Chapter 8
Chapter 8
ana alwala, ita ma ta yi ta nufi masallacin da ta ga ana shiga da sauri ta samu jam'in sallar azahar. Da aka fito yunwa ta addabe ta, ta soma tunanin ta je ta kwada kwadon kwaki sai ta ji wata senior na fadin a fita ‘dining’ za’a rufe hostel. Ta dinga maimaita kalmar 'dining' a ranta, ko mene ne? Ta ga dai kowa fita yake yi sai ta bi bayan wasu yara ba tare da sun san binsu ta ke ba, har zuwa wani katon dakin cin abinci inda ta ga dalibai a zazzaune kowa da filet dinshi ana ta cin abinci. Yawun bakinta ya tsinke, ta bi layin da ake bi a karba ita ma ta karba, jallof din shinkafa ce da yankan nama biyu da soyayyar ayaba (plaintain) sala uku. Ta zauna ta ci ta koshi, ta sha ruwa ta yi hamdala ta mike ita ma ta nufi hostel ta kwanta a gadonta don ta huta zuwa la'asar. Da aka yi sallar la'asar kuma suka koma aji zuwa karfe shida. Haka dai ta yi ta bin abin da ta ga ana yi, har lokacin barci. A sannan ne ta samu damar kwashe kayanta da ke cikin (Ghana Must Go) ta jera a loka, kamar yadda ta ga kowa ya yi. Yaran nan makotanta suka fito da wani irin abu cikin kwali da ba ta taba gani ba suna ci, suna korawa da lemon gwangwani suna hira da Turanci, suna kallonta, ita da kullin kayan kuli-kulinta suna ta dariya. Duk ta bi ta sha jinin jikinta, amma ba ta daga kai ta kalle su ba, ta jika ramarta cikin 'yar robarta ta ajiye akan lokarta tana jira ta jiku ta kwada da kuli. Tana ganinsu har lekowa suke da kai suna leka robar ta, amma ragowar jama'ar da ke dakin ba ruwansu da ita, kowa gararin gabansa yake yi. Ta rasa dalilin wadannan yara na sa mata ido da wulakanci a gare ta, daga baya ta fuskanci daya sunanta Nabilah, daya kuma Kausar. Ta kwada ramarta ta ci ta koshi, ta sha ruwa ta kwanta a katifarta da ko zanin gado babu. Ta rufa da zanin atamfar Innarta, wadancan yaran kuwa irin bargonta da hedimasta ya cinye suka rufa da shi. Hatta filon ya dauke ya cinye saboda rashin tsoron Allah irin nasa. Aka yi (light-off) na gabadayan hostel din, ta shafe jikinta da addu'o'i ta kwanta. Washegari da aka yi sallar asubah ta ga kowa yana bin layin wanka, don haka ita ma ta bi ta yi wankanta ta yi sallah a masallaci tare da Imam. Daga nan aka tafi aji. Suna shiga aji ta ga mutanenta sun dauke bencin gabadaya sun maida shi wurin da ba kowa sun zauna, sun kuma kira wata yarinya sun zaunar da ita a wajenta. Ta rasa inda za ta zauna, ta koma karshen ajin ta sanya littafinta daya a kasa ta zauna akai. Zamanta da kamar minti biyar Uncle din ajin ya shigo. Yana ta jefa ido ya hango Mariaman da ya kwana ya tashi da tunaninta jiya, amma bai ganta ba. Gabadaya ajin aka mike, ita ma sai ta mike kamar yadda suka yi, suka hada baki gabadaya suka ce "Good morning Uncle". Ya ce, "Morning class, how are you all?" Suka sake hada baki gaba daya suka ce "We are fine Uncle". Sannan ya yi umarni da a zauna. A sannan ne ya hangota makure a can layin karshe kamar mujiya, kuma a dandaryar kasa. Bai ce komi ba ya bude rajista ya yi kiran lambar kowa, ya amsa, sai a karshe ya ce "No. 40". Shiru ba a amsa ba, a lokacin ya gane lambar Mairo ce, sai ya ce, "Mariama daga yau ke ce no.40". Ta ce "To". Ya rufe rajistar ya dinke fuska sosai, ya ce "Kausar!" Ta amsa, "Yes Uncle". Ya ce "mene ne dalilinki na janye benci ki hana Mariama zama?" Ta yi shiru ba ta amsa ba. Ya dubi dalibar da suka zaunar a wajen, "Ke Laila ina wajen zamanki? Me ya kawo ki nan?" Ta yi saurin mikewa ta koma wajenta. Ya ce "Kausar fito nan". Ta fito tana gatsina ita a dole ga 'yar masu kudi. Saura kadan ya zabga mata mari, sai dai ya yaki zuciyarshi ga yin hakan, ya ce ta fita waje ta yi kneel down, har zuwa lokacin break. Ta cika ta yi fam, kamar balam-balam, dama ga ta buleliya. Ta zobara baki, ta ce "Ai ba ni kadai na janye bencin ba, har da Nabilah". Nabilah ta ce "Wallahi Uncle babu ruwana, ita ce ta ce wai ba zata zauna da billager ba". Bai yi mamaki ba, sai ya bude murya yana tambayar 'yan ajin "Shin dama akwai banbanci tsakanin musulmin kauye da musulmin birni?" Suka ce "A'ah Uncle". Ya ce "To me ye laifin wannan yarinya da kuke kyamarta?" Wasu daga ciki suka hau matsawa suna cewa "Ta zo ta zauna a kusa da mu". Amma Uncle sai cewa ya yi, babu inda zata zauna sai bencin su Nabilah, don haka idan Nabilah da Kausar baza su zauna tare da Maryama ba, sai dai su koma gidan ubansu. Mairo dai na sauraron ikon Allah. Tana tunanin yadda ta ke abar so a wurin Innarta da Babanta, amma wai yau ake takaddama akan inda za ta zauna sabida ita an ga alamar ba ta da arziki. A lokacin ta ji wata zuciya na shigarta (determination) akan rayuwa. Ta alkawarta wa ranta idan ilimi na kawo arziki, to zata neme shi ko don 'ya'yanta. Za ta nemi ilimi har sai ta ga karshensa, idan har ana gani. Ba zata so a yi wa danta irin wannan wulakancin ba. Uncle ya lura Mairo kuka ta ke yi, sai zuciyarsa ta karye. Don haka tunda ya gama kiran lambar sai ya fita, bayan ya tabbatarwa Kausar kada ta sake ta bar kneel down din da yasa ta har sai ya dwo. Malamin maths ya shigo ya fara ba su darasi, Mairo ta tattara hankalinta akan malamin gabadaya, ba ta damu da hararar da Nabilah ke mata ba. Ya gama ya fita, sai ga Uncle ya dawo wanda kuma shi ne yake daukarsu darasin Turanci. Yana koyarwa, amma rabin hankalin sa na kan Mairo. Ya lura sabanin ragowar ‘yan ajin, Maryama ta ba shi dukkan 'attention' dinta, da wani muradi cikin kwayan idanunta. A zahiri wannan yarinya bakauyiya ce lakadan, amma ga dukkan alamu, ba haka Allah Ya yi nufin barinta ba. Ya kammala darasinsa ya ba da aiki 'Essay Writting' mai take guda uku, ya ce kowacce ta zabi wanda za ta iya yin sharhi a kansa. A rubuta a kawo masa washegari. Hankalin Mairo ya tashi, domin dan ilimin nata bai kai nan ba. Magana ce ake so su rubuto da harshen Turanci akalla shafi daya da rabi na littafi. Aka kada kararrawar fita break, amma Mairo ba ta yi niyyar fita ba. Ta kurawa aikin 'assignment' dinta ido tana tunanin ta inda za ta bullo. Ba ta ankara ba ta ji wani sassanyan kamshi na dukan hancinta da kuma alamun zaman mutum a bencin gabanta. Ta dago a hankali tana kallonsa, Uncle ne. Ya ce "Yaya dai Maryama, kowa ya fita cin abinci, amma ke ban
Table of Contents