Skip to content

Chapter 2

Book one

Maradams Book One Complete Hausa Novel 4,408 words 0 views Progress saved
Download Book

Free page

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO

bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na  kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page2
....Da misalin karfe goma na safiyar ranar asabar mr ATA ya sauko daga saman dakinsa jikinsa sanye da bakin riga da wondo baki yayinda kafafunsa ke sanye cikin wasu hadaddun silifas masu matukar kyau suma black kana gani kasan masu tsada ne haka idanunshi suna makale da farin glass wanda ya zame masa tamkar na gado, ko bacci wani lokacin dashi yake sai idan Mahaifiyarsa ta shigo ta gansa dashi ta cire masa ,yayi kyau sosai acikin shigar kasancewarsa fari ."ya qaraso ya dauki jarida daily trust da'aka ajiye masa ya samu wuri ya zauna akan doguwar kujera mai zaman mutun uku ya daura kafarsa daya a kan daya ya shiga duba jarida "
yana zaune nana da maryam suka fito suna magana akan inda mai decoration zatai decorate din birthday din maryam dana hanan diyar Aunty zabiba kanwar mr ATA da zaa gabatar a ranar ." suna gama qarasowa parlour'n suka gansa zaune Kmr an dasashi a gurin ."suka bishi da kallo suna jin faduwar gaba babu yadda zaka ga mr ATA gabanka bai fadi ba ko kai waye kuwa saboda tsananin tsare gida , ya gansu amman yayi tamkar bai san da wasu halitta tsaye a wurin ba ,nan take kowacce ta shiga taitayinta jiki a sanyaye suka hada baki wurin gaishesa "good morning ya adam" ? sai daya dauki second goma batare daya amsa ba har sun cire rai da zai amsa suka jiyo sautin muryarsa daga can kasan makoshi "morning ! ya amsa batare daya dago ya dubesu ba ."

Naunayen ajiyar zuciya maryam ta sauke dan tasan darajar sister taci yasa har ya amsa gaisuwar dan da ita kadai ta gaisheshi bazai ta'ba amsawa ba Kai tsaye hanyar kitchen suka nufa domin bawa masu aiki umarnin abinda zasuyi na birthday duk da sauran abubuwa masu wuya tun jiya a kammala ,duk abinda suke hankalin maryam na kan mr ATA bini bini ta kallesa taja tsaki acikin ranta dan hakan nan kwanaki take jin matsanancin tsanarsa a ranta dan tasha alwashin tunda bai qaunarta itama bazata qaunacesa ba mai qaunarsa ma baso ."

Sai dai duk da wannan tsanar da tayi masa ta kasa dauke kwayar danunta akanshi har sanda ya mike ya isa dining table ya dauki cup din coffee dinsa baki mai shegen kyau da gani daga wata kasar yazo dashi , a natse ya sake dawowa mazauninsa ya zauna fuskar nan tashi a hade tamkar wanda ake masa wahayi da bacin rai."
"tunda aka haifeta ta bude idanunta akansa bata ta'ba ganin dariyarsa ba ,kuma haka kowa yake fad'a acikin family's ,komai zaayi na dariya sai dai ya bata rai yaja tsaki tare da cewa nonsense ko rubbish ga shegen miskilanci wani lokaci halinsa na dan burgeta Irin mijin da take so kenan mai matukar kamewa da sanin ciwon kai, dan gsky ita dai nmj mai yawon surutu ko shiga abinda bai shafesa ba yawon fara'a matsala ne agurinta bata so sai dai nashi yayi yawa ko dan murmushin nan ba yayi matukar kaga fuskarsa a d'an sake to yana tare da mami ne shima wani lokacin bata gane kansa kome zatayi bazai sakar mata fuska ba ."

byn ya sha kad'an ya ajiye cup ya cigaba da abinda yake har sanda hjy Zulaihat ta fito itama ta shiga kitchen yana nan zaune ya tsurawa jarida idanunshi , al'ameen daya daga cikin securities na bakin get
ya shigo bakinsa dauke da sallama sannan cike da girmamawa hannunsa rike da white lailon da box blue and white ,mr ATA ya amsa sallamar aciki yana mai d'ago kansa ahankali ya zubawa al'ameen lumtsatsun idanunshi "Alameen ya qaraso gabansa kad'an ya rusuna "barka da safiya yalla'bai "mr ATA ya gyada masa kai kawai batare daya amsa ba .
" amm ga sako wai inji Ana's" mr ATA ya d'an kankace lumtsatsun idanushi yana bukatar qarin bayani daga bakin al'ameen,alameen yayi sauri yace "sakon hjy maryam ne ita yace abawa "shiru mr ATA yayi yana kallonsa da sakon hannunsa kamar bazai ce komai ba sai kuma ya nuna masa kan table din dake gabansa yana jan tsaki a fili al'ameen ya ajiye ya juya ya fice da sauri ya kama gabansa."

Maryam dake kitchen wacce daman idanunta da hankalinta yana parlour ta shiga tashin hankali mara misaltuwa, da sauri ta qarasa inda nana take tsaye "sister na shiga uku nah" ta fada tana riko hannun nana cikin nata "me kuma ya faru allah ya rabamu da shiga uku sister ?"kalli can ki gani sister ta nuna mata parlour'n "me ya faru ? "sakon Ana's ne daman ya turo min text message zai zo ya kawo min gift gsky al'ameen bai kyauta min ba maimakon ya kirani ya bani a hannuna tana magana idanunta na cikowa da ruwan hawaye hjy zulaiheart ta juyo a natse ta dubesu "ku kuma lafiya kuka tsaya kuka hade kai wa ya mutu ? a matukar firgice suka juyo suna dubanta maryam na 'kokarin dauke hawayenta a d'an rikice suka girgiza mata kai alamun "babu kowa " to meke faruwa daku ?babu komai suka sake hada baki "to allah yasa babu komai din amman ni dai na fahimce da komai tsayawa sukai suka qasa cigaba da aiki ."

shi kuwa Mr ATA naunayen ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske yana shan yaji kamar yadda ya saba sosai ya tsurawa box din dake dauke da sunan maryam da kallamar happy birthday yana lissafa abubuwa dayawa acikin ransa "wai gashi inji Ana's sakon hjy maryam "ya maimaita abinda al'ameen ya fad'a , kafin daga baya ya kwabe baki tare da kai hannu ya bude box din ,da wani hadadden freme idanunshi ya soma cin karo mai matukar kyau da d'aukar hankali an rubuta sunanta da larabci da kuma hausa ."
"shiru yayi yana jin wani iri a gabadaya ilahirin jikinsa na tsantsar bakinciki ,a hankali ya dinga kallon abubuwan dake cikin box din mug, pray mate ,Casbaha alqurani da wani qaramin greating card na sokon taya murnar birthday sai kuma qaramin yellow takarda mai dauke da kalaman soyayya "ya dauka yana tabe baki kamar yaga wani mugun abu ya soma karantawa ."

hjy Zulaihat ta fito daga kitchen tare da masu aiki mutun biyu zuwa dining maryam da auta suka biyo bayanta jikinsu duk a sanyaye dan basu san abinda zai faru ba "na shiga ukuna sister ki taimakeni karanta sakon fa yake " maryam ta sake fadan hk cikin tsananin tsoro "to sai me idan ya karanta ? " wallahi kin cika abun ban haushi kamarki dan an aiko miki da sako zai zama abun tashin hankali? Ke yarinya ce karki manta master's gareki kuma dole zakiyi aure "ni sister rabani da wani master's na yarda kowa ya karanta sakon amman ban dashi "bangane banda shi ba ? shi waye naki da zakice ban dashi ? tayi mata tmbyr tana kallonta "haba sister ya kike yi kamar baki san abinda nake nufi ba kema kinsan ba haka nake ba ni ba matsoraciya bace amman wallahi shi mugun tsoronsa nake ji ,sannan kinsan halinsa da disgi ."
"Dana san halinsa fa ? shi zai auremu?Ko kuwa munyita zama haka kenan bazamuyi aure ba ?"Kinga idan zaki cire tsoro ki cire dan ni wallahi ina samun miji aurena zanyi na barki bazan zauna ba aiki ba aure ba dole zanyi daya ta qarasa mgnr tana jan tsaki maryam tace "banza kamar kema ba tsoronsa kike ba "ina jin tsoronsa amman ban kai ki ba dan dani anas da abbas suke mutuwar só da son aure da tunin ina gidan daya daga cikinsu "ta fad'a tare da qarasawa wurin Hjy Zulai ta rabe a gefenta."

daga can inda hjy zulai take tsaye ta hangosa ya baje kayan sannan yayi zurfin cikin karata yellow takarda "Lafiya adam !? ta furta tana cigaba da dubansa ,a tsanake ya mike tsaye fuskarsa a yatsine ya nufo wurinta yana cewa "wani haukan shirme nake karantawa ".maryam tayi wuf ta koma kitchen da sauri tana daura hannuwnta duka bisa kanta itama auta tayi nesa da hjy zulaihat "haukan shirme kuma adam ? hjy Zulaihat ta maimaita abinda ya fad'a "yes sweetheart wannan bashi da maraba da haukan shirme ,wai nmj né zai zauna yana wannan haukan abun kunya kawai "yayi maganar yana yatsuna face dinsa kamar yaga wani mummunar abu "wannan ai iskanci ne ba soyayya ba ya sake mgn yana jan dogon tsaki  ."
hjy Zulaihat tayi shiru tana duban mr ATA cikin tsananin tausayawa kanta dashi kanshi ,"bata san ranar da zai canza wannan mummunar halin nasa ba ,bata san ranar da zai bude baki yace ga matar da yake so ya aura ba ko fad'awa soyayya "duba ki gani sweetheart ya mika mata letter yana sake jan tsaki kamar wanda akayiwa dole sai ya karanta."
Jiki a matukar sanyaye mami ta karbi letter daga hannunsa tana dubawa gabadaya bata ga inda zantuttukan dake rubuce sukai kama da haukan soyayya ba ,illa ma maganar soyayyar mai sanyaya zuciya da kwantar da hankalin abokin rayuwa , byn ta gama karantawa ta kalli nana hauwa'u fuskarta dauke da tmby, kai ta gyada mata "mami sakon maryam ne "wani mugun kallo ya wurga mata wanda ya hargitsa hantar cikinta da mugun sauri ta bace masa da gani ."

sai lokacin Hjy Zulaiheart ta fahimce abinda yasa taga hankalinsu a tashe a kitchen ,numfashi ta fesar tana kallon bayansa dan tuni ya juya ya koma inda kayan suke tare da rike kugunsa ,qarara ake iya ganin bacin ransa bancin alqur'ani dake cikin kayan daya banka masu wuta gabadaya ya kona dan takaici ." wannan shine soyayya ta gsky da gsky yaji sautin muryar mahaifiyarsa tana magana tana tahowa zuwa in da yake "duk abinda ka gani anan kyautatawa ce ta soyayya tare da nuna kulawa "okay yanzu ta haka ne zai nuna emotiona dinsa ?kai gsky dai wasu mazan jakai ne, ya fad'a yana jan tsaki tare da nufar hanyar step har yayi taku biyu yaji mahaifiyarsa ta kira sunansa "adam !."
cak ya tsaya tare da juyowa ya tsura mata kwayar idanunshi da suke cike da bakinciki" zaka iya kin yarda da wannan kalaman amman at least kayi respect din emotion din wani ,karka wulakanta soyayyar wani domin bakasan yadda taka soyayyar zata kasance ba ,idan kai baka raayin soyayya karka ji haushin masuyin soyayya domin soyayya maganar Allah ce ."shiru yayi lokaci daya emotion din mafarkinsa ya shiga kai kawo a gabadaya ilahirin jikinsa ,mafarkin ma ya daukesa da mahimanci fiyye da komai arayuwarsa  wannan tunanin yasa ya bude bakinsa da kyar "alright sweetheart amman yana da kyau idan har soyayyar gskiya ce ya turo magabatansa "ya fadi haka ne saboda ya gaji da ganin fuskar maryam din acikin gidan  dan bai san dalilin dayasa ta tare masu a gida ba ,a natse ya juya ya cigaba da taka step fuskar yarinyar mafarkinsa na yawo acikin kwayar idanunshi yayinda mami tabi shi da kallon tausayi  tana girgiza kai ."

Sallamar abida né yasa mami ta dauke idanunta daga kallon hanyar da mr ATA ya bi ta maida bakin kofa tsaye take hannunta rike da hannun yesmin sanye cikin doguwar riga yar saudiya mai tsansi sosai cike da sakin fuska mami ta amsa sallamarta tana mata sannu da zuwa "yauwa mami fatan kin tashi lfy ?" ta fada tana zama cikin daya daga cikin kujerun falon .mami ta qaraso ta zauna kusa daita tana kamo hannun yesmin a lokacin mrym da nana hauwa'u sun gama tattara kayan ."
a mutunce suka gaishe da aunty abida sannan suka bar wurin zuwa dakinsu nana hauwa'u na cewa "ai kin dai ji abinda ya Adam yace ?me yace sister ? ban gane me yace ba yanzu ke bakiji yace idan soyayyar gaskiya anas yake miki ba ya turo magabantasa ba ?"oh ! abinda ya fad'a kenan ai gabadaya rudewar da nayi bai sa naji komai ba?ta numfasa sannan ta cigaba da magana "wannan ai ba matsalarsa bace idan naga dama na zauna har karshen rayuwata babu aure bai shafesa ba ,yadda bai son ana shiga lamarin rayuwarsa bai dace shima yana shiga rayuwar mutun ba ".

oh! ai bansan wuyanki ya isa yanka haka ba amman zo muje ki fad'a masa kar ya sake shiga rayuwarki"
nana hauwa'u ta riko tsintsiyar hannunta ta nufi step din da zai kai mutun samansa ,nan take maryam ta zaro idanuwa waje "haba sister kar muyi haka dake mana wannan ai maganarmu ce " a'a babu wani maganarmu ce Ke dai muje kinga daga yau zai kiyaye ,maryam ta fixge hannunta da karfi sauran kadan kwalin hannunta ya subuce "haba sister ! haba sister Ko gskiya? shegiyar masoraciya kawai iskancinki baya qarewa akan kowa sai akanmu yake qarewa dasu anas."maryam ta kwashe da dariya "ai kema Kinsan oga nada ogansa, ina ni ina tarar aradu da fad'in kai ai sai ya tarwatsani , barni na tsira da raina da lafiyata kar ya rage min sadaki suna tafiya suna magana kuma duk akan mr ATA ne ."

shiru aunty abida tana zaune har kusan mintuna shabiyar sannan ta dubi mami da kyau "wai ina ATA ne nasan yau asabar yana gida dan duk kwanakin nan bana ganin shigarsa da fitarsa ?"kullum sai yesmin ta tmbyeni shi shiyasa ma yau nace bari na kawota ta gaishesa tunda weekend ce ta fad'a tana murmushi ,mami ta gyara zamanta tana kallon fuskar yesmin "Adam yana nan galau yanzu nan ma ya hau sama ,kwana biyu da bakya ganin shigarsa da fitarsa yanayin aiki ne kwanakin nan duk bai dawo wa gida da wuri haka zalika da wuri yake fita amman yau kam yana gida bana tunanin ma zai fita dan ma ya dauko rigima ai da kin samesa a kasa .
"Rigima kuma mami kamar wani qaramin yaro ?ta fad'a tana murmushin farinciki".
"wallahi fa nan mami ta zayyane mata abinda ya faru, dariya aunty abida tayi sosai "lallai kam rigima amman ai wani lokacin akan gsky yake abubuwansa ni wallahi yana matukar burgeni yadda yake gudanar da rayuwarsa babu ruwansa da kowa sannan baya daukar raini kamar su abban yesmin koda yaushe hakoransu a bude Kmr masu tallar close up ."

"ikon allah banda abunki abida me zaayi da miskilili? ai gara masu farar nan akan masu nunkufurci da miskilanci sun dan jima suna hira sannan ta mike "to mami ni zan wuce daman abinda ya shigo dani kenan sai anjima . "shikenan abida
na gode sosai da kulawa amman ki bar yesmin ki aiko mata da sabbin kayanta zuwa anjima zaa kawo hanan domin gabatar da birthday dinta "aunty abida tai murmushi "to ai shikenan  mami zan aiko mata da...." shiru tayi sakamakon jiyo sautin muryarsa yana saukowa daga matattakala cike da izza da shan kamshi hannunwansa duka zube cikin aljihunsa wandonsa, yayinda iPod Ke manne da kunnensa yana amsa waya yesmin na ganinsa ta kwasa da gudu tana kiran sunansa "uncle AD! Hannunwansa duka yayi saurin zare wa daga cikin aljihun wondonsa ya dauketa yayi sama daita na second biyu sannan ya riketa a gefen jikinsa yana shafa fuskarta sai dai ko kadan babu alamun annuri akan a fuskarsa."

qarasa saukowa yayi ya wuce aunty abida da mami ya daurata akan wani dogon stood mai tsawo yana cigaba da wayarsa murmushi abida tayi najin dadi domin duk cikin jikiokin gidan baya daukar kowa sai yesmin kuma ta fahimci yana matukar qaunar yarinyar sosai hakan yasa itama take mugun qaunarsa fiyye da qaunar burinsu akansa."
a hankali ta qarasa inda yake tsaye "AD ..! ta kira sunansa " baki ga abinda nake yi bane ?ya fad'a a matukar hassale yana wasa da gashin yesmin."Taja bakinta tai shiru na second biyu sannan ta sake yunkurin sake yi masa magana ganin bakinsa bai motsi " uhm daman zan wuce ne ma nace mu gai..." bata kai ga qarasa abinda zata fad'a ba cak taga ya dauki yesmin ya sabata a kafad'arsa ya haura samansa a hankali ta juyo tana duban bayansa Yadda yake tafiya ma kawai duniya ne gabadayansa shi din mafarkin kowace mace dake numfashi a duniya ne shiyasa duk runtsi duk wuya sai burinsu ya cika akansa ."

Yesmin ta sakar wa mamanta murmushi tare dago mata hannu tana mata bye bye "abida Kiyi hakuri dan allah nasan Kinsan halin danuwanki ba tun yau ba "no mami ki daina bani hakuri ai idan da sabo na saba da halinsa ya zanyi  da  halin danuwana ?ni gabadaya abubuwansa basa damuna burgeni ma yake ."Masha allah haka ake so duk wani mutumin kirki ya kasance allah ya qara mana hakuri da zaman lafiya da junanmu "Ameen ta amsa ta juya ta fice daga part din hjy zulai ."

"Adam na bani matukar kunya mami ta fad'a a matukar fusace adaidai lokacin da mrym da nana hauwa'u suka dawo parlour'n sosai suna tmbyr ta "kunya kuma mami ?eh mana ku duba kuga yadda abida ta damu da shi amman shi bashi da abun wulakantawa kamarta ,ni na lura ma duk yafi tsanar ta akan kowa acikin family's din nan amman dan iskanci ya iya dauke mata diya ya wuce daita sama ." ta fad'a cike da takaici.
"ta nan bangaren ya Adam fa yana da gaskiya itama banda abunta taya tana matar aure zata dinga wani shishige masa ".?"Uhm auta ai ita ba da wata manufa take yin haka ba tana yi saboda yanuwantaka ne "kai mami kefa bakya fahimta ,wallahi munafuci ce da bakinciki ne taf acikin zuciyar wannan matar da kike kallo amman kin kasa ganewa yanzu da kin qare mata kallo murmushin yake tayi, waya san abinda ke zuciyarta "babu komai sai alkhairi ku dinga yiwa mutane fatan alkhairi ".

*******
Bayan kamar awa biyu da wasu mintuna ya fito sanye cikin wasu kananan kaya riga Orenge da white jeans kana ganin shigar kasan fita zai yi ,lokacin parlour'n Hjy Zulai ya soma cika da kawayen su maryam da yan'uwa sai dai parlour'n babu wani hayaniya a hankali suke komai sanin boss na gida da zarar zasu daga murya, sai maryam ta tsaidasu suna ganinsa kowannensu ya shiga hankalinsa tamkar basa da numfashi ."
yaja tsaki yana janye jikinsa dan kar jikinsa ya ta'ba na wata acikinsu ,ya nufi kofar fita nana hauwa'u da mrym suka hada ido tare da dagawa juna gira alamun jin dadi "nuzla tayi tsalle" yeeee ya Adam ya fita zamu sakata mu wala "tayi mgnr tmkr wata qaramar yarinya "ke dai bari nuzla wallahi tun dazu a firgice muke nida maryam ,wallahi gbdy bama cikin natsuwar mu tun dazu addua nake acikin zuciyata allah ya kawo dalilin da zaisa ya fita ya bar gidan gbdy ko ma sakata mu wala sai gashi allah ya amsa adduata, gashi ma ya fito ya ganmu dayawa bai ce komai ba wallahi baqaramin dadi naji ba inji cewar nana hauwa'u ."

Maryam tai juyi cikin doguwar rigar dake sanye ajikinta sannan ta tsaida kananun danunta akan nana hauwa'u "sister wannan yayan naki mai sufar zaki akwai shi da mugun iyayin tsiya sai dai fa yayi kyau sosai exactly irin mijin da nake muradin aure kenan amman samun irinsu da matukar wahala ,
Ina ma zan samu yadda yayi kyau din nan ace Ana's ne da yau mu dauki hotuna masu yawa mu daura a social media nasan da ba qaramin comments da like's zan samu ba." tunda ta fara magana ya dawo bata sani ba yana tsaye a bakin kofa sai faman zuba take "burin kowace mace a duniya ta samu miji kamarsa amman samun irinsu da wahala amman babu komai mayi hidima wa Allah mu samu a aljanna idan muna da rabo "
"Kun san wani abu dake bani driya dashi ? duk sukai shiru babu wacce tayi tari "abu kadan zai hade fuska ya kalli mutun ya disga mutun da kalmar nonsense , crazy girl " ta fad'a tana karairaya cak ta tsaya tana duban wadan da ke tsaye a gabanta ga mamakinta taga dukkaninsu babu wanda yayi dry Kmr yadda suka saba a duk sanda wani yayi irin maganarsa ."

a hankali ta juya bayanta cike da tsananin faduwar gaba aiko idanunta suka sauka akanshi yana mata wani irin kallo mai dauke da yawon tsanar da yayi mata ,da sauri ta zaro idanuwa waje tana kallonsa kmr a mafarki, ta lumshe idanunta na second daya ta bude taga dai tabbas shi din ne tsaye agabanta ,ta dan juya bayanta tana kallonsu Kmr zatai kuka."
Gbdy jikinta ya kama rawa a hankali ta sakê juyowa ta fuskancesa ta hade hannuwanta duka wuri daya tare da yin kasa har ta kai kasa muryarta na rawa "am very very so.." sorry " .
shiru yayi yana qare mata kallo tsab sanye take ckin doguwar rigar wanda hannunta daya long sleeve ne dayan kuma hamless gabday an canza mata kamani ta hanyar yi mata make up ga gashin kai tayi fix ya sauko har gadon bayanta abinda yafi tsana kenan daga mace too much of kwaliya da qarin gashi da farce ita kuma duk ta kware wurin yinsu "ita fa a ganinta tayi kyau da wannan shigar da kwaliyar da tai ?ya tmbayi kansa yana jan tsaki dan a idanunshi muni tayi masa barin ma rashin tsawon da Allah yayi mata ,shi kam yayi imani banci farin fatan da allah yayi mata da babu shegen nmj da zata dauki hankalinsa har ma ya tsaya bata lokacinsa wajen haukan shirme akanta ".

"kusan second goma ya dauka yana kallonta yana hukuntata da idanunshi kafin daga baya ya bude bakinsa Kmr baya son yin mgn " maid your business duk abinda zaki yi karki sake kuskure ambaton sunana cikin shirmenki me nace ? ya fad'a yana zaro mata ido "Kar...kar !! na sake ambaton sunanka kayi hakuri wannan ma kusku.....you're very stupid dake da kuskuren , daman kin saba this is not your first time koni sa,an wasanki ne ? da sauri ta girgiza masa kai ya gyara tsayuwarsa " ki dinga abu kamar wata mental sam sam baki da natsuwa crazy girl kawai ki godewa allah akwai abinda zanyi mai mahimanci dana tsaya naci ubanki guntuwar banza kawai ." ya fad'a yana sa kai ya hau sama ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya aranta tace "oh my god you save me for the first time ,byn kmr second biyar ya sauko ya fice gbdy daga gidan .

Bayan fitarsa cikin bacin rai tace "ko kun tayani jin abinda ya fad'a? suka kwashe da wata mahaukaciyar dariya "wai kece mental crazy girl mara natsuwa a karshe wai guntuwar banza wallahi ni duk shi yafi bani dariya wai guntuwar banza cewar nuzla ta fad'a tana tafa hannu tana dariya "see me see trouble shi fa idan ba zagi ba babu abinda ya iya arayuwarsa dan wulakanci ma har da zagin halittar Allah cewar diyana "kunga karku qara mata bakinciki byn kunsan yau ranar farinciki ne gareta nana hauwa'u tayi mgnr tana mikar da maryam tsaye dan tunda ta durkushe kasa bata iya ta mike ba tsabar tsoro ."
Byn ta mike tsaye bisa kafafunta ta kallesu daya byn daya tana maka masu harara mai kunshe da bakinciki "gsky gbdy baku kyauta min ba, kuka barni ina ta faman zuba aka rasa wanda zai min alamar nayi shiru acikinku daman burinku yaci min mutunci kuyi dariya ko? Kema idan zakiyi magana next time ki dinga kallon kofar shigowa ba baya zaki bawa kofa ba in case inji cewar nuzla ,asra tace "au ke nan yanzu haushi kika ji da ba ki godewa allah ba kamar yadda yace dan da yanzu ba wannan labarin kike ba "na so oooo I thank god for saving me."

Bayan wani lokaci gidan mami ya cika da ya'yanta da jikokinta da wasu daga cikin jama'ar estate din parlour'n ya hargitse da hayaniyar mutane anci an sha anyi rawa hanan ta yanka cake haka ma maryam tare da daukar hotuna da vedios mutun biyu ne kawai acikin yammatan family's da basa cikin hotunan marigayiya mubina da sultana wacce Ke matakin karshe a jamiar cairo ."

su maryam abun nema ya samu domin kuwa duk hotuna da sukai babu bata lokaci take daurawa a social media "nuzla ta samu wuri ta zauna shiru idanunta na cikowa da ruwan hawaye sakamakon tuno marigayiya mubina ,maryam ce ta lura da yanayinta ya sauya dan haka ta qaraso gareta ta zauna akan hannun kujerar da take zaune tana tmbyrta "Lafiya nuzla kika zauna shiru haka ?numfashi ta sauke tana  furta sunan "mubina...!" tun kafin ta rufe baki sai hawaye sharrr sharr!! sun zubo Kan kuncinta dan haka ta kasa qarasa maganarta , maryam ta tsuke baki tana riko hannunta cikin nata " nuzla ki daina kuka haka addua ya kamata kiyi mata alokacin da kika tunota ,wallahi koni sai data fado min arai kuma nasan gabadayanmu babu wanda bai tunata ba domin mubina ta shiga ranmu fiyye da komai ta fad'a tana goge mata hawaye "ki bar kuka haka kada sauran su fahimta kisa hankalinsu ya tashi ,wanda ya mutu babu abinda yafi bukata kamar addua kuma muna mata babu ranar da zatazo ta wuce banyiwa mubina addua ba allah ya jaddada rahma gareta ta fad'a tana mikar da nuzla tsaye suka shigo cikin sauran yan'uwa nuzla kam baa qarasa gudanar da birthday party daita ba ta wuce ."

******
Byn wata shida

Sanye yake cikin kananun kaya jeans da riga t shirt tsadaddu product din American yana tsaye a haraban katanfarin estate dinsu tare da hisham hannuwansa duka zube cikin aljihun wandonsa , kallo daya zaka masa ka fahimci ransa a 'bace yake dan fuskar nan tashi babu alamun rahma sakamakon abinda ke dawainiyya da rayuwarsa , uwa Uba sweetheart dinsa dake sake hargitsa masa lissafi da batun auren data bijiro masa da yarinyar daya tsani gani a rayuwarsa dan idan yana qaunar mutuwarsa to yana qaunar yarinyar ."Suna nan tsaye hisham nayi masa magana akan sakonnin daya samu akan kasuwancinsu amman shi sam hankalinsa da natsuwar basa garesa , yana nazarin yadda rayuwa ke tangaliliya dashi da Inda zai ajiye akalar rayuwarsa, da rayuwar da mahaifiyarsa da yan'uwansa suke son yayi a yanzu ."
a hankali hisham ya matsa kadan daga gefensa domin amsa kira dan yasan halinsa baya son qarar waya , ringing din wayar hisham daya fara ne ya dawo dashi haiyacinsa ya fesar da iska mai zafi daga bakinsa tare da kai Kyawawan idanunshi saitin gidansu ,maryam da muhd bello babban amininsa ya gani suna 'kokarin fitowa daga cikin gidansu wani irin mugun haushi ya kamashi zuciyarsa ta dinga zafi da tuttukin bakinciki bangaren maryam ganin in da yake tsaye suka nufa yasa bugawar da qirjinta yake ya qaru fiyye da kaida ."

Mmm sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

Table of Contents

Chapters

10 chapters
  1. 1 Book one
  2. 2 Book one
  3. 3 Book one
  4. 4 Book one
  5. 5 Book one
  6. 6 Book one
  7. 7 Book one
  8. 8 Book one
  9. 9 Book one
  10. 10 Book one