Skip to content

Chapter 13

Chapter 70 70

Babu So Mi Yakawo Kishi Book One Complete Hausa Novel 11,869 words 0 views Progress saved
Download Book

........Wasa farin girki wai amarya da tuƙa

tuwon tiya goma. Ashe rikici a waya tsakanin Mommy da Gwaggo Halima somin taɓi ne. Dan kuwa ba'a rufa awa guda cikakkiya ba sai ga Gwaggo Halima tazo gidan. Hakan yayi dai- dai da dawowar Daddy daga wajen aiki gidan shima. Yay sagade yana kallon Gwaggo
Halima data ƙaraso garesa tana huci. “Halima lafiya kuwa da magribar nan?”. “Inafa lafiya Yaya, Share! ya buɗe ƙwanji ya
shashsheka ma Fadwa mari amma saboda
son zuciya irin na matarka ta goya bayansa
saboda itace ta haifesa”.
Da mamaki sosai yace, “Mari fa dai? Ya
ALLAH mike damun Share! haka? Wannan ba
maganar nan bace shiga ciki nafara zuwa salla
kafin su Abubakar su dawo”.
A maimakon sashen Mommy ko Gwaggo da
da idan tazo gidan take shiga yau sai ta nufi sashen Mom.....
________________★
Rashin fitowarsa har aka kira sallar magrib yasaka Anaam kasa zaune ta kasa tsaye. Tana son zuwa dubashi tanajin tsoro. Gani take kamar itama ɗin marin nata zaiyi. Harga ALLAH tana matuƙar tsoron duka a rayuwarta. Koda wani taga ana duka firgicewa take. Ballema har abada bazata taɓa iya

manta dukan dayay musu ba ita da Aysha. Da sauri ta juyo jin motsin buɗe ƙofa. Sukaima juna kallon cikin ido ita da shi, ita ta fara janye nata tana sauke ajiyar zuciya dajin shakkar
kallon fuskarsa dake a matuƙar tsuke. “Ki tashi kiyi salla”.
Ya faɗa a taƙaice da juyawa zai fita. Harya kama handle ɗin ƙofar zai fita ya tsaya cak, juyowa yay a hankali yana kallonta saboda ganin yanayinta. Sai dai baice komaiba ya juya ya fita. Numfashi ta saki a hankali da miƙewa ta shiga toilet domin ɗauro alwala.
Bai dawo gidan ba sai bayan sallar isha'i, kai tsaye kuma sashenta ya zarto. Tunda ta idar da salla ta kasa tashi a wajen, babu abinda ke mata kaikawo, haka kawai marin nan na ɗazun da yay ma Fadwa ya matuƙar tsaya mata a rai, duk da kuwa ƙararsa kawai taji bawai yinsa akan idonta ba. Harya ƙaraso gabanta bata san da shigowarsa ba, ya kai tsugunne gabanta, tare da ɗago haɓarta. Cikin idanunsa ta zuba raunannun nata da babu gilashi, bata ganinsa fes yanda ya kamata, amma hakan bai hanata tsaidasu a
tsakkiyar nasan ba... “Mike damunki?”.
Ƙoƙarin janye idanunta tai a cikin nasa ya hana hakan, taso kauda kanta gefe nanma ya

hana, saita ƙara tsuƙe fuska da tura baki. A karon farko ya saki murmushi, tare da kai yatsansa ya ɗalli lips ɗin nata. “K wai baki san shekarunki sun girmi wannan taɓaran ba Autar mata?”.
Hanunsa ta ture zata tashi, yay saurin
damƙota yana dariya, jikinsa ta faɗa, dan
haka suka zube ƙasa gaba ɗayansu. Ƙafarsa
ɗaya ya kwanta, tare da jawota ya kwantar a
cinyarsa ita kuma. Ya tokarar da ɗayar ta
jingina kanta. “Nayi laifi ne wai?”.
Hanunsa dake kan cikinta ta kamo, ta saka
babban ɗan yatsan a bakinta ta ciza. “Wai wai
shiii! Wace mugunta ce muka wannan?”.
Dariya ta ƙyalƙyale da shi. “Noorie muguntafa
babu ƙyau sam sam”. Ka ɗan ta murguɗa
masa baki “Punishment ɗin mai yawo ne ai”. “Shi kuma punishment ɗin mai rashin kunya
fa? yaya ya kamata ya kasance?”. “Sai an binciko a littafin shara'a”.
Ta faɗa tana ƙoƙarin mikewa ta gudu. Riƙota yay yana ƙaramar dariya. “Sarkin wayo ai ni tuni na binciko. Yanzu kuma zan ƙaddamar da shi”.
“Wayyo yaya! Wayyo ni yunwafa nakeji, tun safe banci komai ba.”
“Nima ita nakeji ai”. Ya ƙare maganar da manne lips ɗinsu waje guda. Ko sau ɗaya batai ƙoƙarin hanashi ba, saima gudunmawa

data fara bashi, burinta kawai taga ya huce
daga fushinsa. Cikin ƙanƙanin lokaci ta gama
hautsina masa kwanyar kansa, tun yana binta
a salon jarumta harya fita a hayyacinsa ya
ɗauka wata hanya da ban da karatun da ya
kasance mai girma ga Anaam. A yanzu kam ita
ya nema gigitawa, yayinda shi tuni ya fita
hayyacinsa har baya gane ita ɗinfa ƙanwarsa
ce. Sunyi matuƙar shagala a farantama
junansu ring ɗin wayarsa ya shammacesu. Da
ƙyar Anaam ta iya janye jikinta dake rawa
gefe. Shima nashin rawar yake fiyema da tata,
sai dai jarumtar ƴan mazan ta ɓoye haka, ya
rimtse ido da ƙarfi ya sake buɗewa saboda
ganin mai kiran. Ko'a turu a kwantosa bai isa
ɗaga wayar nan ba, dan babu makawa sai
Daddy ya gane halin da yake a ciki. Haka ya
barta harta tsinke wani kiran ya ƙara shigowa.
Yanzun ma kasa ɗagawar yay har saida ta
yanke, da ƙyar ya samu iya ɗan dai-daita
kansa bayan wasu mintuna sannan yay kiran
Daddyn Back.
Koda Daddy yaji muryarsa a shaƙe a zatonsa
duk ɓacin rai ne, dan kuwa yasan wanene Share! idan yay fushi. “Ka sameni a gida yanzun nan kai da Fadwa”. Bai jira cewarsaba ya yanke kiran. Shima ɗin baice komaiba ya koma kwance tare da mirginawa jikin Anaam

data juya masa baya ya rungumota da ɗaura
kansa a gefen wuyanta yana shinshina, ga
sanyin tiles na ratsasu dan harya huda
sallayar tana iya jinsa a jikinta shima haka.. Jin saukar hanunsa a ƙirjinta tai saurin
riƙewa. “Yaya kirankafa Daddy yakeyi”. Iska ya ɗan hura mata cikin kunne da ture hanunta ya ɗaura a inda yay niyya tun farko. “Koratama kikeyi kenan?”.
“Eh mana, Daddy ba abin wasa bane ai,
umarninsa yana sama da muradanmu”. Sassanyan murmushi ya saki da sake
ƙanƙameta a jikinsa, a hankali ya furta *_Ina ƙaunarki da yawa_*”. Sosai tsigar jikinta ta yamutsa saboda yanda yay furucin a cikin wani irin wahalallen sauti. Taja numfashi mai kauri da cije gefen lips ɗinta sakamakon saukar kiss ɗinsa saman wuyanta. Bata iya ta ɗago ta kallesa ba harya fice daga ɗakin. Ta sauke sassanyar ajiyar zuciya da sake kananneɗe jikinta waje guda wani abu mai girma na tsikarar ƙasan zuciyarta....
A sashen Fadwa kan duk da yaji a ransa itace takai ƙararsa wajen su Daddy bai mata magana ba, umarnin kawai ta samesa a mota ya bata ya juya ya fita abinsa. Taja wasu mintuna kafin ta fito dan har ya kunna mota

ma.
Tafiya suke amma kowanne fuskarsa na gefe,
ita tana kallon mutane shi kuma titi har suka iso. baiyi mamakin samun Gwaggo Halima ba, Fadwa ta nufeta ta rungumeta tana sakin kuka. Lallashinta ta shigayi tana shafa bayanta da fuskarta wai tana neman tabon marin. Abin sai ya girmi kan kowa amma babu wanda yay magana sai Mommy ce taja tsaki da taɓe baki. Share! kam zama yay ƙasa a tsakkiyar ƙafafun Abie da Abba. Kansa a ƙasa batare daya kalla kowa ba ya gaishesu. Haka kawai yakejin tsananin kunyar Abie da Mommynsa fiye da kowa a wajen.
Abba da yaga mulmular da Gwaggo Halima kema Fadwa na neman yin yawa ya magana a kausashe. “K Fadwa tashi ki zauna da ƙyau bama son shashanci”.
Tashin tai zaune, sai a sannan kuma take
gaidasu. Iya su mazan kawai suka amsa.
mommy da Gwaggo babu wanda ya tanka.
Gwaggo Halima tai ƙaramar ƙwafa da ayyana
(Zanyi maganinku) a zuciyarta.. Abie ne ya
buɗe taron da addu'a, kafin ya maida
hankalinsa ga Share! cikin serious matuƙa. “Al-Mustapha miya haɗaka da matarka
harda mari? Bayan wannan ba ɗabi'ar dakaga wani a cikinmu nayi a gidan nan bane?”.

Ƙasa Share! ya ƙarayi da kansa, cikin
matuƙar girmamawa. “Kuyi haƙuri Abie nayi
kuskuren aikata hakan, sai dai saida na
umarceta ta tashi tabar inda nake dan bana
son yanke hukunci cikin fushi, amma taƙi yin
hakan har takai nayi marin”.
“Amma banda abinka Babana ai kai
babbane, da taƙi tashi sai kai ka tashi ka bata
waje tunda kasan baka iya controling kanka a
yanayin fushin. Su mata haƙuri ake dasu a
kowane hali, domin hangenka da nasu sam ba
ɗaya bane ba, sai dai sunada sauƙin sha'ani
kuma ba koda yaushe ake cizawa a kansu ba”. “Hakane Abie, insha ALLAHU hakan bazata
sake faruwa ba......”
“Tama sake faruwar mana. Wlhy da kaina zan
rama mata mara mutunci kawai. Kai yanzu
dan baka da kunya Share! har kanada hanun
ɗagawa ka daki Fadwa a gidanka?”. “Yaya Halima! Ya kamata kiyi shiru abi
komai a sannu”.
“Wane kuma sannu Abubakar, bayan kanaji
yana lallaɓashi saboda ba ƴarsa aka mara ba”. Murmushi Abie yay da girgiza kansa. Cikin
dattako da nutsuwar da kowa ya sansa da ita ya fuskanci Gwaggo Halima. “Ba haka bane Yaya Halima. Da Share! da Fadwa da Anaam duka su ɗin ƴaƴanmu ne, bazamu taɓa sakaci da cutuwar ɗayansu ba ai. Da kinyi haƙuri zan

kai inda kike buƙata nima ai”.
Baki ta taɓe da juya kai gefe. Nanma
Murmushin Abie ya saki kawai ya sake maida
hankali kan Share! da ransa ya ɓaci. “Babana
ina jinka miya haɗaku takai ga mari?”. “Ban taɓa fatan dan na samu matsala da
wata a cikinsu sai munzo gabanku ba. Amma
tunda ita tafi zaɓar hakan a koda yaushe fine.
Fita nai a gida tun safe ina wajen matsalar can
data taso a company, na dawo kawai na samu
ta cikamin sashe da ƙawayenta wai suna min
gyara. A yanda suke komai kai tsaye ya
tabbatar min ba yau ce rana ta farkon hakan
ba. Korarsu kawai nai na ƙyaleta domin ita
tasan bana son yanke hukunci cikin fushi,
amma saita biyoni bayan nace ta ƙyaleni a
yunƙurin farko da tai. Taya zata kawomin
wasu ƴan iska sashe, ta san adadin abubuwan
dana ajiye masu muhimmanci a ciki? Ko
bamma ajiye komaiba ita bazatai tunani da
hankalinta rashin dacewar kai wani can ɗin”. “Inafa zata san abinda ya dace tunda a nuna
mata barbaɗa magani shine kawai zaman aure”.
A harzuƙe Gwaggo Halima ta dubi Mommy
mai maganar. “Nafi wlhy ki iya bakinki domin
zai kaiki ya baroki allura ta tono galma”.
“Yo ta tono mana dan ubanta, abu mai sauƙi

bayan ta tono ita galmar ta turbuɗata cikin
ƙansa yanda ko mayen ƙarfe ƙaryarsa sake
ganinta”.
Aifa nan take falon ya harmutse da hayaniya
tsakanin Mommy da Gwaggo Halima. Mamaki al'ajab sukabi suka sanya Share! cikin madaukakin imani. Yau kuma aminai biyune kema juna tujara haka akan abinda suke ganin shine mafi ƙololuwar alkairi a garesu idan suka ƙulla. Kai duniya ina zaki kaimu ne haka?. Da ƙyar su Daddy suka samu sukai shiru. Gwaggo kam tayi kamar bata a falon tai muƙutt da cuno baki gaba ita a dole takai maƙurar ɓacin ran abinda su Mommyn ke aikatawa. Acan ƙasan ranta kuwa dariya taketa kwasa. Yanzu kam Abba ne ya amshe da zancen yana mai fuskantar Fadwa.
“K shashashar inace da zaki bama ƙawaye damar shiga ɗakin mijinki? Haka kikaga iyayenki na mana? Wace irin mace ce ke da baki kishin mijinki? Ai wannan jama kanki rainine ma wajen su ƙawayen naki da shi kansa mijinkin. To saurara ki jini, daga rana mai kama irin tayau, hakan ta sake faruwa ni da kaina zan hukuntaki sannan shima nasa ya hukuntaki tunda koba aure tsakaninku
Yayanki ne.. Kinaji na da ƙyau?”.
Hawaye ta ta share tana jinjina kanta. “Zan

kiyaye Abba insha ALLAHU. Amma Abba dama fa haushina yakeji, dan dama a kwanakin nan banda wulakantani babu abinda yakeyi saboda ya ƙara aure. Baya ganin kowa a gidan sai ita ƴar gwal.....”
“Shiyyasa kuka dage boka da matsubbata ke
da uwarki domin sabautamin ɗa. Su Malika na
kawo miki barbaɗe-barbaɗe kina faman zuba
masa dare da rana. To wlhy babu lallai babu
dole tun kan ai nisa sai ya datse igiyar auren
tunda bake kaɗaice mace ba a duniya......” “Dan ALLAH Nafisa idan baki sakashi ya
datse igiyar aurensu ba baki cika uwarsa ba,
kuma shi din bai haifuba a cikinki...” “Haka kikace?”.
“Eh na faɗa. bandama ƙaddara mi Fadwa
zatai da wani Share! can. Ko dama kun ƙulla
a haɗasu aure dan ku dinga maidamin yarinya
baiwarku”.
“Hahaha yo baiwa kuma ta nawa Halima.
Sai dai wata kuma dan ita kam ta riga ta gama zama labari”.
Ƙara hargitsewa falon yay, da ƙyar yanzu kam Abie da Abba suka sakasu yin shiru, dan Daddy dai ya mugun shaƙa zuciyarsa har wani zallo takeyi, gata tokare a maƙoshinsa kamar yay amanta ya huta.............
End of book

End of book
Leave a comment
Post
omments
No Comments posted yet
C*_Typing📲_*

*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

*_71_*

..........Gigitacciyar tsawa Daddy ya daka musu. “Wlhy duk wadda ta sake cewa tak sai ranta yay mummunan ɓaci, idan kuma kunji ƙarya bismillah marasa mutunci kawai. Ku har kun isa ku maidamu mutanen banza. Ku tashi kufita bama buƙatar zaman kowacce a anan”.
       Cikin ɓacin rai suka mike su biyun suka fice. Daddy ya cigaba da faɗa tamkar zai ari baki, da ƙyar dai su Abie ɗin suma suka taushesa. Haɗuwa sukai akan Fadwa da Shareff ɗin duka sukai musu tatas da faɗa musamman Fadwa a matsayinta na mace. Sai kuma suka koma nasiha a garesu. Daga nan suna jiyo hayaniyar Mommy da Gwaggo Halima, hakan yasa Gwaggo da har yanzu bata tofa nata ba ta miƙe ta fita wai zata tsawata musu. Nasiha Abie ya sake musu ta fahimta data saka zukatansu samun nutsuwa, musamman ma Fadwa da taga an nunama Shareff kuskuren marinta da yayi kuma ya nuna nadamar yin hakan da alƙawarin bazai sake ba. Duk da dai itama tasha nata, sun kuma nuna mata illar biyema su aunty Malika cikin hikima. Basu san babu abinda ke cizon zuciyar Shareff ba kamar maganar su aunty Safara'h ɗin nan. Sai dai baice komai ba dan a samu zaman lafiya, amma yay aniyar da kansa zaima tufƙar hanci insha ALLAHU.

        Da ƙyar wajen ƙarfe goma suka baro gidan, dan kuwa rikici ne na gaske ya ɓarke tsakanin Gwaggo Halima da Mommy har sai da Baban Fadwa ya kira waya dan baya ƙasar ne shiyyasa harta samu damar fitowa. Ya kuma janye mata wancan sharaɗin lokacin da zaiyi tafiyar saboda haƙuri data bashi akan komai ya wuce. Ashe akwai wani a gaba. Mommy dai taci alwashin sai ta nunama Gwaggo Halima itace ta haifi Shareff ba wani shege ya haifa mata ba. Haka itama Gwaggo Halima ta tabbatar mata cewa ita bata isa komai ba domin Shareff ɗin ba nata bane ita kaɗai..
     Kuka Fadwa ke masa tunda suka taho, dan kuwa rikicin Mommy da Mamanta ya matuƙar ɗaga mata hankali kuma, tana matuƙar tsoron abinda zai rabata da Shareff, tana masa so ne mai tsanani, wanda takejin in har aka rabasu zata iya rasa har ranta. Ya gaji dajin kukan, saboda shima zuciyarsa a wuya take kuma yanajin ƙuna da raɗaɗin abubuwa masu yawa. Sai dai shi jarumin mutum ne mai maida komai ba komai ba koda kuwa a ce ya zame masa komai. Dan haka har suka iso gida bai ce mata komai ba. Shine ma ya fara fita ya barta a motar, saida ta kai kusan minti huɗu a ciki tana cigaba da kukanta sannan ta fito ta rufe motar. Sashensa ta bisa kai tsaye, yana a falo zaune cikin yanayi na wanda baka iya ganemawa. Cikin jan ƙafa ta ƙarasa gabansa, ta tsugunna tare da dafa guyawunsa.
      “Ina tsugunne ne gabanka a matsayin ƙanwa Yaya Shareff, nasan ni mai laifukace a gareka tari-tari, na kuma yarda nayi kuskuren da kake son na fahimta tun kafin akai ga wannan gaɓar. Wlhy bana son zumincin iyayenmu ya lalace saboda aurenmu......”
    “Garama ya lalace, dan ta hakane kawai dake da su zaku dawo rayuwar hankali irin ta mutane. Ke kam rayuwarki naban mamaki matuƙa, mamaki irin wanda nake shiga kokwanto. Ba haka nai miki zatoba sam-sam a rayuwata ba, amma bazance ki dainaba kiyi tayi, shawara ɗaya zan baki kuma ta ƙarshe. Ya rage naki ki dawo akan ƙyaƙyƙyawar hanya ɗaya tak ki gyara halayenki muyi zaman aure na gaskiya, idan ba hakaba wlhy wlhy zan ɗauki mataki ne na ƙarshe dan bazaki maidani mahaukaci ba. Shawara ta rage gareki, ki cigaba da biyema duk wani mai zuwa gidan nan yana ɗauraki a hanyoyin da shi yake ado da su, koki zama mace tagari ki gina taki rayuwar a karan kanki. Idan kuma kika sake amfani da wani abu na kauce hanya domin mallakata, ko bani wani abu a cikin ruwan sha ko abinci ALLAH ya isa ban yafe ba!”. Ya ture hanunta tare da miƙewa ya shige bedroom abinsa.
     Hawayen da take son su zuba ma sam sunƙi zubar a yanzu, sai dai tasan gaskiya ya faɗa mata, dan kuwa a yanzu tana rayuwa ne da rayuwar su aunty Safarah, a baya komi za'a bata ta zubama Shareff a abinci bata taɓa yin hakan tunma tana gida, duk ma yanda zatai ƙoƙarin hanawa sai tayi, sai dai in Mama ta aikata bada saninta ba. Amma a wannan gaɓar ta rikice, idonta ya rufe saboda kishiya da kanta take aikata komai dan taga haske. Sai dai saɓanin hakan duhu take gani, sannan mai makon mallakarsa suɓuce mata yakeyi, kenan su magungunan na ƙarya sunfi yawa a cikinsu kenan? Ƙalilanne ake dacewa suyi aikin kuma basa wani jimawa sai kaga abubuwa sun ƙwaɓe. ‘Ya ALLAH’ ta faɗa tana mai fashewa da kukan zahiri.

    _____________★

       Harta fara jin barci a jiya bai dawo ba, dan ita bata san tare da Fadwa ya fita ba. Koda ta shirya ɗakin da Aysha ke kwana taje ta kwanta abinta. Ayshan batace da ita komai ba dan tasan yau Shareff ya koma wajen Fadwa. Ta ɗanyi murmushi ganin Anaam ɗin sukuku, ko bata fito ta faɗa ba tasan kewar Yayansu ke nuƙurƙusarta. Sai dai sanin itama Anaam nada halin I don't care wasu lokutan yasa babu wannan alamar akan fuskarta sam. Sai dai kuma koda suka kwanta ta jima batai barci tanata juye-juye. Sai da Ayshan ta ɗauke hankalinta da wasu labarai  sannan ɓarawon yay mata kamun kazar kuku. Ajiyar zuciya Aysha ta saki mai ƙarfi da kai hannu ta riƙo na Anaam ɗin. Tausayinta da ƙaunar ƴar uwarta na ratsa mata zuciya matuƙa....

       ★Kamar yanda ya saba da asuba sai da yazo ya tada su, Anaam ƙin yarda tai ta kalla inda yake taima shigewarta toilet. Juyawa yay ya fita shima yana mai sakin guntun murmushi. Itama Fadwa sai da yaje ya tadasu sannan ya wuce massallaci. Daya dawo bai shiga sashen kowacce ba ya koma nasa sashen ya kwanta dan jiya ya jima bai barci ba yanata faman ƙullawa da kwancewa akan yanda zai ɓulloma matan nasa. Barci yasha sosai dan sai kusan goma da wasu mintuna ya iya tashi, baiyi mamakin ganin an gyara ko'ina ba ga ƙamshi na tashi, sai dai yaji sassauci a ransa dan Fadwa ta nuna masa ta yarda ta gyara abinda take shirin ɓararwa a idanunsa. Wanka ya farayi ya shirya tare da baje jikinsa da ƙamshin turarurrukansa masu ƙamshin daɗi. Koda ya fito a falo ya sami Fadwa zaune cikin kwalliya mai ɗaukar hankali. Tabbas ta ɗauka hankalin nasa da gaske, sai dai ya basar abinsa. Gaisheshi tayi, ya amsa a daƙile, bata gazaba wajen sake jero masa kalaman ban haƙuri da tabbatar masa zata canja fiye da yanda yake buƙata. Har cikin rai ya ɗanjin tausayinta, dan yasan ya mata hukunci dai-dai da laifinta da har idan ita ba ibilisiya bace ya kamata yaga canjin. Huci ya ɗan furzar tare da ware mata hannayensa. Ai da gudu tazo ta shige jikinsa. Ya saki ƙaramin murmushi tare da sauke hannayensa akan bayanta ya fara shafawa alamar lallashi. Hawayene suka dinga silalo mata, ita kanta ta ƙara shaidawa Soulmate ɗinta zuma ne, ga zaƙi ga harbi. Ya ɗagota yana kallon fuskarta har yanzu dai babu fara'ar da take muradin gani a garesa.
“Kin san bana son kukan nan ko?”.
Kanta ta jinjina masa tana sharewa, ya raɓata ya wuce yana faɗin, “Ina zuwa bara na duba waɗan can ya suka kwana”. Kanta ta jinjina masa, ta bisa da kallo tana ƙara tsane hawayenta dake sakkowa. Ta san bawai ya gama hucewar bane, amma ko yanzu ta samu sassauci. Zakuma tabi duk hanyar data dace domin ganin ya huce baki ɗaya sun koma rayuwar farin cikinsu....

A falo ya samesu su duka. Anaam na tsaye riƙe da cup na shayi idonta a tv tana murmushi. “Wato blood film ɗin nan fa zaiyi daɗi, sai dai guy ɗin film ɗin sam baimun ba shegen kunensa uwa na zomaye ALLAH”. Dariya Aysha ta sanya harda ƙyaƙyƙyawa tana leƙowa daga kitchen. “Amma wlhy kinci zarafin mutumin nan, ni banga wani kunen da kike masa sheri da su ba.”
“ALLAH da gaske yanada kunnuwa gasu nan, ga shegen rawan kai a wajensa uwa dangin makaɗan zamanin jahiliyya, ALLAH an cuceta da aka haɗata da shi”.
Alamar komawa yay ma Aysha data leƙo zatai magana, tai saurin komawa cikin bin umarninsa harda turo ƙofar kitchen ɗin dan ta tabbatar wata taɓarar za'ai. Rayuwar Yayansu na birgeta tun akan Fadwa, gashi dai mutum miskili da baya ɗaukar raini amma matansa nashan sharafin soyayyarsa. Cigaba yay da tsayawa a bakin ƙofar hannayensa harɗe da ƙirjinsa yana kallon Anaam ɗin kawai. Ita ko sam bata san da zamansa ba amma tanajin ƙamshin turarensa a hancinta wanda take ganin hakan normal ne tunda dama yana shigowa maybe tunna baya ne. Juyowa tai zata koma saman kujera suka kusa cin karo da shi dan ya baro ƙofar. Da sauri ta ɗanyi baya a zabure dan tsoroma ya bata. Cikin zafin nama ya riƙe cup ɗin shayin dake neman antayewa a jikinta.
Baki ta tura gaba da ƙwaɓe fuskarta da tasha kwalliya. “Kai Yaya ALLAH ka tsoratani”.
Idonsa akan lips ɗinta ya ɗage mata gira ɗaya, “Kin dai so ki tsorata madam”. Bakin ta ƙara tura masa tana ƙoƙarin janye jikinta. Hanata hakan yay ta hanyar riƙo ƙugunta, ya zuba mata mayun idanunsa cikin nata idon, tare da matso hanunta da nasa dake rike da kofin shayin yakai bakinsa. “Wayyo Yaya ni ALLAH zaka shanyemun tea ɗina”.
“K miyasa rowanki yayi yawa ne?”.
“To kai miyasa kwaɗayinka yay yawa ne”.
Murmushi yayi da kai yatsarsa ya ɗalle mata baki, “Magananniya da ba'a kadata. Sammin lipstick ɗin shima Please”.
“Tab ni ban saka da kai ba ni kaɗai zan shanye abuna”.
Dariyarsa ya danne da ƙyar, ya ɗan ƙwaɓe fuska da langaɓe kai gefe, “Babie Please mana”.
“Naƙi wayon”. Ta faɗa dayi masa gwalo tana tura lips ɗin cikin baki. “Ni kikama rashin m ko? Zan rama ALLAH”. Dariya ta ƙyalƙyale da shi da masa gwalo. “Kafin ka rama na ƙara wani rashin m ɗin ma”. Ta zille, riƙota yasoyi amma tai tsalle gefe tana masa gwalo. “Zan rama ne yarinya ai zaki zo hannu. Oya muje breakfast”..
Idanu ta ɗan waro, “Gashifa Aysha na mana anan”.
“Kin manta tsarina kenan”.
Shiru tai cikin ɗan tauke fuska. Dan ta ƙwallafa rai a abinda Ayshan keyi. Amma sai batai musu ba ta kaɗa masa kai. Tare suka fita, sun iske Fadwa na ƙara gyara dining ɗin. A yau ma babu wacce ta kalla ƴar uwarta a cikinsu. Dan haka ya duba kowacce fuskarsa a tsuke. “Kun gaisa da juna?”.
Shiru duk sukayi kowanne idonsa a ƙasa dan a serious yay maganar. Fadwa ce tai ƙoƙarin dannewa a shaƙe tace “Kin tashi lafiya?”. Baki Anaam ɗin ta taɓe da amsawa a shaƙen itama. “Alhmdllhi”. Komai bai sake ce musu ba, dan yasan a haka a haka watarana zai ci nasara. Wayarsa da yake latsawa ya ajiye, Fadwa ta fara haɗa masa abincin. A daidai nan Aysha ta shigo da ƙaramin tray. Wani irin ajiyar zuciya Anaam ta saki a hankali. Ya ɗan saci kalonta ta gefen ido sai yaji tausayinta. Ya fahimci tana son abinda Ayshan ke musu amma tabi umarninsa ta taho, shiyyasa yayma Aysha text yace ta kawo mata. Kasa ɓoye farin cikinta tayi har sai da ta kalla Aysha da murmushi. “Thanks you blood”. Murmushi Aysha ta mata. Itama sai ta sake murmusawa. Har Aysha ta juya zata fita Fadwa tace, “Ki dawo mu karya mana Aysha”.
“No Aunty gashi can na baro kar a barsa ya lalace shima”. Tai maganar tana nufar hanyar fita da ɗan hanzari dan karma Shareff ya tsaidata. Batama san shi baida niyyar tanka musu ba. Abincinsa yake ƙoƙarin fara ci kawai............✍

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*[11/22, 12:11 PM] +234 803 214 5156: *_Typing📲_*

*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

*_72_*

.........Abincin yakeci cike da nazarin kowaccensu. Fadwa nayin komaine a taka tsantsan na gudun yin kuskure fatanta komai ya wuce. Yayinda Anaam ke komanta kai tsaye hankalinta kacokan naga abincin da takeci tamkar ta manta da zaman kowannensu a wajen ma. A haka dai suka kammala Fadwa ta fara gyara wajen, dakatar da ita yay dan haka ta koma ta zauna. Anaam data ɗauka waya yayma magana, itama ta ajiye suka bashi hankalinsu. Nasiha ya fara musu a nutse tare da jan gargaɗi. Daga ƙarshe cikin kaushin murya da tabbatarwa ya ɗan bubbuga table ɗin da yatsansa.
       “Bazan lalace wajen zargi akan ku balle ƙin cin duk abinda kuka bani ba, sai dai zan tabbatar muku, duk wadda ta zuba wani abu koda a ruwan sha ɗinane domin samun wani cikar burinta ban yafe mata ba. Kuma idan na kamata bazan yafe mataba ko iya cigaba da zama da ita duk da babu tsarin rabuwa da ɗayanku a zuciyata. Shawara ya rage naku, kumu haɗu mu zauna don ALLAH cikin soyayya da mutunta juna, ko kuma kowa ya ɗauka layin da yaga zai dace da shi a shirye nake wajen maganin duk wadda take tunanin zata iya fin ƙarfi na. Na ƙarshe respecting juna da kuma iyayenmu. Wlhy idan wata a cikinku ta sake kuskuren yin abinda bai dace ba akan wani ko wata a cikin iyayrenmu sai na sakata nadama ta har abada, ya rage naku ku dawo hankalinku kokuma ku ɗaura daga inda kuka tsaya”.
       Har ƙasan zuciya kausasan gargaɗinsa sun shigesu, sai dai sunfi ratsa Fadwa musamman akan zuba masa magani a abinci fiye da Anaam da wannan gaɓar bama komai ta fahinta ba. Amma dangane da girmama iyayensu da juna ya shigeta matuƙa, dan yanayinsa ya tabbatar musu zai iya komai. Bayan ya sallamesu kowacce ta nufi ɓangarenta tana ƙullawa da kwancewa. Shima fita yay a gidan zuwa can gidansu gaida su Mommy tunda yanzu Daddy ya janye masa sharaɗin hana zuwa gidan. Sai dai koda yaje ya samu Mommy da Gwaggo basa nan. Bai so haka ba, dan yazone takanas ya lallashi mommy ɗin da bata haƙuri akan komai ma daya faru, sannan ya yini da ita yau. Gidan su Anaam ma ya iske Mamie da aunty Mimi sun fita, dole dai ya koma gida dan gwara yaje ya huta kawai shima.

      A ɓangaren Mommy da Gwaggo gidajen su aunty Malika sukaje sukai musu tatas, inda akai hargitsi bana wasa ba har saida takai an gurfana a kotun baba Ibrahim. Shima al'amarin ya ɓata masa rai, dan yajima dajin tsiyatakun da su Malikar keyi a gidajen aurensu. Sai gashi yau suna neman saka Fadwa itama kuma abin takaicin harda haɗin kan mahaifiyarta. Sosai yayima Gwaggo Halima dake matsayin matar ɗan uwansa faɗa, ya nuna mata kuskurenta na son ɗaura ɗiyarta akan bigiren da zai rusa rayuwarta a dunuya da lahira. Suma kuma su Mommy yay musu nasu faɗan, dan tun farko da basu nunama Fadwa komai tayi a gidan aurenta dai-dai bane daba haka ba. Yanzu gashi sun ɗanɗana mata tana niyyar zartasu kuma sun shiga damuwa, ta riga kuma ta ɗanɗana ba lallai abin ya iya barinta ta sauƙi ba.
       Nasihar Baba Ibrahim bata canja komai a jin haushin juna da Mommy da Gwaggo Halima keyi ba. Sai ma ƙara jin zafin juna dan kowacce nada sirrin ƴar uwarta a tafin hannu. Kuma kowacce taci alwashin nunama ƴar uwarta fawa ɗinta akan ƴaƴan nasu da kuma mazajensu da suke amsa yayanninsu. Da haka aka sake rabuwa baran-baran.....

____________________________

          Ga Shareff kam tun yana shashshare Fadwa harya dai ya sakko, mata da miji sai ALLAH. Sai gasu kamar komai bai faruba aka koma faranta ran juna, dan aranar ba ƙaramin rikita Soulmate ɗin nata tai ba, har yaji a karan kasa ta cancanci yafiya. Sai dai tsananin kishin mijinta na nan a zuciyarta. A duk sanda ta tuna akwai wata a yanzu bayan ita tare da shi takanji raɗaɗi mai zafi a zuciyarta. Sai dai ta ɗauka alƙawarin daina biyema su Aunty Safarah, bazata ƙara amfani da wani magani ba insha ALLAHU. Zata tsaya da ƙafafunta wajen kishin mijinta da ƙyautata masa kowacce ta ƙwaci kanta kawai. Dan tayi imani bazata taɓa son Anaam ba a zuciyarta, saboda tunda ta tashi a rayuwa da tsanar iyayenta da ita kanta ta rayu.
      A ɓangaren Anaam ɗin itama sosai take jin kishin mijin nata, dan akwana biyun nan da yake tare da watanta ba itaba tana matuƙar jin raɗaɗi da zafi. Abinda ya sauƙaƙa mata kawai zaman Aysha tare da ita. Amma ko shigowa yay wajensu sai tayi matuƙar dauriya take iya kallonsa har ta sakar masa murmushi. Banbancinsu da Fadwa kawai ita bata zafafa ba. Bata son Fadwa tun fil'azal saboda tunda ta mallaki hankalinta tasan Gwaggo Halima da su Fadwa basa son  iyayenta basa respecting nasu kamar su Daddy. Amma batajin tsananin tsanarta dan ita bata zafafama kanta abu, kawai idan ya ɓata mata rai ta nuna fushintane take anan da kwakwazo a wuce wajen. Daga haka kuma ta watsar zata fuskanci nagaba mai wucewane. Tadai ɗauka alwashin ƙyautatama mijinta da basa tarin tukuycin soyayyar daya jima yana mata tun bata san kanta ba. Duk wuya bazata yarda ta bijirema umarninsa ba ko cutar da Fadwa. Amma zata ƙwaci kanta akowane hali idan akai yunƙurin cutar da ita.

      Lahadi da yamma mijinta ya dawo hanunta, ya gama kwanakinsa a wajen Fadwa. Da taimakon Aysha suka haɗa abincin dare na gaba daya kamar yanda ya sharɗanta. Ta nufi sashensa domin gyarawa Aysha kuma ta gyara mata nata duk da ma babu wani datti mai yawa kasancewar babu yara ba kuma wasu jama'a ne da yawa ke shiga da fita ba. Duk kaiwa da kawowar da Anaam keyi a sashen Shareff a idon Fadwa ne dake leƙe ta window ɗin falonta. Kai tsaye tasan wannan rawar jikin na Anaam wai za'a tarba miji ba basirarta bace Aysha ce. Tai ƙwafa da cije lips, a ranta tana ayyana yarinya ni dake mu zuba a nan gidan. Oho bama tasan tanaiba, dan koda ta kammala rufo sashen tai harda saka key saboda ya bama kowacce key. Batare data ko lura da Fadwa ba ta nufi sashenta dan ta samu tai wanka tunda tasan a koda yaushe zai iya dawowa gidan tunda ba aiki ya fitaba. Yaje can gidane Mommy ta kirashi duk da a cikinsu babu wadda tasan da hakan. Yadai ce musu zai fita kawai.

        ★Ransa fes ya iso gidan domin jiya ma yazo ya gaishesu kuma shida Mommy babu wata damuwa. dan koda ya bata haƙuri akan duk abinda ya faru tace masa komai ya wuce a gareta kawai. Yaso yaji kamar ba haka bane a ransa, amma saita kore masa dukkan tantama ta hanyar sakin jiki da shi sukai hira da suka jima basuyi irinta ba. Kuma abin mamaki ko sau ɗaya bata kawo maganar Anaam ba ko abinda ya shafi aurenta. Hakama Fadwa. Sun tattaunane kawai akan auren Aysha da kuma komawar Maheer wajen aiki a yau.
     Sai da ya shiga dukkan sashen mutanen gidan ya gaida kowa sannan ya nufi sashen Mommy a ƙarshe. Tana falonta zaune Hussaina na haɗa mata ƙwaɗon zogale ya shigo. Fuskarta da murmushi ta amsa masa sallamarsa. Ya kai zaune shima fuskar tasa da murmushi.
      “First love daɗi zakici haka?”.
Murmushi tayi mai nuna haƙora. “Ai gaka kaima kazo sai muci tare ko?”.
    “Harma na fiki lauma”.
Dariya tayi daga ita har Hussaina dake yin tata a ƙumshe. Ya gaida Mommyn, Hussaina ma ta gaishesa sannan tabar falon bayan ta kawo masa ruwa. A kwano ɗaya sukaci zogalan da Mommy cike da nishaɗi. Suna tsaka da cinne Gwaggo ta shigo.
          “Ja'iri kazo zaka cinye mata ɗan zogalan bayan acan na baka kaƙi ci”.
  Murmushi yay da taɓe baki, “Naki kin saka ƙuli ne itako gyaɗa ta saka shiyyasa”.
    “Oh, da gyaɗar da ƙulin duk ba abu ɗaya bane?”.
    “A wajena ni dai da banbanci”.
Mommy dai dariya take musu kawai.

       Sai da suka kammala Gwaggo da Mommy suka dubi Shareff ɗin cikin komawa serious da ƙyau. Hakan daya ganine ya sashi nutsuwar shima ya maida hankalinsa garesu.
    Gwaggo ce ta fara magana. “Mustapha abubuwa da yawa sun faru waɗanda basai mun zauna lissafi akansu ba ko sake maimaita batunsu anan gurin. Sai dai waɗanda suke faruwa a yanzu sune abun dubawa. Kayi haƙuri munyi kuskuren tilasta maka auren Fadwa ba'a san ranka ba, sai dai mu munyune domin ƙarfafa zumincin ALLAH. Amma ashe zuciyar uwarta cike take da tsatsa. Tunda har a matsayinka na ɗan ɗan uwanta zata iya neman asiri taba ƴarta ta zuba amaka a abinci ko abinsha ya tabbata zata iya kasheka wataran domin farin cikin ƴar tata. Mudai bazamuce dole sai ka saki Fadwa ba. Amma ka zauna kayi tunani mizai iya zuwa ya dawo nan gaba. Dan hatta cikin datai ɓari kwanaki mun fara zargin yarinyar nan zubar da shi tai tana akan sani”.
A matuƙar razane Mommy da Shareff suka dubi Gwaggo. Har Mommy ta kasa haƙuri....
“Gwaggo miyasa zakice haka a ina kikaji wannan maganar kuma?”.
Baki Gwaggon ta taɓe, “Yo Nafi abin duniya na ɓuya ne, kawai nayi shiru ne ban faɗa mikiba. Amma a jiyyarta da nai asibiti na karanci abubuwa da yawa game da yarinyar wlhy. Sai dai ban tabbatar ita ɗin ta zubarba. Amma Mustapha kaje kayi bincike harka tabbatar da gaskiya. Sai dai kayi komai a sirrance basai ka faɗa mataba a yanzu dan karta toshe duk wat hanyar gaskiyarka. Abu na gaba akan aurenka na biyu ne, mudai ba son auren nan muke ba sam, amma munga kai kamar kana so. Dan haka mun yanke shawarar barinka da matarka ku zauna. Sai dai da sharaɗin zaka ƙara aure. Kuma munma zaɓa maka wadda zaka aura yarinyar kirki da tasan mutuncin kanta, idan ƙyau ne kuma duka matan naka ta fisu. Mun tabbatar zakaji daɗin zama da ita insha ALLAHU duk wani ƙuncinka zata ƙwaranye akan waɗan nan ƴan iskan yaran”.
Sosai ya tsurama Gwaggo ido ko ƙyaftawa bayayi, babu abinda zuciyarsa keyi sai luguden daka. Ya haɗiye yawu da ƙyar. Harshensa na rawa yace, “Aure kuma gwaggo?”.
Mommy ta amshe da “Eh aure Babana. Shine zai baka kwanciyar hankali muma kuma ya bamu, dan nidai kasan matarka ta biyu ba zan taɓa sonta ba, amma na haƙura in har kabi umarni na a yanzuma zan barka da ita. Idan kuma ka bijire su duka biyun zaka sakesu ka ƙara auren kuma koda bada zaɓina ba. Dan wlhy itama Fadwa ta fitamin arai. Ko kaunar jin sunan yarinyar nan banayi yanzu. Kuma ina nan saina tabbatar da nunama uwarta kai ɗin jinane ni na haifi abuna kuma. Dan haka kaje kayi shawara daga kwana daya har sati guda muna jiranka. Duk abinda ka yanke sai mu sani.”
“Amma First love......”
“Bana son jin komai Shareff. Kaje kawai kayi tunani kafin ka yanke hukunci, yarinyar da muke so ka aura itace *_Bibah_* ɗiyar Luba na san dai ka santa”............✍

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/22, 12:11 PM] +234 803 214 5156: *_Typing📲_*

*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

*_73_*

.........Innalillahi.... Kawai yake jerawa a cikin zuciyarsa har ƙarshe. Ya kafe Mommy da Gwaggo da idanu ko ƙyaftawa bayayi.
“Katashi kaje kar magriba tayi, gashi kace gobe zaka koma aiki kana da buƙatar yin wasu kimtse-kimtse. Dan bana ma son Daddynku ya dawo ya ganka a gidan nan”.
Kansa kawai ya iya jinjinawa, ya miƙe jiki a saɓule ya fice idonsa har wani yaji-yaji yakeyi. Da farko maganar Fadwa ta zubar da ciki ce ta dakesa. Sai dai maganganunsu na gaba sun goge na farko dan a ganinsa Gwaggo ta kawo zancen Fadwa ce ta zubda ciki domin baƙantata su sami damar shigo da zancen auren Bibah, amma kuma zuciyarsa taƙi daina masa wasiwasi. Bashi da wani ra'ayin zama da mata ko biyu tun ful'azal. Sai dai ƙadararsa ta zama haka. A yanzu kuma bayajin duk wuya duk rintsi zai iya rabuwa da Fadwa da Anaam. Dan kowacce da irin kalar soyayyar da yake mata a cikin zuciyarsa. Yama rasa ina zai kama ya riƙe ne a zancen nasu......
Koda ya shigo gidan tsabar yanda zantukan su Mommy suka rikita masa lissafi baibi takan kowa ba tsakanin Anaam ɗin mai karbar girki, da Fadwa mai fita. Kai tsaye sashensa ya nufa. Sai bayan sallar magriba mmn abu ke sanarma Fadwa kamar fa taga motar Shareff. Da mamaki tace “Yaushe ya dawo gidan ban sani ba?”.
“Inaga lokacin kina ciki ne kina wayar nan”.
Ɗan jimm Fadwa tai na wasu mintuna, sai kuma ta shiga bedroom ta dan karo turare ta fito. Kai tsaye sashen nasa ta nufa. Cikin taɓe baki take bin ko Ina na falon da kallo tana mai shaƙar daɗaɗan fresheners da Anaam ta baza ko'ina tare da turaren wuta. Bedroom ɗinsa ta nufa dan baya a falon. Fitowarsa a wanka kenan, ya juyo yana kallonta. Taku take cikin gayu da yanga, sosai kwalliyar tata ta fita da ƙyau dan ko makaho ya shafa yasan ita ɗin gwanace wajen zaman zanawa. Ji yay kaso ashirin bisa ɗarin damuwarsa sun ragu. Ya sauke numfashi a hankali tare da buɗe mata hannayensa alamar tazo gareshi. Da sasaarfa ta karasa ta shige. Suka sauke ajiyar zuciya a tare. Sumbatar gefen wuyanta yayi, muryarsa a sanyaye ya raɗa mata “Kinyi ƙyau Babie na”.
Ajiyar zuciya ta saki da murmushi, ta ɗago tana mai kallonsa, sai kuma ta manna masa kiss a ƙirjinsa. “Nagode Soulmate barka da dawowa”.
Kansa ya jinjina mata, ya kai hannu ya ɗan shafi fuskarta. Murmushi ta sakar masa da janye jikinta a nasa. Baice komai ba ya karasa gaban mirror domin shafa mai. Itama sai takai zaune a bakin gado tana faɗin, “Kayi wani iri kamar mai damuwa. Ko wani abu ya faru ne?”.
Ta cikin Mirrorn ya kallota. Ya ɗan fesar da numfashi a hankali. “Babu komai na gajine kawai”.
“Ayya kona maka tausa?”.
“A'a karki damu nagode wannan aikin ƙanwarki ne ai ko”.
Har cikin rai taji zuciyarta ta sosu, amma saita danne tai ɗan murmushi da mikewa. “Uhhm hakane na shafa'a ne kawai. Kasan idan ina a tare da kai mantawa nake da komai da kowa kai kaɗai ɗin kawai nake iya gani”.
Murmushi yayi mai sanyi yana mai kallonta ta cikin mirror ɗin. “Ngd ƙwarai da gaske Sweety na. ALLAH ya barmu tare har abada”.
“Cikin matuƙar jin daɗi tace amin”.
Itace ta taimaka masa ya shirya, ta rungumesa bayan ta feshesa da turare. Lips dinsu ya haɗe waje guda yana mai mata wani irin fresh kiss da ya nema zautar da ita. Sai da ya tabbatar ya samu wata nutsuwar sannan ya barta suka koma sauke numfashi. agogo ta kalla zuciyarta na raunana ganin lokacin fitarta girki yayi. Dan kuwa ya tabbatar musu daga 6 na yamma ne. Jitai inama ta jawo mintunan su koma baya, dan wata irin matsananciyar buƙatarsa takeji saboda ya sakata a cakwakiya. Sanin komai zai iya faruwa ta fita da sauri tana faɗin tana zuwa. Murmushi yayi har hakwaransa na bayyana ya bita da kallo......

Anaam da bata san da dawowarsa ba ta fito a toilet daga yin alwalar sallar magrib ya shigo. Sannu da zuwa ta masa. Idanunsa kafe a kanta ya amsa mata. Sosai itama tata kwalliyar ta wuce da nasa imanin. Yaji daɗi har cikin ransa ganin yanzu tana kwalliya. Shiyyasa ya hana Aysha wucewa dan yasan koba komai zata taimakama Anaam ɗin da abubuwa masu yawa da bata gama sani ba a irin rayuwar Nigeria.
“Haka ake tarbar miji dama?”.
“Kai yaya alwalafa nayi”. Ta faɗa murya a karye. Murmushi ya saki yana matsota. Ta matsa da sauri zata koma toilet. “Nidai ALLAH karka karya mun alwala”. Dariya yayi da yin ƴar ƙwafa ya juya ya fita. Itama saita sauke ajiyar zuciya dan ta san kaɗan daga aikinsa yace zai shanye jambakin dake a lips ɗinta.

Bai dawo gidan ba sai bayan sallar isha'i. Kai tsaye kuma sashinsa ya nufa, inda ya iske har an shirya abinci a dining. A falon ya zauna yana sauke numfashi da ƙoƙarin kunna television, so yake ya kauda duk wani damuwarsa domin more wannan daren. Kusan mintuna sha biyar da zamansa babu Anaam babu labarinta. Dan haka ya dauka waya yay kiranta. “An barni ni kaɗai kamar maraya”.
Murmushi tayi da har yaji sautinsa a kunensa. “Immhum ni ai bansan ka dawo bane ba fa”.
“Okay, ai yanzu kin sani”.
Min tuna kusan bawai tsakani sai gata ta shigo, tun kan ta iso ƙamshinta ya karaso. ya rasa a matan nasa wacce tafi wata iya gayune. Duk randa sukejin abin arziƙi susutashi sukeyi gaba ɗaya. Ta bayan kujerar ta tsaya, tare da ranƙwafowa kansa ta manna masa kiss a wuyansa. Numfashi yaja mai yalwa tare da fesarwa. Ya kamo hanunta ya zagayo da ita ya zaunar a cinyarsa. “Irin wannan wanka ai sai ki sakani manta kaina autar mata”.
Murmushi tai da ɗan tabe baki, “Ban san daɗin baki ni dai Yaya”.
“Kinfi ƙarfin daɗin baki ai a wajena. Duk abinda bakina ya furta a kanki shine ai nahin gaskiyar zuciyata”.
Sosai taji daɗi har cikin ranta. Amma dai batace komai ba sai murmushi kawai da taɗanyi. “Yau dai lipstick ɗin nan nawane ko?”.
“A'a”.
“Ashe zan miki kuka”.
Dariya ta sanya tana mai lafewa a jikinsa. “Oh oh ya kaga Yaya ana kuka”.
Murmushi yayi mai faɗi da lakace hancinta. “Wato harma hasasowa kikeyi ko”.
“Sosai ma”.
“Uhhyum mugunta.com”. Yay maganar da kaima lips nata kiss. Bai bari ta shaƙi numfashi ba ya maida lips ɗin nasa kan nata again. Sai dai a yanzu salon dabanne dana farko, dan sai da ya shanye lipstick ɗin tas hankalinsa ya ƙwanta. Lamo tai a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya a hankali. “Tsadar tsada ke ta musamman ce”.
Muryarta a dashe tace, “Ai kaima ɗin na musamman ne”.
Ido yake son su haɗa amma taƙi yarda. “Please ki kalla cikin idona ki faɗa Noorie”.
Murmushi tai da juyowa kamar zata kallesan, sai ta mike zumbur daga jikinsa. Kamota yay yunƙurin yi ta zille tana dariya. “Biyu kenan fa, idan kika bari na kamaki zakiji jiki”. Gwalo ta masa da nufar dining. Ya murmusa cikin jinjina kai.
Waya ya ɗauka yay kiran Fadwa. Cikin murya ƙasa-kasa yace, “Babie kizo muyi dinner”.
“Uhm-uhm”. Ta faɗa a shagwaɓe.
Ɗan kallon Anaam yay, ganin hankalinta ba kansa yake ba ya sake ƴin ƙasa da muryar cikin lallashi. “Why”.
“Nifa bana jin cin komai”.
“Idan kika bari nazo da kaina akwai hukunci kenan”.
Dariya tayi da ga can. “Naji zanzo”. Shima sai yay murmushi da faɗin “Matsoraciya”.
Juyowar Anaam dai-dai yana ajiye wayar. batare data fahimci mi yayi ba ta ɗaga masa yatsu biyu. “Hy Yaya abinci na jiranka”.
Fuskarsa ya dan marairaice. “Kin yarda zaki bani da kanki?”.
Ɗan jimm tai na tunani, sai kuma ta kaɗa kanta alamar eh.
“This is for you my Noorie”.
Ya faɗa yana mai kissing hanunsa ya hura mata.
Dariyar da tafi kama data mugunta ta sakar masa. Ta tare kiss ɗin tana mai lumshe idanu da mannawa saitin zuciyrta. Rungumeta yay sannan ya kai zaune a kujer data ja masa baya. Dai-dai nan Fadwa ta shigo. Koda suka kalla juna ita da Anaam sai kowa ya watsar da ɗan uwansa. Sai da ta karaso ta zaunane Anaam ɗin tace, “Barka da yamma”. A takaice itama Fadwa ta amsa da “Barka”. Sai kuma ta ɗan saci kallon Shareff ta sakar masa murmushi. Murtani ya mayar mata ya ɗauke kansa.
Anaam daba lura tai da su ba tana ta ƙoƙarin zubama kanta abinci, koda ta ɗago sai suka haɗa ido itama da shi. Murmushi suka sakarma juna. Nanma ya kauda kansa batare da Fadwa ta gani ba dan itama ta maida hankalinta ga zuba nata abincinne. Yau ne kuma karon farko da Anaam ta fara girki a gidan, duk da dai tayisane da taimakon Aysha dan bata iya girke-girken Nigeria ba sai ƙalilan a ciki. Saukinma zuwa yanzu ta iya cin abubuwa da yawa ba kamar farkon zuwanta ba.

Gaba ɗayansu cin abincin suke cike da nishaɗi, dan kowacce ta samu irin farin cikin da take buƙata daga mijinta. Wanda a nata wautan gani take itace ɗaya ƙwalli ƙwal a zuciyarsa. Shiko cin abincin yake wani yanki na hankalinsa naga umarnin su Mommy, sai dai wani yanki najin matuƙar farin cikin ganin farin cikin matan nasa da har kowacce ta kasa ɓoyewa. Koda suka kammala Fadwa bata wani jimaba tare da su tai musu sai da safe ta wuce zuciyarta cike da kishin mijinta. Anaam kuwa ta shiga tattare kayan waje guda. Falo suka koma ita dashi, ya zauna a 3sitter tare da jawota jikinsa....
Sai da ta bari sun shagala da kallo yana mai cakuɗata a yanda yaso sannan taja numfashi. “Yaya gobe zan koma gun aiki ko?”.
Tamkar saukar aradu yaji maganar amma sai ya danne. Yay shiru kamar bai jita ba sai da ta ƙara maimaita masa tana ɗagowa ta kallesa. Shanyayyun idanunsa ya zuba mata na wasu sakanni. sai kuma ya dan lumashe da kaɗa mata kai kawai. Ta sauke ajiyar zuciya tana mai hamdala ga UBANGIJI. “Nagode Yaya wlhy na zata zakace a'a”.
“Humm”.
Kawai yace mata.
Tasan ya shaƙa dan haka tai shiru, ita dai tunda ya yarda zata koma ai Alhamdulillahi koma mi zaiyi mai sauƙine kuma. Saida ya kammala kallon labarai sannan suka mike. Ta fita domin zuwa tai shirin barci shi kuma ya nufi bedroom ɗinsa bayan ya bata umarnin idan zata dawo tazo masa lipton. Ya mata hakane dan kartai tunanin ƙin dawowar. Kamarko ya sani batai niyyar dawowa ba. Amma babu yanda ta iya kodan son komawarta aiki salin alin tabi umarnin nasa.
Sai da ta shafe kusan mintuna talatin sannan ta dawo cikin zumbulelen hijjab har kasa da cup na lipton. Rashin ganinsa a falo ya sata nufar bedroom ɗinsa kai tsaye. A bakin gado ta samesa yana haɗa wasu takardu da laptap ɗinsa alamar kayan zuwa office yake tattarawa. Ta ajiye cup din a bedside drawer dake gefensa.
“Jazakallahu khairan”.
Cikin jin daɗi ta amsa da “Amin ngd”.
“Kin rufe falon ko?”.
Hakan ya bata tabbacin nan ɗin zata kwana dai, dan haka ta girgiza masa kanta.
“Okay ki rufe kawai”.
Nan din ma kanta kawai ta jinjina cike da tsoro. Sai dai babu yanda zatai dole taje ta rufe ɗin ta dawo. Ta samesa ya fara shan shayinsa. Ya nuna mata gadon da fadin, “Bisamillah ki kwanta gobe akwai fitar safe. In kuma kikace zaki mun irin lattin da kike mun a gida zan tafi na barki ne”.
Baki ta ɗan tura masa batare da tace komai ba. Hijjab ɗinta ta cire ta hau gadon ta kwanta tana mai addu'ar ALLAH yasa kar yace yana bukatar komai. Dan duk da zaren ɗinkin da kansa ya fita saboda yawan shiga ruwan zafi da takeyi ba ƙaramin tsoro da fargaba take shigaba a duk lokacin data tuna za'a iya sake ratsa wajen again. Sauri-sauri tai addu'a ta gyara kwanciya da rokon ALLAH zuwan barci kafin ya kammala shan shayin nasa...........✍

🤣Abun dariya abun tausai😜

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*[11/23, 12:46 PM] +234 704 083 7785: *_Typing📲_*

*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

*_74_*

.......Dariya kawai yake dannewa dan sarai duk ya gama fahimtar inda ta dosa. Sai dai shi yasan a yau bawai zai iya haƙuri bane gara ya maidata ƴar hannu a wuce wajen. Amma a zahiri ya basar tamkar bai san mitake ba. Dan koda ya kammala shan shayin toilet ya shiga ya dauro alwala. Shafa'i da wutiri yayi sannan ya hawo gadon bayan ya fita ya leƙa tsakar gidan ta windows ɗinsa na falo. Ganin babu wani damuwa ya dawo bedroom ɗin shima ya hau gadon ya kwanta. A hankali ya kwanto bayanta yana mai ɗaga duvet din da taja har saman kanta.
       “Bana faɗa miki ni ba'a juyamin baya a gado ba?”.
    Shiru tai ita ala dole tayi barci. Yaji a jikinsa pretending ne kawai, dan haka ya fara mata cakulkule. Duk yanda taso fiskewa hakan ya gagara, dole ta fara dariya da ture hanunsa. Bai bartaba har sai da yaga ta juyo yanda yake bukata. Ya haɗe goshinsu waje guda yana murmushi. “Ni na rasa miyasa kika rainani”.
          “Saboda kana mun mugunta mana”. Ta faɗa tana murmushi.
  “Kin cika tsokana ne shiyyasa”.
Hanunsa da yake cusawa jikinta ta mintsina. “Ouch!!”. Ya faɗa batare daya janye ba. Murmushi tayi zata kauda kanta ya riƙo fuskar. Duk yanda taso ƙwacewa babu damar hakan. Dan wani salo ya ɗauka wanda yasha banban da karatun farko daya koya mata. Cikin kankanin lokaci ya sakata sakin masa jiki ya fara yanda yake so. Tafiya tayi tafiya sun gama cakuɗa juna yanda suke so ya ɗauka babban hanyar garden. Ai tuni mutuniyar taku ta fara sakin magiya da roƙo amma ya nuna mata sam yau babu ɗaga ƙafa garden zai sake komawa ziyara. Hankalinta bai kara tashi ba sai da taji yana ambaton addu'a...
      Wiya kam dai yau ma ta shata, duk da dai ba irin ta farko bace dan babu ma haɗi, dan yau ya bita a hankali kamar yanda Dr Bilkisu ta gargaɗesa. Yau din ma dai harda kukanta. Amma baiyi nisaba kamar na waccan ranar. Tasha albarka kala-kala tare da daɗaɗan kalaman da suka sanyaya mata rai raɗaɗin taji ya raguma. ya taimaka mata ta shiga ruwan zafi kafin su dawo gadon ya bita da tukuycin tausar data sakata yin barci. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi da sake sakar mata kiss a lips da idanunta yana faɗin, “ALLAH yay miki albarka”. Daga haka shima ya rungumeta suka lula duniyar barcin tare..

    *_WASHE GARI_*

Rashin sabon ɗaukar gabaran gida kafin fita aiki yasa saida taimakonsa dana Aysha suka shirya fita akan lokaci, gashi sai langaɓewa take wai jiya ya wahal da ita. Shi dai nashi murmushi kawai, itako tana faman tura baki da tsuke fuska. Kamar kullum tayi ƙyau cikin kayan hidimar ƙasa, sai dai ta ɗaura Abaya yau a sama sannan ta naɗa veil ɗin abayar a kanta. Ƙin fitowa tai har saida ya shiga sashen Fadwa sukai sallama ya fito sannan ta fito suka wuce. A hanya take tambayarsa yaushe zata fara koyan tata motar. Shiru kamar bazaice komai ba. Sai da ya kaucema mai napep ɗin dake neman shiga masa hannu sannan ya ɗan dubeta bayan yaja tsaki da yima mai napep ɗin daƙuwa.
“Mu bari weekend, idan kuma Fadwa ta koya miki to?”.
Baki ta tura gaba sai dai batace komai ba. Hakan yasashi fahimtar zancen nasa bai amsu ba. Ya girgiza kai kawai ransa fal mamakin kishin matan nasa. Ita kanta Fadwan daru ya barta tanayi akan fitar tashi da Anaam. Wai sai dai idan ranar girkintane kawai zasuke tafiya tare. Amma ranar nata bata yarda ba. Itama baice mata komaiba yay fitowarsa, to ga Anaam ɗin ma yace Fadwa ta koya mata mota ta nuna bata so.
Ita ya fara saukewa, da gargaɗi mai girma akan Yaseer sannan yay gaba. Ya samu tarba ta musamman a wajen staffs nashi. Inda sukai ƴar gajeriyar walima lokacin break acewarsu tunda ba'ai ta aure ba. Kasancewar ya samu aiki da yawa Khaleel ne yaje ya maida Anaam gida, shiko sai bayan isha'i ma ya kona gidan. Sanda ya iso ya iske komai yanda yake buƙata, dan dawowar Anaam ɗin tayi amfani sosai.
Yau ɗin ma dai yasha sharafinsa, inda mutuniyar tasa taita masa raki, baibi takanta ba, amma yabita a sannu gudun ɓaro aiki. Washe gari har wani farin ciki takeji zai koma wajen Fadwa ta huta, duk da dai kishinsa na zaune daram a ranta babu sassauci. Safiyar talata sai dai yayma Fadwa ƙaramin hauka akan fitarsa da Anaam sannan suka samu dai-daito, dan ta dage bazai ɗauka Anaam ba dan ranar girkintane. Amma ganin ya juye mata yanda bata kauna dole tai shiru, ya fita ya barta tana rusar kuka

Haka kwanaki suka cigaba da tafiya, tun Anaam na masa raki a duk ranar girkinta harta fara zama ƴar hannu, duk salon da yazo mata da shi zata amsa kuma ta bashi haɗin kai yanda zai samu farin ciki. Babu abinda ya dameta da sabgar Fadwa, abinda ke gabanta kawai takeyi, sai dai kuma bata ragawa idan Fadwan ta shiga shirginta. Dan kuwa saita tsefeta tas ake samun zaman lafiya a gidan. Shareff yayi kurarin yayi masifar akan tsiwarta amma a banza, dan tace in ba'a shiga gonartaba bazata shiga ta mutum ba. Ita kuma Fadwa tsokanar magana ne matsalarta. Komai ta gani saita tanka. Duk kankantarsa sai tayi magana ga Shareff ɗin ko ga Anaam. Sauki ɗaya aka samu ta rage kai ƙararsa wajen iyaye, koda yake yanzu fa itada Mommy babu wani mutunci, dan kuwa ranar daya kaisu gidan su duka domin gaishesu Anaam tasha kallo, Mommy ta dinga yamutse-yamutse, abibda ya bata dariya Fadwa zata fara iyayi ita masu Mommy, mommy ta gwaleta. Aiko ta fita baki gumtse tana danne dariya. Tuni ta gudu gidansu wajen Mamie, inda ta ruƙunƙumesu harda kukanta wai tayi missing nasu. Suma sunyi missing nata matuƙa, amma sai suka dinga lallashinta. lokacin da Fadwa da Shareff suka shigo gaida su Abie ɗin kowa yayi mamaki Fadwa, dan yau babu rashin kunya ta gaishesu da girmamawa saboda tsoron butsutsun Shareff, dan kafin su taho ya buga mata warning bana wasa ba akan su Abie ɗin. Sai kuma abinda Mommy tai mata a gaban Anaam ya sake dagula mata lissafi.

Zuwansu gidan da kwana biyu maganar auren Bibah da Shareff ta fito, dan kuwa a kwanakin nan dama sunata bugawa ne tsakaninsa da su Mommy, ta kuma tabbatar masa idan yana fa son zama da matansa sai ya auri Bibah, a gefe kuwa burinta ita da Gwaggo ya auri Bibahn su fidda Fadwa da Anaam kuma a gidan dan sun ɗau alwashin bazasu barshi zama da su ba.

Wannan maganar aure itace ta tada gagarumar ƙurar data tada hankalin kowa a family guda biyu, dan kuwa sarƙa-sarƙar tayi yawa ai. Saboda Shareff na ɗan gatan duniya sai a dinga haɗa masa ƴaƴan dangi yana aure dai. Mamie da Abie dai basu ce komai ba, sun kuma yima Anaam nasiha akan koda a fuska karta nunama Shareff komai. Taji ciwo a ranta, sannan taci kuka amma sai tabi maganar iyayenta.
A ɓangaren Gwaggo Halima kuwa sabon yaƙi ne ya tashi tsakaninta da su Mommy, nanfa aka shiga ƴar tone tonen asiri ta yanda har akaima Shareff asirin daya nisantashi da su Abie. Abubuwa dai babu daɗi, dan tsabar takaicinsu Daddy har sai da yaji ƙwalla sun cika masa ido. Gwaggo Halima tace sai Fadwa ta koma gida babanta yace ƙarya haramun, idan Fadwa ta rrabuda Shareff ta nema wani uban bashi ba. To itama dai tana son mijinta, duk da kuwa maganar zai ƙara aure yake, kuma da kawarta data san sirrikanta.
Ruguntsumin masifa akeci na haƙiƙa a wannan gaɓa tsakanin Fadwa da Bibah, Gwaggo Halima da su Mommy da maman bibah. A gefe kuma ga shirye-shiryen bikin Aysha, sai kuma Khaleel da tasa budurwar shima. Sosai hankalin Shareff ya kasu. Ga company, ga rikicin Mommy da Gwaggo data noƙe tabar Mommy na raba hali. Ga rikicin Fadwa, Dan ita Anaam da sauƙi. Bata fasa komai da take masa ba amma yabar ganin murmushinta gaba ɗaya itama. Dama zuwa yanzu da motarta take fita wajen aiki kasancewar ta ƙware, dan bai kulla sati biyu yana koya mataba da yake ta saka kanta sai gashi ta iya, idan zasu fita yana gaba tana biye da shi, komuma tana gaban yana biye da ita duk dai dan ta ƙara sanin hanya.
An shiga shagalin bikin Aysha ne cikin ruguntsumin maganar Bibah, amma hakan bai hana Shareff sharɗantama matan nasa zuwa taron bikin ba. To Anaam ma basai an sharɗanta mata ba. Bikin Aminiya ya wuce tace bata zuwa, hakama Yaya Khaleel. Dan haka tun ranar kamu tace masa zata koma can gidan gaba ɗaya har sai biki ya tashi. Da farko yace bai amince ba, tako saka masa kuka. Da farko shareta yayi, sai dai ganin kukan nata bana kare bane yace taje cikin fushi. Sai kuma jikinta yay sanyi.
Yayi zaton zai taso aiki ya tarar ta wuce, sai ya samu tana gida babu ma niyyar tafiyar tare da ita. Ganin kallon da yake binta da shi ya sata tunzura baki gaba ta ɗauke kanta gefe.
Baki ya ɗan taɓe, “Motar ce babu mai komi?”.
“Ni na fasa”.
Ta faɗa idonta na cikowa da ƙwalla.
“Dalili?”.
Kuka ta fashe masa dashi. “Toni ya kake so nayine dan ALLAH Yaya. Taya zanje wani waje kana jin haushina. Salon kawai kasa ALLAH ya sakani a wuta”.
Ɗan murmushi yayi da girgiza kansa yana furzar da huci. “Ni bance ina fushi dake ba kar kimun sharri, kune dai kuke fushi dani akan abinda na tabbatar muku nima bana ra'ayinsa. Mi zanyi da wata Bibah can da har zamu zauna kuna dagula min lissafi. Kun haɗe kai ku a dole bakwa son kishiya. Kun san tun yaushe ake maganar nan ina ta yaƙin ganin bata fitaba? amma kuke ɗaukar laifi kuna ɗauramin. Koda yake ke nagama kamar baki damu da zuwan amaryar tawa ba, dan kwanakin nan wata ƙiba kikeyi da haske ƙyawu na musamman na fita a fuskarki, kamar wata black American”.
Throw pillows ta ɗauka ta fara jefa masa. Ya shiga karewa yana dariya. Ganin haka ya sata mikewa ta haye kansa tana cigaba da kai masa kananun duka da pillow. Dariya yake mata da son kwace filon yana karewa, har dai ALLAH ya bashi sa'a ya damƙe hanun ya mirgina ta koma ƙasa yana a sama. Turesa ta farayi shi kuma yana kai mata kisses a wuyanta zuwa ƙirji. Kukan shagwaɓa ta fara masa ya koma mata cakulkule dole ta fara ƙyarƙyala dariya. Daga haka labarin ya canja aka koma neman lada. Dama a kame yake kwanakin nan ko nauyi bai iya saukewa saboda zafin da kansa ya ɗauka matuƙa............✍

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[11/23, 12:46 PM] +234 704 083 7785: *_Typing📲_*

*_❤‍🔥BABU SO....!!❤‍🔥_*
_(Miya kawo kishi?)_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_BABU SO👉🏻AREWABOOKS_*

https://arewabooks.com/book?id=63447a616580db4ec203d718

*_75_*

........Rungume yake da ita yana sanya mata albarka bayan samun nutsuwarsu. “Noorie na wai miye sirrinne?. Kwana biyun nan fa kin ƙara zama mai tsadar tsada ta gasken gaske. ALLAH gigitani kike na manta da kaina gaba ɗaya. Ni'imomi sun ƙara cika garden ɗina”.
Kunya ta sakata tura kanta a ƙirjinsa tana murmushi. “Kai Yaya ko kunya bakaji?”.
“Kunyar mi zanji ina a gaban autar mata. Idan ban faɗa miki abinda ke raina game da ƙyautarki da ALLAH ya bani ba mi zanyi tauraruwa a cikin taurari?”. Ya ƙare maganar da manna mata kiss a gefen kunne. Tsam ta ƙara matsesa a cikin jikinta. Ƙaunarsa ta musamman na sake ratsa zuciya da ɓargonta. A duk sanda take tare da shi mantawa take da kowa da komai, bata tuna bayan ita akwai watanta. Farin ciki take bashi fiye da hasashen zuciya. Kamar yanda shima yake riritata tamkar ƙwai a cokali. Ya gama ɗorata da koya mata salo-salo na rayuwa dakan ƙara raunana rauninta taji koda agaban wanene batajin shakkar nunasa matsayin *_Jan-gwarzonta_*....
Sumbatar goshinta yay cikin katse mata tunani, ya ɗagota suna mai kallon juna a tsakiyar ido. “Anya bani da ajiyar baby a wajen nan Noorie?”.
Idanu ta waro sosai a kansa. Ya dage mata gira daya da ƙyafta idanun yana murmushi. “Am serious kin canja Juwairiyya. Jiba nan ya ƙara girma. Baƙya raki kamar da, saima so cikin zalama. Garden ya ƙara zama zakwai-zaƙwai”.
Doke masa hannu tai da ƙoƙarin juya baya ya riƙota. “Shike nan, shike nan na daina magana. Yanzu dai na haƙura Ki shirya kije kawai, bazan hanaki zuwa bikin ƙawarki ba”.
“Woow dan ALLAH da gaske My hero?”.
“Yes my Heartbeat”.
Wani irin ɗan ihun farin ciki tayi, tare manne lips ɗinsu waje guda. Cikin ƙanƙanin lokaci ta susuta masa lisaafi.....

(🚶🏻🤕jaraba).

★Shi da kansa ya kaita, bayan yayima Fadwa magana ta shirya itama taje ɗin har sai biki ya tashi tace a'a. Bai matsanta mataba ya ƙyaleta, dan shima dai yana buƙatar ɗaya ta zauna tare da shi kar a maidashi gwauro.
Sosai Anaam ta tsinta kanta cikin farin cikin ganinta tare dasu Abie ɗinta. Nan fa sabuwar shagwaɓa ta tashi. Suko suna biye mata dan farin cikine baibaye da zukatansu. A ranar akai ƙunshi, sai dai tana nane da su Mamie bata shiga cikin gida ba. Washe gari kamu ta tashi duk batajin daɗin jikinta tun safe. Amma sai ta danganta hakan da kewar Shareff dake damunta. Tun wajen sha biyu ta shige cikin gida, kasancewar sashen Mom dana Mommy duk cike yake da baƙi saita nufi sashen aunty Amarya dan su Aysha nacan da gayyar ƙawayenta. Tuni ta shige cikinsu anata shan shafta har akai mata ƙunshi da Aysha ta matsa. Tun ana lallin take complain ayi maza a gama kanta ciwo yake, Aysha na hararar ta wai ƙunshinne bataso, in ma an gama anjima kaɗan tare zasuje Saloon ko taƙi ko taso.
Kamar wasa tace musu jiri takeji, kuma tana ganin hayaniyar gidance, Aysha dai taita lallaɓata ta shige bedroom ɗin aunty Amarya ta kwanta. Sai da ƙawayen amarya suka gama shiri suka fita tsakar gida Aunty Rahma ta shigo ta gata ita da Aunty Bintu. Sune suka sakata tashi dole tai wanka. Amrah ta kawo mata kayanta ta shirya anan. Jin yanzu babu jirin saita fito tsakar gida inda kamu ke gudana. Dan ƙarfin hali harda shiga fili taima amarya liki. Masu kiɗan kwarya suka shiga koɗata da kirarin Amaryar babban yaya Shareff. Ana haka Khaleel ya shigo shi da Shareff da Maheer. Anaam ta nufesu tana murmushi ta farama Khaleel ɗin liƙi. Hakan yasa aka dawo aka baibayesu masu kiɗan ƙwarya na cigaba da kwarzantata. Shareff dake kallonta yana murmushi baima san ya zaro nasa ƴan kudaɗen ba ya fara liƙeta, hakan yasa shima Maheer zarowa yana musu liƙin su duka uku. Aifa sai waje ya ɗauka ihu, dangi aka zagayesu su duka huɗun ana musu liƙi. Tun Anaam najin hayaniyar sama-sama harta fara jinta nesa-nesa. Idanunta suka fara limshewa tai baya zata sulale Shareff daya farga yay saurin tarota jikinsa. A take waje ya ɗau shiru. Da sauri Aunty Bintu ta kawo ruwa aka shafama Anaam ɗin saita kawo nannauyan numfashi. Kanta ta riƙe hawaye na ziraro mata. “Yaya kaina, kaina zai fashe Yaya”.
Hankali tashe ya sungumeta akai sashen aunty Amarya da ita, dan nan ɗinne kawai keda karacin mutane, dama ƙawayen amaryane sai danginta tsiraru kasancewar ba ƴar kano bace, kuma duk sun fito. Maheer ne yay kiran Dr Jamal. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi ya iso, har yanzu Anaam na'a jikin Shareff tana masa kukan kanta. Yana riƙe da kan yana mata addu'a, su aunty Amarya zagaye da su. Dan hatta Mom da Aunty Mimi duk suna a wajen. Tuni kuma an kaima Mommy da Gwaggo rahoto sai dai basu fitoba. Mamie ma nacan cikin damuwa a tsakar gida amma dattakonta ya hanata shigowa taga halin da Anaam ɗin ke'a ciki. Su Daddy dai suna can gidan su Anaam din tare da Abie dan can ɗin babu mutane sosai duk anyo nan cikin gida.
A kallo ɗaya Dr Jamal ya fahimci matsalar Anaam ɗin, dan haka ya kalli Shareff cikin ido. Hararsa yayi yana motsa laɓɓansa ahankali alamar magana yayi sai dai bata fitoba kasancewar falon cike yake da su Mom. Jininta ya ɗiba ya kuma bata maganin ciwon kan kawai. “Inaga zanje ai text first, amma dai tasha maganin sai taje inda babu wannan hayaniyar ta kwanta ta huta. Inba hakaba ciwon kan zai cigaba da damunta. Zuwa da safe insha ALLAHU zan kawo sakamakon ”.
“Kana nufin wannan maganin kawai zaka bata ka barmin mata cikin ciwo kenan?”.
Shareff ya faɗa cikin suɓutar baki dan ya ma manta da su aunty Mimi dake wajen. Babu wanda baiyi murmushi ba, ƙanensa na gulmarsa a zuciya ina miskilancin nasa yaje. Sai dai babu mai damar cewa komai. Maheer kam jikinsa ne yay sanyi, ya dubi matarsa da sam tama ƙi sakewa a gidan saboda a wajensa ma bata samu farin ciki ba. Auren watanni huɗu ya kasa sakin ransa ko kusantarta yaƙi yi, ita kuma ta tura masa aniyarsa duk abinda ya dace mace ta gari taiwa miji bata gazaba tana masa gwargwadon iyawarta.
Yanzun ma ko kunya babu shine ya kaita can gidansu dan acanne kawai akeda ƙarancin hayaniya. Kai tsaye sama ya kaita ɗakin Mamie ya kwantar a kan gado, yana daga zaune kanta bisa cinyarsa yana tofa mata addu'a a kanta aunty Mimi ta shigo ɗauke da ƙaramar roba da towel ƙarami a ciki. Shine ya amsa, tai murmushi a ranta tana faɗin, (Ƴan banzan yara dakun cigaba da pretending da rabo ya kashe har mu bama ku kaɗai ba. Dan wannan daga gani ciki ne). A zahiri kam juyawa tai tayi ficewrta ta bar musu ɗakin. Towel ɗin ya dinga matsewa a cikin ruwan yana goga mata a goshi zuwa fuska har wuyanta da hannayenta. Sai da kanta dake zafi ɗau ya huce sosai sannan ya koma kafafunta. cikin ƙanƙanin lokaci sai ga barci ya ɗauketa. Ya sauke ajiyar zuciya da komawa gefen gadon ya tsugunna saitin fuskarta. Kallonta yake da murmushi, ƙaunarta na ƙara ratsashi. Ya kai lips ɗinsa kan nata ya sumbata, hakama idanunta dake lumshe. Har cikin ransa yana fatan hasashensa ya zama gaskiya. Addu'a daya jima yanayi ta samun rabo daga kowaccensu ta tabbata a wannan karon. Dan ko kwana biyu ba'ai ba da gama yima Fadwa ƙorafi akan hakan.
Shigowar Mamie data kasa haƙuri ce ta sashi mikewa yana shafar ƙeya. Haka kawai yanzu yake jin tsananin kunyarsu ita da Abie babu gaira babu sabar. Cikin sanɗa da dabara ya zare jikinsa ya gudu a ɗakin.....

Su Daddy ma sun shigo dubata bayan sallar isha'i, har sannan kuma bata tashi ba tanata barci. Sun mata addu'ar samun lafiya suka fice. Sai da Abie ya rakatane ya dawo domin sake duba tilon ƴar tasa. Yana a ɗakin Shareff ya dawo, ji yay duk ya daburce, dan haka yaki sakewa ya gudu, duk da Abie nace masa ya dawo shi fitama zaiyi amma yaƙi tsayawa wai dama yazo ya sake dubatane zai wuce gida goma tayi.....

*_WASHE GARI_* al'ummar wannan family suka tashi da farin cikin bayyanar cikin Anaam ɗan watanni biyu da wasu kwanaki da adadinsu baida yawa na cika watanni uku. Zokaga murna wajen su Mamie da su Daddy. ALLAH mai alheri, su sunsha kuka da damuwar rashin samun haihuwa da wuri ga Anaam da bata rufa watanni huɗu ciff ba da ciki. Wannan rahama ce ta UBANGIJI mai yin yanda yaso a lokacin da yaso. Isar wannan al'amari kunen Gwaggo da Mommy tamkar saukar aradune a tsakiyar dare mai duhuwa. Dama dama ma Mommy bataji zuciyarta ta zafafa ba a wannan karon har hakan ya bata mamaki. Amma Gwaggo gaba ɗaya birkicewa tayi har bakinta ya dinga subucewa wajen sakin wasu maganganu. Koda ta kira Mommy gefe kan hakan sai Mommyn ta nuna mata ita duk da bata son Anaam da su Abie taji son cikin dan koba komai gudan jinin Shareff ne ai. Wannan furuci ya matuƙar ƙona zuciyar Gwaggo. Dan haka ta ɗau alwashin sai ta ɓata taron bikin nan. Cikin halin ko'in kula Mommy tai komawarta cikin danginta ta cigaba da hidimarta. Gwaggo ta bita da kallo zuciyarta na suya matuƙa, ita Nafisa zataima wannan ɗibar albarkar, to ai idan tasan wata bata san wataba wlhy. Barin wajen tai fuuu kamar zataci tun tuɓe zuwa sashenta tana ƙulla wutar da zata kunno a gobe idan ALLAH ya kaimu.
Bayyanar cikin Anaam ta matuƙar tada hankalin Fadwa, musamman dataga kamar dai nata Shareff bai wani zumuɗi ba ko rawan kai a zahiri. Amma kuma yanayinsa na son nuna kulawa ga Anaam ya tabbatar mata nunawarsa a fili bashi ke nufin baya son haihuwaba. Kawai dai hakan naturally ɗin halayyarsace ɓoye sirrin zuciya. Ba ita kaɗaiba hatta Gwaggo Halima maganar cikin nan ya tada mata hankali. A karon farko sai gata gidan Shareff ɗin dan bata taɓa zuwa ba. Cikin shirin tafiya gidan biki take, dan acewarta zataje bikin Khaleel ne bana Aysha ba, dan ita da Mommy a yanzu babu shiri kwata-kwata, saima yaƙar juna da akeyi.
Kuka sosai Fadwa ta dinga yimata akan ta shiga uku itakam, ga Anaam tazo a bayanta ta samu ciki amma ita tun miscarriage data samu babu wani bayani (Karfa ku manta ko Gwaggo Halima bata san Fadwa zubda ciki taiba. Ƙawayenta ne da Gwaggo kawai suka san wannan sirrin, sai ko Anaam. Gwaggo ma ita da Bibah da hajiya Luba maman Bibah kawai suka sani).
“Kinga kwantar da hankalinki a gama hayaniyar bikin nan sai mu tafi Germany kiga likita, karma ki bari wani abu ya tada miki hankali kinji shalele”.
Lallashin Mamanta ya saka mata samun ƴar nutsuwa harta shirya ta bita sukaje gidan bikin, inda da ace sun san mi Gwaggo ke ƙullawa da basuje ba, sai dai bawa bai isa sanin gaibuba daga kadarar abinda zai faru a minti guda na gaibunsa sam.........✍

Humm, yau fa akeyinta🚶🏻🤕🚴🏼😝.

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*[11/23, 5:13 PM] Marsy😘: BABU SO

Table of Contents

Chapters

15 chapters
  1. 1 billy *_Typing📲_*
  2. 2 Chapter 58
  3. 3 Chapter 60
  4. 4 Chapter 62
  5. 5 Chapter: 63
  6. 6 Chapter 63
  7. 7 Chapter: 64 Share:
  8. 8 Chapter 64 64
  9. 9 Chapter: 67
  10. 10 Chapter: 68
  11. 11 Chapter 69 69
  12. 12 Chapter: 70 Share:
  13. 13 Chapter 70 70
  14. 14 Chapter: 76
  15. 15 Chapter 77