Chapter 4
Chapter 4
kama kanta dake sarawa ta ce, “Lokacin tashina ya yi, yanzu Dr. Surayyah za ta Zo……… ” Nurse din ta katse ta, “Ki ceci rai kamar yadda kika saba, sakayyar ki na wajen Allah! Daga matar har Babyn suna cikin hadari, ga shi babu likita ko daya duk sun shiga meeting. Sannan Surayyah babu wanda ya san lokacin da za ta karaso”. Hadizah mai sanyin zuciya, matar ta kashe mata gwiwa da tausasan kalamanta. A take ta manta da ciwon kanta, ta rufe motar ta koma gun mai haihuwa. Wannan halayyar ta ce da ta sha banbam da ta sauran likitocin labour room da kowa ke kuka dasu. Zuciyarta mai laushi ce, shi ya sa daga likitocin har Nurses zuwa labourers ke son ta, suke jin dadin aiki da ita. Hadiza is simple, komi nata a saukake yake. Da gaske ne matar ba za ta iya haihuwa ba. Ta kai matuka wajen galabaita, ta soma ba ta dukkan taimakon da ya dace. Tana cikin aikin Dr. Surayyah ta iso, suka tsaya a kan matar nan. Cikin dan lokaci sun yi nasarar fitar da jaririn amma ba rai. To alhamdulillahi an samu uwar. Tana zare safar han nunta ta ce da Surayyah, “Ko da ban zo gobe ba, don Allah ki kular min da matar nan, haka kawai nake jin tausayin ta, dube ta yarinya karama, ga dukkan alamu ba ta isa auren ba suka yi mata. Allah ne ya taimake ta sun zo asibiti da wuri, da babu mamaki BBF ya same ta”. Surayyah ta ce, “Matsalar mutanen karkararmu kenan, ban san yaushe za su hankalta ba. A kullum fadakarwa ake a radio da talabijin, amma kamar ana kara zuga su. Allah ya kyauta. Balle ma me zai hana ki zuwa idan da rai da lafiya?” Ta girgiza kai ta yi dan tsaki, ta ce, “Bana jin dadi ne”. Surayyah ta ce, “To Allah ya kawo sauki, a shafa min kan Munib”: Da haka suka yi sallama ta fita. Da yake yau kowa a motar shi ya zo, wato itada Sulaiman, kasancewar lokutan ayyukan nasu sun banbanta. Akwai tazara sosai daga inda ta yi parking zuwa cardiology. Tana tukin tana duba agogon ‘gucci’ da ke daure a damtsen hannun ta na hagu. Yau Dr. Sulaiman aikin kwana gare shi, kudin Fati sun tsaya mata a rai, ga shi jakarta (is empty). Sannan is too late ta je banki ta fitar da kudi (lokacin ba ATM). Ba al’adar ta ba ce tambayar Sulaiman kudi ba, saboda duk wata yana cika mata account ba tare da la’akari da albashin ta ba. Ita da kudin ta sai dai ta yiwa iyayen ta da ‘yan uwanta hidima, amma duk wani nauyin rayuwar ta Sulaiman ya dauke shi. Sau tari, ta kan ji kawayen ta da ba suyi aure ba irin su Dr. Surayyah, na tattaunawa a kan abinda ya hana su yin aure, su kan ce da ka yi aure shi ke nan ka shiga matsalar da namiji (wulakanci, rashin tsayawa ga mace daya, rowa da sauran su). To ita dai yau shekaru biyar cif, ba ta ga ta inda nata da namijin ya kuskuro ta ba; Matakin iliminsa bai sa shi ya zamo cikin kowanne irin aikin ashsha ba. Bai sa shi ya zamo mai tauye mata hakki ba, bai sa shi ya zamo mai girman kai a gare ta ba. Kullum tambayar shi, “No problem Haddizah (babu matsala Hadiza)?” Ta kan tambayi kanta, yadda neman mata ya zamo ado ga akasarin mazan wannan zamanin, masu matakin rayuwa irin nashi, mai ya sa ban da Sulaiman? Duk da kasancewar shi mutun mai tsananin bukatar diya mace. Ta yadda duk juriyar ta wani lokacin har ta kan nuna gazawar ta. Ta taba tambayar shi cewar, “Don me ba zai kara aure ba?” Sai ya kankame ta. Ya ce, “Haddizah you are okey for me, in dai ba za ki yi min rowar, ni’imtaccen jikin ki ba……… ” Ta ce, “Doctor gani nake ina kwarar ka, you seem not o.k…….. ” A hanzarce ya ce, “Ni na gaya miki?” Ta girgiza kai. Ya ce, “To kar ki kara yi min wannan zancen, silly girl kawai”. Ta yi murmushi, da tunanin ta ya zo nan. Dai-dai lokacin da ta iso cardiology, ta yi parking a inda aka tanada don adana motoci ta fito rike da jakarta. A nutse ta karasa (male ward) inda office din Sulaiman yake, ta tura kofar bayan ta murda tare da sallama. Da alama aiki ya kacame masa, yana ta rubutu cikin file-file dake gabansa, ya daga kai yana duban ta duba na so da kauna, kuma na nutsuwa kamar yana son karanto ainihin damuwar da ke fuskarta. Ya mike ya baro kujerar sa ya zauna a masangalin kujerar da ta zauna, ya zare mata gilashi, ya ce, “Ya ya ne Dr. Hadiza, you look edhausted!” (Da alama kin gaji likis). Ta lumshe zara-zaran gashin idonta ta ce, “Migraine ke damuna (ciwon kan barin kai guda)”. Ya kai lallausar tafin hannun shi goshinta, har sai da ta ji wani shock kamar yau ya fara taba ta. Ta yi saurin ture hannun sa, za ta yi magan Dr. AbdulJahi ya turo kofar ya shigo, da sauri ya koma yana “edcuse me plzzz……. {” Duk suka yi murmushi. Ya ce, “Kin sha magani?” Ta girgiza kai, “Ina so in je Karkasara ne”. “Amma lafiya na gaba da komai ko?’ Ta ce, “Zan biya emergency in amsa kamin in wuce”. Ya kai hannu cikin rigarta wai zai ji temperature na jikin, ta yi saurin rike hannun ta ce, “Haba Sulaiman…….” Shi ma ya ce, “Haba Hadizahbh….! Ni kadai zan kwana fa, babu dumin jikin ki Hadizah…..?” Ta yi murmushi ta rusunar da kwayar idon ta cikin jin kunyar furucinsa, domin dai ita mace ce mai tsananin kamun kai a gaban mijinta da jin kunyar sa, kai ka ce basu haihu tare ba. Yace “Ke kwanta in duba ki, ban yarda dake ba, har yanzu ba ki cire wannan loop din ba”. Ya soma laluben ta. Ta rike hannun shi ta ce, “Wallahi na cire”. Ya ce, “To ko ke fa? “Ya’ya nake so Haddizah, ki yi ta cika min gida dasu. Bani da harshen da zai iya bayyana hakikanin son da nake miki, you are my life Hadizah….., kada Allah ya rabamu……. ” Ya shiga nuna mata son, practically, (a aikace) irin yadda bai taba yi ba. Murmushi tayi. Ta ce, “Sulaiman naka son ka sani, amma baka san nawa ba. Sannan ban san yaya zan yi in fassara ba. All I can say (abinda zan iya cewa shine) ina son ka Sulaiman son da nake yiwa raina……’ Ya kai hannu ya toshe mata baki, wayar shi ta yi kara ya juya yana amsa call din amma bai saki hannunta ba. Ya gama ya kashe ya maida aljihun shi, yana yi mata wani sassanyan kallo ya ce, “Ki yi min alfarma ki taya ni kwana ko hira ce ki dinga yi min ina aikin”. Ta ce, “Ka yi min afuwa Baban Munib, Fati zan kai ma kudi za ta yi registration gobe”. Da sauri Ya ce, “Registration din Fati ya fini?” Ta bude baki ta rufe da hannun ta, ta kasa cewa komai. Ya tsare
Table of Contents