Chapter 132
Chapter 132
sunana a bakinki. Wani dogon ajiyan zuciya Hajia Mama ta sauƙe cikin fargaba tace. "Tashi Kuje ku gaida sauran. Allah yayi muku al'barka ya baku zaman lafiya. In sha Allah babu komai". Kamar jira Shatu takeyi a basu izinin tashi tayi fit ta miƙe. Da tarin mamaki Umaymah da Ummi suka miƙe, dan abubuwan da suka faru da yanayin Shatu, ya tsaya musu a rai. Shima Sheykh Jabeer miƙewa, yayi kana suka jere suka fita. Sai dai Shatu na ɗan sassarfa. Cike da mamakin wannan abun suka nufi Side ɗin Gimbiya Saudatu. A falonta suka sameta tana hakimce bisa kujerar ikonta, ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya tana karkaɗa ƙafar cike da izza. Ummi na gabansu suna bayanta Umaymah na bayansu. Cikin rusunar da kai Jakadiyarsu ta durƙusa gefenta tare da cewa. "Barka da safiya Gimbiya Saudatu, ga Sheykh Jabeer ya kawo miki da amaryarsa!". Cike da izza ta ɗan kallesu sama da ƙasa, kana ta nuna musu gabanta. Alamun su zauna, cikin sanyi Shatu ta rusuna tare da sunkuyar da kai ta zauna gabanta. Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo yayi mata, mai cike da ma'anoni, gefen ta ya kalla inda wata kujerar ke kusa da tata komansu iri ɗaya. Taku yayi cike da ƙasaita ya isa gaban kujerar, kana ya juyo ya zauna kan kujerar. Hakan yasa ya fuskanci Shatu da Umaymah. zaman ƙasaita da isa yayi. wani mugun kallo take binshi dashi har ya zauna. Ita kuwa Shatu kanta a duƙe tana murzam ƴan yatsunta. Umaymah ce ta ɗan taho zata zauna kusa da ita, a hankali ya jujjuyawa Umaymah kai, alamun. A a kada ta zauna a ƙasa. gane manufarsa ne, yasa ta zauna bisa kujera. Shiru kakejin falon, sai takun sawun hadimanta dake kawo ababen motsa baki, suna ajiyewa gaban Shatu. Suna gama jerawa suka koma can gefen. Jin shiru-shirun yayi yawane yasa Shatu ɗan ɗago kwayar idanunta, ta kallesu. A ranta take mgnar zuci. "Ikon Allah, ohoho ni Shatu wannan wanne irin bahagon gidane, mai cike da sarƙaƙiya da tubkar baƙin zare, To ko dai ita wannan ɗin kurmace." Muryar Gimbiya Saudatu ce ta ƙatse mata tunani ta, cikin isa da izza ta kalli Sheykh Jabeer, kana ta juyo ta kalli Shatu, murya a daƙike tace. "Bakiyi sa'an mijiba, yarinya duk da gashi kamar kinada nitsuwa". Ido Shatu ta jujjuya cikin hular al'kyabbar jikinta. Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko ta kan mgnar ta bai biba, sabida ai dama ya tsammaci, hakan kai ta juyo ta kalli Umaymah cikin ɗagawa tace. "A buɗe min fuskar amaryar in ganta da kyau, inga wanne irin idone da ita". Bata rufe bakintaba taji yana cewa. "Baza'a buɗe ba!." Murmushi Umaymah tayi sabida tsamar Sheykh Jabeer da Gimbiya Saudatu wani lokacin yadda kasan shi ubanta ne, haka yake mata mgna da yanke hukunci kai tsaye a karan kanta ma bare akan abinda ya shafeshi. ita kuwa Shatu a hankali take juya ƙwayar idanunta, tana kallon sawun Gimbiya Saudatu. cikin al'kyabbar ta ɗan juya idonta da kyau ta maidasu, kan kyawawan fararen sawun Sheykh, wanda suke tamkar ka taɓa jini yayi yo tsalle ya fito, sabida taushi da laushin fatar Wanda duk mutun mai zama da al'wala da yawan karatun al'ƙur'ani tafin hannunshi da ƙafarshi sukanyi wani kala mai masifar kyau da ɗaukar hankali koda baƙin mutun ne sai fatar hannunshi dana ƙafarshi sunyi kyau na musamman, hakama kuma fatar jikinshi wannan shine baiyanennen darajar zama da al'wala da yawan ambaton Allah kenan. Da ƙarfi ta rumtse idanunta tare da buɗe su. kan babbar yatsar kafarshi ta zubawa ido, sosai da sosai. wani ɗan zane baƙi mai suffar tafiyar maciji ta gani. sai dai bata samu ganinshi ras yadda take soba, shiyasa taketa zare ido, shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya ɗan turo ƙafar damanshi gaba. Dan ya gyara zaman ɗayan a kanta. Hakanne ya bawa Shatu damar zubawa yatsun nashi ido, suna nan zara-zara alamun mutum ne mai matsakaici tsawo. Ras zanen bindin maciciyar nan yake kan babbar yatsarshi. har zuwa bisa rumfar ƙafar kamar zanen dayis, cikin tarin mamaki da al'ajabi take bin zanen da idanunta. har inda igiyar takalminshi ya tsare zanen. Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali. sabida rashin ganin ƙarshen wannan zanen, da kuma inda ya nufa, da kuma ganin ya saman zanen yake. Hankalinta kab ya tafi ga zanen shiyasa bata jin ta ƙaddamar da Gimbiya Saudatu ke zubawa ba. Muryar ta taji da ɗan ƙarfi tana cewa. "Bata da sunane? Ke me sunanki". Ta ɗago kai da nufin yin mgna kenan sai kuma tayi shiru. jin Umaymah na cewa. "Sai kisa mata naki sunan, ba sai kiji namu ba". A gyatsine ta kalli Umaymah kana, ta ɗan matso bakin kujerar, hannu tasa ta ɗauki tupa cikin jerin ƴaƴan itatuwan da aka jera a gaban Shatu. miƙa wa Shatu tayi tare da cewa. "Kici kada ki tafi bakici komaiba,". A hankali tace. "Alhamdulillah!". Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace. "A ni ba'a zuwa sashina a tafi ba abinda akaci". Hannu ta miƙa ta amshi tupan kana ta riƙe shi. Shi kuwa Sheykh Jabeer miƙewa tsaye yayi alamun tafiya hakane yasa. Suma suka miƙa suka fita. Daga nan kai tsaye Side ɗin. Baba Nasiru suka nufa. A falo suka samu matarshi da yaranshi dama shi kanshi. Bayan sun zaunane. ya kallesu sama da ƙasa yace. "Dama baku zauna ba, a hakama na ganku. ba sai kun zauna ba". Cikin sanyi ƴarshi Jamila ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa. "Ayyah Baba ka barsu mu gaisa". Haɗe fuskarshi yayi sabida yasan irin masifeffen son da Jamila keyiwa Jabeer lokuta da dama, takanyi ta kuka in taji abubuwan da mahaifinta yakeyi mishi. shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya zauna ya harɗe ƙafa, Jamila kuwa cikin nitsuwa ta gaidasu kana. Ta kawo musu abin sha, Ummanta ku ko kallo Bata ishesuba yadda itama bata lallesu ba. Haka dai suka fita suka tafi. gidan Baba Basiru kuwa suna shiga ya tashi ya bar musu wojen. Daga nan suka shiga gidan Barrister Kamal Baba Kamal kenan. Yana ganinsu ya tashi ya ruggume Sheykh tare da cewa. "Masha Allah, Alhamdulillah yau dai Allah ya nuna min ɗana da matarsa". Zama sukayi bayan sun gaisane yayi musu addu'o'in al'khairi. Daga gidanshi gidan Dr Aliyu sukaje, wanda yake mutun mai mutunci da kamar Barrister Kamal. Sosai suka jima a sashinsa, yayi musu addu'o'in da sanya al'khairi da al'barka. Daga nan kuma sai Sashin Mom tsakar gidan Abbanshi. Maman Imran, ba yabo ba fallasa ta amsa musu. Daga nan wurin Amryar Abbansu sukaje, wanda suka sameshi a can. Daga nan sukaje gidan Ya Hashim da sauran ƴan bappanunsu. Gida na ƙarshe dai gidan Aunty Juwairiyya ne, can suka samu Hibba da Ya Jafar. Bayan sun gaisane, Umaymah ta ɗan matso kusa da ita cikin sauƙe numfashin gajiya tace. "Ɗago kanki Shatu kinga nan ƙofar Aunty Juwairiyya ce, ga mijinta shine babban yayan Jabeer, kuma yanada matsalar ƙwoƙolwa. Yanzu daga nan Side ɗinkin zamu wuce, wanda yana nan kusa da nasun. Sai gefen nakun kuma nasu Jalal ne." A hankali ta ɗago kanta ta kalli Ya Jafar, yana riƙe da hannun Jabeer yana karatun shi a hankali. Cikin sanyi tace. "Ina kwana yaya!". Kafaɗarta Umaymah ta dafa tare da cewa. "Baya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185