Chapter 29
Chapter 29
kake duk abinda kaga dama ko.?" Cikin ina ina yace "Ba haka bane yallaɓai ayi min afuwa." Tsawa ya daka mai cikin fusata ya kuma yin magana yace. "Afuwar me za'a maka, wato kai kaje ƙasar waje kana sha'aninka koh, ace ina tare da commisioner of police gabaɗaya amma a kama Raliya kusan fiye da sati uku amma ankasa yin komai akai." "Innalillahi! Yallaɓai Alpha kace an kama Raliya." "Bani da buƙatar maimatawa tunda kaji me nace." "Amma garin yaya waya kamata." "Wa kake tunani.?" Ido C.P ya waro waje kamar wanda yaga wani mummunan abu mai firgitawa yace. "Zarahh.???" "Ka amsa tambayarka." "Ohh shit! Dole zan dawo ƙasar gobe a fito da Raliya." "A fito da Raliya fa kace! kasan ko a wani ofishin ƴan sanda Raliya takr zan iya zuwa na fiddata, amma ba anan take ba bansan a ina yarinyar nan ta ɓoyeta ba. Kayi gaggawar kiranta ka bata umarnin fito da ita a ko ina ta aje ta." "Bari na kira ofishin su yanzu, Raliya bazata kuma kwana a hannunta ba" Umma"Ina jiran sakamako mai kyau." "Toh yallaɓai yanzu zan kira." Cikin rawar jiki ya danna lambar mataimakin shi, ringing biyu ya ɗauka yana gaidashi, bai tsaya amsawa ba ya fara magana. "Ka kira office ɗin ASP Zarah ka bata umarnin sake yarinyar da ta kulle a cell, ka gayamata wannan umarni na ne." "Yallaɓai ai babu wata yarinya a ofishin nan wacce aka kulle." "Ba tambayarka nakeyi ba umarni ne nake baka." "Amma yallaɓai naga Zarah yanzu ba anan take aiki ba, kila bata zda masaniyar abinda ke faruwa ko dai ba ita ɗin bace.?" "Bata aiki kuma ??? ASP Fatimah Zarah Abduljalal nake nufi fa." "Ehh yallaɓai ai ta nemi takardar transfer zuwa Bauchi saboda za'ayi aurenta, jiya ma muka dawo daga ɗaurin auren." "Damn it!! Wane ne ya aiwatar da hakan ba tare da sani na ba." "Yallaɓai ta je Abuja ne daga can ta gama komai, wasu signing ne kawai da akeson kayi ni nayisu a madadinka." "Meyasa ba'a tuntuɓeni ba eyee??" "Ranka ya daɗe kamar naga babu buƙatar hakan." Tsaki ya ja gami da ya kashe wayar batare daya kuma magana ba, kanshi ya dafe cikin taraddadin yadda zai kira Alpha ya gaya mai wannan labarin, gabanshi ne ya faɗi ganin kiranshi na kuma shigowa, cikin fargabar mai zai faru ya ɗaga kiran. "Ya ake ciki??" ya tambaya babu walwala. "Ehmm dama.." "Straight to the point, banason dogon zance." "Yallaɓai wai anyi mata transfer zuwa garin Bauchi saboda zatayi aure acan, jiya ne aka ɗaura auren nata a garin Bauchi." Shiru yayi baiyi magana ba har hakan ya baiwa CP tsoro, sai can yace. "Duk abinda kakeyi kabari a yau ɗin nan ka dawo ƙasar nan, sannan karka kuskura ka kirani matuƙar ba shaidamin zakayi ka kuma Bauchi da aiki ba." daga haka ya yanke kiran. Babu yadda commisioner yayi iya dole ya fara haɗa tarkacensa bayan ya sallami baturiyar da suke tare, cikin lokaci ƙanƙanin lokaci ya gama shirin komawa ƙasarsa Nigeria....✍️✍️✍️ *Tammat bi Hamdulillahi!! Littafi na ɗaya ya ƙare anan, zamu shiga littafi na biyu da izinin Allah kafin sallah. Nima zan ɗanje hutu na kwana biyu kafin mu ɗora.* *Ina yinku sosai Zarah's fans, Mrs. Khaleel from VIP ina yinki sosai ina godiya da ƙaunarki a gareni Allah ya bar xumunci a tsakanin mu. Sai kunjini a kashi na 2*🥰 *By* *Jasmine*🌸🌸
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29