummey kuwa da ido ta rakasu tana fatan Allah yasa fata da shirin Bappa da Arɗo Yabani ya tabbata. Suna fita suka sameshi zaune bisa dakalin ƙofar gidan nasu. Da sauri Junainah ta isa gareshi tare da cewa. "Oyoyo yaya Salmanu". Ajiye kwanon tayi a gefenshi. Da sauri yasa hannunshin suka tafa da hannunta data miƙa mishi, cikin sakin fuska da nitsuwa yace. "I miss you ƙanwali". Dariya mai ɗan sauti tayi tare da cewa. "Miss you too my dear". Dariya mai sauti sukayi a tare cikin jin daɗi wanda aka kira da Salmanu ya lakace hancin Junainah tare da cewa. "Alhamdulillah alama ta nuna ƙanwaliya tana zuwa makaranta babu wasa". Cikin jin daɗi tace. "Sosai ma ya Salmanu yanzu ajiyana huɗu fa, yanzuma dan hutu mukeyi, kuma gashi ko a gidama Ina karatu". Jinjina mata yayi da hannunshi kana, ya jawo kwanan data ajiye tare da cewa. "Ƙanwaliya me kika kawo mim ne?". Cikin murmushi tace. "Gasheshen naman tattabarune Ya Salmanu barima in koma ciki inci rabona inci na Addana". Kafin ya ankarama tuni ta juya da sauri tayi cikin gida. Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da kallon Aysha dake jingini da bakin kofar zauren, Cikin sanyi yace. "Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?". A hankali tace. "A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na". Murmushi yayi tare da cewa. "Kin rama kena". Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace. "Ga wuri kizo ki zauna mana". A hankali tace, "A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana". "Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?". Salmanu ya faɗa a hankali. Da sauri tace. "Eh". Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa. "Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?". A hankali ta zauna gefenshi ɗan nesa dashi. Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace. "Gaya min me kike tsoro?". Kallonshi tayi cikin yin ƙasa da murya tace. "Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar alaƙarmu ya zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana son abinda zai cutar da kai". Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace. "Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan taƙadirin, domin baki cancanci zama matar mushurkiba". Da sauri tace. "Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare mgnar ta koma kunnenshi". Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buɗe. Numfashin yaja jin ƙamshin naman a hankali ya fara ci, saida yaci ɗaya kab sannan ya rufe kwanon yace. "Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon". Cikin yanayin nitsuwarta tace. "A a kaci kawai Ya Salmanu". Da sauri yace. "No kada kimin musu". Shiru tayi jin yaci gaba da cewa. "Muddin dai ina raye in sha Allah. wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk azabar da zai shayar dani na shaɗi in Sha Allah zan aureki". Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu. A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da budurwarshi suna ɗan hirarsu Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin komai. Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa. "Ummey". "Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba mata, ganin hakane yasa a hankali tace. "Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru, Cikin kulawa da shaƙuwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace. "Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?". Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace. "Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa Baba Arɗo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?". Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa. "To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi". Kai ta juya tare da cewa. "Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko". Murmushi Ummey tayi kana tace. "Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki". da haka suka konta bacci. Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu, dan yanzu yanayin sihirinshi ƙaruwa yakeyi sosai, Wasu lokutan ba hawa ba sauƙa sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan ɓatarshi tama fi ta baya ƙarfi, ya dage wai zai bawa Shatu taƙi fir daya matsama kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta. Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda zai faru ya hana yarda da kowa, gaba ɗaya kuma yanzu Ƙabilar ɓachamawan nan masifa tuƙuru suke neman fulanin Bani dashi sabida baƙin ciki da hasadar ganin yadda shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake, gyaɗa, gujjiya, riɗi, da dai sauransu. Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma. To waɗannan abubuwan sune suke ƙara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da al'barkasu a jikinsu. Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi shaɗi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin

Table of Contents

Chapters

185 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
  164. 164 Chapter 164
  165. 165 Chapter 165
  166. 166 Chapter 166
  167. 167 Chapter 167
  168. 168 Chapter 168
  169. 169 Chapter 169
  170. 170 Chapter 170
  171. 171 Chapter 171
  172. 172 Chapter 172
  173. 173 Chapter 173
  174. 174 Chapter 174
  175. 175 Chapter 175
  176. 176 Chapter 176
  177. 177 Chapter 177
  178. 178 Chapter 178
  179. 179 Chapter 179
  180. 180 Chapter 180
  181. 181 Chapter 181
  182. 182 Chapter 182
  183. 183 Chapter 183
  184. 184 Chapter 184
  185. 185 Chapter 185