Chapter 153
Chapter 153
sannu. Ajiyeta bisa kujera Ummi tayi tare da cewa. "Baki sha ruwan ba ma ko?". Kanta ta gyaɗa mata alamar eh. Hakane yasa Ummi tacewa Hibba ta ɗebo mata, abin shan ruwan a take kuwa ta kawo mata. Bayan tasha ruwanne duk suka nufi cikin ɗaki dan yin salla. Daga yin sallan magriba su Jamil suka dawo sukaci abinci kafin aka kira sallan isha'i, kana suka koma akayi sallan isha'i da asham sannan suka nufi harkokin su. Shi kuwa Sheykh Jabeer daga Masallacin gidan Radio Ɓadamaya ya wuce, wurin yin shirin Fatawa. Sai tara dai-dai ya dawo, gida. A kitchen ya jiyosu. Bisa alamu duk girkin abincin sahur sukeyi. Shi kuwa bayan ya shiga, wonka yayi-yayi shirin bacci kana ya fito falonshi. Soyayyan Arish da kwan ya ɗanci tare da tarfa ferfesun ya ɗan ci. masa biyu. Jin cikinsa yayi tib ne, ya miƙe ya dawo falon. zama yayi bisa kujera yana kiran Umaymah, tana ɗagawa tace. "Jazlaan ina autata, ya azumin yau dai?". Gajeren murmushi yayi tare da cewa. "Umaymah autarki akwai raki, yau ita har ta fara lissafin an kai ɗaya saura 29/28". Dariya ta ɗanyi tare da cewa. "Kaɗan ma daga aikin Hibba". Sai kuma tace. "Ina ɗiyata kuma, ya azumin?." Kanshi ya ɗan jingina da kujera kana yace. "Alhamdulillah". Jin muryar Haroon na cewa. "Wai ɗazu ina ka shigane inata kiran wayar ka baka ɗagawa". Gyara zamanshi yayi tare da kurban coffee ɗinshi kana yace. "Na bar wayar a gida, da ɗaya na tafi na Fatawa". "To ya Amarya?". "Ban sani ba". Cikin dariya Haroon yace. "Allah baka haƙuri". Amsar wayar Umaymah tayi sukaci gaba da mgnar kan tafiyarsu Umrah. Daga bisani sukayi sallama, ya miƙa ya nufi ɗakin baccinsa. A kitchen kuwa, bayan sun gama komai na sahur ne. Ummi ta cewa Shatu taje ta ɗauko Foodflaks ɗin dake falonshi. To tace kana ta juya ta tafi. Koda ta shiga ɗan kalle-kalle tayi ganin baya nan, yasa ta harari falon ma gaba ɗayatare da cewa. "Mugu". Sannan ta ɗauki kwanukan ta fito. Duk sauran abincin Saratu suka haɗawa ta kai musu ita da sauran hadiman. Wanke-wanke tayi kana ta tattare komai sannan ta wuce part ɗin su. Su kuma ganin har goma tayi ne, yasa sukayiwa juna saida safe duk suka shiga. Yauma kamar daren jiya haka sukayi. Washe garima haka suke tafiyar da rayuwarsu. Cikin tsari da kuma samun damar hutu da ibada dan ribatar watan Ramadan ɗin. A hankali aka fara nisawa cikin watan Ramadan, kwanaki suna ɗan mirginawa da kaɗan-kaɗan. Yau wunin azumi na biyar kenan. Da hantsi bayan sunyi walaha sunyi karatun al'ƙur'ani. Sanin yanzu Ummi na jin tabsir ɗin da yakeyi a masallacin Masarautar Joɗa ne yasa, Shatu tana gaisheta ta fito. Hibba kuwa Side ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa. Ita kuwa Shatu falonta ta fito. Bisa kujera ta zauna, tare da kiran number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare. Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa. "Ban gane wake mgna ba". Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace. "Junaidu Adda Shatu ce fa". Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa. "Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu, ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah". Cikin sauri tace. "Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri da Laure da Innaji da jikin". Murmushi yayi tare da cewa. "Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai. Sai dan Baba Madune yana shan wuya, Satin daya wucema an sake yi mishi aiki". Cikin sanyi tace. "To yanzu su waye ke kula daku". Kanshi ya rausayar tare da cewa. "Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci. An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje". Cike da jin daɗi tace. "Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi". Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa. "Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,". Uhum tace a taƙaice. Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi. "Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado. Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu dawo? Kina mgna dasu ne?". Cikin dariya tace. "Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu. Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo." Da sauri yace. "Dan Allah Adda Shatu turo min number su". To tace tare da gyara konciyarta. Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama. Sannan ta tura mushi number su ɗin. Suna gamawa ta kira Number Bappa. Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga. Cikin jin daɗin jin muryarshi tace. "Ina kwana Bappa na". "Lfy lau Alhamdulillah Shatu ya Azumi, da baƙon wuri". Cikin sanyi tace. "Alhamdulillah, Bappa yaushe zaku dawo". Dariya yayi mai ɗan sauti kana yace. "Bayan salla". Cikin lumshe ido hawaye na zuba tace. "Bappa ina jin kewarku, bani da kowa nawa kusa dani. In na tuno su ya Giɗi hankalina na tashi Bappa inyi ta kuka babu mai sanin irin ciwon da nakeji a raina". Cikin sanyi yace. "Kwantar da hankalinki Shatu, su Ya Giɗi suna raye, sai dai suna cikin mawuyacin hali, suna buƙatar addu'o'in ki musamman a cikin wannan mata mai alfarma, na sanki bakya wasa da riƙo da ibada, amman ki ƙara kan yadda kike, in sha Allah wata rana zasu dawo garemu, cikin sauƙaƙƙiyar hanya, addu'a itace abinda suke so, shiyasa na gaya miki abinda Allah ya nuna min a mafarki a kansu". Cikin sassanyan kuka murya can ƙasa tace. "Zanyi Bappa zan ƙara zan dage, kuma zan roƙi a tayamu addu'o'in a masallatai da wurin tabsir." Cikin jin daɗi yace. "Yauwa Shatu na, ki kwantar da hankalinki, ki zauna lfy da mutanen da kike tare dasu, kiyiwa mijinki biyayya, kiyiwa mayanshi biyayya bana son musu in babba ya gaya miki abu matukar bai saɓawa shariyar musulunci ba." Cikin sanyi tace. "To". Da sauri yace mata ga Junainah". Cikin jin daɗi tace. "To a bata waya". Tsalle Junainah tayi tare da cewa. "Adda Shatu, kizo Lardi garin da daɗi kullum sai an gasa mana zabbi ko Tattabaru, insha nono da zuma inci naman insha zuma, inci su inabi sai na ƙoshi". Cikin so da ƙauna da shaƙuwar ta da yarinyar tace. "Allah sarki Junnu ke ko kewata bakiyi bako?". Dariya tayi tare da cewa. "Nayi kewarku mana harda Ya Junaidu ma nayi kewarshki". Murmushi tayi tare da cewa. "Na bashi number ku, zai kira ku gaisa". Tsalle tayi tare da nufar ɗakin Ummey. Ita kuwa Shatu cikin dariya tace. "Azuminki nawa". Da sauri tace. "Azumi na ɗaya ranan nayi rabi daga safe zuwa azahar jiya kuma na ƙarisa rabin daga azahar zuwa mangriba". Wani irin dariya ne ya rufe Shatu dariya takeyi sosai. Kewa da bege da son ƙanwar tata ya rufeta. Da Sauri
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163
- 164 Chapter 164
- 165 Chapter 165
- 166 Chapter 166
- 167 Chapter 167
- 168 Chapter 168
- 169 Chapter 169
- 170 Chapter 170
- 171 Chapter 171
- 172 Chapter 172
- 173 Chapter 173
- 174 Chapter 174
- 175 Chapter 175
- 176 Chapter 176
- 177 Chapter 177
- 178 Chapter 178
- 179 Chapter 179
- 180 Chapter 180
- 181 Chapter 181
- 182 Chapter 182
- 183 Chapter 183
- 184 Chapter 184
- 185 Chapter 185