Chapter 1
Novels Elite
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe Page 7 complete
by
Novels Elite Admin
May 15, 2024
Sponsored Link
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القدر💋✊🔥
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace"Ina da banbanci dasu, Har Yau har gobe sunƙi mantawa da matsayina a gidan ku, Suna yi min kallon ƙasƙantacciya Ƴar aiki, babu abunda Ya canza"
Ya fahimci baƙaramin jin shakkarsu ta ke yi ba, muryarshi a kausashe ya furta"kamar ba matar Sir mubarak ba, kin bani kunya, wlh daga yau zan baki last warning, idan na kuskura na sake ganin kin zubda hawayen ki ko kina jin tsoron wani acikin su, sai na sa6a maki" ƙiris ya rage ta fashe mashi da kuka, jin yadda yake mata magana da faɗa.
Zare mata ido yayi"ina fata kin fahimce ni"? Muryarta na rawa furta"yea..h" ruƙo hannunta yayi acikin nashi, yaja ta a hankali suka nufi katafaren falon gidan, ko da su ka shiga masu yi masu hidima suka taras sai kai komo su ke yi a cikin falon, ganin sir mubarak yasa suka yi saurin gaishe su cikin girmamawa bayan ya amsa masu ya tambayi ina gimbiya mujeedat.
Ɗaya daga cikin hadiman ce ta bashi amsa da cewa"su na a garden"
Damƙa mata hannun Turai yayi wadda tuni jikin ta yayi sanyi lakwas.
Cikin kuwala yace da hadimar "she's my wife, inaso ki rakata wurin su, ki bi min ita a hankali' murmushi hadimar tayi aranta ba karamin burgeta yayi ba, daga gani yana daraja matarshi
"In sha Allah yalla6ai" ta faɗa tare da ruƙo hannun mom Turai suka nufi ƙofar fita daga falon, tana tafiya tana waiwayon shi, kamar yadda shima yake kallon ta har sai da ta 6ace ma ganin shi kafin ya nufi ɗakin prime minister.
Jin motsin shugowar Sir Mubarak ne Yasa shi Buɗe idanunsa Yana dubanshi
Daga gefen gadon shi Ya zauna Yana fadin"ƙanina Ya Gajiyar tafiya," miƙewa Hateem Yayi da wata irin kasala Ya zauna Yana fuskantar Sir mubarak
"Gajiya tabi Jiki, yayana nakaina, kaima ya gajiyar taka"
Da zolaya Sir mubarak Yace"nifa Sojane tafiyar da mukayi bata isa ta gajiyar dani ba" murmushi Hateem Ya sakar mashi
Cikin kulawa Sir mubarak Yace"Meke damunka? Naga yanayinka ya canza ko baka Jin dadine"?
Cikin sanyin Murya Yace"lafiyana lou" ya fada yana kokarin danne damuwarshi
"Nifa Yayanka ne Hateem, baka Isa ka 6oye min damuwarka ba, dan Allah ka faɗamin, Idan ba haka ba hankalina bazai kwanta ba, na fahimci tun da kazo ƙasar nan ka canza gaba daya"
Ruƙo hannun sir mubarak Yayi acikin nashi ya damƙe shi sosai.
Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta"bansan ya zanyi ba da ƙaunar yaron nan na wurin Owais, shine silar duk wani hali da nake aciki, Har mafarkin shi nake Yi" ya faɗa yana mai sanyaya muryarsa.
"Allah Ya jarabce ni da son shi, bani da alaƙa da shi amma sai nake jin kamar ni na haife sa, na faɗa maka ne saboda kana ɗaya daga cikin waɗanda suke fahimtana"
Tun da ya fara magana Sir mubarak yake binshi da kallo mai nuni da tausayawarsa gare shi, yasan bakomai ke damun shi ba face rashin samun ɗa namiji, shiyasa ya kwallafa rai akan yaron da owais ke ruƙo.
"Ban ta6a ganin shi ba, amma saboda kai In sha Allah zanje har gidan owais ɗin In ga Yaron zuwa Gobe In Allah Yakaimu"
"Yana kama dani, tamkar Anyi photocopy din fuskana, hasken fatane kaɗai Ya banbanta mu da shi, Fatarshi farace Sol, tamkar Nazli, Dalilin dayasa kaga nashiga halin nan, bana son inbar ƙasar nan batare da yaji saukin lalurar shi ba, ina matuƙar son mu gana dashi, sai dai na rasa wannan damar da nake da ita, baba ya hanani kusantar shi, Gidan Owais dinma An hanani zuwa saboda shi, dole In hakura" cikin karyayyar murya ya faɗa yana faman sauke numfashi.
Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, yana neman rudar dashi, Aranshi Ya ayyana wannan wata irin kaunace haka? Abu kamar aikin asiri Allah na tuba.
Lallashin shi ya somayi yana kwantar mashi da hankalin shi, Har saida Yaga yafara sakewa tukunna suka cigaba da tattaunawa a tsakanin su.
__________________✍️
Lokacin Da Hajiya Turai, Ta shigo garden din tare da Hadimar data rakota, Tunkafin Ta ƙarasa inda su Gimbiya mujeedat suke, Hajiya laurat ta rafka salati tana fadin"wa nake gani kamar Harriet ƴar aikin gidan baba obie" ta kira ta ne da ainihin sunan ta, gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta, Hadimar data rakota Harta Juya ta nufi hanyar komawa gidan, Jiki asanyaye turai take tafiya tana tunkarar su.
Wani irin Matsiyacin kallo Hajiya laurat da Hajiya saratu suke watsa mata.
Tuni tasha jinin jikinta, da hannu Hajiya laurat ta nunata"ke! meya kawo ki nan? Ko kinga sa'ar Yin ki ne"
Shiru tayi bata tanka mata ba, Hajiya saratu ta kwashe da dariya Tana fadin"shisshigine da kutsu irin na ɗan talaka, malama wani tsautsayinne ya kawo ki wurinmu? Ko aiko ki akayi don ki yi mana hidima ne"?
Cike da shaƙiyanci her excellency Muhibbat tace"jibarta kamar wata mutuniyar kirki, ita kanta ta raina kanta shiyasa take jin shakkar shiga cikin mu, Ni wlh bansan me mubarak Ya gani a jikinta da har Ya aureta ba, in banda hasken fatarta da gashin da take da shi, Mace kullum kamar ana ɗibar namanta ana miya da shi, babu ƙiba babu tsawo, Duk arziƙin da take ci," Dariya suka sanya, mutun ukune basu tanka mata ba, Gimbiya mujeedat da hajiya malikat sai Hajiya madina. Sauran sune hatsabiban.
Hajiya Jamila tace"ai auran nata da yayi bana Allah da annabi bane wama yasani kota asirce shine, saboda Sir mubarak yafi ƙarfinta nesa ba kusa ba, Babban gorone, Shiyasa ta nace mashi don aci arziƙi, don Ma Allah Yasa bata ta6a haihuwa da shi ba, sai dai taci ta zubda.... " Hankalin turai ba ƙaramin tashi yayi ba, Jin cin mutuncin da suke Yi mata, Tuni hawaye sun soma wanke fuskarta.
Hakan ba ƙaramin daɗi yayima hajiya laurat ba, Ita dama burinta takala Ya ƙuntata.
"Nifa Har yanzu ban daina zargin Yaron nan nata shege bane, tun da bashi da uba, ahaka tazo da shi aiki gidanmu daga ƙasar england, matar nan muguwar munafuka ce, babu Allah aranta, Allah kadai Yasan maƙarƙashiyar da take kulla mana" zaro ido waje Hajiya turai tayi jin abunda Saratu take fadi, Maganar ta ƙona mata ranta, zuciyarta har wani tafarfasa take Yi sam takasa buɗe baki ta dakatar da su, sai dai binsu da take Yi da idanu.
"Gobe kada in kuskura Inga ƙeyarki awurin taron shagalin dinner din da za'ayi na Hateem, Idan ba haka ba agaban idon kowa zan watsa maki ruwan lemu akan fuskarki" Hajiya laurat ce ta fada tana nuna ta da cup din hannunta.
"Dake da wannan ɗayar munafukan meye ma sunanta"? Da sauri hajiya saratu tace"hajjaty" hajiya laurat tace"yawwa ita nake nufi, uwar iyayi, mai shafa turaren ƴan bori, ku biyun nan bamu buƙatarku a family din nan don kawai ba yadda zamuyi daku ne amma very soon zamu yi maku korar kare" ta faɗa tana sakar mata shu'umin murmushi.
Fashewa Turai tayi da kuka mai cin rai, kamar an ruƙe mata ƙafafuwanta takasa tafiya tabar wurin su.
Gyaran murya Gimbiya Malikat tayi masu, gaba ɗaya suka kalleta.
"Ba girmanku bane, kun bani Kunya, ni banga amfanin maganar da kuke gaya mata ba, ku kama mutunci ku mana" rai 6ace ta furta maganar, babu wasa a fuskarta.
Sai lokacin Gimbiya Mujeedat ta buɗe baki cikin nutsastsiyar muryarta ta furta Sunan turai.
Baiwar Allah muryarta na rawa ta amsa mata da na'am.
"Zo ki zauna kusa dani" ta fada tana nuna mata gefenta.
rai a6ace Laurat da muhibbat suka miƙe tsaye suna fadin Allah Ya kiyaye su haɗa kafada da ita, Indai turai zata zauna sai dai su su tafi" ko kallon su mujeedat batayi ba.
Muryar turai da shessheƙar kuka tace"bazan Iya zama ba Aunty mujeedat, bana so na shiga tsakaninku, ni zan tafi kawai, dama yaya mubarak ne Yace in zo wurinki don inyi maki bangajiyar tafiyar da ku ka yi, don haka zan tafi tun da naganki..... " tana ƙarasa maganar, ta juyawa da sauri ta nufi hanyar fita daga garden din.
Zuciyar Gimbiya mujeedat ta sosu, ranta ya 6aci da kalaman da Su laurat sukayi ma Turai.
Yunƙurawa tayi tare da miƙewa tsaye tana gyara rigarta,
Har suna hada baki wurin tambayarta ina zataje?
Batare da dube su ba tace"zan shiga cikine, nagode da ziyara sai mun haɗu gobe idan Allah yakaimu" Ta fada tare da kallon Gimbiya malikat tace"mu shiga daga ciki," miƙewa hajiya malika tayi suka ruƙe hannun juna atare suka nufi cikin gidan.
Bayan tafiyar su, Tsoki Hajiya laurat taja tana fadin"wannan munafukar matar duk itace taja mana, Muna zaman mu lafiya, ta tarwatsa mana farin cikin mu"
Hajiya Jamila tace"Halin talakan kenan, Yanzu gashi tasa Ran gimbiya mujeedat Ya 6aci"
Hajiya saratu tace"banji dadi ba wallahi, amma nasan ta inda zan rama, Allah yakaimu gobe lafiya, Idan har matarcan ta kuskura ta zo dinner din ya hateem jikinta zai gaya mata sai nayi mata abun da bata ta6a tsammani ba" ta faɗa tana faman haɗe fuskarta, Sun jima a garden din kafin daga bisani kowaccensu ta shiga motarta suka nufi gidajensu.
Baiwar Allah Hajiya turai tana azaune cikin motar Sir mubarak, tasha kuka tamkar ranta zai fita tayi danasanin zuwa gidan prime minister, kalaman su sun ƙona mata rai, musamman da hajiya saratu ta ambaci jazz da sunan shegene, tayi alkawarin bazata fadama sir mubarak abunda suka gaya mata ba, don kuwa idan yaji sai sun yabama aya zakinta.
_______________________✍️
Baka jin sautin komai a falon tamkar babu mutane acikinsa, alhalin nan kuwa Suna zaune kowa Ya hakimce abun sa, tsabar miskilanci ne Yasa basa iya buɗe baki su tanka ma Junan su, Kowannan su da abunda Ya ɗauke mashi hankali, fitowa Dr jazz yayi daga bedroom dinsa ya kimtsa kanshi cikin shadda launin blue sky abunka ga farar fata ta ƙara fiddo mashi da hasken shi, ga wani daddaɗan ƙamshin turarensa dake fesowa, Ya gyara sumar kanshi hannun shi ɗaya ruƙe da key din motarsa, wani irin annurin farin cikine akan kyakkyawar fuskarshi ga dukkan alamu akwai wani abu daya faranta mashi rai.
kafin Ya ƙarasa cikin falon, Idanunsa suka hango ma sa Matasan Samarin Family din dake zaune saman sofas Har sai da gabanshi Ya faɗi da idanunsa suka yi mashi tozali da su, Baisan da zuwansu ba, aranshi ya ayyana to fa ashe yau muna da manyan baƙi a gidan na mu ba, meyasa Ibad bai faɗa min sunzo gidan nan ba? Ya ƙarasa zancen zucin nashi cike da jin fagabar tunkararsu, Ya kasa motsa ƙafafuwanshi Ya tsaya atsaye kamar wanda aka yi mashi Iyaka da shiga falon, ɗaya bayan ɗaya ya soma bin su da kallo, Zaki Yana a azaune saman 2 seater Yayin da Apple Laptop dinsa ke akan Table din gabansa, Gaba ɗaya ya tattara hankalin shi akanta yayin da yake operating dinta atsanake, Short ne a jikin shi tare da Denim shirt tabi shape dinsa, Kau da idanunsa yai daga kan Zaki Ya mayar da su kan Wani Matashin saurayi fari Sol, fatarshi ko ƙwarzane babu, Ga wata nannaɗaɗɗiyar sumar kai dark brown, kai daga ganinsa wani shege ne mai ji da naira, Allah yayi shi da kyau mai jan Hankali, Jallabiya ce a jikin shi launin grey, ta zauna mashi sosai, bakowa bane wannan face Captain YASEER ɗan gidan His Excellency Abdul Razak da Her Excellency Muhibbat shuwa arab ne kamannin shi sak dana su Chief Owais, banbancin su launin fatane dana Ido, hannun shi ruƙe da Expensive phone dinsa da yake daddanawa da zira ziran yatsun hannunsa, yayin da Justice Nadeem ɗan gidan His excellency Deen Yake a kishingide kan doguwar Sofa, Ya zagayo da hannun shi ɗaya saman forehead dinsa, idanunsa suna a lumshe tamkar mai yin bacci.
Ziyad ne kaɗai yake a zaune saman lallausan Carpet din dake a shimfiɗe tsakiyar Sofa set din falon, faffaɗan farantin da aka kawo masu fresh fruit acikinsa ya tasa a gaba yana shan kayan marmari, duk acikin su Ziyad yafi su sauƙin kai kasancewarshi ɗan jarida da son labari, A yanzu haka da yake a zaune cikinsu A takure yake jin kanshi sunƙi sakar mashi fuska su yi fira kowa Ya kama harkar gabanshi shiyasa ya sauko kan carpet yaci gaba da shan kayan marmari.
Ƙamshin turarensu Ya gauraye Falon, Jazz dake kallon su ba ƙaramin burge shi su ke yi ba, ba tun yau ba Yana son Yaga jikokin Baba Obie sun haɗu suna sada zumunci aranshi sai yaji inama ace shima Jikan Baba obie ne da Allah ne kaɗai Yasan irin Farin cikin da zaiyi a duniyar nan.
Ganin basu lura da shigowarshi falon bane yasa shi yin saurin tafiya cikin sanɗa Ya nufi ƙofa Ya fuce daga ciki Yana faman sauke ajiyar zuciya, da sauri Ya nufi Harabar Ajiye motocinsu, Ya buɗe motarshi Ya shiga daga Ciki, tare dayi mata key, zuciyarshi acike fal da tunaninta, fatan shi Allah yasa wannan karan ta kula shi.
Yana driving fuskarshi dauke da annurin farin ciki, A haka Ya nufi Gidan baba obie.
Ganin shirun nasu bamai ƙarewa bane, Yasa shi miƙewa, Ya nufi Zaki Ya sanya hannu ya ɗauke laptop din da yake dannawa, Ya juya Ya nufi Captain Yaseer Ya kar6e wayarshi, kafin Ya tunkari justice Nadeem Ya sanya hannu Ya kamo Hancinshi Yaja Shi da karfi har sai da Justice Nadeem Ya buɗe idanunshi dake dauke da bacci Fuskarshi adaure yake kallon Ziyad.
Harara Ziyad Ya watsa masu Ranshi a6ace yace"wai meke damunku ne? Kullum muka haɗu kamar wasu kurame babu mai magana kowa ya kama harkar gabansa? Haka ake zumunci? Ni banga amfanin kirana wurin nan donmu haɗu ba.... " gaba ɗaya sun ɗaura idanunsu kan fuskarshi babu alamun zasu tanka mashi.
Guntun tsoki Yaja"kun wani zuba mun idanu kuna kallona wato ni ga shashasha"
Yamutsa fuska Zaki yayi tare da miƙa mashi hannu yace"Bani laptop dina ziyad"
"Ta ƙarfi ce zoka kwata" A faɗace Ya faɗa Yana haɗe mashi fuska.
Murmushi gefen fuska Zaki Ya sakar mashi.
"Meye damuwarka"? Ya tambaya yana faman lumshe idanunsa.
"Damuwata shine ku bani aron hankalin ku muyi fira kan abunda ya shafi rayuwarmu, daga gobe fa shikenan kowannanku zai koma inda Yake rayuwarsa, yawanci ba akasar nan kuke zaune ba why ba zamu kula juna yadda ya dace ba? Bamu da tabbacin ko zamu sake haduwa da junanmu"
Yanayin yadda yayi masu maganar Ya ta6a zuciyoyinsu,
In a calm voice Zaki Ya furta"In sha Allah zamu sake haɗuwa, Yanzu dai ka yi haƙuri, Ka zauna mu yi fira"
Ta6e baki Ziyad yayi, kafin Ya koma Ya zauna, Batare daya miƙa masu Kayansu daya kar6a ba.
"Bro, Ni bansan ta yadda zan fara firar bane, ko zaka taimaka mana da abun da zamu tattauna akai"? Captain ne Ya faɗa Tamkar baison furta maganar, justice Nadeem dake a kishingiɗe tuni Ya gyara zama saman Sofa Yana duban su
"Me zai hana Mu yi magana dangane da matayen da muke da burin aure"? Acewar ziyad.
kallon Harara Captain Ya watsa mashi"mu yi magana kan abu mai mahimmanci, Idan ba haka ba zan ja baki na nayi shiru"!
"Aure shi yafi komai mahimmanci domin kuwa Sunna ce mai karfi ta Manzon Allah SAW, Allah Ya bamu komai da zamu buƙata, Kowannanmu Yana da aikin yi, Aure shi ya rage mana yakamata ku yi tunani yanzu fa lokaci ne da zamu more rayuwarmu, mu ma yi aure mu hayayyafa kamar yadda Iyayen mu suka yi.... " Ziyad ne ya kora masu jawabi.
"Look, Ni aure baya a gabana yanzu, har yau banga macen data kwanta min arai na ba, tun lokacin dana rasa wadda nake da burin aure naji matan ma sun fitarmin araina"
Justice Nadeem dake kallon Captain Ya saki murmushi tare da cewa"Ai ba ita kadai bace mace a family dinmu ba, Kai ma kaso ka wahalar da kanka, Ai ni tun lokacin dana fahimci macace mai izza da ji da kai, na sanyama zuciyata salama, saboda bana son macen da namiji bai isa yayi iko da ita ba, ba zata yi dadin zaman aure ba, kwara wadda zaka Iya juyawa son ranka ba wadda zaka dinga jin fargaban tunkararta ba"
Ziyad yace"ka faɗi gaskiya mutumina, ita fa gaba ɗaya namiji ma baya agabanta, bata da burin yin aure, kai ma mai yaja maka yin dakon soyayyarta? Bayan Ga matasan ƴan mata nan masu jini a jika a family namu.... " kafin Ziyad ya ƙare maganar, Zaki yai gyaran murya tare da cewa"wai kuna Nufin Nazli"? Ɗaga mashi gira Nadeem yai, matashin murmushi ya saki kafin yace"Kuna nufin bakusan alaƙar dake a tsakaninta da chief Owais namu ba"? Atare suka haɗa baki wurin furta meke nan"?
Jim ya ɗanyi kafin Ya furta"Uncle Hateem, Ya riga daya mallaka mashi ita, bata da wani miji daya wuce shi a duniyar nan, tun kafin tazo duniya, wannan alƙawarine dake atsakanin Uncle sharafudeen da uncle Hateem, zasu haɗa auran ƴa'ƴansu... " da mamaki suke kallon shi
Ziyad yace"amma ni banta6a ganin alamun suna kula junansu da sunan soyayya ba, Ko ranar Birthday din grandfa da suka haɗu ko kallo ba su wa junansu ba"
"Dama taya za'ai su kula juna?bayan kowannansu Yana ji da kanshi daga ita har shi Owais din, duk abunda take taƙama da shi shima Yana da shi, gaskiya Uncle sharafudeen da Hateem basu yi tunani mai kyau ba, bayan sanin cewa Izza A jinin su take, tayaya Nazli zata yi mashi biyayya amatsayin matarshi? Justice Nadeem ne yayi maganar.
Captain da ke sauraransa fuskarshi babu annuri babu walwala ya furta"da ace nasan da zancen nan da tuntuni na cireta araina, dama ni ba Iyawa zanyi da ita ba, owais din shi yafi dacewa da ita, suje can su ƙarata," Ya faɗa tare da jingine kanshi jikin Sofa.
Shiru suka yi na ɗan wani lokaci, babu wanda Ya furta magana sai daga bisani Justice nadeem Ya furta"Zaki Ina budurwarka ta Canada Kyakkyawar balarabiyar nan"
Da zolaya ya faɗa yana duban shi.
Kallo ya jefa mashi mai kama da harara kafin Ya furta"ta koma gidan su"
Zaro ido justice Nadeem yayi"me? Kana nufin tabar gidanka"
Ɗaga mashi gira yai alamar eh,
"But why"?
Bai cika son tada maganarta ba, saboda hakan Yana fama mashi raunin dake a zuciyarshi.
Cikin sanyin murya ya furta"bansan meyasa ba, rana ɗaya ta haukace min ta soma kokarin juya min ba, badan naso ba nabarta ta dawo Nigeria"
Justice Yace"banji dadi ba, me zai hana ka nemi gidansu inyaso saika gabatar da kanka wurin Iyayenta"?
Murmushin takaicin Zaki yayi"tana da aure har da ƴarta, ban ta6a fada maka bane"
Jin wannan maganar Yasa Captain ware manyan idanunshi, hatta Ziyad dake sauraransu saida Ya zaro ido da alamun mamakin kalaman Zaki
A ruɗe justice Nadeem ya maimaita maganarshi"tana da aure har da ƴa? Amma ta zauna a gidanka tsawon shekaru tamkar ma'aurata? Kafin Ya ƙare maganar Captain Yace"tayaya hakan zai yiwu? Nima fa nasan Matar duk lokacin da zanje canada a gidan ka nake taras da ita, nayi tsammanin Ƴar aikin ka ce, shiyasa ban ta6a kawo ma raina wani abu ba,"
Girgiza kai Zaki yayi"ba ƴar aikina bace, Taimakon ta nayi, na ruƙe ta agidana saboda ta nuna min bata da kowa bayan mun fara shaƙuwa take bani labarinta, Hankalina Ya tashi jin cewa tana da aure, amma agidana mijinta ya tura mata da sakon saki, ganin hakan yasa muka cigaba da yin rayuwarmu, naso ta amince min in aure ta saboda bani da burin daya wuce na mallake ta, nasan tana sona sai dai tafi ƙaunar takomama mijinta saboda ƴarta da tabar mashi"
Gaba ɗaya sun lura da canzawarshi, hakan Ya ƙara tabbatar masu da irin kaunar da yake yi mata.
Miƙewa yayi da sauri Ya nufi bedroom dinshi, Da sauri justice Yabi bayanshi, Yana Shiga Ya zura hannayenshi cikin aljihun short dinshi, Yayin da zuciyarshi ke cigaba da tafarfasa
"Bana so hakan Ya dame ka, Yarinyar nan ko tana so ko bata so, Kai ne mijinta, Saboda kafi cutuwa, Tsawon shekara goma sha shidda kuna rayuwa agida ɗaya tamkar ma'aurata? Ka raineta ka kashe mata maƙudan kudi, Idan har ta butulce maka Allah ma bazai barta ba"
Justice ne yayi maganar, yana daga tsaye abayanshi
"Duk abunda nayi mata nayi ne don Allah..." kafin Ya ƙare maganar justice yace"nasan don Allah kayi mata amma wallahi bazan bari ta karya maka zuciya ba, tun da nake da kai baka ta6a nuna kana son wata ƴa mace ba, sai akanta, don haka dole ta aure ka, shi kuma mijinta Ya haƙura ya nemi wata, nasan ma yayi auranshi tun da jimawa"
Juyawo Zaki yayi idanunsa akan justice Yace"nagode da kulawarka agare ni, amma mubar maganar, saboda hakan bamai yiwuwa bane, Ni bazan tursasa mata akan ta so ni ba, ta ɗauke ni tamkar yayanta tana girmamani, tun da nake da ita ban ta6a nuna mata inasonta da aure ba itama haka "
"Ita ai ba makauniya bace, in ba kaiba wani namijine zai dauki dawainiyar baligar mace kamarta almost 16years, idan bazan manta ba, lokacin da naje gidanka a canada, ina lura da duk wani motsinku, Idan ka shiga daki da dare zaka kwanta tana binka bata fitowa har saita tabbatar da kayi bacci take fitowa, kaima kuma haka, sannan baka Iya cin abinci idan ba atare da ita ba, itama haka, kana nufin wani abu bai ta6a shiga tsakaninku ba"? ya faɗa yana bin sa da kallon tuhuma.
"Nadeem, Ba abunda kake tunani bane, nasan nayi kuskure na ajiye macen da ba muharramata ba a gidana, amma wallahi ban ta6a shigarta ba..... " muryarshi na rawa ya ƙare maganar, wani irin yanayi yake jin kanshi tunawa da rayuwarshi da ita.
Numfashi yaja kafin yaci gaba dacewa"Ta saba min da kanta, komai ita take yi min, bansan menene so ba sai akanta, ban fara muradin yin aure ba sai akanta, ashe ita din ba rabona bane...."
"Da ace kuɗi zasu Iya siyamin ita, wallahi har dukiyata zan iya salwantarwa saboda ita, bana tunanin zan samu macen da zata Iya maye min gurbinta, Ni ita kadai nakeso Nadeem" kwallar dake taruwa a cikin idanunsa har sun fara kokarin gangarowa saman kuncin sa.
Hankalin Justice Ba ƙaramin tashi yayi ba, ko a mafarki bai ta6a tunanin mace zata Iya tanƙwara zuciyar Zaki ba.
Dafa kafadunsa yayi da hannayenshi
"Inaso ka faɗamin shi mijinta tsawon shekara nawa su ka yi atare"?
In a low voice zaki Ya furta"ƙasa da 2 years, ta faɗa min aranar data haifa mashi baby tabar gidan badan bata son shi ba, kawai taji ya futar mata arantane"
"Kasan mijin nata"?
"Taya za'ai nasan shi? ni ko sunan shi ban ruƙe ba, saboda kishinta da nake ji"
Murmushi justice yayi tare da ruko hannun Zaki, suka zaune gefen gadon shi.
"Iyayenta masu hali ne"? ya jefa mashi tambayar.
"Yeah, mahaifinta ya ta6a ruke mukamin Governor a jihar joss, amma bai jima a mulkin ba ya sauka sakamakon ciwon kafar dake damun shi, bayan haka Ƙanin Mahaifinta Former president ne Na nigeria, Alhaji Musa wadata, Yayan Matar Uncle sharafudeen Hajiya Laurat, nima a wurin ta naji labarin ta" jinjina kai justice yayi"Ƴar masu Hali ce, Alhaji musan nan Yana ɗaya daga cikin wadanda suka fi kowa kuɗi a africa bayan family dinmu, amma nayi mamakin da har ta gudu tabar nigeria basu nemo ta ba, meyasa tabar mijinta da ƴarta? Shine abun tambayar"
"Naikaina Labarinta Yajima Yana ɗaure min kaina, Sonta ne Ya makantar dani shiyasa ban mayar da ita ga Iyayenta ba, saima na taimaka mata wurin 6oye kanta agidana, naci gaba da bata kulawa"
Justice ya ce Labarinta Akwai ruɗani Acikinsa, Ta fito daga babban family, ga ta kyakkyawa da ita amma ahaka har ta gudu daga gidan mijinta? Akan wani dalili? Me ta nema tarasa?"
Ya faɗa yana kallon Zaki,
"Nayi kokarin nemanta don inji ya ta koma gidansu? Iyayenta sun kar6eta ko kuwa? Shine fargabana sai dai bani da hanyar da zan Iya kiranta, tabar min wayarta a hannuna, bansan kowa nata ba, in ba hajiya Laurat ba"
Numfasawa Justice yayi kafin yace"kada ka damu ɗan uwana, zan iya yin komai akanka, gobe Idan Allah yakaimu a family dinner zanyi magana da hajiyar laurat din dangane da ita Yarinyar," har cikin ranshi yaji dadin maganar justice, ya kwantar mashi da hankalin shi sosai harya fara tunanin yadda haduwarsu zata kasance da ita, sun jima adakin suna tattaunawa daga bisani suka dawo falo wurin su Captain.
______________________✍️
A hankali Motar Dr Jazz Ta ƙaraso bakin Entry Hall na shiga gidan baba Obie, Bayan yai parking ɗinta ya fito ya nufi cikin gidan, A katafaren Main Falo din gidan Ya taras da Twins zaune saman sofa tare da wani matashin saurayi kyakkyawan gaske kallo ɗaya zaka yima fuskarshi ka shaida ɗan uwan Justice ne, gaba ɗayan su wankan suit ne a jikin su, Cike da jin fargabansu Ya nufe su, Cikin sanyin murya yace"barkanku da hutawa"
Ko kallo bai ishe su ba, Kamar Yayi magana da bango, kuma sun ganshi.
Kusan sau uku Yana maimaita maganar da yayi masu amma babu wanda Ya amsa mashi, hakan Yasa shi yanke shawarar Tafiya yabar wurinsu Har Ya ɗaga ƙafa zai tafi muryar Zayn takatse shi.
"Kai zo nan"! da kakkausar Murya Ya faɗa tare da yafuto shi da hannu, Irin kiran da akeyima kananin Yara, Jazz baiji komai aranshi ba Ya nufi Zayn.
Yamutsa fuska zayn yai yayin da yake binshi da kaskantaccen kallo Yace
"Kai makaho ne? Baka gan mu bane zaka wuce batare daka gaishe da mu ba"? Fuska adaure yayi mashi maganar.
Cikin sanyin murya Jazz yace"Nayi maku magana kusan sau uku babu wanda Ya kula ni"
Harara Zayn ya watsa mashi, Dr. nawaz dake a kishingide yana duban su Yace"zayn dama har yanzu wannan kwandon sharar Yana agidan nan? Nayi tsammanin Uncle Mubarak Ya saki babarsa sun koma kasarsu"
Ta6e baki Zayn yayi"gayanan dai kana kallon shi, baida banbanci da masu gida, Har yafi mu jin daɗi, Uncle Mubarak ya ɗaure mashi wurin zama"
Yamutsa fuska Dr.Nawaz Yai"Kaci sa'a ba'a ƙasar nake zaune ba, da tuni nasa anyi watsi dakai, donni bana son bare ya ra6i Ahlinmu," Jazz dake atsaye yana sauraron Rashin mutuncin da suke yi mashi, tuni idanunsa sun cicciko tab da kwalla.
"Ya isa haka!" Zaid ne Ya faɗa tare da kallon Jazz, Da hannu Yayi mashi alamar Ya tafi, bawan Allah Jiki asanyaye ya nufi Hanyar kitchen din gidan, tunkafin Ya karasa Able ta fito daga ciki hannunta ruƙe da tray na kayan marmari, ganin jazz yasa ta dakata da tafiya fuskarta da fara'a tace"Jazz Ya jikin naka"?
Fuskar shi babu walwala Yace"da sauki"
"Allah Ya kara lafiya" ya amsa mata da ameen, ganin Yana ƴan kalle kalle Ne yasa ta fahinci akwai wani abu da yake nema don haka tace"ko akwai wani abu da kake bukata ne"?
Ɗaga mata kai Yai haɗi da cewa"Eh, Ina neman Faryat ne,"
"Muje na raka ka, Nima wurin su zanje kai masu Kayan marmari," amsa mata yayi da toh, ta yi gaba yabi bayanta, aranta ta ayyana ko me zai kai shi wurin faryat? Tantiriyar Yarinyar nan da babu Allah aranta"
Upstairs suka hau, bayan sun sauka third floor, suka nufi Balcony dake acan sama,Tsayawa fasalta kyawun wurin 6ata baki ne sai wanda Ya gani, tunkafin su karasa Jazz Ya hango Su zazzaune saman wasu hadaddun Kujeru Bugun Dubai, Matasan Ƴan mata ne masu ji da kansu, A kalla sun kai su uku Kowaccensu Ta dauki wanka na kece raini, Kamshin turarensu tuni Ya soma Cika mashi hancinshi.
Kaitsaye idanunsa suka sauka akan Faryat, wadda ke asanye da mini skirt ya matse jikinta, daƙyar skirt din Ya wuce Ass dinta, Rigar jikinta kuwa Ko cibinta bata rufe ba, ta bayyana shape din kirjinta hatta nipples dinta kana iya ganin tsininsu, babu mayafi akanta Kitson kalabar da akayi mata ne mai kyan gaske ansanya mata sparkling stones masu jan hankali saman gashin kanta, yatsun hannunta yana asanye da gold knuckle rings, Haka zalika Hancinta na amanne da nose ring, wata ziririyar sarka ce a kafarta, Yarinyar karshe ce wurin Iya barikanci, Hatsabibiyar gaske bata jin magana ko miskala zarratin, sai dai fa akwai kyan sura, komai nata irin na hajiya saratu ne banbancinsu girman jiki da shekaru.
Matashiyar dake a gefenta, Yusra ce Ƙanwar Yaseer, Kallo ɗaya zakai mata saika sake kallonta, Tsabar haɗuwarta, itama fara ce sol, kamanninta sak dana mahaifiyarta Her excellency Muhibbat, gata doguwa tubarkalla, bayan ita sai Zulaihat kanwar Ziyad Wankan tarwaɗa ce alaunin fata tana da saukin kai ko a fuska ka kalle ta, babu wanda Ya lura da Jazz A cikinsu Hankalinsu na akan firar da suke Yi.
able ce tayi masu sallama, Tare da ajiye masu tray din kayan marmarin saman round table din dake a tsakiyar kujerun su, juyawa tayi da sauri ta fuce tabar wurin.
Wani irin shakkar Yi masu magana Yake ji, Sai faman bin Faryat Yake Yi da kallon ƙurulla.
"Na jaraba kiran layin Sister Hindu bata yi picking ba, may be ko bata a kusa ne da wayar, ita dai Yazrin nayi mata uziri, saboda tafiyar da suka sha nasan haryanzu gajiyar tafiya bata sakesu ba" Zalaihat ce tayi maganar tare dakai hannu ta dauki tufa tana ci
"Ina ga mezai hana mu shiga gidan yi masu bangajiyar tafiya, Su mommy ma suna acan"
"Ni dai ba inda zanje, sai zuwa gobe idan mun haɗu wurin Dinner din daddy Hateem" Acewar Faryat Tana faɗa tana farfari da idanunta.
"Gobe akwai shagali, zamu yi sharholiyarmu son ran mu, Har nakagara goben nan tayi," Yusra ce ta fada tana karkaɗa kafarta.
Har Faryat Ta buɗe baki daniyar tayi magana, Sautin ringing din wayar Jazz Ya dakatar da ita, Kusan atare suka wurga idanunsu kan fuskarshi, nan take yaji gabanshi ya faɗi rass saboda kwarjinin da suka yi mashi.
Yamutsa fuska Yusra tayi tare da kau da idonta
Zulaihat kuwa Murmushi tasakar mashi
"Dan uwa, Tun yaushe kazo wurin nan ne?
Yana faman Kame kansa Yace"tare da abla muka zo"
"Amma meyasa bakayi mana magana ba jazz," cikin kulawa ta fada tana dubanshi Ta fuskanci Hankalin shi ba kwance yake ba
"Wa kake nema ne"?
Kallon Faryat da yayi ne yasa ta gane ita yake son gani"
Murmushi zulaihat tayi,
Faryat dake kallon shi, wani irin shu'umin murmushine akan fuskarta, yunƙurawa tayi ta miƙewa ta dubi su Yusra"ni zan shiga ciki, bazan jima ba yanzu zan dawo" Yusra dake harararsa tace"faryat kin bani kunya, Ki rasa wa zaki kula sai wannan halittar" ta fada tana nuna shi da yatsa
Zulaihat tace"Please Yusra, babu ruwanki da shiga sabgarsu" Ta6ebaki Yusra tayi
Ba tare daya ankare ba, Faryat ta ruƙo hannunsa tare da jan shi suka soma tafiya atare, wani sanyine yaji ya ratsa zuciyarsa, duk da yasan ba lallai Faryat ta sassauta mashi ba, Ya riga daya san halin ta.
Kaitsaye suka nufi bedroom dinta dake a gidan, adai dai bakin kofar shiga Dr.Jazz Ya dakata da tafiya, da sauri ta kalle shi hadi da kashe mashi ido ɗaya tace "my babe meyasa ka dakata da yin tafiya? Let's go inside," ta fada tana matse hannunsa dake acikin nata, har cikin zuciyarshi yake jin matsar da take yi mashi. Muryarshi ƙasa ƙasa Ya ce"basai na shiga ciki ba, mu koma falo mu yi magana"
Ɗaure mashi fuska tay "Jazz, you will lose your chance to talk to me if you don't go in," she warned. "If you don't go in, don't expect to see me again"!
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga D
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 8
by
Novels Elite Admin
May 23, 2024
Sponsored Link
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القدر💋✊🔥
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Tana ƙarasa fadar hakan ta sanya hannu ta ture ƙofar ta shiga ciki, A ƙalla Yafi karfin mintuna biyar a bakin kofar yana yanke shawara da zuciyarsa, haƙiƙa Yana matuƙar jin tsoron Allah, bayason zama daki ɗaya da macen da ba muharramarsa ba, hakanan ba tare da wata lalura ba, balle kuma faryat da ta kasance tantiriya, sai dai baya jin zai iya rasa wannan damar, Allah ya jarabce shi da tsananin ƙaunarta, Itace mace ta farko da ya fara jin tsantsar sonta tun lokacin daya mallaki hankalinsa, ya mutu akan kaunar faryat yana son yarinyar duk da kasancewarta mara jin magana.
Numfasawa yayi kafin ahankali ya tura kofar dakin nata ya shiga daga ciki, katafaren dakin kwana ne, kamar na ƴar sarki, tsabar haduwar furniture din dakin, Komai na cikinsa Launin black pink ne.
Bayan shigarsa dakin, Sanyayyan sanyin A.c ne mai haɗe da daddaɗan kamshin turaren faryat ya ratsa hancinsa da fatar jikinsa, Lumshe idanunsa yayi slowly ya buɗe su akan faryat dake a tsaye gaban dressing mirror, ta juya baya kitson kalabar kanta ya sauko har mid back dinta, ta cikin madubin ta ke jifar shi da shu'umin kallo.
Ganin yaƙi ƙarasowa gare ta, yasa ta juyo ta nufe shi, dab dashi ta ɗaya suka soma jefa wa junansu kallo.
Ba zai iya jurar shaƙar ƙamshin turarenta ba da kallon surar jikinta hakan ba ƙaramin jefa shi yanayi ya ke yi ba, Muryarshi na rawa ya furta"Am.. umm.. tun da naganki zan tafi"
ba zato ba tsammani yaji ta ɗaura hannayenta saman kirjinshi, muryarta da shagwa6a ta furta"Ni ban gaji da kallon ka ba, My honey, tsawon lokaci bansanya ka a idanuwana ba, nayi kewar komai naka jazz.. " kafin ta ƙare maganar, jazz ya tari numfashinta da cewa"Faryat tayaya zan yarda da kalamanki? Bayan ke da kanki kika faɗi cewa bazaki ta6a sona ba, kuma ba zaki iya aure na ba"
Juya mashi baya tayi haɗi da goya hannayenta saman kirjinta kafin ta soma magana.
"Jazz, I won't hide it from you. Nothing has changed. I love you, but I can't marry someone who has no origin", (Jazz bazan 6oye maka ba, Har yanzu babu abun da ya canza, Inasonka amma bazan Iya auran wanda bashi da asali ba,)" ta faɗa tana girgiza kanta, kafin ta ɗaura da cewa.
"kaima ka sani jazz mommyna da daddyna ba zasu ta6a yarda mukasance atare ba, jazz I come from a wealthy family. How can I love someone like you who has no origin? What is your family status?" ta jefa mashi tambaya ba tare da ta jira amsar shi ba taci gaba da magana
"Ta ya ya zan auri ɗan tsohuwar mai aikin gidan mu" tun da ta fara magana sai yanzu ta juyo ta fuskance shi, Jikin shi yayi sanyi lakwas, hawaye tuni sun soma taruwa a cikin fararen idanuwansa, kalamanta sun kashe mashi kwarin gwiwarshi, sai yajima gaba ɗaya ya tsani kan shi, ta fahimci halin da ya shiga sai dai ko kaɗan bata ji tausayin shi ba.
"Jazz Hamshaƙan masu kuɗi suna rububi akaina, waɗanda duniya tasan da zamansu, How can I choose a meaningless future for myself when I could have so much more?" a tsiwace ta faɗa tana zare mashi kyawawan idanuwanta masu dauke da zira ziran eye lashes.
Hawayen da suka cika idanunsa tuni sun wanke fuskarshi
Cikin karyayyar murya yace"Nasan ni bakowa bane faryat, bani da asali, amma inaso ki sani, ina son ki tsakani da Allah badan wani abu naki ba, ba lallai ki sami wanda zai so ki kamar yarda nike sonki ba, nayi maki alkawarin zan baki kyakkyawar kulawa idan har kika amince da soyayya ta, ba zaki ta6a danasani ba faryat"!
Shu'umin murmushin gefen fuska tasakar mashi, wani irin kyawuntane Ya kara bayyana.
Matsawa tayi tare da shige mashi, Har takaiga mumfashinsu na kokawar fitowa, hannayenta biyu ta ɗaura saman waist dinsa, da sauri ya yi kokarin kwace kansa daga gareta sai dai taki bashi damar yin hakan, gaba ɗaya ta kashe mashi jikin shi.
"Jazz ka daina wahalar da kanka akaina, cos I will never marry you. Owning me is not an easy thing, idan mommy taji zancen kana neman soyayyata kai kasan me zai biyo baya, shiyasa nake rufa maka asiri, saboda ina da buri akanka," lumshe idanunsa yayi cikin jin ƙunar rai, Allah ne kadai yasan Irin azabtuwar da zuciyarsa take yi mashi akan soyayyar faryat, zai iya jure komai amma bazai juri ya rasa ta ba.
Jin motsin hannunta akan Trouser dinsa ne yasa shi yin saurin buɗe idanuwansa a hanzarce ya buge hannunta Yana faman fitar da huci...
Kashe mashi ido ɗaya tayi tare da zuro harshenta waje ta lashe pink lower lips dinta, cikin jin shaukin shi ta furta"jazz, har yanzu ban canza ra'ayina akanka ba, ka bani dama, in ɗebe maka kewa, kaga babu mai kallon mu daga ni sai kai, zan faranta maka rai, sannan inyi maka abun da zai zautar dakai ya gigita ka" ta faɗa cikin jin shauƙin shi tana kokarin tura mashi boobs ɗin ta da suke acike fam.
Jikin shine ya soma kakarwa a ruɗe ya furta"bani da wannan ƙazamin tunanin araina, dan Allah ki daina fadamin kalaman nan, Hakan Yana karya min zuciyata, Ni tsakani da Allah nake sonki, Idan babu mai kallon mu Allah Yana kallon mu faryat, Bazan bari mu sa6a mashi ba, "
Harara ta jefa mashi"matsalata dakai kenan, Har yanzu bakauyene kai, sai kace ba bature ba, sam baka da wayewar nan irin ta zamani, Daga anyi magana sai ka ambaci sunan Allah kamar kafi kowa tsoronsa, Ay Allah gafurirrahim ne, Idan mukayi sai mu roƙi rafiyarsa... " tunkafin taƙare maganar yace"Idan kuma muka mutu muna cikin aikatawa fa"? Murguɗa mashi baki tayi"nima bansani ba, tun da baka buƙatana ka tafi kawai, zan nemi wanda zamuyi da shi" ta fada tana ruƙe qugunta.
Wani irin kishine ya ziyarce shi, tamkar Ya haɗiyi zuciya haka yake ji
"Faryat ba ki jin kunyar fadin hakan agabana ba"? Ɗaga mashi gira tayi
"Yeah i can sleep with someone in front of you. tun da kai bazaka bani abun da nakeso ba, jazz bakason farin cikina, na jima ina sha'awar son kasancewa dakai amma kaƙi bani haɗin kai" cikin rauni na murya yace" idan kina son kasancewa dani ki aure ni mana, zan zama naki ke kadai, Mallakin ki, ko da yaushe kike bukatana zan kasance atare dake",
Girgiza mashi kai tayi"A'a nidai kawai kayi min abun da nakeso, ay na fada maka bazan iya auranka ba, sai dai mu kwanta in baka kaina" Lamarin faryat ba karamin mamaki yake bashi ba, A shekaru bazata wuce 22 Years ba, Mace har mace sai dai babu kunya ko kadan.
Ganin Ya tsareta da idanunsa ne yasa ta fara tunanin ko ya amince mata ne, ɗaura yatsun hannayenta tayi akan wandonsa da niyar ta zame masa shi, A hanzarce Ya buge hannunta, da sauri jiki na rawa ya nufi kofar dakin zai fuce, da gudu tabi bayanshi tayi hugging dinshi, ta soma raira mashi kukan shagwa6a, hakan baƙaramin yanayi ya jefa shi ba, baisan da wani yare zaiyi mata magana ta fahince shi ba, ya riga daya gane faryat tana sonshi, Rashin asalin shine yasa take gudin shi.
Muryarta da shessheƙar kukan ƙarya take fadin"Jazz, kada ka tafi kabarni, Ina buƙatarka Jazz, Ina son kasancewa tare dakai, dan Allah ka amince min muyi nayi maka alkawarin bazan faɗama kowa ba, Idan ma kana fargaban wani ya gan mu, sai mu je hotel in kama mana room, ko muyi a cikin motana" ta faɗa tana murza mashi mararshi da hannayenta, gaba ɗaya tagama susutar dashi wata irin zuface tasoma wanko fuskarshi
Muryarshi da matsananciyar kalasa sautinta ke fita
"Bazan iya sabama mahaliccina ba faryat, Ina jin tsoron Allah, kiyi haƙuri, Nima inajin abun da kike ji amma bazan iya ba, Kina bani wahala faryat, kema kuma kina cutar dakanki, saboda kina sona, Kina son kasancewa dani, amma kin haramta ma kanki aurena akan wani dalili naki mara ma'ana, Meyasa bazaki tausaya mana ba daga ni har ke? Faryat ki cika mana burinmu na ganin mun raya soyayyarmu, kada ki bari shaidan Yaci galaba akanki, ki fi karfin zuciyarki faryat, ki zauna kiyi tunani... " daƙyar ya ƙare maganar muryarshi na sarƙewa ya daddage ya 6an6are hannayenta daga ruƙon da tayi mashi, da sauri ya ruƙo handle din ƙofar ya fuce daga dakin
A jikin kofar Ya jingina kanshi hawaye masu ɗumi suka shiga zarya akan kuncinsa.
Sautin shessheƙar kukan faryat ne ya cika kunnuwansa, baisan ya zaiyi da ita ba, yasan da irin mugun sha'awar dake gareta sai dai shi bazai amince mata su aikata sabo ba, saboda babu ɗa'a ga abokin halitta wurin sa6ama mahalicci Allah! Bazai juri sauraron kukanta ba, zuciyarshi karaya take yi, da sauri Ya sauko down stairs Cikin takun sauri Ya Nufi part din baba Obinna, zuciyarshi na cigaba da tafarfasa, Abakin kofar dakinsa Ya tsaya da yin tafiyar Ya zaro hanky, Ya goge kwallarsa, Kafin ya daidaita nutsuwarsa, sallama yayi mashi.
Daga Ciki Ya jiyo muryar baba obie
"Shigo daga ciki" Buɗe kofar yai tare da shiga Ciki, adai dai lokacin Baba Obie, Yana zaune saman darduma hannun shi ruƙe da cazbaha.
Ba zato ba tsammani, Yaji saukar Jazz saman bayanshi, gaba ɗaya ya rungume shi tare da cusa fuskarshi saitin kafadarsa, Hakan ba ƙaramin ɗaga mashi hankali yayi ba, saboda a duk lokacin da jazz yayi mashi irin wannan rungumar to an 6ata masa raine," Yana Iya jiyo sautin fitar numfashinsa, dakatawa yayi da jan cazbahar, Ya ruƙo hannun Jazz Ya zagayo da shi ta gabanshi, tare da rungume shi ya kwantar da kansa saman kirjinsa tamkar ɗansa na cikinsa ko jikansa.
Cikin sigar lallashi yake bubbuga bayansa batare daya furta masa ƙala ba, har saida Yaji alamun Ya fara samun nutsuwa tukunna Ya soma magana
"Waya ta6a min shalelena"? Muryarshi adisashe Ya furta"Baba ka ta ya ni da addu'a, ita kadai nake bukata daga gare ka" ya fada batare daya raba jikin shi daga na Obie ba.
"Jazz kasan bana son damuwarka, Ka fada min koma menene nayi maka alkawarin indai baifi karfina ba wallahi zanyi maka shi," babu wasa a kalamansa
Jazz yayi fatan ace zai iya fada mashi abunda ke damunshi amma bazai iyaba, Yasan muddin baba obie yaji zancen Yana son faryat sai ya aura mashi ita, koda kuwa Iyayenta basa so, shi kuma abunda yake gudu tada husuma, saboda ba lallai hajiya saratu da Pravin su amince mashi ya aureta ba, komai zai iya faru.
Shafa bayanshi baba obie yaci gaba dayi yana fadin"Ina sauraronka, Fadamin meke damunka rabin raina"
Ɗagowa yayi da fuskarshi wadda tuni ta jiƙe sharkar da hawaye, cikin rauni na murya yace"baba, Bana jin daɗin yadda wasu suke guduna saboda rashin asalina, meyasa sauran mutane ba kamar kai da daddy mubarak suke ba"? Zuciyar baba obie ba karamin karaya tayi ba, nan take ya gane gori akayi masa, bawan Allah tsantsar tausayinsa ne yakama shi.
Cigaba da yin magana yayi"Na tsani kaina baba, Rashin asalina Yana neman Yaja min na rasa abunda nakeso, kowa ya buɗi baki sai yace ni ɗan mai aikine bani da asali, Har shege ake kirana baba" daƙyar ya kare maganar wani irin kukane Yaci karfinsa da sauri Baba obie Ya janyoshi zuwa jikinshi sosai Ya rungune shi, Yana lallashin shi.
"Toh toh ya isa ka yi shiru, Bana son Kana sanya damuwa aranka, Kukan Ya isa haka, kowani ɗan adam da ka gani a duniyar nan da irin tashi ƙaddarar, babu wanda Allah baya jarabta, inaso ka rungumi wannan amatsayin ƙaddararka, Kada ka ta6a bari wani Yasa ka canza tunaninka, Allah Shi yake son ganin rayuwarka haka, Kuma shine zai nema maka mafita" nasiha mai ratsa zuciya baba obie Yaci gaba dayi mashi har saida yaji ya daina kukan tukunna Ya raba shi daga jikinshi
Cikin kulawa yace dashi"Yanzu fada min wanene Ya tsokane ka"?
Shiru yayi batare dayace komai ba, baba obie ya fahimci bayason ya sanar da shi, hakan yasanshi cewa"Ko da yake basai ka fadamin ba, ni da kaina zan binciko wanene, kuma zan hukuntashi" ya fada yana daure fuskarshi alamar ranshi ya 6aci.
"Baba," Kallon shi obie yayi ina sauraronka
"Kamar yadda nasaba fadamaka,Yau ma zan maimaita maka, Ni dai inason family ɗinka, Ina alfahari daku, nayi fatan ace nima ina ɗaya daga cikin jikokin ka sai dai Allah bai nufa"
Wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskar baba obie.
"Jazz baka ɗauke ni kamar yadda na dauke ka ba, ko da yake ba laifinka bane, laifin wadanda suke yi maka gorine, sune sukasa kake jin kanka bare afamily dina, amma inaso kasani, baba obie baya yi maka kallon bare, inasonka jazz kamar yadda nakeson jikokina, Kamar yadda kake fatan ka zama daya daga zuri'ata nima haka nake fatan ka kasance" yayin da baba obie ke yin maganar, wani irin sanyi da daɗi ne ke tsuma zuciyar jazz, har abada bazai ta6a mantawa da halaccinsu agare shi ba.
Ganin Ya faranta masa raine yasa baba obie cewa"namanta ban tambayeka ba, Ya jikin naka"?
Fuskarshi dauke da murmushi Yace"naji sauki, nagode na kulawarka agareni"
Jinjina kai baba obie yai"gobe idan Allah yakaimu, Ina fata zaka halacci Dinner din Hateem"
Jim ya ɗanyi harga Allah baison zuwa kodan gudun a ci mutuncinsa, amma saboda yana son ya faranta ma baba obie yasa shi cewa "In sha Allah tare dani za'a buɗe taro"
Murmushi baba obie yai masa"Naji dadin jin hakan rabin raina.
Jan shi da fira baba obie yai, kamar wani abokinsa, tuni jazz ya saki jikin shi.
*💋 UMMIN AMERICA❤*
Duk Yinin Yau Bata fito daga ɗaki ba, ta killace kanta tun safe bata jin daɗin zuciyarta, duk ta ƙuntata kanta, tayi jiran zuwansu unaisah su shigo don su ɗe6e mata kewa sai dai shiru babu alamarsu, tuntana sa ran ganin su har ta fidda ranta, ta ƙundundune kanta cikin lallausar bargonta, Sallah ce kaɗai take tada ta daga saman gado
Har ta fara nutsawa cikin baccinta kwatsam wayarta dake ajiye kan nightstand ta soma yin ruri, da wata irin kasala ta ɗago da kanta, sumar kanta duk ta hargitse babu gyara, laluba Hannu tayi ta kamo wayar batare data duba sunan mai kiranta ba tayi picking tare da kara wayar a kunnanta.
Sautin Muryar NATASHA ne ya Daki Dodon Kunnanta"nayi fushi Kin manta dani ko"? ta faɗa cikin harshen turan ci.
Muryarta da kasala Ta furta"ba haka bane Natasha, Kina araina, dake nake kwana dake nake tashi"
"Ban yarda da kalamanki ba Ummi, Idan Dagaske kinyi kewata meyasa baki kirani ba? Sai da na kira ki ni da na damu dake ko"?
Shiru tayi na ɗan wani lokaci har sai da Natasha Ta furta Naji kinyi shiru tukunna taja numfashi tana faman sauke ajiyar zuciya tace"bansan yadda zanyi maki bayani ba NATASHA, ni kaɗai nasan halin da nake aciki, ina cikin damuwa, Ina cikin kaɗaici, Rayuwata a ƙuntace take natasha, bani da wani ƴan ci, ba wanda Ya damu dani, tun safe bana jin daɗin jikina babu wanda ya leƙo ɗaki na don Yaga awani hali nake aciki.... "Muryarta na rawa ta ƙare maganar, tamkar zata fashe da kuka, hakan Ba ƙaramin ɗaga Hankalin Natasha Yayi ba, Jin sautin miryar aminiyarta da alamun matsananciyar damuwa..
Cikin saurin mirya ta furta"Ummi, muyi magana ta video Call, Inason naganki ko hankalina Ya kwanta"
"Toh, amma kafin nan zan shiga toilet, Ƴan mintuna kaɗan Idan na fito zan kiraki" natasha ta amsa mata da toh, bayan ta yi rejecting Kiran, ta daura wayar kan drawer, kafin Ta sanya hannu ta yaye bargon data lullu6a da shi, Jallabiya ce a jikinta launin dark ash, saukowa tayi daga kan gadon ta nufi toilet, After Some minutes ta fito fuskarta da alamun lemar ruwa, Laptop dinta dake ajiye kan desk ta dauko ta koma kan gado ta zauna daga tsakiya ta ajiyeta agabanta, kafin ta buɗe ta soma sarrafata, Natasha ta kira video Call nan take ta ɗaga, kallon juna suka soma yi tamkar suna a wuri ɗaya, Natasha tana a kishingiɗe saman beach chair dake a ga6ar teku, babu suturar mutunci a jikinta, dama ita bata cika son sanya suturar da zata rufe mata tsiraicinta ba, tafi sha'awar ta sanya pant da bra.
cikin harshen turanci suke yin magana.
"Yanayin fuskarki Ya tabbatarmin da bakyajin dadin Ummi, Ki faɗamin meke damunki? Waya ta6a min ke"?
Yamutsa fuska Ummi tayi tamkar batason furta maganar tace"kamar yadda na faɗa maki bana jin daɗin jikina, narasa gane meke damuna, amma ina da tabbacin hada kaɗaici, ban ta6a ƙuntataba Irin na Yau, Jin kaina nake tamkar Ina a prison"
Cikin kulawa Natasha tace"meyasa ba zaki janye aikin da Commender Ya baki ba? Ummi dama ni nasan bazaki Iya jurewa ba, tuntuni naso In gargaɗeki saboda ba zaki Iya ba, mu da muka saba da yawo kullum sai mun fita wurin abokan harkar mu, taya zaki Iya jure rayuwar kulle"? Ta faɗa tana mai dubanta,
Dafe kai Ummi tayi da hannu ɗaya"Har yanzu banyi danasanin kar6ar aikin kula da yaran nan ba, Saboda Inaji araina akwai wani alkhairi atattare da zamana da su, shiyasa bana danasani, ni kawai abunda ke damuna rayuwar kullance ke banaso, Yana ƙuntata Rayuwana, hada ƙarin Yaran da suke ɗebe min kewa basu zo wurina ba yau, ni kuma nakasa tashi naje gare su" fuskarta a yamutse tayi maganar
"Har Yanzu ba zaki fahimce ni ba Ummi, Ni inaso na kwatarmaki ƴan cinki ne, Inason farin cikin ki, Kina buƙatar abokan Harka, kefa ba irin matan da za'a ƙuntata ba ne...' tunkan Natasha ta ƙare maganarta, ummi tayi saurin tarar numfashinta da cewa
"Akwai labari mai daɗi, nasan idan na fada maki zakiyi mamaki"
Ta faɗi hakan ne don batason Natasha taci gaba da yi mata zancen Ajiye aikin da take Yi.
"Naƙosa naji labarin nan fadamin mana" ta fada tana sakin murmushin shaƙiyanci.
"Mutumin Ya ziyarce ni Har cikin gidan da nake,"
Waro idanu waje natasha tayi da mamaki ta furta kina nufin Big Boss? Ya ziyarce ki? Ɗaga mata gira ummi tayi alamar eh.
"Amma ya akai ya iya shigowa gidan Jami'an Isod, bayan kin faɗamin acikin sharuddan da suka baki, babu shige babu fuce basu buƙatar wani naki yazo inda kike, har zuwa lokacin da kika kammala Yi masu aikin su" ta faɗa a kagare da son jin ƙarashen xancen.
Dariyar shaƙiyancin Ummi tasaki tamkar babu damuwa aranta"kinsan mutumin na dabanne, ni kaina bansan tayaya akai ya shigo gidan ba, Har tambayarshi nayi sai yace min idan na yarda dashi indaina tambayarsa.... " dariya natasha tayi cike da nishaɗi tace"Namijin Duniya, Nayi kewarshi ummi, kullum cikin begen ganinsa nake yi, yayi min nisa yanzu, ba kamar lokacin da nake yi mashi rainon babynsa Pretty ba, tun da Ya kar6i Yarinyar sai nayi dagaske nake ganin shi, ko wayana baya picking... " kafin Natasha ta ƙare maganar Ummi tayi hanzarin tarar numfashinta da cewa"wai ina yarinyar take ne? Na jima ina son na tambayeki ita, nayi missing dinta, tun ranar dana fara Yin tozali da ita naji kaunarta ta shiga raina, duk da bata jin magana amma tana da kyau"
Natasha tace"hmmm, Ummi Ya raba ni da ita, tsawon watanni, duk idan na tambayeshi ina baby Pretty na sai yace min ya mayar da ita wurin mamanta, har alfarma na nema awurin shi akan ya amince min inbiyo shi nigeria saboda ina son ganinta amma Ya hanani.... "muryarta na rawa ta ƙare maganar idanunta sun cicciko tab da kwalla.
"Ummi Inason yarinyar nan, Ina ƙaunarta, nayi fatan ace ni na haifeta ko dan saboda mu kasance atare har abada, mun shaƙu da juna, na saba da ita, Amma yayi min yankan ƙauna.... " tunda tafara magana ummi ta natsu tana kallon fuskar Natasha ta cikin screen din laptop tamkar suna awuri ɗaya.
"Ummi nasan zaki Iya taimaka mani, tunda Yana kaunarki, Yasha fadamin ke kadaice kike Iya sarrafashi son ranki, please kiyi amfani da damar da kika da ita, Ki lalla6a shi Ya dawo min da baby pretty" cikin sanyin Murya ta ƙare maganar, Ummi dake kallonta tuni tausayinta Ya kamata, bata ta6a ganin Natasha tana zubar da kwallarta akan wani ɗan adam ba sai akan babyn da take mutuwar so, tasan da irin kaunar da take yima yarinyar a lokacin baya.
Cikin kwantar da murya ummi ta furta"Am sorry, Kinsan bana son ganin hawayenki, zan Iya yin komai akanki, saboda halaccin ki agare ni, Kin wuce ƙawa a wurina sai dai ƴar uwa, saboda kin kaunace ni a lokacin da kowa yake guduna, abun da nakeso dake ki kwantar da hankalin ki, zanyi kokarin ganin na shawo kanshi don ya dawo maki da babyn ki"
Murmushin farin ciki natasha tasaki tana fadin"thank u ummi, nasan zaki iya yin komai saboda farin cikina, shiyasa nake ƙara kaunarki, ina nan ina shirye shiryen zuwa Nigeria saboda ke"
Martanin murmushin ummi ta mayar mata,
"Ina handsome boy din nan, namanta ban tambaye ki shi ba"
"Bashi da lafiya, Yana a kwance"
Yamutsa fuska Natasha tayi"najiye mashi ba dadi, Allah Ya bashi lafiya, har yau ban manta da fuskar shi ba"
Murmushi Ummi tayi mata" dama ke ay bakya mantawa da abu mai kyau, naga kin kirani da layinki Na england, hakan na nufin kin koma gidanki"?
Ɗaga mata gira tayi alamar eh. Jinjina kai ummi tayi, shiru sukayi na wani lokaci yayin da suke kallon juna batare da ƙyaftawa ba.
"Kin tsareni da ido Kina kallona, Kamar akwai wani abu da kikeson fadamin" acewar natasha ta faɗa tana ɗage mata gira.
Dariya Ummi tayi, Harta Buɗe baki da niyar furta magana, Sautin knocking ƙofar da akayine Yasa ta fasa yi mata maganar,
"Zan Kiraki Anjima Ki kula min da kan ki"
"Bangaji da jin muryarki ba ummi, amma shikenan zan jira zuwa anjiman inma kin manta baki kirani ba, Ni zan Kira ki, ki kula min da kanki and pls ki daina sanya damuwa aranki" a hankali ummi ta furta mata"toh, nagode da kulawarki agare ni" bayan sunyi sallama, Ta kashe video Call din, ta sauko tare da laptop din a hannunta, ta nufi desk ta ɗaurata, kafin ta shiga wurin closet dinta, mayafi ta daura akanta.
ɗaga Murya ta yi Wanene"?
Daga waje tajiyo Muryar Batool Tana fadin"aunty Ummi ni ce" wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta jin muryar Batool.
"Ki shigo daga ciki," turo ƙofar batool tayi tare da shigowa ciki, tana bin dakin da kallo kafin ta ɗaura idanunta akan fuskar Ummi, Murmushi suka sakarma juna
"Nayi fushi Batool, sai yanzu zaki tuna dani? Nayi tsammanin kece mutun na farko da zaki zo gare ni idan kika ji shiru ban fito ba, amma sai naji shiru babu ke babu unaisah" tafaɗa tana haɗe mata fuska alamar ranta Ya 6aci.
"Aunty ummi am sorry, Kina araina, tun ɗazu nake taso in shigo wurin ki'
Miƙa mata hannu Ummi tayi da sauri Batool ta ƙarasa gabanta tare da faɗawa kan chest dinta, sosai Ummi tai hugging dinta.
"Nayi missing dinki My babe, kun barni a daki ni kaɗai inata kewarku, Ina unaisah ne"! Ta faɗa batare data raba jikinta daga na batool ba.
"Nima bansan inda take ba, ɗazu muka rabu"
"Okey,ina fata kina lafiya, " ɗago dakai Batool tayi"Lafiyata lou, amma ke kamar baki da lafiya"
Shafa gefen fuskarta ummi tayi"bana jin dadi, amma kada hakan Ya dame ki, ganinki da nayi ya faranta raina" ta ƙare maganar tare da ruƙo mayafin Pakistan din batool"kayan sunyi maki kyau sai naga kinyi min kama da wata Old friend ɗina da muka rabu da dadaɗewa, kamar ita ta haifeki, Itama doguwace fara, Mom dinta balarabiya ce"
Murmushi batool tayi"amma ni da Unaisah nake kama"
Girgiza kai Ummi tayi"No, baki kama da Unaisah kun dai yi yanayi da ita"
Kwa6e fuska Batool tayi saboda ita tafison ace tana kama da Unaisah, ummi ta fahimci hakan sai tayi saurin cewa"wasa nake maki, dama don in ga reaction dinki ne, gaskiya kuna kama da ita sosaima kamar twins" jin hakan yasa batool sakin dariyar farin ciki, ummi dake kallonta batayi mamakin hakan ba ta riga data fahimci tsantsar ƙaunar da suke ma junansu.
"Mu zauna ki tayani fira, Ko baki gaji da tsayuwa bane"
"Aunty ummi, nasan kina jin yunwa, ki tafo muje falo zan sama maki abunda zaki ci" wani irin kallon ƙauna ummi keyi mata ba ƙaramin dadi take ji ba idan Batool ta nuna damuwa akanta.
Ruƙo hannunta ummi tayi acikin nata atare suka fito daga dakin.
Sautin Muryoyinsu Naufal ne Yajawo Hankalin Ummi Ga kallon su, tun Dazu suna a falo, Tare da Boss Man, Sun tasa shi gaba sai surutu suke zuba mashi.
Jin takun Takalmansu Yasa su dagowa suka kalli su Ummi dake saukowa down stairs, Har suna haɗa baki wurin ambaton sunanta Aunty Ummi.
Saukowa Jamimah da azeeza su ka yi daga kan sofan da suke zaune, da gudu suka nufe ta, Hannah da Parveen ma suke miƙe suka nufe, wani irin daɗi taji aranta,
Ɗaya bayan ɗaya ta soma rungumarsu a jikinta,
"Aunty Ummi, Yanzu kika tashi daga bacci"? Azeeza ce tayi mata tambayar
Girgiza mata kai tayi alamar a'a
Parveen tace"Ko dai baki lafiya" Harara Ummi ta jefa ma Parveen tare da cewa"kun damu dani ne? Meyasa ba ku zo bedroom ɗina kun duba ni ba? Shiru sukayi sai jamimah ce tai kokarin cewa"mantawa mu ka yi" Jan kumatunta Ummi tayi da hannu"Aku sarkin ɗumi, Na riga da nage baku kaunata, Shiyasa baku damu dani ba" ta faɗa haɗi da marairaice masu fuska,
"Wallahi aunty Ummi Muna ƙaunarki, kuma mun damu dake" Hannah ce tayi maganar
"Ni dai Inasonki aunty Ummi, kiyi hakuri idan mun 6ata maki rai," murmushi ummi tasakar ma Azeeza da tayi maganar.
Ruƙo hannunta Jemimah Tayi"Aunty ummi nima ina sonki"
"Naji na Yarda kuna sona, Yanzu mu shiga ciki," ta fada tare da Jan hannun Batool suka nufi ciki tare da su Hannah
Tunkafin Su ƙaraso, Boss man Yake Kallon Ummi, sam ya manta da ita.
"Barka da hutawa Yalla6ai, Fatan ka wuni Lafiya, Ya iyali"
A hankali Ya furta"Lafiyalou Ummi, Ina fata kema haka"? Ɗaga mashi gira tai alamar eh, ta faɗa tare da samun wuri saman Sofa ta zauna, suma sauran duk suka zauna.
hankalin Sajeed na akan screen din wayar Unaisah, Haris da javed suna zaune gefe da gefen shi tare da naufal sai kallon Game din da Yake bugawa suke yi, baijima da sauke shi akan wayar ba.
Gyaran Murya Ummi tayi masu atare suka dago suna kallon ta.
"Sannunku, ba hello ba Hi kun samu Waya kunata danna waya baku ita ne"
"Ta Unaisah ce," Acewar Sajeed
Da mamaki Ummi tace"Unaisah ke da waya iphone15pro? Amma ban ta6a ganinta ba"
"Dr Laurace ta bata Kyautarta, ɗaya daga cikin Likitocin da suka yi jinyarsu a america"
Boss man ne Ya bata amsa, Jinjina kai tayi.
"Ina ita Unaisah dinne"? Tayi tambayar tana kallon su
Boss Yace"Bansan meya tsayar da ita ba, tunɗazu da muka shigo tare da big guy Ya tafi da ita zai nuna mata kitchen din gidan nan ban ƙara ganin ta ba, ba mamaki ta tsaya taya masu aiki girkin dinner"
"Dan Allah ka nuna min kitchen din, Inaso In kar6o ma aunty Ummi abinci, Yunwa take ji" acewar Batool.
Murmushi boss man Yayi yana dubanta yace"kin damun da auntyn nan naki da alama, kada ki damu, bari na kira big guy awaya, idan suna a kitchen din zansa akawo mata abincin.... " kafin Ya ƙare maganar, Parveen tayi saurin cewa"Dan Allah Nima zanci" dariya sukayi gaba dayansu.
Ummi tace"foodie, Baki Gajiya da cin abinci, shiyasa kika fi sauran ƴan uwanki jiki"
Kwa6e fuska tai"ay bani kadai bace me cin abincin ba, Ki kalli kumatun jamimah sunyi manya manya da su" maganarta ta basu dariya.
Harara jemimah ta watsa mata"ay dai ban kaiki Cin abinci dayawa ba, Ni madara da bonbita nake sha, Sai dafaffan kwai da Fika fikin Kaza," boss dake kallonsu murmushine dauke akan fuskarshi, Firarsu ba karamin nishadi take sanya shi ba
Wayarshi Ya zaro daga aljihu Ya danna ma Big guy kira, Bugu uku Yayi Picking
Miƙewa yai da sauri Ya nufi cikin falon nesa da su ya tsaya saboda hayaniyarsu.
"Malam Ina ka shiga ne? Ka tafin mun da rabin raina"
On the other hand sautin dariyar Big guy ta karaɗe Kunnuwansa,
"Nifa Yanzu Haka Ina daki kwance saman gadona"
"Bana son Iya shege, To ita ina kabarta?
"Ka riga da kasan Halin Jarin naka, yarinyarce da kiriniya, Tunfa dazu dana nuna mata kitchen din nace mata ta dawo cikin yan uwanta, bayan na fada mata hakan na wuce room dina, yanzu haka bata wuce kitchen din, Cikin kattai" ya karasa maganar Yana dariya.
Daure fuska boss yayi tamkar Yana agabanshi,
"Zamu hadu dakai ne, Allah idan wani abu Yasamu Yarinyar nan jikinka ne zai gaya maka dan rainin wayau" ya fada tare da yin rejecting kiran,
Cikin takun sauri Ya nufi hanyar zuwa kitchen din, ba laifi akwai tazara tsakanin kitchen din da main falo,
Lokacin da Ya Isa katafaren kitchen din gidan tamkar a restaurant tsabar haɗuwarshi, kai kace ba wurin Girka abinci bane saboda girman shi da ƙawatuwarshi, An zuba kayan aiki masu tsada da inganci, gaba ɗaya masu girka abincin Gidan Jami'an Isod ne cikin chef'uniform, matasan samari masu jini a jika, daga ganin Yadda suke aiki zaka shaida kwarewarsu a 6angaren catering, ko mace bazata nuna masu Iya sarrafa abinci ba, A ƙalla sunkai su Bakwai, Babu wanda Ya lura da shigowar Taj acikinsu, Gaba ɗaya Hankalinsu na akan Unaisah, dake agaban kitchen island tana Yanka masu kayan Lambu, abun da ya ɗaure ma taj kai, ganin Yadda sukayi mata rumfa kamar zasu haɗiyeta tsabar yadda suke binta da mayataccen Kallo, Ta saki baki sai Labari take basu su kuwa sun Kasa kunne suna sauraron daddaɗar muryarta, Tunda suka kafe ta da idanunsu ko kyaftawa basa yi kamar zasu haɗiyeta.
Gyaran Muryar da Taj yayi masu ne Yaja Hankulansu ga dubanshi, kamar sunga wani mugun abu, A gaggauce su kayi saurin barin Inda Take, kusan atare suka buga ƙafa Haɗi da sara mashi.
Kallon Harara Ya watsa masu, Cikin harshen turanci Ya furta"wannan wani irin gangancine zaku bar Yarinya tana amfani da wuƙa? Kun wani tsareta da idanunku kamar zaku lashe ta" Sunnar dakai su kayi Suna faman sosa keya suka hada baki wurin furta"sorry Sir, ba laifin mu bane, Itace ta buƙaci damu koya mata girki, munyi kokarin Hanata amma saita sanya mana rigima"
Wurga eye balls dinsa Yayi akan Unaisah dake Kallon shi, Har ta ajiye wuƙar hannunta, nufo shi tayi fuskarta da murmushin Yaƙe tace"ay ni nace su bani In tayasu aiki, Kuma dama Na iya ba yar koya bace" ta fada tana ruƙe qugunta da hannu.
Wani kallo Ya jefa mata me kama da harara, bakomai Yake tunawa ba face lokacin da tana yar ƙaramarta, ranar daya tafi aiki yabarta a gida tana jin yunwa taje ta kunna cooker gass da sunan zata yi girki, wuta ta kama a gidan, wai yau itace take mashi kurin ta Iya girki ba yar koyo bace? Girgiza kai Yayi haɗi da yin murmushi tacikin face mask dinshi
"Daughter, ƴan uwanki sunata nemanki, Yakamata Kizo Mu koma falo" maƙe mashi kafaɗa tayi"ay bamu gama girkin ba"
"Bana son gaddama, zo ki wuce mu tafi"
Marairaice mashi fuska tai"dan Allah kabarni wallahi inason In Iya girki kala kala,"
"Kada Ki damu, zansa a koya maki amma ba yanzu ba, dokar Aikin mu ce mace bata shiga hurumin mu, baki ga maza bane a kitchen din"? Cikin lallashi yayi mata maganar Yana nuna mata chefs din dake tsaitsaye cirko cirko suna kallon su
"Yalla6ai, da dai anbarta ta koya tun da ta nuna tana so, kuma ni aganina maca ce ita, wata rana zataso tayi ma mijinta.... "Tunkafin chef din daya dauko Maganar Ya karasa boss Yayi mashi wani kallo mai nuni da kashedi, Hakan yasa shi yin saurin Katse maganar,
Janyo hannun Unaisah Yayi dakarfi Ya fito da ita daga kitchen din, Chefs din basu ji dadin zuwan Shi ba, Ya raba su da Yarinyar data ɗe6e masu kewa yau, zuwanta Ya faranta masu rai, sunji dadin surutun da tadinga yi masu, komai nata burgesu Yake yi.
Ranta Ya 6aci, Ganin yadda ya janyota daga kitchen din, da sauri ta fusge hannunta tana fadin"Ni ka ƙyale ni, in tafi da kaina" Ta faɗa tana daure mashi fuska, Sam Yakasa ce mata komai sai dai kallonta da yake yi.
"Bansan meyasa ka takura rayuwata ba, girki fa kawai na roƙa kabarni In tayasu amma ka hanani, dan Allah menene alaƙata dakai ne? Na lura so kake kana Yin iko dani, Idan don saboda taimakon da kukayi mana ne ay dan Allah ku ka yi ko"? A fadace ta faɗa tana zare mashi gray eyes dinta tamkar zata rufe shi da bugu,
Har saida Yaji gabanshi Yaɗan fadi, sauƙinta ma yasan halinta,
"Meyasa ni kadai kake ma haka?
"Saboda ke jini na ce" a zuciyarshi Ya furta maganar
"Kiyi haƙuri Idan na 6ata maki rai, bana son 6acin ranki, Ƴan uwanki ne suke ta nemanki, bayan haka kamar yarda na fada maki dokar aikin mu ce mace bata shiga hurumin mu, waɗannan chefs din da kike gani dukansu a lokacin baya ba mutanan kirki bane, Dayawansu Ƴan shaye shaye ne da masu bin matan banza, wasun su mugayen ƴan ta'adda ne wadanda suka gagari Iyayensu da hukuma, Ire iren su chief Yake kamowa Ya koya masu hankali, Idan suka shiryu sai ya maida su Jami'an Isod..."
Waro ido waje tayi jin Ya ambaci mugayen ƴan ta'adda.
"Ba Zanso abun da zai cutar min dake ba, Haƙƙina ne kula da rayuwarki Unaisah dan Allah kada ki hanani Yin aikin lada... " in cool voice ya faɗa...
Wani irin kallo yaga tana bin shi da shi, kamar akwai wani abu da take son ganowa
Muryarta na rawa ta furta"dan Allah ka cire min face mask din fuskarka inason ganinka"
Girgiza mata kai yayi"zaki ganni amma ba yanzu ba, amma meyasa kike son ganin fuskata"?
"Saboda muryarka, tayi min kama da ta daddyna wallah sai nake ji kamar daddyna ne kai, duk da nasan ma ba shi bane, ina ji araina baya araye ma" idanunta har sun ciko da kwalla.
"Kina ji aranki ni daddyn ki ne" ɗaga mashi kai tayi alamar eh"
"Ki ƙaddara aranki cewa Ni ne" ya faɗa tare da ruƙo arm dinta, Ya janyota jikin shi, haɗi da kwantar mata da kanta saman kirjinsa, wani irin sanyine taji ya ratsa zuciyarta, lumshe idanunsa yai a hankali ya sanya hannu tare da zame face mask dinsa, Sumbatar head dinta yai, kafin da sauri ya maida mask din fuskarsa.
Tsawon mintuna biyar cuf suna manne da juna, sai daga bisani ya raba ta da jikin shi, baiwar Allah jikinta yayi sanyi tamkar an watsa mata ruwan sanyi,
Shafa gefen fuskarta yayi da tafin hannunsa"Ina sonki my daughter" murmushi tayi mashi"Nima ina sonka daddy na"
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*(Kaɗan daga cikin na sati mai zuwa idan Allah yakaimu da rai da lafiya, unaisah zatayi waya da Benazir😍 Garkuwa zaiyi tashin bazata, kada ku bari abaku labarin walimar hateem😂🤣 Ni kaina zumuɗin ta nake yi🔥🔥🔥)*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 9 Complete
by
Novels Elite Admin
May 24, 2024
Sponsored Link
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القدر💋✊🔥
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Har Ya ruƙo hannunta za su shiga ciki sai kuma Ya dakata yana faɗin "Au namanta, Auntyn ku ummi tana buƙatar abinci ban sani ba, ko akwai abunda chefs suka gama girkawa yanzu"? ya tambaya yana duban ta.
"Akwai naga sun kammala Rice and chicken stew tare da coleslaw hada zobo ma ... " kafin ta ƙarasa lissafa mashi yace"Okey, Ki jira ni, bari na shiga ciki in kar6o mata" amsa mashi tayi da toh.
Bayan shigarsa kitchen din ta soma tunanin ko awani hali Garkuwarsu ya ke a ciki? ta yi matuƙar damuwa da shi, ganin shi da take yi a mawuyacin hali ba karamin karya mata zuciya ya ke yi ba, rabon da ta sanyashi a idanunta tun da asuba da su ka shiga yi mashi addu'a, da tunanin shi ta wuni ta bari sai da anjima ta shiga duba shi.
"My babe, I'm back" Muryar Boss man ce ta fargar da ita, da sauri takai dubanta gare shi, Hannayen shi ruƙe da handle din wooden tray mai faɗi, daga saman shi haɗaɗdun warmers ne babba da ƙarama tare da plates da sauran tarkacen kayan abinci"
Miƙa mata yayi kar6i nan, ta sanya hannu ta kar6a cikin kitchen din Ya koma jim kaɗan Ya dawo hannayen shi ruƙe da wani madaidaicin faranti mai ɗauke da mixed drinks masu sanyi.
Ganin tana kallon shi yasa shi kashe mata ido ɗaya, murmushi tasakar mashi, a tare suka jera zuwa cikin falon.
Jikin Batool Har Kerma Yake Yi wurin mikewa da wani irin sauri ta nufi Unaisah zata rungumeta, ganin Tray a hannunta yasa ta dakata tana faman ɗaure mata fuska tace"Ina kika shiga inata nemanki"
"Ina a kitchen fa, Girki Na tsaya taya masu aiki" ta faɗa tare da wucewa ta sauke tray din hannunta saman Carpet, Parveen tun da tayi tozali da Abinci takasa samun sukuni, Tafi kowa zalama.
A Plate Batool ta zuba ma Ummi abincin ta hada mata da pineapple juice ta miƙa mata, fuskarta da fara'a ta kar6a tana fadin nagode My babe," a tsanake ta soma Ci.
Ɗaya bayan ɗaya unaisah ta soma kasa masu abincin tana miƙa masu a plate, bayan ta gama da su itama ta zuba nata tare da Boss man a plate ɗaya, suka zauna suna ci gwanin ban sha'awa, falon Yayi tsit baka jin sautin komai saina taunar abincin da suke ci...
"Ummi Ina son Yin magana dake bayan sallar magrib" Boss ne yayi mata maganar, amsa mashi tayi da toh.
"Amma wannan ɗin abincin daren mu ne"? Acewar Parveen, Harararta Naufal Yayi.
"Kusan ƙarfe shida na marece, A haka Har kike tambaya, toh abincin dare ne, mu da cin wani abincin sai gobe da safe in Allah yakaimu" javed ne Ya bata amsa Yayin da yake kur6ar lemu me sanyi.
"Ba'a magana idan Ana cin abinci," Boss ne ya faɗa yana duban su.
"Dariya fa da murmushi suma ba'ayi"?
Jemimah ce ta jefa mashi tambayar yayin da take cunkusa abinci abaki tana tauna.
Dariya suka sanya gaba ɗayansu cikin raha.
"sajeed Ina wayata"
Dafe kai Yai da hannu ɗaya"Am sorry sister, Na cinye maki chargy, bansan ko kina da charger ba"
"Akwai charger bani wayar" da sauri ta miƙe taje gaban sofa din da yake a zaune, Wayar Ya zaro daga trouser pocket nasa ya miƙa mata ita.
Tasa hannu ta kar6a, kafin ta nufi bedroom dinsu, shigarta keda wuya wayar hannunta ta soma ringing, tana kokarin ɗaga Wayar ta kashe kanta kamar tayi hauka saboda ta gane number da suka kirane ita da sajeed.'
Cikin takun sauri ta nufi backpack din su, ta buɗe ta dauko cazar wayar ta jona a socket, akan idonta wayar tayi haske alamar ya ɗauka, lumshe idanunta tayi tare da jingina bayanta jikin gadon, zuciyarta a cike fal da tunanin shi.
*💋NAZLI👑*
Sautin daddaɗan kiɗa ne da ke tashi a katafaren gym room (ɗakin motsa jiki) da ke a gidan prime minister, an ƙawata shi da manyan injinan motsa jiki, a tsaye take saman thread mill tana gudu cikin shiga ta kayan motsa jiki, sport bra tare da short launin black colour, sunyi bala'in yi mata kyau, sun bayyana farar fatarta sol ko kwarzane babu, tamkar bata ta6a yin rarrafe ba arayuwarta saboda hasken fatarta harta gwiwar ƙafarta tayi jawur da ita, dirar mace doguwa ga kyan sura, ta ɗaure lallausar baƙar sumar kanta sai salƙi take yi da sheƙi ta sauko har saitin waist din ta, gaba ɗaya ta tattara nutsuwarta akan abun da take yi, sautin music din ba ƙaramin ni'ima yake samar mata ba, kyawawan idanunta na akan tanƙameman madubin dake manne da bango, zufa ce ta soma tsastsafo mata ta ko'ina ta jiƙe sharkaf da ita, babu alamun gajiya atattare da ita, daga gani ta ƙware a 6angaren gym.
Bakomai ne acikin zuciyarta ba, face zallar begensa, duk yadda taso ta hana kanta tunawa da shi abun yaci tura, tayi tunanin zata iya sarrafa zuciyarta wurin hana ta tunaninsa sai dai abun yaci tura, a kowani daƙiƙa son shi ƙara ninkuwa yake yi a zuciyarta, ga dukkan alamu Nazli batasan menene So ba, ko da yake girman kai da izza sun hana ta gane cutarwar da take yima kanta, shiyasa ta kasa miƙa wuya"
Tunanin shi ne ya haifar mata da jin Kasala, ba arziƙi ta dakata da motsa jikin, ta kai hannu ta ɗauki short towel fari ƙal ta soma tsane jikin ta da shi, bayan ta kammala fitowa tayi daga gym room din ta nufi bedroom dinta, kai tsaye ta shiga bathroom domin yin wanka.
Shigowa ɗakin Yazrin tayi cikin shiga ta riga da wando black and white, tayi rolling veil akanta, hannunta ruƙe da wayarta.
Ganin babu ita a dakin yasa tayi tsammanin ko ta fita ne har zata juya ta juyo motsin ta a toilet da sauri ta la6e a bayan labule.
Gently ta zuro ƙafafunta dake sanye cikin slippers, bathrobe ce a jikinta fara ƙyal, hannunta ɗaya ruƙe da towel sai faman tsane sumar kanta take yi.
Yazrin dake a la6e bayan labule, wayarta ta danna ta shiga camera ta ɗage labulen a hankali ta soma ɗaukar Nazli video batare da sanin ta ba.
Dressing mirror ta nufa cikin takun qasaita, wasu tsadaddun mayukan gyaran jiki ne asaman mirror din, bayan ta zauna ta soma bin ko'ina tana shafe shi a tsanake, kafin ta dauko bakhhoor burner ( turaren wuta) ta soma turara jikinta da sumar kanta, komai nata cikin aji take yin shi, Nazli macece mai tsafta ga son gayu, kuma ma'abociya son ƙamshi.
Duk wani motsinta, Yazrin na kallonta ta cikin camera, bayan ta gama gyaran jikin nata, closet ta nufa jim kaɗan ta fito, har ta canza kayan jikin ta zuwa kimono robe, yazrin da ke ta daukar ta video kayataccen murmushi ne kan face dinta, aranta ta ayyana ukhty Nazli badai iya gayu ba, bata gama zancen zucin nata ba, taga Nazli ta haye saman Royal bed dinta hannun ta ruƙe da wayarta, bakomai take kallo ba face hotonsa, har zooming dinshi take yi da zira ziran yatsun hannunta, hoton da take kallo tsohuwar ajiyace a kalla yakai shekara biyar, lokacin yakai masu ziraya a canada, ba tare da sanin shi ba ta dauki hotan, dama duk in yaje basa jituwa da Nazli, har ya bar ƙasar basa sakarma juna fuska kai kace makiyane, Yazrin ce kadai suke mutunci da juna, kuma a lokacin suna matuƙar ƙaunar junansu, amma izza ta hanasu bama juna kulawa sai dai su yi magana ta text message, tamkar basa a gida ɗaya.
fita tai daga gallery ta shiga wurin messages dinsu
Har ta rubuta "I miss u.... ' sai kuma ta goge, zuciyarta na raya mata zubda aji ne ta nuna ta damu dashi, shi ne yakamata yafara yi mata magana
Jefar da wayar tayi gefenta, tare da kai hannu taja lallausan duvet dinta ta lullu6e fuskanta, ganin hakan yasa Yazrin fitowa daga bayan labulen cikin sanɗa ta nufi gadon, tare da hayewa ta janyo wayar Nazli cike da fargaba cikin sa'a ta ɗauko ta batare da security din wayar ya shiga ba, hakan ba karamin dadi yayi mata ba.
Whatsapp dinta taso ta shiga sai dai kash password Ya hanata, tunani ta soma yi me Nazli ta rubuta a matsayin password dinta?
Gudun kada ta tayi mistake ta samu matsal
Zurfi tunani ta shiga, can zuciyarta ta raya mata cewar ta jaraba rubuta date of birth din Aki Owais saboda ta ta6a ganin ta rubuta shi a diary din ta amatsayin rana mafi mahimmanci agare ta.
Wani irin tsalle ta daka ganin Ya buɗe, da sauri ta shiga nutsuwarta tana leƙen Nazli, wadda tuni bacci yayi awon gaba da ita
Yazrin tayi mamakin ganin tsawon lokacin da suka dauka ba suyi magana wa junansu ba, Ranta ya sosu bata ji daɗi ba, ji take kamar ta dauki pillow ta bubbuga mata akanta tsabar haushin da taji.
"Ƴar bakin ciki, In sha Allah baki da miji a duniyar nan daya wuce big bro, bazan zauna na zuba maki ido kina cutar kanki ba, Akhi Owais shi ya dace ya mallake ki, nayi maki sha'awar auran shi saboda samun miji nagari irin shi ba abu ne mai sauƙi ba, Ina son kiyi rayuwar farin ciki yar uwata, dole na shirya tsakaninku.... " acikin zuciyarta ta furta maganar tare da cigaba da danna wayar, daga wayarta ta tura video din data dauka, kaitsaye ta yi mashi sending, shaf shaf ta rubuta mashi text message da harshen turanci kamar haka
_Nayi kewarka bugun zuciyata, ina mai baka haƙurin nuna halin ko'in kula da nayi, ba'asan raina ba, nayi danasanin hakan don ba ƙaramin cutuwa nake yi ba na rashin jin ɗumin jikinka a kusa dani, ka duba whatsapp in ka, na tura maka video dina don ya ɗebe maka kewar rashi na, nasan zaka ji dadin kallon shi_
fuskar yazrin dauke da murmushin mugunta ta tura mashi message din, bayan ta gama ta ajiye mata wayarta, ta nufi kofar fita daga dakin tana faman sakin dariya, ta riga da tasan me zai biyo baya muddin Nazli taga aika aikan da tayi mata ba ƙaramin husuma zata tada ba, zata ce ta zubda mata aji awurin chief owais.
*A GIDAN UNCLE ƊAN IYA*
Kusan Atare Su ka yi Parking din motocin su, Mahboob ne Ya fara fitowa daga front seat hannun shi ɗaya ruƙe da key din Motarshi, fuskarshi dauke da murmushi yake kallon Motar zahra.
"Sannu da dawowa Hajiya Zahra Surukar Kaka Obinna" Ya faɗa tare da buɗe Back Seat din Motar Shi Ya duƙar da kai Yana leƙan Baby Junaid dake zaune Hannayenshi rungume da Food basket dinshi, Ga school bag din shi a gefe, Sai faman ɗaure fuska Yake, Da alama rigimar tashi ce ta motsa.
"Ranka Shi daɗe, Mun ƙaraso gidan, zaka iya takawa da kafarka ne mu shiga ciki ko kuwa ni kake so In goyaka"? Da zolaya mahboob yayi maganar yana dariya.
Yamutsa mashi fuska baby junaid yayi "ni ka goyani" Ya fada A kule.
Juya mashi baya Mahboob Yayi Ya ɗan zuƙunna Baby Junaid Ya Haye bayan nashi, Bayan Ya miƙe Ya ɗauko mashi Backpack dinsa tare da kwandonsa
Adai dai Lokacin Zahra Ta fito daga motarta, tayi shiga cikin Lafaya, Hannunta ɗaya ruƙe da Ƴar purse dinta
Fuskarta da fara'a take duban Baby Junaid Da Mahboob
"yau wata rana mun dawo gida atare, baby junaid dina zo nan" ta faɗa tare da miƙa mashi hannu, babu musu Ya soma kiciniyar saukowa daga saman bayan mahboob, daukarshi tayi Mahboob yace"Wato ni kake gudu? Zamu hadune ɗan rainin wayau, tun da naje dauko shi Daga school Yake ta jin haushina saboda naje amakare shi kaɗai Ya rage ba'aje daukarsa ba, baisan nima bada son raina ba, Motarce ta samu matasala sai da nakaita gyara tukunna naje daukoshi da ita"
Dariya zahra tayi"Gaskiya baka kyauta ba, taya zaka bar mana Baby Shi kadai Ga yunwa, meyasa baka kirani awaya naje daukosa ba"
"Banyi dabarar yin Hakan ba, Yanzu dai tun da mun dawo gida, gashi nan ki kaima jatumarsa, nagaji da kallon kumburarran fuskarshi"
"Mahboob baka da mutunci, zamu rama ne" ta faɗa tana dariya, baby junaid kuwa Ya ɗaure fuska, Kumatunshi sunyi jawur da su, da alama kuka Yake so yayi.
Atare suka nufi cikin gidan, tana agaba mahboob Yana abayanta
Bayan shigarsu Falo, Suka taras da mami da Ummi zaune suna kallo a plasma tv din falo, Cikin girmamawa suka gaishe da su.
"Sannun ku da dawowa, Ya gajiyar aiki"? Cikin Kulawa mami tayi maganar, atare suka hada baki wurin cewa"yawwa mami"
Ummi dake kallon Baby junaid tace"to fa, Me akayi masa ne naga yana ɗaure fuska"
Mahboob Na dariya Yace"wallahi Ummi Rigimarshi ce ta motsa, Kinsan Halin shi.
Zahra tace"bawani nan, shine Yaƙi zuwa ɗaukarshi da wuri, Yabar shi a school yana ta jira"
"Gaskiya mahboob Baka kyauta mana ba, saboda Allah, Haka akeyi? Sai kabar mana Yaro ga Yunwa" Ummi ce ta faɗa tana satar kallon baby junaid duk don ta nuna mashi taji Haushi.
"Ay mashi uziri mana, hakanan dai Mahboob bazaiƙi zuwa ɗaukar baby junaid ba sai dai idan wani uzirinne Ya ruƙe shi" mami na fadan hakan Mahboob Yace"ay har bayani nayi ma zahran, motana ne Ya samu matsala sai da nakaita gyara, in sha Allah Hakan ma bazata ƙara faruwa ba zan dinga zuwa ina dauko shi akan lokaci"
Ummi tace"haka Yakamata"
"Zonan babyn mommynsa" acewar Ummi ta fada tana miƙa mashi hannu, maƙe mata kafaɗa yayi alamar bazaije ba, Saima Ya ƙara ƙanƙame Zahra, mami na dariya tace"In banda abunki sai kace bakisan halinsa ba idan Yana fushi Yafi buƙatar jin ɗumin mommynsa,"
"Ina auntyn tawa take"?
"Tana a kitchen"
Maimaita kalmar kitchen Zahra tayi, aranta ta furta me kuma Aunty Aneelerh take yi a kicin"? Batayi Ƙasa a gwiwa ba, Ta nufi kitchen din Mahboob Har Ya zauna kan sofa, sai kuma Ya miƙe Yabi bayan zahra.
Tunkafin su ƙarasa kitchen din suka hango Aneelerh ta haɗa uban gumi a kitchen tana girki, Ita kadai.
Sam bata Ji alamar shigowarsu ba, ta zage damtse sai motsa miya take Yi
"Aunty Aneelerh"? atare suka haɗa baki wurin kiran sunanta, da sauri Ta rufe soup pot din, Ta juyo tana fuskantarsu, kafin ta ɗaura idanunta akan Baby Junaid,
Murmushi ta sakar masu "Sannunku da dawowa,"
"Yawww, Auntyna, Yau ke kike Aiki akitchen Ina Ana"? Zahra ce ta jefa mata tambayar, Mahboob Yace"Allah yasa dai lafiya"
Girgiza kai tayi cikin sanyin murya ta soma magana"ba lafiya...." gaba ɗaya ta labarta masu abunda Ya faru zuwansu dakin Ana tare da su mami, Hankalinsu Ba ƙaramin tashi yayi ba, Musamman Mahboob.
"Bansan Ya zanyi ba, Taƙi faɗa mana abun da ke damunta, Ni tsorona kada wani abu Ya faru da ita" fuskarta da tsantsar damuwa ta furta maganar
"Nima hankalin bai kwanta da ita ba, dafarko nayi tsammanin Damuwar halin da ƴan uwanta suke aciki ne ke damunta, ashe ba haka bane, daga gareta ne" Acewar Mahboob.
Kafin Zahra ta furta magana baby Junaid Ya fashe da kuka, Dama ranshi a6ace Yake, da sauri Aneelerh Ta miƙa hannu ta kar6e shi cikin sigar lallashi take jijjiga shi tana fadin"Am sorry My baby boy, kayi hakuri nasan nice na 6ata maka rai,' muryarshi da shessheƙar kuka Yace"wayyo Allah mommy, Kuna ta surutu Kin ƙi kulani, baki missing ɗina ba" dariya zahra da mahboob su ka yi, hakan Ba ƙaramin 6ata mashi rai yai ba, Hada Jifar Su da harara
Shafa sumar kanshi tayi"Na kar6i laifina, ay min afwa... " zumbura mata baki yayi,
Zahra tace"aunty Aneelerh, Ki tafi dashi ɗaki Ni zan ƙarasa girkin, Inyaso da anjima Sai mu ƙarasa tattaunawa"
"Keda kika dawo daga aiki a gajiye kuma kike neman in bar maki girki, a'a gaskiya Ki bari na ƙarasa ai ba ni kadai nake yi ba, Tare da Ummi muke Yi, bata jima da komawa falo ba.. "
Kafin Ta ƙare maganar, Mahboob Yace"tun da tace zatayi kibar mata kawai, Nima saina tayata, baby junaid yana buƙatar kulawarki, Kije Ki lallashe shi"
Murmushi tasaki Tana kallonsu, Har cikin ranta take jin tsantsar kaunar Yan uwanta, Haɗin kansu Na burgeta, fatanta Allah Ya dawwamar da farin ciki arayuwarsu, Hakika suna kyautata mata.
"Nagode, zahra, Mahboob, Allah Ya barmu mun ku,"
Amsa mata su ka yi da ameen
"Zan shiga ciki, pls zahra Ki dafa mashi indomie" amsa mata tayi da toh, Bayan fitar Aneeleeh daga kitchen din, Mahboob Ya ajiye food basket din Junaid, Yabi bayan aneelerh hannun shi ruke da backpack din Baby junaid,
Bayan Ya ajiye mashi adaki, Ya fito Ya nufi nashi room din, shaf shaf Yayi wanka Ya sanya gajeran wando da ƴar singlet, Kafin Ya nufi kitchen don Ya taya zahra girki kamar wani mace, atare suka cigaba da kula da girkin, suna tattauna fira dangane da matsalar Ana.
"Amma kai a tunaninka meke damunta"?
"Sister Ni kaina nakasa gane wani tunani zanyi dangane da matsalar Ana, sai dai kawai mubita da addu'a, Allah ya yaye mata abunda ke damunta,'
"Ni aganina, Mu kar6i Contact din Ƴan uwanta , mu tuntu6esu may be sunsan meke damunta, tunda sunfi kusa da ita"
"Nima nayi tunanin hakan, Yanzu dai mu jira, zuwa lokacin da su Abie zasu dawo gidan, nasan zasu Kirata su tambayeta,"
"Hmm kana ganin zata Iya faɗa masu gaskiya? Bayan Aunty Aneeleeh tace tare da su mamie suka je dakin nata amma taƙi fada masu, ai ni aganina idanma akwai wanda Ya dace ta fadamawa baiwuci su mami dinba"
Jinjina kai Mahboob Yayi"kin fadi gaskiya,"
"Ni abunma Ya fara bani tsoro, da naji aunty aneeleeh tace Ana ta dinga kwala masu ihu tana fadin su fita subar mata dakinta, Anya mahboob bata da matsalar kwalwa?
Mahboob Yace"Bana tunanin hakan, wata'kil Aljanune suka shige ta, mu cigaba da tayata addu'a Allah Ya kawo mata saukin abunda ke damunta"
"In sha Allah zamuyi mata"
Daga haka basu ƙara magana ba, sun maida hankali akan Girkin da suke Yi.
Fitowa Aneelerh tayi daga Bathroom, Bayanta goye da baby junaid, tayi mashi wanka, sai faman hade mata fuska Yake Yi, Riga da wando ta Dauko ta zura mashi ajikinshi, ta feshe shi da turare, zama tayi gefen gadonta,ta ɗaura shi saman laps dinta, hannunta ɗaya dafe ta shi,tarasa meke yi mata daɗi, Ita dai Hankalinta bai kwanta da halin da Ana take aciki ba, Ji take aranta kamar wani abunne Zai faru, zuciyarta batayi mata daɗi, sam ta manta da baby junaid Tayi zurfi a tunaninta, Har Ya fara lumshe ido zaiyi bacci, Muryar Zahra ta fargar da su,
hannunta biyu ruƙe da plate din indomie, Sai tiriri Take Yi, daga saman indomie din ta shimfiɗa mashi Soyayyan kwai, Mahboob Yana abiye da bayanta, Hannun shi ruƙe da mugs biyu na kakkauran Tea.
"Sannunku da kokari, nasanya ku aiki ko hutawa ba ku yi ba"
"Pls ki daina fadin hakan, Mu yakamata mu Yi maki sannu, anbarki da girki a kitchen, Su mami suna a falo fira tai dadi" Mahboob Ne yai maganar
Asaman Table zahra ta daura plate din, Mahboob Ma ya sauke nashi mugs din, atare suka fuce daga dakin.
Baby junaid tunda yayi tozali da indomi Ya soma sakin murmushin murna, Har wani lashe le6ensa Yake Yi
"Mommy da zafi, kuma ni Yunwa nake ji Allah" ashagwa6e Yayi maganar
"calm down Your Mind my baby boy, Ni zan baka da hannuna, kasan dai mommy bazata bar baby junaid dinta Yaji zafi ba ko"? Ɗaga mata kai yai alamar"
"Yawwa my boy" ta faɗa tare dakai hannu ta dauki fork, ta soma nannaɗo taliyar tana hura mashi da baki idan ta huce saita tura mashi abaki, kusan atare suka cinye indomie din dakwai, Kafin suka sha tea din su.
"Kada kayi bacci, Yanzu za'a fara kiran sallar magrib," ɗaga mata kai yai alamar toh, Janshi ta soma yi da fira duk dan kada yayi bacci.
Bayan Kammala sallar Magbrib, A lokacin Abie da Uncle ɗan Iya sun shigo gidan, babu wanda Ya tuntu6esu da maganar Ana, sun bari ne sai sun huce gajiyar da suka kwaso ,Har saida suka kammala cin abincinsu, Tukunna Ummi ta sanar da su Halin da ake ciki, babu 6ata lokaci, Abie Yasa suka hallara A falon gidan gaba ɗayansu, Ana ce kaɗai ke babu acikin su.
Aneelerh da zahra da Mahboob suna zazzaune kan Carpet, A lokacin baby junaid Ya jima da yin bacci, Yana can kwance saman gado.
Abie da Uncle ɗan Iya suna a zaune saman Sofa mai mazaunin mutun uku, Abie Yana sanye da farar jallabiya ya manna farin glass a idanunsa, Yayin da Uncle ɗan Iya yake asanye da Riga Yar shara ta farin Yadi, daga ciki ya sanya gajeran wando baƙi.
Su Mamie da Ummi suna zaune saman Sofa mai mazaunin mutun biyu, dukansu Hijabai ne a jikin su. tamkar mutuwa ta gifta babu mai magana acikinsu, Har na tsawon mintuna kafin daga bisani Uncle ɗan Iya yayi masu gyaran murya, suka ɗago suna duban shi, da hannu Ya nuna Mahboob
"Je ka kira ta" Amsawa mahboob Yayi da toh, ya miƙe ya nufi bedroom din Ana, abakin ƙofar Ya tsaya tare da kai hannu yayi knocking kofar kusan sau uku bata buɗe ba, Har ya fara tunanin ko bacci tayi ne sai kuma Yajiyo mutsu mutsunta ta cikin ɗakin.
A hankali ta turo ƙofar ɗakin, tare da leƙo da kanta,
Ko da mahboob yai tozali da fuskarta sai da gabanshi ya faɗi ganin yadda ta kumbura suntum, idanuwanta sun kaɗa jawur, daga gani kukan take cikin yi
In a calm voice Ya furta"ina fata ban katse maki baccin ki ba"
Muryarta adisashe tace"ban kaiga Yin baccin ba,"
Jinjina kai yayi"Uncle ne yace in kira ki, su na a falo shi da su mamie da abie"
Shiru tayi jimmm kamar bazata motsa ba, har saida ya maimaita mata maganar tukunna tace Toh, ka jirani mu tafi atare"
"Okey"
Maida ƙofa tayi ta rufe ta, badajimawa ba sai gata ta fito sanye da doguwar riga, ta yafa mayafi akanta,
Jin ta ruƙo hannun shi acikin nata ne yasa shi saurin kallonta, sam hankalinta ba akwance Yake ba, bai yi yunƙurin raba hannun shi daga nata ba, A haka suka nufi falon, sai da suka kusa isa yayi saurin zame hannun shi daga nata, Takun tafiyarsu ne Yaja hankalinsu mami ga dubansu
Cikin girmamawa Ana ta gaishe da su, tare da samun wuri gefen Aneelerh ta zauna tana faman jan numfashi, bayan mahboob Ya zauna.
Abie dake kallon Ana Ya soma Magana a tsanake
"Inaso ki natsu ki saurare ni," jinjina mashi kai tai alamar toh
"Ki ɗauka tamkar mahaifanki ne suke yi maki magana, kada ki ji shakkun faɗa mana abun da ke damunki, saboda mu kaɗai ne makusantanki a yanzu, Haƙƙinmu ne mu kula da rayuwarki, Idan wani abu ya same ki ba zamu ji daɗi ba" wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta, haƙiƙa kalaman abie sun yi tasiri a zuciyarta.
Uncle ɗan Iya ya ɗaura da cewa"banji daɗin abun da Ummi ta fada min ba, baki kyauta mana ba, ashe baki ɗauke mu yarda muka ɗauke ki ba, meyasa zaki zauna abu na damunki ki gaza gaya ma kowa? Meye amfanin 6oye mana eye"? Muryarshi da faɗa yake yi mata magana, alamar ranshi ya 6aci.
Sunnar dakai ƙasa Ana tayi yayin da idanunta ke akan Yatsun hannayenta
"Meke damun ki ne, inaso ki faɗi mini gaskiya"? Ya jefa mata tambayar, Su Aneelerh da su mami sun natsu suna kallon ta.
Numfashi taja tare da sauke shi A hankali ta furta"Idan na 6ata maku rai, dan Allah ku yafe ni, Aunty Aneelerh, mami, ummi, Zahra, Mahboob, abie, uncle, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku, duk da kasancewata yar aiki agidan nan, Sannan ba musulma ba amma kun daukeni tamkar jinin ku, ko dan saboda nuna damuwar da ku ka yi akaina zan fada maku gaskiyar abun da ke damuna...." ta faɗa tana mai ƙanƙan da kanta, gaba ɗaya duk sun ƙagara da suji meke damunta, musamman Mahboob Ya kasa ɗauke idanunsa daga kan fuskarta, wani irin tsantsar sonta da ƙaunarta yake ji, ga matsanancin tausayinta dake addabar zuciyarsa.
"Cikin kwanakin nan, Ina yawan yin mugayen mafarkai, waɗanda suke neman haukata ni, bansan meyasa hakan yake faruwa dani ba, idanuwana suna gane min abunda yafi ƙarfin gani na wanda silar hakan yasa nafara zaucewa, ni gani nake ma kamar mutuwa zanyi..... " muryarta na rawa ta ƙare maganar nan take ta fashe da kuka mai sautin gaske, Hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba, Jikin kowannansu yayi sanyi
"Kiyi shiru, Kukan Ya isa haka, Ki faɗa mana me kike gani a cikin mafarkin naki"! Uncle ɗan Iya ne yai maganar
Cikin shessheƙar kuka tace"wallahi duk yadda zanyi maku bayani ba lallai ku fahimce ni ba, ni kaɗai nasan halin da nake aciki, ni kaɗai nasan bala'en da nake gani, Ba tun yanzu ba, tun ina ƙaramata idan nayi mafarki mummuna yana zama dagaske, hatta rasuwar iyayenmu saida nafara yin mafarkin zasu yi hatsarin mota, sai gashi ya tabbata, uncle ɗina ma ni nayi mafarkin mutuwarsa kuma ya tabbata, da wuya inyi mafarki mummuna bai zamto gaske ba, ni damuwata mutanan da nake a tare da su bana son wani abu ya sami wani daga cikin ku...." tashin hankalin da ba'a saka mashi date, A matuƙar ruɗe Zahra take kallon Aneeleerh, Ummi ta kalli Mamie, Idanuwansu azare, mahboob kuwa kusan suman zaune yayi.
Shiru tayi Tana faman yin shessheƙar kuka,
Abie dake kallonta, nazarin maganarta yakeyi, yaso ace musulmace ita, kodan ya bata shawarar ta runƙa yawaita yin azhkar, da sauran addu'o'in neman tsari.
Tsawon lokaci falon yayi tsit, babu mai magana acikinsu, sai kallon kallo da suke jefawa junansu.
Muryar Uncle ɗan Iya ce ta katse Shirun nasu
"Ki daina sanya damuwa aranki, Mafarki ba gaskiya bane, shaidan ne yake assasashi, Ki yawaita yin addu'a, muma kuma zamu tayaki, Allah shi yake tsare bawansa, in sha Allah babu abun da zai same ki, damu kanmu,"
Ajiyar zuciya ta sauke, Cikin sanyin murya tace"in sha Allah uncle, zanyi hakan"
"Aneelerh, Idan zata kwanta bacci ki rakata dakinta, Ki yi mata addu'a," Ya fada yana duban Aneeleerh, Cikin girmamawa Ta amsa mashi da toh,
Kwantar mata da hankali suka cigaba dayi, Kowa sai da ya sanya bakin shi wurin Lallashinta da bata baki, Har saida suka tabbatar Ta samu saukin damuwarta tukunna mamie tace"daga yau kada ki sake ware kanki a daki! Kina jina ko"? Daga mata kai tayi toh
"Kidaina kuntata kanki adaki, ki dinga fitowa waje wurin su Aneelerh Kuna yin fira, hakan zai ɗebe maki kewa don na fahimci hada kaɗaici ke damun ki" jinjina kai ana tayi alamar toh.
Gyaran murya abie yai tare da cewa"Idan kina buƙatar wani abu, Ki fadama Aneelerh ko zahra, su sanar dani in sha Allah zamuyi maki shi, kada kiji komai ki dauka tamkar Iyayenki ne" wannan maganar da abie Ya furta mata ba karamin ta6a zuciyarta yayi ba, nan take ta fashe masu da kuka mai tsuma zuciya, sautin muryarta dakyar yake fita wurin yi masu godiya.
"Ku tashi ku rakata daki ta kwanta ta huta" Ummi ce tayi maganar tana nuna su zahra, ruƙo hannun Ana Aneeleerh tayi atare suka miƙe, Zahra tabi bayansu, Har cikin dakinta suka kaita, Bayan ta kwanta Aneelerh da zahra sukayi mata addu'o'i, Kafin daga bisani suka yi mata sallama, Kamar karsu barota haka suke ji, bayan sun fito daga dakin sun kulle mata kofar, zahra ta kalli Aneelerh
"Nifa tsoro yakamani aunty na, tun da naji Ana tace mafarkinta yana zama gaskiya, wallahi bana so wani abu ya samu ɗaya daga cikin mu"
Ita kanta Aneelerh hankalinta ba akwance yake ba, zuciyarta taki Aminta da kalaman ana, sai dai tayi kokarin danne damuwarta wurin kwantar ma zara da hankalin ta
"Zahra kin riga kin sani, mafarki ba gaskiya bane, Ni ko kadan hankalina bai tashi ba, kema kuma inaso ki kwantar da hankalinki, In sha Allah babu abun zai faru, face alkhairi"
Cikin sanyin murya zahra tace"Allah Yasa" Ta fada a yayin da suke shiga falon, komawa sukayi saman carpet suka zauna kowa zuciyarsa da fargaban maganar Ana.
Idan muka koma 6angaren su Ummin america tun bayan kammala sallar magbrib, tayi wanka ta shirya cikin Baƙar jallabiya, tayi rolling veil akanta, ta bi ko'ina na jikinta ta feshe da turare, bakomai take jira ba face kiran Boss man, tun da ya fada mata yana son magana da ita gaba daya ta rasa sukuni ta kosa taji me ya ke son faɗa mata, tana cikin yin safa da marwa a room dinta, wayarta tayi ringing a hazarce tayi picking call din, muryar boss ce ta isar mata da sakon ta same shi a down, jiki na rawa ta fito daga dakin ta sauko down stairs babu kowa a falon, duk suna a dakunansu
A falo ta same shi tsaye cikin shiga ta jallabiya, ya goya hannayensa akan kirjinsa, fuskarsa a sanye da face mask.
Da fara'a ta nufe shi batare da 6ata lokaci ba, suka jera a tare suka nufi swimming area din gidan, ko'ina ka kalla hasken fitilun lantarki ne tamkar da rana.
"ina sauraron ka Yalla6ai, tun da muka fito kayi shiru baka ce komai ba" ummi ce ta fada tana kallon Taj dake a gefenta.
"ga dukkan alamu Kin ƙagara da kiji dalilin kiran da nayi maki"
Jinjina mashi kai tayi alamar Eh, A yayin da suke zama saman kujerun dake a bakin pool din masu kyan gaske, suna fuskantar Junansu.
"Nasan zakiyi mamaki idan nace maki chief ne Ya bada Sako A fada maki"
A ruɗe tayi mashi farfari da idanunta cikin kagara ta furta"A message from the chief for me? Does he know about me? So what did he say?
Calmly Boss Ya furta"Yeah Yasan da zaman ki fiye da tunaninki, chief da kike gani baya zama wuri ɗaya da mutumin da baisan tarihin rayuwarsa ba," Wani irin bugu kirjinta yayi mata cike da fargaba ta furta.
"I don't understand what you mean! Chief ya san komai dangane da rayuwana! How is that possible?"
Dariya boss yayi ganin yadda ta shiga ruɗani
"Ki kwantar da hankalin ki Ummi, Amsarki tana atare dani, ki natsu ki saurari me zan fada maki" fuskarta a yamutse ta amsa mashi da toh.
Numfasawa yayi kafin Yaci gaba da fadin"sakon da chief Yace A fada maki shi ne, Gobe Idan Allah ya kaimu, zamu fita tare da Yaran nan zuwa cikin estate din su, muna so su halarci Farewell dinner din Uncle ɗinsa Hateem, amma fa bama so kowa yasan da wannan zancen! Zuwan bazata zamuyi tare da su, ke kuma abun da muke so daga gare ki, ki yi kokarin shirya mana su.... " kafin Ya kare Maganar tace"wai kana nufin prime minister Hateem na canada ne za'ayiwa dinner din? ɗaga mata gira yai alamar eh, but amma meyasa naji kace zuwan bazata za'ayi da yaran"? Ta faɗa tana mai neman ƙarin bayani.
Bai 6oye mata komai ba, dangane da budurin da aka sha lokacin da Danish ya rikiɗa, naƙin amincewa da zaman su a family din"
Jikinta yai sanyi"Allah sarki, ashe abun da ya faru kenan, ko da yake dama zaiyi wuya su yarda da su, ni kaina lokacin daya rikiɗa ba ƙaramin firgita nayi ba, saboda abu ne da ban ta6a gani ba, toh su kansu abun da zai sa su ƙi yarda da zamansu kenan, bayan haka hukuncin da shi baba obie ya yanke na raba alaƙar prime minister hateem da danish yayi dai dai, a fahimta na yayi hakan saboda gudun kada ɗansa ya cutu.... " jinjina kai taj yai alamar gamsuwa da bayanin ta, kafin wani ya qara magana a cikin su, sai ga jami'in isod Ya fito daga ƙofar falo, hannun shi ruƙe da plate mai ɗauke da mugs biyu na coffee, akan table din dake a tsakatsakiyarsu ya ajiye plate din kafin yabar wurin
Tura mata mug ɗaya taj yayi"kisha, ni nasa a kawo mana dan muji dadin tattaunawa' murmushi tayi har cikin ranta taji dadin karamcinsa, A hankali ta ɗauki mug din ta soma kur6ar coffee din, shima ya dauki nasa yana sha, bayan ta tsagaita da sha ne taci gaba da magana "kowani bawa da irin tashi jarabtar, Idan kaji na wani kai naka ba komai ba, shiyasa a koda yaushe akeson bawa ya zamanto mai hakuri dakai zuciya nesa, haƙiƙa ina tausayin wadannan bayin Allah, duk da ban kaiga jin tarihin rayuwarsu ba... ' murmushi taj ya ɗanyi tare da cewa"kada ki damu, nan badajimawa ba zaki ji tarihin rayuwarsu, In sha Allah"
Gyaɗa kai tayi "A ina za'ayi dinner din sannan ƙarfe nawa ne zasu je can din"?
"A cikin Estate din nan, Bayan sallar la'asar"
Shiru tayi alamar tana nazarin wani abu, yayin da yake binta da kallo.
"Menene dress code din da za'a sanya a wurin dinner din"? ta tambaya tana kallon fuskarsa.
"abaya matan za su sanya, A cikin suturunsu mun sanya masu abaya na larabawa kala kala, A ciki za'a daukar masu masu kyau na mutunci, sannan bama son suyi shigar da zata baiyana sumar kansu, a rufe masu ko'ina na jikin su.
Gyaɗa kai tayi"okey, in sha Allah amma baza'ay masu make up ba"?
"Duk kyan da Allah yayi masu"? Ya faɗa da murmushi kan fuskanshi, Itama ummin murmushin takeyi"masu kyaun ma su na yin make up, ko da yake naji ka ce arufe masu ko'ina na jikin su, ba buƙatar yin make up, ɗaga mata gira yai alamar eh.
"Tare da ni zaku tafi ne"?
"Idan kina ra'ayin zuwa"
Girgiza kai tayi alamar a'a
"Meyasa"?
"Nafi so kubarni a gida, nasan Su Unaisah zasu bani labari, har ma su daukar min video na dinner din in gani nima"
"Ban yarda ba, yakamata kema ki shirya mu tafi tare dake, zaki ji dadin shiga cikin family ɗin Obinna," jim ta ɗanyi tana wani tunani aranta.
"Kinyi shiru baki ce komai ba"
Numfasawa tayi tare da cewa"ka yi hakuri amma zuwana ba lallai ya zama alkhairi agare ni da ku kan ku ba, bana so na 6ata maku shagalin ku, nasan ka fahimce ni" jim ya ɗanyi yana jujjuya mug din hannunsa, tabbas ya fahimci me take nufi,shi kanshi yasan ba lallai chief Ya amince su tafi da ita ba, yadai ɗan bugi cikinta ne don yaji idan tana son zuwa sai kuma akaci sa'a bata ra'ayi.
"Alfarmar da nake nema a wurin ku, dan Allah ku barni in fita gobe, Inaso zan ziyarci gidan ƙawata dake aure anan abuja"
"Bani da wannan hurumin, Amma in sha Allah zanyi kokarin nema maki alfarma wurin chief, but inaso kisan da sani duk inda zaki je jami'in mu ne zai kai ki," har cikin ranta taji dadin maganarsa.
"Idan akwai abun da kike buƙata ki faɗa min" cikin kulawa yayi mata maganar yana dubanta.
"Dan Allah ka fadamin shin dagaske ne chief Yasan komai dangane da rayuwana"? Ta fada cike da fargaba.
Jim ya ɗanyi yana dubanta kafin Yace" "I'll give you an assignment. If you can find the answer, then I'll tell you what you want to hear," A ƙagare ta ke kallon shi, A hankali Ya sanya yatsun hannayen shi tare da zame mask din fuskarshi.
Wani irin kallo ummi ta soma binshi da shi, Yau ne karo na farko da ta fara Yin tozali da fuskar Boss man, bata ta6a tsammanin Yana da kyawun fuska har haka ba.
"Dama haka kake da kyau"? da alamun mamaki ta furta maganar, Murmushin gefen fuska Ya sakar mata har dimple dinsa ya lotsa, nan take ta soma kokarin tariyo inda tasan fuskarshi sai dai kash takasa tunawa amma tabbas tana ji aranta ta ta6a sanin shi ko kuma wani ne me kama da shi.
"Ina da aure, Ki daina kallona, matana tana da kishi, zata iya yin komai akaina" da zolaya taj yayi maganar.
Ummi tace"tasan tana da kishi meyasa ta auri namiji mai kyan sura? Ay kamata yayi ta auri mummuna, ni fa bazan 6oye maka ba, ka jima kana bani mamaki kai da abokin aikin ka big guy da chief din ku, tun da nataso rayuwata da wuya a samu namijin zan gifta awuri batare daya bi ni da kallo ba harma ya neme ni, amma ku sam babu wannan tunanin aranku, zuciyarki a tsarkake take, hakan ba karamin daure min kai yake yi ba, shi chief mace ko kallo ma bata ishe shi ba, wata irin dakakkar zuciya ce da shi.
Ƙayataccen Murmushi Taj Ya sakar mata batare daya furta mata ƙala ba
"Wallahi nasan ka, sai dai bazan Iya tuna a ina nasan ka ba, ni hatta muryarka na jima ina son tuna ina na son ta," still face dinsa da murmushi Yake dubanta.
"Amma meyasa kake yi min kama da Unaisah? Ko dai idanuwana ne suke nuna min badai dai ba"?
"Ba laifin idanuwanki bane, Unaisah Ƴata ce, Jini na ce, Ni mahaifinta ne, asalin sunana Tajuddeeen,"
"I can't believe it, Unaisa fara ce zan iya sanyata a jinsin larabawa, kai kuma daga ganin ka hausa fulani ne"
"A salin sunana Zaheer Tajudeen, Zaheer sunan Mahaifina ne, Tajudden kuma sunana ne, Ki tambayi Unaisah menene full name dinta zata fada maki da bakinta, Ita kanta ayanzu haka batasan cewa Ni mahaifinta bane ƙaddara ce ta rabamu, sai gashi cikin ikon Allah mun sake haɗuwa," murmushi ummi tayi"Allah sarki, Na tayaka Murna, amma mahaifiyarta wani jinsi ce"?
"Hausa Arab ce" Dariya Ummi tayi cikin raha ta furta"hausa arab! Bayan hausa fulani har Hausa rab ke da akwai, ban ta6a ji ba sai akanka"
"Ina nufin Half cast ce, Mahaifinta hausa fulani ne, mahaifiyarta kuma Balarabi ce" gyaɗa kai tayi"masha Allah, shiyasa yarinyar taka takasance fara sol, Ga gashi tubarkalla amma tsakanin kai da mahaifiyarta halin wa ta ɗauko"? murmushi yasaki yana dubanta yace"meyasa kika tambaye ni"?
"Unaisah tana da faɗa, daga ka kalli idanunta zaka shaidan hakan, ga wayau da kaifin basiri Allah Ya bata fiye da sauran ƴan uwanta" haƙiƙa Yaji daɗin Yabon da ummi tayi mata,
"Haka mutane suke cewa, shiyasa nima nake alfahari da ita, Inason Unaisah, fiye da yadda nakeson kaina, A halin Yanzu bani da tamkarta a duniyarnan, Itace ta rage min wadda nake gani naji sanyi araina, silar unaisah nasamu alheri da dama wadanda idan na fada maki su zakiyi mamaki, ɗaya daga ciki Unaisah itace silar haɗuwana da Chief" da mamaki Ummi ta ɗan zaro mashi sexy idanunta haɗi da buɗe baki, Jinjina mata kai yayi" Murmushin gefen fuska tasaki"Ina ƙara tayaka murna, Yarinyarka Jarinka ce, Allah Ya albarkaci Rayuwarta" amsa mata yayi ameen, daga ita har shi sun ji daɗin zaman firar da su kayi, Haƙiƙa taj ya ɗebe mata kewar kaɗaicin dake damunta, ta ƙara ganin mutuncinsa da ƙimarsa a idanunta, Sai dai tarasa gane meyasa take jin kamar ta ta6a sanin shi? Musamman daya faɗa mata sunan shi sai yawo yake mata akai.
Ni'imtacciyar Iskar dake kaɗawa ta ƙara masu ƙaimin firar ta su, kafin wani lokaci taj yace da ita"kada na cika ki da surutu, ko zaki koma ciki ne"? Fuskarta da fara'a tace"no ko kusa, ni baka takuramin ba, saima ɗebe min kewar da ka yi, naji dadi fiye da tunanin...... " bata ƙarasa maganarba sakamakon sautin dirar motar daya ratsa kunnuwanta, kusan atare suka juyo suna duban motar.
Bayan sojan dake driving din motar yayi parking, Ya fito Ya zagaya ya buɗe mashi murfin back seat dinta, Ƙafarshi kaɗai ya zuro waje Gaban ummi ya faɗi rasss, jikinta ya soma kakarwa, A hankali ya ƙarasa fitowa daga cikin motar, kamar kullum cikin shiga ta malamai magadan annabawa, bai ɗaura idanunsa akan kowa ba sai akan Ummin america, a sukwane ta miƙe tana gyara mayafin da tayi rolling, taj kuwa fuskarshi dauke da murmushi ya nufi sheikh imam yana fadin"Ya sheikh Barka da zuwa tun ɗazu muke ta sa ran ganin ka" Martanin murmushin Shiekh Imam ya mayar masa a yayin da yake kokarin kau da idanunsa daga na ummi ya mayar da su akan fuskar taj, musabaha su ka yi shikeh imam yace"Ay min afwa, ban samu damar zuwa duba mara lafiya na ba, wallahi yana araina da shi na wuni, wani uziri ne ya ruƙe ni"
Jiki na rawa Ummi ta juya ta nufi ƙofar shiga falo, Duk don kada su gaisa da sheikh imam, har ta kusa kaiwa ga ƙofar muryar taj ya ratsa kunnanta
"Ummi, ki zo mana ku gaisa da sheikh imam" tamkar an dasa mata aya ta tsaya cak, tana mai mayar da numfashi, Har cikin ranta bata ji daɗin dakatar da itan da yayi ba, sai dai bata jin zata iya watsa mashi ƙasa a ido, musamman yau daya faranta mata rai.
Tunkafin ta juya ta soma jin takun tafiyarsu bayanta, jiki asanyaye ta waiwayo tana dubansu, lokacin da suka ƙaraso da sauri ta sunnar da kanta ƙasa, muryarta na rawa ta furta"sannu da zuwa"
Cikin sanyin murya ya amsa mata da yawwa
Taj dake dubansu a fakaice yace"sheikh bari na gabatar maka da ummi,"jinjina mashi kai yai alamar toh
"Ummi Tamkar uwa take a wurin yaran da muke raino, ita ce take kula da su"
Fuskar sheikh babu annuri ya furta"anya kuwa sunyi dacen uwa"? Har sai da gaban ummi ya fadi rass jin abun da yace, hatta shi kanshi taj aruɗe ya kalli fuskar shaikh imam
*Daga alkalamin Boss Bature💋✊✍️*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 10 Complete
by
Novels Elite Admin
May 25, 2024
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القدر💋✊🔥
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Har sai da gaban ummi ya fadi rass jin abun da yace, hatta shi kanshi taj aruɗe ya kalli fuskar shaikh imam.
"Ya sheikh ko zan iya sanin dalilin da ya sa ka ce haka? Acewar Taj
Sheikh imam yace "Tun da nake zuwa gidan nan ban ta6a ganin ta taka zuwa ɗakin yaron nan ba, domin duba lafiyarshi, bansani ba ko tana shiga bayan bana nan amma raina na bani tamkar bata zuwa, a matsayinta na maruƙiyarsu yakamata ace tafi kowa bashi kyakkyawar kulawa ko da kuwa addu'a ne take zuwa tana yi mashi akai akai" tun da sheikh imam ya fara kora jawabi hankalin ta ya kwanta jikinta yai sanyi laƙwas.
"sheikh maganarka gaskiya ne, ummi baki kyautawa, kinga har sheikh imam ya fahimci baki zuwa duba lafiyarki ɗan ki" ya faɗa yana kallon ta, murmushin gefen fuska ta saki, cikin sanyayyar murta tace "nagode sheikh da tunasarwa, na gane kuskure na kuma in sha Allah daga yanzu zan dinga zuwa duba shi'
"Masha Allah, yanzu naji magana, bismillah malama ummi mu shiga ciki, kiyi mashi addu'a in gani" ta fahimci sheikh imam kamar ya gano wayanta nason ta gudu, shiyasa yake kokarin ruke ta.
Babu yadda ta iya adole ta amince suka nufi cikin gidan atare tana mai jin wani irin sanyi aranta.
Bayan shigarsu ɗakin, kamar yarda suka barshi da asuba haka su ka taras da shi, babu abun da ya canza yana a kwance rabin jikin shi lullu6e da bargo, sumar kanshi an ɗaure mashi ita, ta kara tsayi har kusan mid back din sa, ga wani irin pure white da skin dinsa tayi har wani glowing ta ke yi, jikin ummi ba ƙaramin sanyi yayi ba, kasancewar yau ne rana ta farko da ta fara shigowa dakin danish, bata ta6a tsammanin jikin yayi tsauri har haka ba, kamar matacce babu abun da ke motsi a jikin sa.
Tsananin tasauyin shi ne ya kama ta aranta ta ayyana wato duk kyan mutun bai isa ya hana kanshi ciwo ko mutuwa ba, jiki asanyaye ta matsa bakin gadon, sheikh imam da taj suna daga tsaye suna kallon shi, yanayin fuskokinsu ya nuna damuwa.
Girgiza kai sheikh yayi cikin jimami ya furta"Ya Allah ga bawan ka nan, kafi mu sanin a wani hali yake a ciki, ya Allah ka sauƙaƙa mashi abun da ke damun shi, Ya Allah ka raba shi da shaidanun dake azabtar da rayuwar sa... cikin harshen larabci yaci gaba da karanto addu'o'i yana tottofa mashi, rashin lafiyar danish ba ƙaramin ɗaga mashi hankali yai ba, damuwarshi kada yaƙi tashi, duk da yayi imanin addu'o'in da yayi mashi, da sallar daren da yake yi mashi basu tafi hakanan ba, sai dai idan lokacin shi ne yayi.
Cikin rauni na murya ummi ta furta"baya iya tashi"?
Taj da jikin shi ya gama mutuwa laƙwas, Muryarshi babu karsashi ya bata amsa da cewa "baya iya yin komai, sai dai ayi mashi, ta hanya daya muke gane ya farka daga bacci, yatsun hannayensa dana ƙafafuwansa suke kerma"
Jinjina kai ummi tayi, tare da kau da idanunta daga kallon Taj ta dubi sheikh imam adai dai lokacin shima ya dawo da dubanshi gare ta, haɗa ido su ka yi da juna duk saita rasa sukuninta kamar wata mara gaskiya.
"Addu'arki yake buƙata a matsayinki na mahaifiyarsa" har sai da taji gabanta ya faɗi jin sheikh imam ya furta a matsayinta na mahaifiyarsa.
Ɗauke idanunta tayi daga kanshi, kafin ta dai daita nutsuwarta, ta ɗan ɗukar da kanta saitin inda Danish yake a kwance, cikin harshen larabci ta soma karanto addu'oi tana tottofa mashi, bayan ta gama ne ta ɗago tare da kallon fuskar sheikh imam, tayi mamakin murmushin da ta gani ɗauke akan fuskarshi, sunnar da kanta tayi ƙasa saboda kwarjinin da yayi mata
"Chief yana nan ko ya fita ne"? ya tambaya yana kallon Taj.
"Bayanan tun ɗazu da rana ya fita, yana a villa wurin daddynsa, Idan kana buƙatar yin magana zan iya kira maka shi"
Girgiza kai sheikh imam yayi"a'a, dama na tambaya ne in ji ko yana nan"
"yanzu me yakamata mu yi sheikh"?
"Naga har yanzu bai farka daga bacci ba, nasan dole akwai yunwa atattare da shi sannan yana buƙatar wanka, amma kada a tada shi idan har bashi ya farka da kan shi ba" amsa mashi taj yai da toh.
"Ina sauran yaran su ke ne? Sun yi mashi addu'o'in da suka sa6a yi"? ya tambaya yana kallon Man.
"tun da asuba rabon su da dakin, bansani ba ko sun ƙara leƙowa"
"Inason ganin su gaba ɗayan su yanzu"
da sauri ummi ta ce"bari naje na kira su" dama neman hanyar da zata bar dakin take yi.
Bayan fitarta daga ɗakin sheikh Imam ya ɗan haura saman gadon, tafin hannunsa ya ɗaura saman forehead din danish, ya fara jera addu'o'i na musamman yana tofe mashi jiki, tsawon lokacin kafin yacire tafin hannun ya maidashi kan saitin zuciyarshi, yaci gaba da yi mashi kira'ar alkur'ani mai girma, Taj dake kallon sheikh imam dake janyo kira'a ba karamin nutsuwa yaji ba a cikin zuciyarsa.
Tun da ummi ta fito, a bakin kofar ɗakin ta la6e tana sauraron kira'ar sheikh imam mai ratsa zuciya, wasu irin zafafan hawayene suka cika mata idanunta, Jikinta har kerma yake yi, ga dukkan alamu akwai wani abu da yai silar jefa ta yanayin da take a ciki.
Runtse idanunta tayi sosai, jin kukan na shirin kubce matane yasa tai saurin toshe bakinta da tafin hannunta, muryar ta na rawa ta furta
"uhibuk kathiran ya 'abi har yanzu kai mahaifina ne ba abun da ya canza..."
Duk waɗannan sambatun da take yi, A kunnan Unaisah, wadda fitowarta kenan daga dakin su ta kamo hanyar zuwa dakin Danish don ta duba jikin shi, karaf taci karo da ummi ta runtse idanunta tana matsar kwalla.
Muryarta da ruɗani ta furta"Aunty Ummi!"
Furgigit ummi tay saurin buɗe idanunta wadanda suke ajike sharkaf sun kaɗa jawur
Ganin unaisah yasa tai saurin sanya tafukan hannayenta ta share hawayen dake karanyo mata
"Aunty Ummi, yaushe kika shigo? Ina boss? Meyasa ki zubar da hawayen ki? Wani abu ya faru da danish dina ne..." hankalin ta atashe ta fada
Muryar ummi adisashe ta furta"bamu jima da shigowa ba, ni da boss tare da sheikh imam... " ta fada muryarta na ɗan rawa
"kada ki damu ba wani abu bane ya faru da ɗan uwanku, kawai naji tausayin shine ya kama ni, bansan ciwon nashi yakai har haka ba, naji haushin kaina da ban ta6a leƙowa domin duba lafiyar shi ba, yau da naganshi jikina yayi sanyi shiyasa kika ganni awaje ina sharar hawaye... ' wannan maganar da ummi ta furta tayi matuƙar karya ma Unaisah zuciya, idanunta tuni sun cicciko tab da kwalla, ganin hakan yasa ummi tayi saurin furta"dan Allah kada ki yi kuka, addu'armu yake buƙata A halin Yanzu"
duƙar dakai ƙasa unaisah tayi, jiki asanyaye tace"bari na shiga in duba shi"
ta faɗa tare da buɗe kofar tasa kai ta shige ciki, bayan shigarta Ummi ta sauko down stairs don ta kira su Haris kamar yadda sheikh Ya buƙata.
Kafin wani lokaci gaba ɗayansu sun hallara a dakin danish, kowannansu ka kalla babu walwala, tsantsar damuwace akan fuskokin su.
Ɗaya bayan ɗaya sheikh imam yake dubansu har sun yi shirin kwanciya bacci, kowannansu yana asanya da sleeping dress dinsa, kafin ya soma magana cikin sanyayyar muryarshi
"Ku naso ɗan uwanku Ya samu lafiya"! har suna haɗa baki wurin furta eh
"To ku dage da yi mashi addu'a, Ita yake buƙata daga gare ku, nasan kunayi to ku ƙara abisa wadda ku ke yi mashi, Kunga har yanzu mun rasa gane yanayin da yake aciki, yau jikin shi yayi tsauri fiye da kullum, tun safe babu alamun zai farka daga wannan dogon baccin da yake yi, shi kadai yasan me yake ji a jikin shi, addu'a da kuke gani takobin mumine ce da itane zamu yaƙi shaidanun dake sarrafa shi, kullum suna aiki akanshi, safe da dare, why mu bazamu iya tsayawa tsayin daka wurin ganin mun ruguza shirin su ba! Mu da ma mu kayi imani da Allah balle su da su ke mushirikai.... ' tun da sheikh imam ya fara yi masu magana suka nutsu suna sauraron shi, sun kewaye gadon da danish yake a kwance, kokari yakeyi ya tunzurasu donsu harzuƙa su kuma dage damtse wurin yi mashi addu'a, duk maganganun da sheikh imam keyi a kunan ummi da ke a la6e bakin ƙofar dakin tana sauraronsu.
Sautin shessheƙar kukan unaisah ne ya soma karaɗe dakin, kamar jira sukeyi tafara kuka, Jemimah da azeeza suka fashe da kuka, suma sauran kowannansu kwalla ce a idanunsa.
"Ba kuka yakamata kuyi mashi ba, kamar yarda na fada maku addu'arku yake buƙata, A cikin ku akwai wanda ke tashi yin sallar dare domin yi mashi addu'a akan Allah ya bashi lafiya"?
Shiru su ka yi, saboda basu da amsar da zasu bashi, unaisah dake faman zubda kwalla muryarta a raunace ta furta"ina yi mashi, amma ba kullum ba, wani lokacin kona kwanta da niyar tashi inyi mashi bana farkawa, saboda bani da me tada ni"
"Ni bansan yadda akeyi ba, da ace na sani har bacci zan iya hana kaina don inyi mashi addu'a, saboda danish yayi mana abin da bazamu ta6a mantawa ba, ya cancanci mu sadaukar da komai akanshi" cikin sanyin murya batool ta ƙare maganar, taj da sheikh iman sun nutsu suna sauraronsu haɗi da kallon la66an duk wanda yayi magana a cikin su.
Cikin shessheƙar kuka jemimah tace"wallahi nima zanyi ma shi, saboda bana so Danish ɗin mu ya mutu kamar yadda na rasa Majnoon ɗina...." wannan maganar ta jemimah taja hankalin sheikh imam da taj sosai akanta, ta dage sai ku ka ta ke yi, kumatunta har sun yi ja, ruko hannunta sheikh imam yai tare da lallashin ta akan ta daina ku ka.
Hanna dake matsar kwalla ta ce"In sha Allah babu abun da zai same shi, zamu yi iyakar bakin kokarin mu don ganin mun ceto rayuwar ɗan uwan mu da iznin Allah..." daƙyar ta ƙare maganar
"In sha Allah daga daren yau zan fara yin mashi nafilfili, ni saima naji haushin kaina, bamu kyauta ba, har zamu iya dariya muyi bacci, bayan ɗan uwanmu yana akwance rai hannun Allah, komai sai anyi mashi, mutumin daya sadaukar da farin cikin shi akanmu? Ya hana idonshi bacci saboda ya bamu kariya, sai mune zamu gaza hana idanun mu bacci anya kuwa mun kyautawa kanmu"? gaba ɗaya suka fashe da kuka mai tsuma zuciya, haƙika maganar Haris Ta ta6a zukatansu, hatta ummi dake jingine da kofar dakin sai da ta zubda kwalla duk da batasan takan tarihin rayuwarsu ba, amma ta hasko wani abu.
daga gefen gadon Danish sheikh Imam ya zauna jikinsa yayi sanyi lakwas, bai ta6a ƙaguwa da son jin labarin rayuwarsu ba irin yau.
Cikin sanyin murya taj yace"kada ku ɗaurama kanku alhakin laifin da bana ku ba, hana ido bacci ba shi ke nuni da kun damu dashi ba, saboda ku kanku bazaku samu kwarin gwiwar yi mashi addu'a ba muddin baku da kwanciyar hankali da nutsuwa, abun da yakamata, tun da dare yayi in za ku yi bacci ku kwanta da wuri, wuraren ƙarfe uku na dare zan kira unaisah awaya in tunasar da ita, in yaso ita sai ta tashe ku daga bacci ku tashi kuyi nafilfili ku kai kukan ku wurin Allah akan halin da ɗan uwa ku yake a ciki, in sha Allah zamuyi nasara"
Shawarar da boss man ya yanke masu tayi masu dadi.
"Mungode sosai, Allah yasaka maku da mafificin alkhairinsa, Allah ne kadai zai iya biyanku, " godiya suka shiga yi ma shiekh imam da boss man......
"Yakamata kuje ku kwanta, ku yi bacci kada a makara" amsa mashi su ka yi da toh, bayan sunyi ma sheikh imam sallama, Suka nufi hanyar fita daga dakin jin takun tafiyar sune yasa ummi tayi saurin nufar bedroom dinta tana shiga ta fada saman gadonta taci gaba da yin kuka tamkar ranta zai fita...
Unaisah taso ta samu damar ganin danish dakyau, amma saboda shiekh imam yasa takasa tsayawa, Idan har ba ita ta kashe mashi switch din dakinsa ba, ta kuma lullu6e shi da bargo ba, to kuwa hankalin ta bazai kwanta ba, tunani zatai tayi kamar ba'a lullu6e shi.
Ɗaya bayan ɗaya kowannansu ya nufi room dinsa bayan sunyi sallama wa junansu, zuciyoyin su cike da zullumin halin da danish yake a ciki.
Basu bar dakin shi ba, sai da Taj Ya lullu6e shi dukanshi da bargo, ya kuma kashe switch din kafin Suka fito tare da sheikh imam, har bakin motar da aka kawo shi ya raka shi, sun ɗan juma a jikin motar suna tattaunawa duk dai akan halin da danish yake a ciki ne, har ƙara jaddada mashi sheikh yayi akan su dinga dubawa akai akai ko Allah zaisa ya farka daga baccin, kafin daga bisani su ka yi sallama.
_______________________Boss Bature✍️
💋CHIEF OWAIS💪
Aso Villa.
A yayin da yake a kwance saman katafaren gadon shi dake a Villa tsantsaran gaske, ya lullu6e half body dinsa da lallausan duvet dinsa, cikin kwanciyar hankali da nutsuwa yake fitar da numfashin sa, ga wani irin sanyin A.c daya ƙarama dakin nashi ni'ima, babu haske dakin sai na bedside lap ɗaya da aka bari a kunne...
sautin ringing ɗin wayarsa ne ya farkar shi, da wata irin kasala ya kai hannu ya lalubo wayar, A hankali yaɗan ware reddish eyes nasa masu dauke da bacci ya duba sunan mai kiran nashi, yayi mamakin ganin kiran prime minister Hateem, slowly ya dubi agogon bango ƙarfe wani abu na dare.
Ya ilahi ya faɗa a zuciyarsa kafin ya miƙe zaune ya ɗaga kiran ya ƙara a kunnansa
"Uncle... " iya abunda ya iya furtawa kenan.
On the other hand muryar prime minister ta karade kunnuwansa.
"I'm sorry na katse maka baccin ka, na tashi yin night prayers ne, shi ne na kiraka don inji awani hali yarona yake aciki, saboda mafarkinsa ne ya tada ni daga bacci" chief owais dake ta faman lumshe idanunsa, cikin yanayi na kasala ya furta"uncle saboda shi ka tada dani daga bacci"?
"I'm so sorry my son, bansan ya zanyi maka bayani ba"
Lumshe sexy eye dinsa yai kafin a hankali ya furta "Uncle, ka kwantar da hankalin ka, yanzu ni bana agidana, nazo Villa ne, amma in sha Allah gobe zan koma gidana da wuri saboda shi'
Har cikin ran prime minister yaji dadin maganar Owais
"Zullumi nakeyi, daga gobe shikenan bazan sanya shi a idanuwana ba, jibi da asuba jirginmu zai bar nigeria, gani nake kamar idan na tafi ba lallai na sake dawowa ba, balle har na sa ran ganawa da shi.... " dafe kai chief owais yayi da hannu ɗaya, Lamarin yafara kokarin rikata mashi lissafin kwalwarsa, aranshi ya ayyana anya kuwa Daddy Hateem bai fara zaucewa wa ba? ko dai ya samu matsalar kwalwa ne? Ko kuwa yafara ɗaga kwalba ne, Idan ba haka ba akan wani dalili zai ɗaga hankalin shi akan yaron da bai haɗa alaƙar komai da shi ba? Wannan wata irin ƙaunace?
Jin shiru chief owais bai furta mashi magana bane yasa shi cewa"naji kayi shiru son, ko ka koma baccin ne...
Slowly ya mayar da kanshi saman pillow,.
"Uncle, I'm confused..."
kafin ya ƙare maganar prime minister ya tari numfashin sa
"I'm confused too, Owais....nasan me ka ke tunani aranka, may be ma kana yi min kallon kamar nafara zaucewa, owais na dauki soyayyar yaron nan amatsayin jarabta daga Allah, ni dai kawai fatana ya zama alkhairi agare ni, dan Allah ka tayani da addu'a Allah ya bashi lafiya...
Lumshe ido chief owais yai, bakomai yake tariyowa ba face ranar da suka fara tozali da juna shi da danish suna a saman bene, suka jefa ma junansu kallon kallon, aranshi ya ayyana ba lallaima idan yaron ya dawo hayyacinsa ya kula prime minister ba saboda Yana da ilmin sanin halayyar ɗan adam, da ido kawai ya kalli danish ya fuskanci yana da wuyar sha'ani, yin mu'amala da shi ba abu ne mai sauƙi ba.
"In sha Allah zan tayaka da addu'a, ni dai fatana ka daina sanya damuwa aranka, ka kwanta ka yi bacci, muna da liyafa a gobe"
Yana iya jiyo sauke ajiyar zuciyar prime minister ta cikin wayarshi.
"Nagode da kulawarka agareni my son, Allah yayi maka albarka" amsa mashi yayi da ameen
Har zaiyi rejecting kiran muryarsa ta sake katse shi
"Pls kada ka koma bacci, ka tashi ka shiga toilet ka dauro alwala, kayi mashi nafila ko da raka'a biyu ce, Allah ya bashi lafiya"
Babu musu yace"In sha Allah zanyi" bayan sunyi sallama, chief owais yayi shiru yana tariyo kalaman Daddy hateem, shi kanshi yafara hasashen tabbas akwai wani 6oyayyan sirri dake a tattare da kaunar da uncle dinsa ke yima yaron Allah kadai yasan ko menene.
Jefar da wayar yayi saman gadon, kafin ya miƙe ya zura ƙafafuwansa ƙasa inda ya ajiye gucci slippers din sa, yunƙurawa yayi ya miƙe ya nufi switch din dakin ya kunna a hankali haske ya gauraye ko'ina, wato wani hamshaƙin bedroom ne, komai na cikinsa launin royal blue and white colour ne.
A gaban dressing mirror ya tsaya tare da ɗaura hannun shi ɗaya ya dafa mirror chair.
Wasu hadaddun Cashmere pajama ne a jikinsa riga da wando masu tafshi launin sky blue, sumar kanshi tasha gyara sai daukar ido take yi ga wani kamshi dake fita daga cikin ta, chief karshe ne a fagen haɗuwa.
Moving slowly ya nufi ƙofar toilet dinsa ya shiga daga ciki, alwala ya ɗauro ya fito fuskarsa da lemar ruwa ya nufi walk-in closet dinsa jim kadan ya fito sanye da jallabiya, ya hau kan darduma ya dai daita nutsuwarsa da kyakkyawar niya ya kabbara sallah.
A kalla yayi kusan raka'a goma sha takwas batare da gajiyawa ba, har sai da yaji kafafuwanshi sun soma rurruƙewa tukunna ya dakata, ya zauna yana jero addu'o'i duk dai akan danish yayi su kamar yarda Uncle hateem ya nemi alfarmar yayi mashi.
Bayan ya kammala komawa yayi saman bed nasa ya kwanta, tare da kai hannu ya ɗauki wayar shi, jim yayi yana mai mamakin ganin sakonta, a kalla sunfi wata biyar ko sallama basa yi ma juna, shiga cikin message din yayi, tare da karanta sakon da ya gani, ko kusa bai ji su a zuciyar shi ba, saboda kokwanton da yake yi, video din Ya kunna ya fara kallo, yana faman lumshe idanun shi, tayi mashi kyau yaji dadin kallon video din, almost 3 times yana maimaita kallon shi, kafin daga bisani ya fita daga chat din ya daura idanunshi kan hoton wallpaper din sa.
A tsanake yake kallon baby face dinta, ta zare idanunta a hoton daga ganin hoton screenshot din shi aka dauka, kuma anyi hoton ne batare da sanin ta ba.
Sam baya gajiya da kallon hoton, A hankali ya ɗaura soft pink lips dinsa saitin fuskar ya sumbace ta, kafin ya ɗaura hoton saman kirjinsa a haka bacci yai awon gaba da shi.
________________________✍️
Taƙi runtsawa ta addabi kowa ta hana su bacci saboda Jazz baizo ba, tace in har baizo ba to bazatayi bacci ba suma kuma bazasu yi ba, dakyar Salsabeel Ya shawo kanta Ya samu ya lalla6ata har ta ƙyale sauran ƴan uwanta suka kwanta a dakunansu, itama takwanta harfa ya kwanta da niyar ya runtsa can tsakar dare yajiyo bugun ƙofa, a firgice ya farka Yaje ya buɗe, Khadeeja ya gani tsaye ta ruƙe qugu tana faman kumbura mashi fuska tace Ina jazz din yazo? Agogo ya kalla sam yama kasa buɗe baki ya bata amsa, tace dama nasan baizo ba, ya manta dani, wlh Allah nima nayi fushi da shi.
Cikin kwantar da murya salsabeel yace"dan Allah kiyi hakuri kije ki kwanta bacci, dare ne yanzu, gobe in Allah yakaimu da safe zan kira maki jazz"
Maƙe mashi kafaɗa tayi alamar bazata kwanta ba, ganin zata 6ata mashi lokaci yasa shi ɗaure mata fuska ya daka mata tsawa tare da fadin"Zaki wuce kije ki kwanta ko saina yi ƙwallo dake" fashe wa tayi da kuka da gudu ta nufi falo ta zauna saman sofa tana kuka, ko tsoro bata ji ita kadai kamar aljanna" ko ta kanta baibi Yaja kofa Ya rufe Ya koma ya kwanta.
Sai da tayi kukan mai isarta, kafin Ta miƙe tana shafa ciki Alamar yunwa take ji, kaitsaye ta nufi Kitchen ta shiga ta soma kiciniyar kunna gas, tsabar rigima.
Mutsu mutsu tajiyo a kunnanta, hakan yasa ta dakata ta juya tana ƴan waige waige don ganin menene, Karaf idanunta suka sauka akan Ƙatoton 6eran dake tafiya saɗaf saɗaf Yana tunkarota baƙi wulik da shi, sam bata ji tsoron shi ba, Abun ka game ta6in hankali, Praying Fan ta ɗauko cikin sanɗa tabi bayan shi ta daddage ta kwaɗe shi da fan ɗin, ko shurawa baiyi ba ya sheƙa, Bindin shi ta ruƙo tana faman sakin nishi tace"Zaka ci ubanka, Kai ne 6arawon dake cinye mana sauran da muka rage a kitchen ko"? Ta faɗa tana leƙen idanun 6eran Yayi zuzuru dashi.
"Ba zaka yi magana ba? Baka da gaskiya bakin munafuki, kai ne kake gwigwiyar mana bready, Bari na kai ka Gaban Alƙali Ya salsabeel Ya kashe min kai har lahira"
Ta faɗa tare da fitowa da gudu ta nufi bedroom din salsabeel, Har Ya koma bacci, Yajiyo muryar khadeeja tana fadin"Ya salsabeel Ka buɗe min kofa na kama 6arawon dake cinye mana sauran abincin mu, gashi nan a hannuna, Ya salsabeel ka buɗe zai gudu'
Afirgice Ya farka har yana tuntube garin sauri, koda Ya buɗe ƙofar Miƙa mashi 6eran tayi
"Gashi ka kashe shi ko ka cire mashi hannayensa"
Fuskarshi a yamutse ya kalli 6eran da idanunsa masu dauke da bacci, sun kaɗa jawur da su, yayi mamakin da har ta iya kamo 6era, tun da suka fara zama gidan bai ta6a ganin gifcin 6era ba sai yau.
Muryarshi adisashe yace"khadeeja ba zaki barni inyi bacci ba? Ke baki runtsa ba nima kuma kin hana in runtsa, Meke damun ki ne"?
Ta6e mashi lips dinta tayi alamar zata fashe mashi da kuka
Da sauri yace"ya isa ni bance kimin kuka ba, Yanzu fada min ya kikeso ayi da 6eran nan da kika kama"
"Ka cire mashi hannuwa" gyada kai yayi tare da sanya hannu ya kar6i 6eran"ki jira ni yanzu zan dawo amsa mashi tayi da toh, fita yai daga dakin tana atsaye tana jiran shi, badajimawa ba ya dawo hannunsa babu 6eran
"Yana ina"?
"Na cire mashi hannuwa na yar" murmushi tasaki"mun hutu da masifa ko"? Ɗaga mata gira yai alamar eh
"Muje na rakaki daki kiyi bacci" maƙe mashi kafada tayi"Ni yunwa nake ji, kaje kitchen ka dafa min abinci"
Wahalallan kallo yabita dashi gaba ɗaya ta takurasa
"Shikenan muje" Ya fada tare da yin gaba tabi bayan shi suka shiga falo, ta zauna saman sofa.
Kitchen Ya shiga bawan Allah ga gajiyar bacci A haka Ya dafa mata indomie, Ya haɗo mata da water bottle, Ya shigo Da plate din Ya miƙa mata, gefen ta ya zauna don yasan koya koma daki indai batayi bacci ba to shima bazai runtsa ba.
Yana kallonta Har ta cinye taliyar ta kora da ruwa, kwanciya tayi saman sofa din ta daura kafafuwanta saman laps dinshi bai tanka mata ba, yasan rigima take nema, Cikin sa'a bacci yai awon gaba da ita, A hankali Ya zame ƙafafuwanta ya miƙe tare da ɗaukarta ya nufi upstairs da ita, a kan gado ya kwantar da ita, yabi da bargo ya lullu6e mata jikinta, kafin ya fito ya datse kofar dakin nata, cikin sauri ya nufi dakinsa don ya kwanta ya karasa baccin dabai isheshi ba, bayan shigarshi daki har ya kwanta ya soma tunanin ko me ya hana jazz zuwa? Tun safe yake jaraba kiran layin shi baya picking, har ta 6angaren danish ba a kira shi ba wunin yau, fatan shi Allah yasa lafiya da wannan tunanin bacci 6arawo ya ɗauke shi.
*💋BENAZIR❤*
Kwance take a saman darduma, tun bayan data kammala sallar Isha bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita, yayin da zeenatu take a can saman gado tana bacci.
Tana a nannaɗe cikin dogon hijab dinta, tayi nisa acikin baccin ta, Ba zato ba tsammani hasken fitilar bedroom ɗinta ya ɗauke ɗuff, wani iko na Allah ba wutar gidan bace ta samu matsala, ɗakinta ne kadai hasken ya ɗauke, abun ka game bacci sam bata ji alamun hasken dakin ta ya ɗauke ba.
Kwatsam! taji an damƙi wuyanta, tsabar zafin shaƙar da akayi mata ne yasa ta ware idanunta waje, bata iya ganin komai sai duhu baƙi wulik a idanunta
Wani irin mahaukacin bugun fargaba zuciyarta keyi mata, Hankalinta a matuƙar tashe ta soma kokarin kwace wuyanta daga hannun mutumin daya shaƙeta, wuyanta tuni ya soma yi mata zogin azaba, zufa ta ko'ina ta wanke fuskarta, duk yadda benazir taso ta kwace kanta sai dai kash takasa, ga zeenatu kwance saman gado sai dai babu halin da zata iya buɗe baki ta nemi agajin ta, koma wanene yayi mata muguwar shaƙar da ko yatsanta takasa ɗagawa, bakinta tamkar an ɗaure mata shi takasa buɗe shi, hakan yasa tafara kukan zuci tana ambaton sunan Daddy, mommy, yaya shurem, Zeenatu, A karshe ta kamo kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraji"un tacigaba da anbatonta acikin zuciyarta.
Tana acikin wannan mawuyacin Halin har tafara fidda rai da rayuwa kwatsam wayar zeenatu da ta ajiye kan gado ta soma ringing, taken karatun al'ƙur'ani mai girma ne, Kamar Walkiya taji alamun an sakar mata wuyanta, kuma nan take hasken ɗakinta ya kawo, a gigice ta zabura ta miƙe zaune tana faman zazzare idanunta, bin ko'ina na dakin tayi da kallo bata ga kowa ba, Lamarin ya daure mata kai, tagaza gane meke shirin faruwa da ita? Don wannan yafi karfin a kirashi da mafarki, tabbas akwai me son rabata da rayuwarta, lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka tamkar ƙaramar yarinya ita kadai tasan radaɗin da wuyan ta ke yi mata, zeenatu dake ta sharar baccin ta tuni ta soma mutsu mutsun farkawa saboda sautin kukan benazir daya fara addabar kunnuwanta, da sauri benazir ta tsagaita da yin kukan gudun kada zeenatu ta farka taga halin da take a ciki, cikin juriya ta miƙe ta zame hijab din jikinta, ta jefar da shi gefen gado, gaban madubi taje ta tsaya tana kallon wuyanta yayi jawur da shi hada sawun yatsun hannuwan mutun rudu rudu..
Hakika Ta gigita ta kuma tsorata a yanzu ta ƙara tabbatarwa kanta cewa akwai me son ganin bayan ta? Wanene? Laifin me ta aikata da har ake son kashe ta? Zuciyarta ce ta raya mata cewa zai iya yiwuwa jinnu ne, tafi yarda da abun da zuciyan nata ta raya mata saboda babu wanda take zargin zai iya yi mata haka acikin mutanan da take rayuwa da su,ta dai yanke shawarar zata sanarwa yaya shureim ko dan su nemi mafita a tare.
Miryarta na rawa ta furta"Ya Allah ban cutar da kowa ba, Kada ka bada damar da wani zai cutar dani" ta jima atsaye gaban mirror, zuciyarta cike da rudani, ta nufi toilet, tsawon mintuna kafin ta fito jikinta da alamun lemar ruwan da ta watsa ma kanta.
Tunawa da kiran wayar da akai mata ne yasa ta nufi bakin gado ta ɗauko phone din ta soma daddanawa call logs ta shiga nan take taga missed call na bakuwar number din nan
Sai da ta fara kallon agogo, karfe wani abu na dare kafin ta danna call tana faman zazzare idanunta, jikinta nata kerma kamar wadda aka kada ma mazari
Adai dai wannan lokacin Unaisah tana a zaune kan darduma ta zumbula hijabi a jikinta ta ɗaga hannayenta sama fuskarta sharkaf da hawaye bakomai take yi ba face yima danish addu'ar samun lafiya, Batul tana a kwance gefen ta, tun bayan da boss ya tashe su domin yin nafilfilin da za su yi kowannansu bai koma bacci ba, duk suna a dakunansu suna yin sallah, ita dama batul bata da jumurin yin sallah duka raka'a biyu ta samu tayi adaddafe kafin bacci yai awon gaba da ita, shigowar kiran wayar ta ne yasa takai hannu ta dauke ta, a inda ta ajiye ta gefen prayer mat din da suka akai
Ko da tayi tozali da layin da take ta dannawa kira taga da shi aka kirata Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin yin picking din kiran, hadi da kara wayar a kunnanta.
Tamkar kurame sunyi shiru suna sauraran sautin fitar numfashin juna.
Jira take taji wanene mamallakin layin nan daya kira, Haka zalika itama benazir jira take tafara jin wanda ya ɗaga kiran yayi mata magana.
Jin shirun yayi yawane yasa unaisah tace"Assalamu Alaikum" sautin daddaɗan muryarta ne ya daki kunnan Benazir, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin faɗuwar gaba ba.
Muryarta babu nutsuwa ta amsa mata sallamar"Wa'alaikum Salam, barka da dare, dan Allah zan iya sanin dawa nake magana" ta fada cikin ƙagara.
Shiru Unaisah tayi tana tunanin wacece wannan matar mai muryar ƴan gayu? Daga ji dai wayayyiya ce.
Jin shiru ba'a ƙara magana ba yasa banezir furta"nayi magana anyi shiru b'a bani amsa ba, in ansan baza'a tanka min ba meyasa za'a takurani da kira da tsakar dare"? Har zata katse kiran Unaisah tayi saurin cewa"Aunty kiyi haƙuri, bakisan wacece ni ba, nima bansan ki ba"
Ajiyar zuciya Benezir ta sauke kafin tace"okey, amma meyasa kika kira layina bayan baki sanni ba"!
"Nayi kuskurene wurin rubuta number din da zan kira"
"Okey" shiru su ka yi, babu mai magana na tsawon mintuna kafin benazir tayi karfin hali cewa"meye sunan ki? Shekarun ki nawa"? ta tambaya ne jin muryar kamar ta ƙaramar yarinya
"sunana Unaisah, shekarata goma sha shida, ke fa"?
Murmushine ya bayyana akan fuskar benazir, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin farin ciki ba.
"Sunana Aunty pretty, Amma fa ni ba yarinya bace, na girme ki, Shekarata talatin da wani abu"
Murmushi unaisah tayi ita kanta dadi take ji, duk da halin damuwar da take aciki silar kiran nan ya haifar mata da kwanciyar hankali.
"Kiyi hakuri na kiraki bisa kuskure, sannan na katse maki baccin ki"
"Kada ki damu, Naji dadin haduwa dake"
Shiru sukayi Kamar karsu Kashe kiran haka suke ji.
"Baki so na sake kiranki"? Unaisah ce ta jefa mata tambayar .
Murmushi benazir tayi don ta fahinci yarinyar batason su daina magana.
"Ina so mana, tun da naji muryarki naji kin kwanta min araina, da ace babba ce ke da mun kulla kawance sai dai kin min ƙanƙanta"
Cike da zumuɗi Unaisah tace"zan dinga kiranki muna gaisawa a matsayin aunty na, Idan kuma kina da ɗiya kamar ni, ko ƙanwa to ki hadani da ita sai mu dinga zumunci"
"In sha Allah, yanzu ki kwanta ki yi bacci kada mommyn ki ta kama ki kina waya da dare, gobe zan kiraki mu ƙarasa gaisawa, Yanzu kinga dare yayi,"
Kamar karsu rabu, Haka sukayi sallama da junansu, fuskar kowannansu dauke da murmushi.
Karatun kur'ani benazir ta kunna a wayar, saboda ta fahimci Kiran wayar da akayi mata sautin karatun kur'ani ya fita shine silar da Aljanin daya shaƙeta ya gudu, Gefenta ta ajiye wayar, ta kwanta tare da jan bargon da zeenatu ta lullu6a da shi, itama ta lullu6e kanta, zuciyarta acike fal da annurin farin ciki, Harta kosa gobe tayi, kodan ta kira Yarinyar su ƙara gaisawa, ita kadai take ta tufka da warwara har ta yanke shawarar zata haɗa yarinyar da zeenatu su dinga zumunci, in yaso ita sai ta kar6i layin maman yarinyar suna gaisawa da wannan tunanin wani baccin ya kuma daukarta.
Bayan Unaisah ta kashe Kiran, wani irin daɗi take ji, aranta ta ayyana meyasa nake farin ciki akan matar da bansan wacece ita ba, wata'kil ma maman Sajeed ce, dole gobe in fada mashi munyi waya da matar dake a ruƙe da layin wayarsa, bata koma bacci ba sai da ta kara zuwa dakin danish cikin daren ta leƙa don ganin koya farka, kamar yarda suka barshi haka ta same shi, addu'o'i ta ƙara tofe shi da su
ta ruƙo dogayen yatsun hannayensa ta sumbace su, tasha kuka a yayin da take agefen gadon shi ta roƙi Allah akan ya ba man dinta lafiya tamkar zatayi hauka ita kadai a dakin sa ko tsoro bata ji, raba dare tayi tana gadinsa har bacci yafara kokarin daukarta sai da aka fara kiran sallar Asubahi tukunna ta baro dakin tana sharar kwalla..............😥💋✍️
*FRIDAY MORNING*
*Hajjaty the head maids*
Sautin ringing ɗin wayar pravin ne ya katse mata baccin ta, A hankali ta buɗe idanunta masu dauke da bacci ta kalli ceilling na tsawon mintuna kamar mai nazarin wani abu, sam ta manta da abun da ya farkar da ita daga bacci har saida aka ƙara kira tukunna ta miƙa hannu saman mattress ta janyo wayar ta karata a kunnanta ba tare da ta duba sunan mai kira ba.
Bankaɗo kofar toilet da akayine ya firgitar da ita kafin tayi wani yunkuri taji ya fisge wayar daga hannunta, har sai da gabanta ya faɗi ganin kumfar sabulu a jikin shi, Ko sutura babu haka ya fito daga bathroom zindir haihuwar uwarsa, duk dan kada taɗaga mashi waya' juyawa yayi da sauri ya koma toilet, hajjaty dake kallon shi da tsantsar mamaki ta miƙe zaune tare da jingina bayanta jikin headboard tana jiran fitowarshi
Badajimawa ba pravin ya fito daga toilet waist dinsa daure da towal, fuskarshi babu walwala tunkafin tayi mashi magana yai saurin tarar umfashinta da cewa"Karki kuskura kiƙara gigin ɗaga min waya idan an kira ni, babu ruwanki da wayata" lamarin ya ɗaure mata kai adabarbarce ta furta"laifine idan an kiraka na daga? Anya pravin kana da gaskiya kuwa saboda kawai na ɗaga wayarka shi ne ka fito tsirara daga toilet da ruwan kumfa a jikin ka"!
Harara ya galla mata"wannan bai shafe ki ba, Nidai ina ƙara jan kunnanki babu ruwanki da wayata, ban yi maki iyaka da komai nawa ba, amma banda wayata," Kallon tuhuma take jefa mashi, ba tun yau ba ya tsani yaga ta ta6a wayarshi kamar ta tsunkuli ranshi ne.
"Kallon Ya isa haka, ki tashi kije ki yi wanka" ta6e baki tayi kafin tace"ba yanzu ba, sai zuwa anjima idan zamu je dinner din Hateem"
Ɗaure fuska yayi babu annuri ya furta"ay na faɗa maki, bazan bari ki halarcin dinner ɗin nan ba"
"Amma dai dawasa kake min ko"?
"Na ta6a yi maki wasa irin wannan"?
"Amma meyasa zaka hanani zuwa bayan na riga dana kwallafa raina"? fuskarta a yamutse ta jefa mashi tambayar
Shiru yai bai tanka mata ba, taci gaba da cewa"bazaiyiwu ba pravin, matan family din nan gaba ɗaya zasu halarci taron sai ni kadai zaka hana zuwa"?
Gaban mirror ya tsaya yana gyara jikin shi,
"Dakai fa nake magana"?
Sai da ya mula yasha iska tukunna yace"abun da nakeso ki fahimta, zuwanki dinner din baida amfani! Saboda matan family din nan ba kaunarki su ke yi ba, iyakaci suci maki mutunci su zazzageki ni kuma abun da banaso kenan, sannan ni ina kishin kije wadannan dattawan masu gemu su kalle min ke"
Kwantar da kanta tayi jikin pillow
"Wannan ba hujja bace pravin, meya kawo maganar cin mutunci a taron bankwana da hateem kaima in banda abun ka, sannan kishi da kake ji ay bani kadai bace matar da zanje dinner din ba muna dayawa...." kafin takare magabar ya tari numfashinta da cewa"Amma ay ke kadai ce ba'asan da igiyar aure akanki ba, kowa kallon bazawara yake yi maki, uwa uba kuma surar jikin ki dake jan hankalin su"
Saukowa tayi daga kan gadon ta nufe shi, ta tsaya daga bayanshi tare da ɗaura kanta saman bayanshi.
"Hubbyna, dan Allah kada ka hanani zuwa, wallahi na ƙwallafa raina akan dinner din nan, ka taimaka min pls nayi maka alkawarin zan kare mutunci na, indai ka yarda dani pravin kabarni inje' da shagwa6a ta ƙare maganar tare da zagayo hannayenta kan waist dinsa tuni yafara jinshi a wata duniyar, ta san duk wata hanya da zata canza mashi ra'ayin shi.
Lumshe idanunshi yayi, yayin da yake kallonta ta cikin mirror, tsantsar sonta da kaunarta yake ji,
Ɗago dakanta tayi daga bayanshi ta daura kan kafadarsa ta hagu.
Suka ci gaba da kallon juna.
"Inaso ka faɗamin tsakanin ni da kai waya fi kama da ɗan mu"
Shiru yayi tamkar baison furta maganar ya ce "kin fi kama da shi"
Murmushi tasaki har dimple dinta ya lotsa
"Allah ya ji ƙan shi" ya amsa mata da ameen.
Sumbatar wuyanshi tayi, hakan ba karamin dadi yayi mashi ba
"Zaka barni inje babyna"?
Baiyi niyar barinta taje ba, amma yanayin da tayi mashi maganar yasa shi amincewa batare daya shirya ba.
Wani irin farin cikine ya lullu6eta shi kanshi ya shaida hakan
"Atare dakai zamu je ne"?
"No,ni ba lallai naje ba,"
"Amma yakamata kaje kaima zaiji daɗi, kaga daga yau shikenan gobe ba lallai ka samu danar ganawa dashi ba may be tashin asuba jirginsu zai lula"
Janyo hannunta yayi ya dawo da ita ta gabanshi, yadda zaiji dadin kallonta dakyau
"Nima zanje in sha Allah"
"Bari na taimaka maka ka idasa shiryawa, nasan hajiya Saratu tana can tana dakonka, daga zuwa sallar asuba ka gudo dakina"
"Matar da bata damu dani ba, ni fa banda amfani awurinta... " bata bari ya karasa maganarba ta rufemashi baki, don bata son yana aibata hajiya saratu awurinta.
Shirye shiryen sun kankama, Don tun wuraren ƙarfe tara na safe Zungureriyar motar kamfanin su zahra mai ɗauke da tambarin Zahra World of beauty ta karaso estate din, kafin shigar motar sai da Security officers su ka yi mata wankan tsarki ciki da bai suka bincike komai da na'urorin tsaro, hatta Interior designers din dake a cikin ta ƴan matasa mata sai da Sojoji suka bincike su from head to toe, suka tabbatar ba su shigo da wani abun cutarwa ba, kafin suka bar motar ta shiga ciki, Hajiya saratu ce ta tsara lokacin da za'a fara aikin decoration din dakin taron saboda friday ne kurarran lokaci kwara ay komai da wuri acewar ta
Masu aikin gidan kuwa tun asuba suka fara ɗaura girke girke, saboda uban aikin dake gare su, abinci ne za'a girka kala kala, Na ƙabilu daban daban, kafin kace me cikin ƙanƙanin lokaci ƙamshi ya gauraye ko'ina na gidan baba obie, don anan ake aikin girkin....
Hajiya zahra kuwa yau tsabar murna kamar wadda akaiwa albishiri da gidan Aljana, tun jiya akayi mata saloon da kunshi na jan lalle kamar amarya, taci buri akan dinner din nan kamar ranar auranta, Saboda son ta dau gayu na kece raini motar Aneelerh ta ara da yake tafi tata motar tsada da kyau, Tuni taba mahboob motar ta hada shi da ƴan canji ya tafi kai ta wurin da za'a wanke ta don ta ƙara kyau, kowa na gidan sai da yasan da zancen zuwan Zahra Obie estate saboda ta addabi kowa duk bayan ƴan mintuna sai ta kalli agogo burinta lokaci kawai lokaci ya ci ka....
Ƙarfe 9 na safe, Zeenatu tana a zaune kan mirror chair, tana ƴan shafe shafen ta, bata jima da fitowa daga wanka ba, jikin ta sanye da bathrobe mai kyan gaske, ta ɗaure gashin kanta
Fitowa benazir tayi daga toilet da alama itama wankan tayo, ta yi daurin gaba da towel, fuskarta babu walwala ta kumbura jawur da ita saboda kukan da tayi adaren jiya da abun nan ya faru
Ganin zeenatu dake ta shafa powder yasa ta ɗan saki face din ta da zolaya tace"uhum su baby shuriem wa ake ma kwalliya" kunyar maganar Benazir yasa tayi kamar bata ji me tace ba
Gyaran murya benazir tayi still bata ɗago ba, saima ta ɗauki jan baki tana shafawa
"Wato kinyi imanin sai kin zautar min da yaya na"? Cak zeenatu ta tsaya da shafa jan baki, cike da jin kunyar benazir ta sunnar dakai ƙasa
"Duk hasken da Allah yayi maki zeenatu har sai kin ƙara da powder in ban da asara, so kike ki koma zabayyana ne'? dariya ce ta kubce ma zeenatu har fararen hakoranta suka bayyana masu kyau da tsari
Muryarta ƙasa ƙasa tamkar ta mai yin raɗa ta furta"aunty benazir mommy ma tana shafa powder in zata ma daddy kwalliya, shiyasa nima nake shafawa" dariya benazir tayi hadi da ɗan girgiza kanta..
Wucewa wurin closet din dakin tayi domin shirya kanta, within minutes benazir ta fito asanye da riga da skirt sun ɗan kama jikin ta
Gaban madubin ta tsaya daga gefen zeenatu tana fadin"naga abun naki bamai karewa bane, ki tashi ki je ki sanya kaya, kafin darling din naki ya farka daga bacci" cike da jin kunyar maganarta, zeenatu ta miƙe tana faman sakin murmushi sai da tafara daukar hijab dinta dake ajiye bisa gado kafin ta nufi hanyar fita dakin don taje nata dakin ta sanya kaya
Fitarta ke da wuya suka yi kici6us da dr shureim wanda ke kokarin doka sallama, tun da ya sauke idonshi akanta ya kasa janye su, cikin jin kunyarsa ta sunnar da kanta kasa tana faman noƙe kai ta furta"yaya shurem ɗina ina kwana, fatan ka ta shi lafiya.. ' ta faɗa la66anta na dan kerma without looking at him
Gogan naka ya kasa magana saboda kyanta da ya dauke ma shi hankali
Muryar ta da shagwa6a ta furta ya shureim ina magana ka share ni...
Lumshe idanunsa yai yayin da yake shakar kamshin turaren dake fesowa daga jikin ta
Muryarshi can ƙasa makoshi ya furta" nabd alqalb (نبض القلب) kin yi min kyau ban yi tsammanin idanuwana za suyi min tozali da kyakkyawar fuskar ki ba..." arude ta maimaita kalmar nabd alqalb ta dago tana zare mashi blue eyes din ta, muryarta na ɗan rawa ta furta"ya shureim bansan me kake nufi ba"
Side smile ya sakar mata, tare da matsawa dab da ita, tamkar zaiyi mata raɗa a kunne ya furta"Bugun zuciyata" farfari tayi da idanunta wani irin farin ciki Ya lullu6eta
Batai wanai aune ba taji ya manna mata sumbata saman soft cheek din ta' waro idanu tayi a ruɗe ta watsa da gudu ta nufi hanyar bedroom din ta
Bin bayanta yayi da kallo tamkar yabi ta haka ya ke ji
"Yaya Shureim kaine? Yaushe ka zo shine baka min sallama ba" kamar daga sama yaji muryar benazir firgigit yai tare da dubanta
Yana kokarin bude baki yai mata magana karaf idanunsa suka sauka akan shatun yatsun hannun dake akan wuyanta ruɗu rudu fatar wurin tayi dabra dabra jawur, gabansa ne yayi wani irin mugun faɗuwa ji kake rass
Benazir bata lura da abun da yake kallo ba, gaba ɗaya ta faɗa kirjinshi ta rungume shi haɗi da manna mashi peck kan kuncinsa, irin gaisuwarsu ta larabawa
Idanunsa a zare yake kallon fatar wuyanta, kafin ya daddage ya ɗaura tafukan hannayensa kan kafaɗunta ya ɗago da ita
"Benazir! " da karfi Ya ambaci sunanta
"Me nake gani akan wuyan ki"? Ya jefa mata tambayar
Farat ɗaya ta gane me yake magana akai, da sauri taja hannun shi suka shiga dakin gudun kada wani yajiyo su
"Tambayarki nake yi kinyi shiru baki ce komai ba!" adan tsawace ya furta maganar
Batasan sa'adda ta fashe mashi da kuka ba, cikin shessheƙar murya ta labarta mashi abun da ke faruwa tun daga rana ta farko da aka fara kawo mata hari
Ranshi yayi mugun 6aci na kin fada mashin da batayi ba,
In a breaking voice ya furta"shi ne baki faɗa min ba"?
"Yaya shureim bansan wanene yake son rabani da rayuwana ba, bansan meke shirin faruwa dani ba, na 6oye maku ne saboda ban dauki abun serious ba, da farko nayi tsammanin mafarki ne, ashe ba haka bane so ake akashe ni yaya shureim bansan zunubin dana aikata ba.... ' ta ƙarasa maganar tana faman shessheƙar kukan, Hankalin shi idan yayi dubu toh ya tashi, ya gaza yarda da abun da idanuwanshi suke gane mashi
Ɗaura yatsun hannayenshi yai akan wuyan nata ya shafa shi a hankali, runtse idanunta tayi saboda raɗaɗin da taji, ganin hakan yasa shi janye yatsun sa
Yama rasa tunanin da zanyi dangane da bakon al'amarin nan
Ruko hannayensa tai acikin nashi tana cigaba da kuka take fadin"yaya shureim ka tayani da addu'a, bana son in mutu ban hadu da mijina da ƴata ba, yaya shureim ka taimaka min idan ba haka ba wata rana za'a iya farkawa ataras da gawata, jiya ba don kiran da akayi min ba har sautin karatun al'kurni ya fita da tuni na jima da mutuwa... Bai bari ta ƙare maganar ba, Ya toshe mata bakinta da tafin hannunsa
Kwantar da kanta yayi kan chest dinsa muryarsa kasa kasa yake ambaton Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un yayin da zuciyarsa ke dakan uku uku!!!
"Yaya shureim ko dai aljanune suke son kashe ni? Idan ba su ba to waye zaiyi min hakan a gidan nan? Babu wani bare a cikin mu, sai house maids da security officers, babu abun da ya ta6a haɗani da wani daga cikin su, bansan su ba, balle har ace na aikata wani abu ne da zaisa a nemi rabani da rayuwana...... ' cikin jin kunar rai ta furta maganar.
"Yaya shureim dan Allah mubar gidan nan, dama saboda mu haɗu da aneeleerh ne yasa na ƙwallafa raina akan zuwa, tun da ban samu hanyar da zan hadu da ita ba, mu koma gida zai fi min kwanciyar hankali na...."
Tuni idanun dr shureim sun cicciko da hawaye, yai matuƙar girgiza da jin abun da ke faruwa da yar uwarsa tabbas yana ji aranshi wani abu ne ke shirin faruwa da ita, dole ya miƙe tsaye don ganin ya ceci rayuwarta
*(Mu haɗu Jibi Alhamis Idan Allah Ya kai mu da rai da Lafiya, Don jin Yadda zata kaya)*
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 11 Complete
by
Novels Elite Admin
May 26, 2024
Sponsored Link
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القدر💋✊
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘Best gifts for your loved ones
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘Best gifts for your loved ones
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Shafa sumar kanta ya soma yi cikin sigar lallashi ya furta"Allah yana atare dake, duk wani mai neman ki da sharri kanshi zai koma, bi'iznillahi bazan bari wani cutar min dake ba a karo na biyo, zan yi iyakar bakin kokarina don ganin na baki kariya da ayar Allah, zan iya hana idona bacci don inyi gadin ki a kowani dare kafin lokacin da zamu bar gidan, Inaso ki kwantar da hankalin ki, bana so ki sanya damuwa aranki, mu bi komai a hankali don ganin mun gano wanene ke yi maki hakan, bana son jin maganar nan abakin wani, kibarta kawai daga ni sai ke!!" kwantar mata da hankali yaci gaba dayi, tare da karfafa mata gwiwa har ya samu ya shawo kanta....
*💋CHIEF OWAIS💪*
Kasancewar Jiya bai samu isasshen bacci ba, sakamakon nafilfilin da ya tsaya yi, hakan ya haifar mashi da jin matsanancin bacci mai nauyin gaske, tun wuraren ƙarfe bakwai na safe Daddy sharafudden yake ta faman zarya zuwa room din shi don ganin koya farka amma shiru har ya tafi office dinsa dake anan cikin Villa.....
Wayarsa ce ta soma yin ringing, da zarar ta katse wani kiran ke shigowa, da wata irin kasalar bacci ya buɗe eyes dinsa wadanda suka canza launi, addu'ar ta shi daga bacci ya ambata aransa kafin ya maiƙa hannu ya dauko wayar dake kan nightstand, ba tare daya miƙe daga kwancen da yake ba ya soma duba me kiran nashi, missed calls ya gani har shida, Uku daga Prime minister, biyu daga boss man, lumshe idaninshi yayi kafin ya aje wayar ya sauko ya nufi bathroom, Ƴan mintuna ƙalilan Ya fito waist dinsa ɗaure da towel fari ƙyal, gaba ɗaya ƙirar Ƙarfinsa ta ƙara baiyana, ƙirjin nan nashi acike ya ke da albarkatu.
A gaban mirror ya tsaya tamkar mai nazarin wani abu, A lokacin da baiyi tsammani ba kwatsam yaji An rungumo shi ta baya, A ruɗe Yakai idaninsa ga hannun wanda ya rungumo shi, nan take ya sauke ajiyar zuciya dama sai da ranshi ya bashi cewar shi ne.
"Daddy ba sallama, har kasa gabana Ya faɗi"
Tuntsirewa sharafudeen yayi da dariya ba tare daya raba jikin shi daga na chief ba
Muryarsa da tsantsar farin ciki Ya furta"Nayi kewar ka ne sanyin idaniyata, da tunaninka na tafi office, nagaza ta6uka komai shiyasa na dawo don inga ko ka farka, Ina fata ka yi breakfast din ka" cikin kulawa yai maganar yana leken face din sa ba tare daya raba jikin sa daga na shi ba
"Ban kaiga yin breakfast ba, saboda ban jima da tashi daga bacci ba"
"Hakan na nufin baka samu isasshen bacci ba daren jiya, bana hana ka kaiwa dare kana aiki ba"? ya faɗa yana ɗaure mashi fuska'
Chief owais dake kallon daddyn nashi wani irin sanyi ne ke ratsa heart dinsa
"Ay min afwa dad, zan kiyaye hakan, nagode da kulawarka agare ni"
"Good, yanzu faɗa min me kake son ci insa a haɗa maka"
"Bazan samu damar yin breakfast ba, gida zan wuce"
juyo da shi Dad sharafudeen yayi suka fuskanci juna
"Yau ma kana nufin bazan samu damar cin abinci a tare da kai ba? Saboda kai na hana kaina yin breakfast duk don saboda muci atare, shi ne yanzu kake fada min tafiya za ka yi"?
fuskarshi babu annuri Ya furta maganar,
"Nayi jiran banza kenan, Bari na koma office, Allah ya kiyaye hanya"
Juyawa yayi cikin takun sauri Ya nufi door room
Kafin ya buɗe kofar, Chief owais yai hanzarin bin bayan shi, Gaba ɗaya yayi hugging dinshi ta baya
"Am sorry dad, kasan bana son Bacin ranka, sannan bansan ni ka tsaya jira mu yi breakfast ba"
Lumshe ido dad sharafuddeen yayi, yayin da yake sauraron shi
"Lokaci na naka ne daddy, duk wani abu mai mahimmanci yabiyo bayan naka, Idan ma kace kada na fita, wlh ba inda zanje zan tsaya tare da kai ne"
daɗaɗan kalamai chief owais yake furta mashi, cikin ƙankanin lokacin zuciyar sharafudeen ta sassauto daga fushin da yayi.
Juyawa yai suka fuskanci juna ido cikin ido
"Idan na tuna yadda Dan uwana hateem yake kukan rashin ɗa da Allah bai bashi ba, Ni kuma Allah Ya bani ɗan sai dai bamu da lokacin juna, abun ba ƙaramin karya min zuciya yake ba, bana so na bata maka lokaci, Ka tafi kawai, ay zamu hadu ne a wurin dinner da anjima"
Girgiza kai chief owais yayi, calmy ya furta"ba zan iya fita ba daddy, idan har banyi breakfast tare dakai ba, ka yi hakuri, ka bari mu yi kawai, daga ni har kai zamu fi samun kwanciyar hankali"
Dafa broad shoulder dinsa yai da hannu ɗaya"Ina alfahari dakai bugun zuciyata, kaga kuwa yadda ka kara girma da kyau? Ya fada yana duban jikin shi from head toe,
"Da gaskiyar mutane da suke fadin na iya haihuwa" murmushin gefen fuska chief ya dan saki har dimple dinsa na chin ya lotsa wani irin madarar kyau.
"Amma dai yau zanga Surukata ko"? ya tambaya yana ɗage mashi gira
Jinjina mashi kai chief owais yayi alamar eh
"Kasan ban ta6a ganin ta ba, saboda busy da nake shiga, amma tana araina, yau ka tabbatar tazo dinner din nan, Ina son ganin ta, ka kawo min ita gabana in sanya mata albarka"
"In sha Allah dad"
"Good, Ka shiga ka karasa shiryawa zan jira ka a dining room" amsa mashi yai da toh.
Har Ya buɗe kofar zai fita ya ɗan dakata tare da waiwayowa baya ya kalli chief dake kallon shi
"zan fada mata, tayi dacen miji," yana fada ya fuce daga dakin, qasaitaccen murmushi chief ya saki, fatan shi kamar yadda kowa ke fadin tayi dacen miji itama tayi alfahari dashi a matsayin a bokin rayuwarta.
Da wannan tunanin ya nufi walk-in closet dinsa, within minutes Ya kamma shiryawa cikin Jalabiya launin ocean blue.
A dining room ya taras da su gaba dayan su sun hallara, tun daga kan momynsa malikat tare da younger sis dinsa Hindu ƴar matashiya ce da bazata wuce 22 Years ba, Black beauty tana asanye cikin shiga ta jumpsuit Dark navy, kitson zanene akanta wutsiyar gashin har kan shoulders din ta, Allah yayi ta da ruwan kyau kamar ita ta zana kanta, Komai nata ƙaramine ɗan pink lips dinta da Asian eyes din ta, ga dogon hanci, Bata da ƙiba siririya ce, a haka structure din jikinta ba karamin kyau ne da shi ba, Kamannin ta sak dana Mommyn su Gimbiya Malikat Sarauta.
ɗaya bayan ɗaya yayi hugging dinsu cikin mutunta juna suka gaisa, kafin ya zauna sukayi breakfast dinsu, daddy sharafudden yaji dadin cin abinci tare da ɗan nasa, har abaki yake bashi bayan sun kammala yayi masu sallama agurguje Ya nufo gidansa.
_________________________✍️
A 6angaren su Unaisah kuwa bayan kammala sallar asuba, bacci mai nauyi yayi awon gaba da su kamar matattu, har wurin karfe tara babu alamun zasu farka, ummi sai faman yin zarya ta ke yi daga dakin ta zuwa nasu don ganin ko sun farka, saboda tana son ta fara gyara masu jikin su, ganin baccin nasu bamai ƙarewa bane yasa tabi su ɗaya bayan ɗaya ta farkar da su, wani abu da ya ɗaure mata kai, duk wanda ta tada daga cikin su sai taga ya watsa da gudu ya nufi upstairs second floor, da sauri tabi bayan su don ganin ina za su je, a dakin danish ta same su zuƙunne bakin gadon shi suna kuka kamar ran su zai fita, hankali a tashe ta tambaye su meya faru suke kuka? Cikin shessheƙar kuka suka ce mata meyasa danish din su bai farka ba? Sun hana idon su bacci jiya sun roƙi Allah akan ya bashi lafiya amma shine Allah bai kar6i addu'arsu ba bayan wahalar da su ka sha ko dan saboda danish baiyi imani da shi ba ne....." waro idanu waje ummi tayi tana kallon su, ita dai unaisah ko magana ma takasa furtawa lamarin yafi karfin ta ashe har yanzu akwai sauran rina akaba, abun ka ga masu ƙarancin ilmin addini
Lallashin su ummi da unaisah suka dinga yi suna basu baki, akan su yi hakuri su daina fadin hakan babu kyau, gaggawa aikin shaidan ne, indai sunyi imani da Allah to su bi komai a sannu in sha Allah ɗan uwan su zai farka..." daƙyar su ka shawo kansu har suka samu komai ya lafa, ta sanya suka fito daga dakin ta rufe mashi ƙofa
Ko da aka shirya masu breakfast kasa ci su ka yi saboda fargaba da zullumin kada su rasa ɗan uwan su, Hankalin ummi duk ya tashi saboda tausayin su da ya kamata, Kamar marasa lafiya haka suka koma, lalla6a su ta dinga yi har ta samu suka ci abincin kaɗan bayan sun gama ne ta tarasu a falo ta fada masu dangane da Farewell dinner din da zasu halarta na uncle din chief, sun ji dadi yau zasu shiga cikin family din chief koba komai zasu ɗebe kewar abun da ke damun su, duk cikin su mutun ɗayace batayi farin ciki da fitarsu ba, hakanan take jin gabanta na faduwa, babban abun da take jimawa ba lallai su samu kar6uwa a wurin family din chief ba, bugu da kari rashin wayewar ƴan uwanta, yafi komai ɗaga mata hankali, tana jin tsoron su shiga bainar jama'a su yi kauyacin da zaisa a gane jahilcin su harma a goranta masu ko a ƙyamace su.
Hankalinta sam yaƙi kwanciya, har sai da taja aunty umminsu gefe ɗaya ta faɗa mata abunda take zullumi tace tana neman alfarmar abarsu su zauna a gida kada aje da su wurin dinner din nan.
Ummin tace ta kwantar da hankalin ta, ba abun da zai faru saboda basu kadai zasu tafi ba, hada su boss man kuma tasan bazasu bari a wulakanta su ba awurin taron zasu basu kariya, sannan tasha jin labarin familyn obinna mutanene masu karamci da daraja ɗan adam don haka kada ta sanya damuwa aranta in sha Allah zasu samu kar6uwa a wurin su.
Jin wannan maganar ya sa hankalin ta ya kwanta, Har ta fara zumuɗin lokaci ya cika don atafi da su.
Ba tare da 6ata lokaci ba, Ummi ta tattara matan suka shiga Home beauty saloon din gidan, domin gyara masu jikin su, mazan kuma taj ne ya tafi da su 6angaren jami'an isod na gidan acan za'a gyara masu sumar kansu, ɗaya bayan ɗaya ta wanke ma kowan nan su sumar kanshi tagyarata tsaf tayi masu hair style kala kala, Unaisah da batool kalar nasu gyaran gashin all layers around ne yayi bala'en yi masu kyau sumar kan har kyalli take yi tana ɗaukar ido saboda mayukan da aka yi masu amfani da su, gashin ya ciza launin shi dark brown yayi washar washar da shi daga baya ya lullu6e wuyansu da tsakiyar bayansu kamar hijabi, Azeeza da jemimah kuwa kalar nasu styal din braided bun ne, wanda ake dunƙule gashin daga tsakiya sai kaga ya yi kamar donut, gyaran gashin su yayi kyau sai ya ƙara fito masu da beauty baby face din su, sun fito a jar fatar su ta turawa, Parveen da Hannah su nasu gyaran gashin Classy ponytails ne yara sun fito suffarsu ta kyawawan ƴan mata, Sai farin ciki sukeyi tamkar babu abunda ke damun su, bayan an gama gyaran gashin, ummi tafara gyara masu kafafuwansu da akaifinsu, Hakiƙa tayi kokarin yadda kasan ƴa'ƴan ta haka ta dinga tsaftace su ciki da bai, har hakoransu bata bari ba sai tayi masu amfani da tooth care product wurin wanke masu su, dalilin dayasa take yi masu gyara duk da boss yace kayan da za'a sanya masu ya zamanto sun lullu6e ko'ina na jikin su, ita tasan ba yadda za'ay a shiga da yaran nan wurin dinner ta prime minister ba tare da security din dake tsaron wurin su sanyasu cire mask din fuskarsu ba, shiyasa ta dage damtse wurin gyara su, don agansu da mutuncin su, saboda itama maganar unaisah ta sosa ranta, batason ayi masu kallon ƙasƙanci, harta fatarsu sai da ummi tagyare masu ita, Kamar Ƴa'ƴan Furanni saboda tsabar Kyan da su ka yi, ita kanta da take kallon su ba karamin tafiya da imanin ta suke yi ba, inaga idan suka shiga wurin dinner din tabbas zasu Ja hankalin jama'a,
Bari dai in takaice maku zance, Ummi har yadda zasuyi magana ta ƴan gayu wayayyu da yadda zasu yi tafiya mai jan hankali sai da ta koya ma su, duk don kada suyi kauyacin da za'a tozarta su, sai wuraren sallar Juma'a ta sallame su tace suje su yi sallah after sun kammala su kwanta su huta kafin lokaci ya cika, A lokacin itama daki ta shiga don ta yi sallah ta kuma kwanta ta huta, fatanta Allah yasa taj ya nema mata alfarma a wurin chief ko ta samu ta fita yawo anjima
Badajimawa ba, Su sajeed suka dawo atare da taj, Wa'iyazubilla yadda kasan mazan hurul aini a kyau, Musamman masu tarin sumar cikin su, Sajeed da Naufal sai Javed, wani hadadden gyaran suma akayi masu irin na gayun nan, yadda kasan ya'yan wani shege mai ji da naira, shi kan shi haris da bai kai su sumar kai ba, gyaran gashin da akayi mashi ya kara fiddo mashi da Inner beauty dinsa, bayan taj ya rako su sun dawo gidan basu taras da ƴan uwansu a falon ba duk suna a daki suna hutawa A falo suka zauna suna jiran lokaci ya ƙarasa cika, dadi suke ji za'aje da su wani wuri kamar su zuba ruwa ƙasa su sha tsabar murna.
*DINNER HALL*
Wuraren karfe huɗu da wanu abu.
Katafaren Ɗakin taro ne dake a cikin Obie Estate, Aljannar duniya ce mai zaman kanta, saboda tsabar haduwar Hall din idan Ka shiga ciki gaba ɗaya zaka rude ka kasa tantance a ina kake ma, musamman a yanzu da yasha uban decoration an kawata shi da kayan ado masu ƙyalƙyali da ɗaukar ido, gaba ɗaya kewayen hall din Fusatattun sojoji ne majiya ƙarfi ke tsaron shi tare da Canadian polices ga kuma gwarazan jami'an Isod, bayan ga wadannan jami'an hada na'urorin cctv dake a kowace kusurwa har ta cikin fitilun lantarki da jikin kofafi, ciki da wajen ɗakin taron domin ba su tsaro daga dukkan wani abun cutarwa, yadda aka sanya tsaro a hall din bana tunanin ko sauro zai iya haura ƙafa Ya shiga batare da alburushin bindiga Ya tarwatsa kan shi ba, Entry way na shiga hall din tana a cikin Garden din gidan An kawata saman ta da gefenta da adon string lights mai walwali da daukar ido, ga wani shamfidaddan carpet da zai isar dakai cikin dakin taron lallausan gaske daga saman Entry door din anyi wani rubutu da adon furanni aka sanya
*Welcome to the farewell dinner of Prime minister Hateem Obinna*
Idan muka koma cikin hall ɗin kuwa sai dai muce masha Allah, Zahra world of beauty interior designers sun baje basirar su wurin ƙawata cikin ɗakin taron, wasu haddun dinner tables ne rukuni rukuni a kalla sun kai set hamsin kowani table yana a kewaye da rantsastsun kujeru masu nunfashi zubin bean bag chairs, daga kan kowani table an ƙawata shi da Centerpiece wanda ya kunshi Glass candle sticks An kunna wutar su gawanin ban sha'awa a kewaye da containers na furanni launuka daban daban, ga wasu jerin Crystal glasses ƴan uban su masu ɗaukar ido, bayan su kuma akwai Silverware and napkins with table ware a kowani dinner table hada menu card ajiye bisa tables din, komai fa ya tsaru ga wasu Crystal Sparkling chandiliers masu haskaka tsakiyar ɗakin taron da wani irin twinkling lights hakan baƙaramin ƙawata ɗakin taron yayi ba, ga wata ni'ima dake kurɗaɗowa ta cikin na'urorin A.c mai ratsa sassan jikin mutun, idan muka koma 6angaren abun da za'aci hohoho duniyar dadi wato daga can 6angare guda dinner buffet ne jerin nau'ikan abincine da aka killace su a cikin chafing dishes wato wani irin aroma ne ke tashi na daddaɗan kamshin abinci mai cika makoshi, ga jerin large glass bowls na kayan marmari da zungura zunguren glasses na Juice masu sanyi komai fa an tanada, babu ce kadai ke babu a dakin taron, anyi 6arin dollar, naira kuwa ta raina kanta a wurin, dukiyace aka narkar wurin ƙawata ko'ina, idan kuwa nace zan fayyace komai dake a hall din tabbas zamu ƙare takun karshe ne wurin kwatanta haduwarshi shiyasa na takaita da bayani don mu shiga kaitsaye cikin taron.
Sannu a hankali danƙara danƙaran motocin su na alfarma zubin Mercedes benz S. Class suka soma shararowa izuwa cikin garden din a jere suke tafiya yayin da jami'an sojojin dake take masu baya suke bin motocin da kafafuwansu suke tafiya gefe da gefen su, hannayen su ruƙe da jibga jibgan bindigu ga wasu kuma soke a qugunansu sai faman mazurai su ke yi, tamkar a filin daga.
Ƙarasowar motocin ke da wuya A hanzarce Sojojin suka buɗe back seat na motar farko, A hankali sheikha mujeedat ta zuro kafarta dake asanye cikin hadaddun takalman alfarma wadanda kudinsu kadai ya ishi wani talakan jari, kafin ta ƙarasa fitowa tabarakallahu ahsanun khalikin gaba ɗaya sojojin dake a wurin saida suka saki baki kamar lehen sakarai saboda tsabar kallon ta a fakaice.
Embellished abaya ce a jikinta launin royal blue anyi mata adon stones work, fuskarta tana asanye da Gold chain mask, adon dake akan fuskarta kaɗai abun kallo ne, tayi masifar haduwa, daga ƙasa har sama ta ca6a ado nasu na sarauta tamkar ɗawisu a fagen haɗuwa, bata jima da fitowa ba, jami'an suka budewa Prime minister hateem other side din motar ya fito tamkar tauraro a cikin taurari yayi shiga na mutunci, hadaddiyar shadda ce a jikin shi gezna launin blue anyi amshi senator style abun ka ga dogon namiji ga kira kayan sun zauna mashi kamar a jikin shi aka dinka su, wata expensive watch ce a hannunsa sai kyalli take tana daukar ido, Yatsun hannunsa na sanye da zoben azurfa mai shegen kyau, sumar kannan tashi tasha gyara har ta gaji da haduwa,
Bayan fitowarsu motar dake abayansu tasu Yazrin da Nazli ce, Lokacin da suka fito Kiris Ya rage zuciyoyin wasu su buga saboda tsabar haduwar wankan dasuka dauka na emirati abaya launin Silver, kowaccensu ta manna glasses a idanuwanta, ga adon gold knucles rings dake a yatsun hannayensu, sun yi rolling veils a kansu yadda kasan asace su saboda kyau.
Bayan fitowar su Nazli, sojojin suka cigaba da buɗe ma sauran motocinsu, gaba ɗaya zaratan samarin family din maza da iyayensu ankon shadda gezna su ka yi, matasan ƴan matan kuwa arab abaya suka sanya masu kyau da tsada na alfarma na kuma kece raini da fita tsara, wasu sun sanya lace abaya, wasu embellished abaya wasu open front abaya, wasu kaftan abaya, wasu egyptian abaya kowa da kalar nashi wankan, kowaccen su tayi lagin gyale akanta, wasu ma babu gyalen zallar sumar kansu ce har gadon baya kamar indiyawa, duk wadda ka kalli wuyanta zaka ganshi manne da ziririyar sarka ta diamond wasu kuma ta zinari, gayu mutanan Allah, Hajiya saratu fa ta dauki kur adakanta rantsastsiyar dubai abaya ce a jikinta tsadaddar gaske launin maroon rigar harta gaji da haduwa abunka ga manyan mata masu dirin jiki kayan sun ladabtu a jikin su kamar donsu aka kera su, kwansu da kwarkwatansu suka jera izuwa cikin hall din, iyayen su maza kowannansu yana ruke da hannun matarshi, wani irin daddaɗan sautin kiɗe kiɗe da raye raye ne ya karaɗe ko'ina na ɗakin taron, Hada wani irin busa tamkar na sarewa Suna tafiya suna taka rawar dattako, cikin nishadi da raha, fuskokinsu dauke da annurin farin ciki da annushuwa.
Prime minister Hateem ne yafara shiga hannun shi ruƙe dana gimbiya mujeedat, daga bayan su Nazli da Yazrin ne, bayan su sai Mai girma sharafuddeen shima ya shiga hannun shi ruƙe dana gimbiya malikat, ɗayan hannun nashi ya ruƙo hannun uwargidansa Hajiya laurat daga bayan su Chief Owais ne wanda zan iya cewa shine farkon haduwa saboda kyawun surar shi, Shaddar jikin shi ta bayyana zazzafan kyanshi kamar shi ya ƙera kanshi, hannun shi yana a ruƙe dana kanwarshi Hindu itama ta dauki wankan abaya.
Bayan wucewarsu Sir mubarak Ya shigo hannun shi ruke dana Mom turai, daga bayan su Zaki ne tare dr Jazz sai Ibad.
Fuskar kowan nan su da fara'a, bayan shigarsu Senate lateef ya shigo shima tare da Mom madina hannun su ruƙe dana juna, Yayin da zulaihat da Ziyad suke abiye da bayan su.
Abun gwanin ban sha'awa, bayan suma sun shiga His excellency abdul Razak ya shigo tare da her excellency Muhibbat, suma sun dauki nasu wankan, atare da ya'yan su suka shigo Captain Yaseer da Yusra.
Daga su sai His excellency Deen Ya shigo fuskar nan awashe da annuri yayin da yake a ruƙe da hannun her excellency Hajiya Jameela, daga bayan su Dr nawaz ne da ɗan uwansa justice Nadeem sun dauki nasu adon.
Basu jima da wucewa ba, Hajiya saratu tamu ta mutunci ta shigo hannunta ruƙe dana Pravin sunyi matuƙar haɗuwa abunka ga ba'indiye shaddar tayi mashi kyau.
Daga bayan su Twins ne zayn da zayn wohoho wanka Yabi jiki, na madina masu kamshin zamzam tsayawa fasalta kawunsu a cikin shadda 6ata baki ne, Hannayensu na ruƙe dana kanwarsu Faryat, ta ca6a uban ado ciki riga red colour duk matasan wurin babu wadda tayi shigar fitsara irinta, abayar jikinta ta matse kirjinta, ko arziƙin ɗan kwalli babu akanta sai zallar kitson kalabarta, gaba dayan ƙamshin turaren su ya gauraya da na iskar A.c wata irin ni'ima ke tasowa.
Har sun nufi inda aka tanadar masu kowa ya nannaɗe rigarsa zai zauna, kamar daga sama muryar Mc ta katse su da cewa"ban bada iznin a zauna ba"! Gaba ɗaya suka kai idanunsu gare shi don ganin wani isasshen ne mai walkin Sa, Ruke yake da mic can saman step fuskar nan ta shi a murtuke tsoro tukuf da shi, gashin kanshi duk hurhura hatta jagirarsa da gashin bakin shi hurhurar ce ga wani dogon gemu har kan cikin sa, daga ganinsa ɗan drama ne, ganin shi bakuwar fuska yasa suka soma tunanin wanene wannan?
Hajiya saratu har ta fara karkata baki zata fara zabga mashi masifa muryarshi ta katse mata hanzarinta
Kirari ya soma korowa yana nuna hanyar shigowa hall din da mic din hannun shi, gaba ɗaya suka kai idanunsu don ganin mai shigowa Obinna ne Ya shigo Cikin shiga ta alfarma tare da Babban amininsa Jan kunne.
Lokaci ɗaya suka sauke ajiyar zuciya, tare da sakin murmushi, saboda jin yadda ake yabon mahaifinsu bayan mc din yagama da baba obie Ya koma kan prime minister ya soma koɗa shi yana fadin.
_Tsakin tama gagara tauna Prime minister Hateem Obinna, Shugaba mai cikakken iko, na Mujeedat ba maza a gabanka. Kasar Canada taka ce, Namijin duniya Taka lafiya, hasken wata sha kallo, fari mai farar aniya, adalin shugaba namu na mutun ci_
sautin tafin hannayensu ne ya cika hall din.
Mc din Yaci gaba da yi ma su kirari ɗaya bayan ɗaya
"Ina kike 'yar sarki jikar sarki, basarakiya 'yar mun gada, uwar gida sarautar mata, sarauniya ɗaya tak dake mulkar zuciyar hateem, Damisa ki sabo, Sheikha Mujeedat Al Maktoum, Dubai da kewayenta ikonku ne. Damisa kike, kin ki kallo biyu. An gaishe ki uwar Nazli da Yazrin, ku ne yau ku ne gobe, har kullum ku ne. Sukari kuke ba ku yi farin banza ba.....' yayin da yake yi masu kirarin murmushine dauke akan fuskar Mujeedat, duk da kasancewar bata jin hausa prime minister hateem ne ke fassara mata abunda mc din Yake fadi hakan ba karamin dadi yayi mata ba
Bayan ya gama koɗa Su gimbiya mujeedat Ya koma kan sauran Iyayen family din yaci gaba da cewa.
_Ina ka ke, Sanata Lateef, fari mai farar aniyya, ina ka gane mini His excellency Abdul Razak, farin wata mai haske duniya. Ban manta da kai ba, His excellency Deen, na Hateem. Ku garafa ga manya nan, Soja birgimar hankaka, Sir Mubarak, Soja marmari daga nesa. Soja na gwamna ga rawa ga yaki_
gaba ɗaya filin taron Ya karaɗe da sowarsu, Sir mubarak dai murmushine dauke akan fuskarshi bashi ba hatta mom turai taji dadin yabon da akayiwa mijinta.
_ina kake Sharafuddeen, Namijin duniya, An buga dakai an barka, Namijin uban maza, kaga adalin shugaba, nigeria taku ce ciki da wajen ta, Ban manta da ke ba, auta shalele, Hajiya Saratu. Auta ba kya laifi ko kin kashe dan masu gida. Bushiya kike kowa ya kwana da ke ya kwana salati._
Ƙasa ƙasa da murya hajiya saratu tace"lallaima dattijon nan! ya raina min wayau, wato ya rasa dame zai koɗa ni sai da bushiya"? Ta6e baki tayi babu yabo babu fallasa taja guntun tsoki, Ita da ba'ay mata gwanin ta.
Cikin mutunta juna suke ƙara gaisawa da junansu ga sautin kiɗa na tashi, sun ɗan jima atsaitsaye suna ta fira cikin raha kafin daga bisani kowa ya samu wuri tare da Iyalansa, gaba ɗaya suka natsu suna sauraron mc
Addu'ar buɗe taro ya fara karantowa
Innalhamda lillahee, nahmaduhu wa nasta'eenuhu wa nastaghfiruhu, wa na'oodhu billaahi min shuroori anfusinaa wa min sayyiaati a'maalinaa. Mainyah dihillaahu falaa mudillilahu, wa mainyudlil falaa haadiya lah.
"Alhumdulillah. Indeed, all praise is due to Allah. We praise Him and seek His Help and forgiveness. We seek refuge in Allah from our souls' evils and our wrong doings. He whom Allah guides, no one can misguide; and he whom He misguides, no one can guide."
Wa ashhadu anlaa ilaaha illalaahu, wahdahu laashareeka lahu, wa ash hadu anna muhammadan 'abduhu wa rasooluh.
"I bear witness that there is no god except Allah- alone without any partners. And I bear witness that Muhammad is His 'abd (servant) and Messenger."
Allahumma salli 'alaa muhammadinwa 'alaa aali muhammadinwa 'alaa aali muhammadin kamaa sallayta 'alaa aali ibraaheema innaka hameedumajeed. Allahumma baarik 'alaa muhammadin wa 'alaa aali muhammadin kamaa baarakta 'alaa aali ibraaheema wa 'alaa aali ibraheema innaka hameedum majeed.
Bayan ya kamalla ya soma gabatarwa cikin harshen turanci
"We are gathered here today to hold a farewell party for Prime Minister Hateem Obinna, who is a wise and compassionate leader, and a beloved member of the Nigerian community. Though he is the Prime Minister of Canada, he has graced us with his presence and leadership here in Nigeria.
Despite his many responsibilities as the leader of Canada, Prime Minister Hateem has shown great dedication and compassion to our community.
Prime Minister Hateem, you have demonstrated the qualities of a great leader, and your kindness and wisdom have touched the lives of many.
Though we will miss your presence in Nigeria, we know that your work will continue to make a positive impact on our world.
Please accept our gratitude and well-wishes as you return to Canada. May Allah bless you and your family, and may you continue to be a beacon of compassion and strength to all those around you.
Ya ɗan dakata da yin bayanin yana bin kowan nan su da kallo ɗaya bayan ɗaya, ga dukkan alamu kalaman shi sun tsuma zuciyoyinsu duba da yanayin da suka shiga, jikinsu duk yayi sanyi wani irin kewar prime minister da family dinsa suke ji,
Cigaba da magana mc din yayi
_Dear Prime Minister Hateem, We love you, and our love for you extends deep into our hearts. It is with heavy hearts that we say goodbye to you, but we must do so, as it is necessary for you to return to your home, May Allah guide you wit your family and protect you on your journey, and may you return in good health to your loved ones_Best gifts for your loved ones
Jikin su gaba ɗaya yayi sanyi, musamman prime minister, Idanun shi har sun ciko da ruwan hawaye juriya ce ta hana shi fitar da su, bakomai yake tunawa ba face yaron daya kwallafa rai akanshi, mai girma sharafuddeen dake a gafenshi Ya lura da halin da ɗan uwan nasa yake a ciki, ruƙo hannun shi yayi acikin nasa ya ruƙe gam Yana lallashin shi haɗi da bashi baki.
Daga bisani mc din ya gayyaci prime minister daya taso yayi jawabi, jiki ba kwari Ya miƙe Ya hau kan step, cikin sanyin murya yayi magana mai ratsa zuciya, bayan ya gama aka kira gimbiya mujeedat itama tayi nata, Harta su Senate lateef saida suka hau kan step suka bayyana yanayin da suke a ciki na kewar rabuwa da ɗan uwansu, baba obie ma yayi nashi speech din wanda Ya ta6a zukatansu sosai.
Daga bisani komai Ya lafa, Sautin kiraɗa ya cigaba da wanzuwa a cikin hall din, Yayin da servers da ke jigilar raba abinci da kayan sha suka soma gudanar da aikin su.
"Har Yanzu banga mutuniyarki ba, ko ina ta shiga? Watakil taji tsoron hada kanta da mu ne" Her excellency muhibbat ce tayi maganar tana karkaɗa kafarta, Hannunta ruƙe da glass na lemu tana sha.
"Hauka takeyi da zata kawo kanta cikin mu? Ay rijiya ba wurin gaɗar makaho bane, ina nan ina jira inga ta inda zata 6ulo kinsan ba zuciya kare lashe ni nasan zatazo ne" acewar Hajiya saratu, ta fada tana faman tura dambun nama abakinta atsayice take taunsar shi.
Ta6e baki Hajiya Laurat tayi tana fadin"ga ɗayar munafukar can, da yake yau tana a tare da me bata kari ko kallo bamu ishe ta ba, Ƴar kan uba, dalla jibi yadda ta ƙankame hannun shi kamar uban wani ya ce zai kwace mata shi" gaba ɗaya suka sanya dariya suna satar kallon 6angaren da su Hajiya turai suke, baiwar Allah sam hankalinta ba akansu yake ba, batasan ma sunayi ba.
"Taci albarkacin Yaya mubarak, da wallahi yau saina sa ta raina kanta Allah," Acewar Hajiya saratu
Mom madina dake sauraron su bata tanka masu ba, sai dai duk wanda yayi magana ta dube shi.
"Mubar wannan maganar, shin ko kun lura prime minister baya fara'a? Ko dai baya farin ciki da dinner din nan ne wai"? Hajiya muhibbat ce ta fada tana faman yamutsa fuska
Hajiya saratu tace"kinsan yayan nawa bai cika son surutu ba, duk da kasancewarshi ɗan siyasa abu kaɗan ke takura shi, may be baya jin dadin jikin shi ne"
"Anya kuwa? Ni dai nafi tunanin wani abu ke damun shi," acewar Hajiya laurat
,
Hajiya jamila tace"may be yana kewar family dinsa ne, dole yaji ba dadi in fa suka tafi babu wanda yasan ranar dawowarsu, zamuyi missing din su sosai"
Hajiya laurat jefi jefi take wurga idonta ta saci kallon Chief Owais wanda tun shigowarshi hall din yake a hamkimce kan kujera, tare da su Zaki da Justice Nadeem, hankalin shi na akan wayar hannun sa.
Hajiya muhibbat ta lura da ita, hakan yasa tayi mata gyaran murya tare da cewa"Lafiya kuwa naga kin kurawa ɗan naki ido,"
Ta6e baki ta ɗanyi kafin tace"kawai ina mamakin halayansa ne, ni tun da nataso arayuwana ban ta6a ganin baudaddan mutun irin shi ba, mai wuyar sha'ani, kwata kwata owais baya kula ni a matsayina na matar daddyn sa, bansan meyasa ba, babu abun da ke shiga tsanina dashi in ba gaisuwa ba"
Kwa6e fuska Muhibbat tayi"kin ban dariya, ay duk rashin sakarwa mutane fuska da baiyi, bai kai wannan yayan naki ba uban ƴan ji dakai, tun lokacin da yake akan mulkinsa har ya sauka ban ta6a ganin hoton shi da fara'a ba...."
Hajiya Jamila tace"abun da zance kenan, wlh kamar kin shiga zuciyata, Allah najima ina mamakin Alhaji musa gashi dai namiji har namiji sai dai babu annuri a fuska, Har tambayar kaina na ke yi ko yaya matarshi take iya sarrafa shi? Don kuwa wannan mutumin zaiyi wuyar sha'ani"
Hajiya saratu tace"ni kuma wallahi burgeni yakeyi, don bancika son namiji mara kamun kai ba, mai ɗan banzan surutu amma shi daga ganin shi namijin duniya ne, ni har kun tuna min da matar shi muna mutunci da ita sosai lokacin baya"
Murmushin gefen fuska hajiya laurat tayi yayin da take sauraron su
Babu alamun zata tanka masu, ay tun da suka soma zancen yayanta taja baki tayi shiru.
Suna cikin yin fira wayar hajiya saratu tayi ringing daga cikin yar purse dinta, curo wayar tay ta duba me kiran.
Miƙewa tayi har suna haɗa baki wurin tambayarta ina zuwa.
"Surukata ce ta ƙaraso, tun ɗazu nake jiran ta, Yanzu haka jami'e ne suka hana ta shigowa ciki, Bari naje na taho da ita"
Da tsantsar mamaki suka kalli juna, bata bi takansu ba, tayi saurin nufar hanyar fita daga hall din..........
Miƙewa pravin yayi daga mazauninsa Ya nufi area din da bakowa, Ya curo phone dinsa ya danna ma hajjaty kira har sai da ya kusa tsinkewa kafin tayi picking
"Me ya tsayar dake ne har yanzu baki shigo ba, gaba ɗaya kinsa bana jin dadin dinner din"
On the other hand muryar hajjaty tamkar zata fashe da kuka tace"waren ɗan kunnan da zan sanya ne bangani ba, shi na tsaya nema"
Muryarshi da faɗa yace"saboda ibada ne sanya ɗan kunnan ko?
"A'a"
"Idan kika ƙara mintuna baki zo ba, kada kiyi tsammanin zan shigo da ke, kuma wlh Allah yasa inga kin ca6a wannan adon a jikin ki, Ni da ke ne...." ya faɗa tare da katse kiran ya koma mazaunin sa.
Ganin yadda ta ƙanƙame mashi hannu ne yasa shi furta"matsoraci" sunnar dakai ƙasa hajiya turai tayi fuskarta dauke da murmushi
Muryar shi tamkar zaiyi mata raɗa yace"Ki tashi kije wurin ƴan uwanki mata ku yi fira" girgiza mashi kai tayi alamar a'a, ɗaure mata fuska yayi"umarni nake bani" hankalinta ba karamin tashi yayi ba, muryarta na rawa ta furta"dan Allah kabarni anan bana sai naje wurin su," harara ya ɗan watsa mata"kada ki bari na maimaita maki"
jinjina mashi kai tayi alamar toh, ba don taso ba, ta miƙe jikinta na kerma ta juya tana kallon 6angaren da su Hajiya laurat suke, sai fira sukeyi suna shan dariya, tunawa tayi da maganar da ta gaya mata jiya, ji tayi bazata iya zuwa wurinsu.
Miƙewa Sir mubarak yayi a tsanake Ya nufi inda su Prime minister Hateem suke a zaune, ganin ƴan uwan shi maza sunyi mashi rumfa alamar wani abu na faruwa.
yana isa ya shiga cikin su Yana tambayar lafiya, Daddy sharafudden dake a ruƙe da hannun prime minister ne yace"baya jin dadin jikin shi, amma da sauƙi, nasan bai wuci damuwar tafiyar da zaiyi bane," gimbiya mujeedat dake a gefen shi gaba ɗaya ta rasa sukuninta sai faman bin fuskarshi take yi da kallo
Cikin kulawa senate lateef yace"dan Allah ka daure ka saki jikin ka, Idan baba ya fuskanci hankalin da kake a ciki bazai ji dadi ba, bama shi kadai ba, kalli kaga yarda mutanan ka suke raha cikin dangi" ya faɗa yana nuna mashi chief of staff din shi tare da national security advisor na canada sunyi shiga ta hausawa teburin da suke a zaune anan baba obie da abokinsa jan wuya suke, Sai fira sukeyi musamman da aka haɗo masu da High-end whiskey sun sha sunyi tatul in ka cire baba obie shi kadai ne baya shan giya a cikin su.
Lumshe idanu prime minister yayi a hankali batare daya buɗe su ba, shi kanshi baiso yanayin damuwar da yake a ciki ya bayyana ba, ko dan saboda al'ummar da suka taru domin shi.
"Idan akwai abun da kake buƙata ka faɗa mana muyi maka shi," acewar his excellency deen ya fada cikin nuna damuwarshi.
Daƙyar ya bude idanunshi wadanda suka kaɗa jawur da su
Muryar shi ƙasa ƙasa ya furta"lafiyata lou, dan Allah ku kwantar da hankalin ku, kada halin da nake a ciki Ya dame ku"
"Taya zamu iya kwantar da hankalin mu bayan kana a cikin damuwa? pls kayi kokari ka danne zuciyarka ko mun samu a kammala taron nan lafiya, duba fa ka gani gaba ɗaya mun taru ne saboda kai" fuskar Abdul razak A yamutse yayi maganar.
Sai lokacin Hajiya malikat dake a hakimce gefen su tayi ma Gimbiya mujeedat raɗa a kunnanta"ki ja shi ku ke6e ki ji meke damun shi, saboda ke kadaice zaki iya shawo kan shi"
Gimbiya mujeedat taji dadin shawarar malikat.
Duban ƴan uwan nashi tayi"idan ba damuwa inason zanyi magana da shi"
Ta faɗa tare da miƙewa ta ruƙo hannun Prime minister, da sauri jami'an sirrin dake a cikin filin suna shawagi suka take masu baya don basu tsaro, wata corridor suka nufa an ƙawata ko'ina na wurin abakin ƙofar shiga ɗaya daga cikin resting rooms din dakin taron jami'an suka dakata abakin kofar su kuma suka shiga daga ciki.
Duk abun da ke faruwa akan idon chief Owais, ya riga dayasan meke damun uncle din nashi, shi kanshi zuciyarshi ta karaya,
"Babban mutum me kake tunanine"? Muryar Justice ce ta katse mashi zancen zucin nashi
"Tun da muka zauna na lura baka fara'a meke damun ka ne"?
Yamutsa fuska chief owais yayi"bakomai"
"Ko ruwa baka sha ba, Kuma nasan kana Jin yunwa"
Ya fada tare da janyo glass mai ɗauke da juice Ya tura mashi agabanshi, Ya haɗo mashi da suya,
Ba dan yana jin yunwa ba, ya ɗauki glass din ya kur6i lemun wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar shi
"Zaki gafa mutuniyar ka," ɗagowa zaki yayi tare da kallon direction din da justice ya ke nuna mashi, hajiya laurat ya hango.
"ita kaɗai ce makullin da zata buɗe maka kofar haɗuwa da pretty ɗin ka" murmushin gefen fuska ya saki.
"Kana ganin zatayi mana hanya? Ni fa ban ta6a kula ta ba, ko magana bata haɗani da ita"
Cike da kwarin gwiwa Captain Yaseer dake a gefen shi yace"ay dolen ta ne tayi mana abun da muke so,"
"Kwara dai mubi ta lalama, don wlh matarcan da kake gani ba karamar kwaruwa bace, ƙanwar fa Alhaji musa wadata, hmmm baka san shi bane, wlh mutumin nan ba karamin jan wuya bane" acewar justice
Ta6e baki Yaseer yayi"ni ina ruwana da wani alhaji musa, ina magana akan kanwarsa ne,"
"Da yaushe ne zaku yi magana da ita? In ba damuwa ku bani dama ni na tunkareta bayan an gama dinner din" acewar ziyad
"Ni nasan ta yarda zanyi mata magana"
Captain yace"ay dama kai zaka fi iyawa da ita, don wlh ta ce zatayi min ji dakai, tsaf zan dauke ƴar mutane da mari abainar jama'a" gaba ɗaya suka sanya dariya banda chief wanda hankalin shi ba akansu yake ba
"Wlh da kuwa ka kare rayuwarka a gidan kurkukun ƙaddara, don kuwa ta6a matar can ba abune mai sauƙi ba, kai ko shi daddy sharafuddeen ba iyawa zaiyi da itaba, saboda mugun jin kaine dasu ga tarin dukiya da Allah yayi masu" justice ne ya faɗa
Ta6e baki yaseer yayi ba tare daya ƙara furta kalma ba
Idan muka koma 6angaren Hajiya turai, dake atsaye kamar wadda tarasa galihu fargaba Ya hana ta tunkari su Hajiya laurat, baiwar Allah tayi tsaye ita kadai, Sai faman yan waige waige take yi tana neman jazz tasan shi kadai ne zai share mata hawayen ta
Kamar daga sama taji anyi hugging ɗinta ta baya, lokaci ɗaya ta sauke ajiyar zuciya jin sautin dariyar Hajjaty da sauri ta juyo suka fuskanci juna, tun shigowarta Alhazawan nan Na canada suke bin ta da kallo, musamman abokin baba obie dama yajima da dakon soyayyarta a zuciyarsa.
Ita kaɗai ce a filin taron ta sanya Sari na indiyawa, launin red colour, masu ƙyalƙyali, fuskarnan tasha over make up, ga wasu highhills ƴan uban su dake a kafarta, hannunta ɗaya ruƙe da ƴar purse dinta
Wani irin farin cikine ya lullu6e mom turai har batasan sa'adda ta kara huggin dinta ba, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"I'm glad to see you hajjaty, kinga yadda ki ka yi kyau?" ta faɗa tare da dago da kanta tana kallon ta
Su hajiya muhibbat dake kallonsu ransu ya 6aci sai faman buga tsoki suke yi, sunji haushin zuwan hajjaty ɗakin taron saboda yadda taja hankulan dattawan dake awurin, har takaiga sun rasa sukunin su
Ruƙo hannun juna sukayi sai faman sakin mirmushi takeyi kamar wadda akayiwa Albishir da gidan Aljanna
"Me kike yi atsaye ke kadai? Sannan naga idanuwan ki sun ciko da kwalla fada min meya faru" cikin kulawa hajjaty keyi mata magana
Cikin sanyin murya tace"bakomai, kawai banjin dadin zama nikadai," nan take hajjaty ta fahimci abunda ke damunta
Bin ɗakin taron tayi da kallo karaf idanunta suka sauka kansu Her excellency muhibbat
Wani irin mugun kallon harara suke jifarsu dashi.
Ko ta kansu hajjaty bata bi ba, ta ruƙo hannun Mom turai suka samu wuri kan kujeru suka zauna suna ƙara gaisawa, pravin ne yayi magana da masu raba abinci suka kawo masu shaƙe da table, sai rawar kai yakeyi akan hajjaty don yaga hajiya saratu bata a hall din, ƙarfin hali hada zama wurin su.
"Lallai mutumin can, wato don yaga hajiya saratu batanan shine ya zauna yana goga kafaɗa da waccan kilakin" rai a6ace laurat tayi maganar
Muhibbat tace"zata ci ubanta ne wlh, ni dama tun fil azal na tsani matar can, ay tun farko kuskuran da hajiya saratu tayi na auran dangin masu bautar shanu ta kawo su cikin family dinta, wlh mutanan can basu da amana, sun iya munafunci da kisisina, ga kwaɗayin abun duniya, nidai fatana Allah yasa bada wata muguwar manufar suke zaune a family din nan ba"
Guntun tsoki her excellency Jamila taja tace"takaici ma ya hana inyi magana, dalla jibi yadda ta ca6a ado ko kyau babu, mace kamar Aljanna, ita ala dole sai ta fi mu haɗuwa, kowa ya sanya abaya sai ita isassa mai walkin sa taje ta sanya sari, su kuma wadancan dattawan dake ta satar kallon ta bansan uban me suka gani a jikin ta ba.
Hajiya madina na dariya tace"ba dole su kalle taba, mace tana tafiya mazaunai suna jujjuyawa kamar an jera marmarar sakwara" dariya suka saki gaba ɗayan su.
Adai dai lokacin Hajiya saratu ta shigo hall din hannunta ruƙe dana zahra, nan fa hankali ya dawo kansu, zarah duk tasha jinin jikinta ganin zaratan samari da ƴan mata maƙil da hall din, duk da itama ba abaya ba, abaya din dake a jikinta irin na can ƙasan closet ne wadanda ake ji dasu ta dauko ta sanya launin skin pink, ta yi rolling veil akanta ga glass data manna, duk tabi ta ruɗe ganin yadda wasu ke kallonta, bakomai ne yasa suke kallon nata ba face ganin fuskar bare, koda shigowarsu pravin yayi saurin mikewa daga teburin su hajjaty gudun kada Hajiya saratu ta gan shi, lalla6awa yayi ya koma wurin su baba obie ya zauna.
Sai da ta fara zuwa da zahra wurin su hajiya laurat ta gaishe su cikin girmamawa, da fara'a suka amsa mata taci albarkaci Hajiya saratu da kuwa ko kallo bata ishe su ba
"Wacece wannan ko itace surukar taki"? Hajiya jamila ce ta tambaya
Murmushi hajiya saratu tasaki hannunta ɗaya dafe da shoulder din zahra tace"kwarai kuwa, to Ya kuka gan ta"?
"Masha Allah, kyakkyawa da ita son kowa kin wanda ya rasa, malama zahra sannu da zuwa" muryarta ƙasa ƙasa ta amsa masu.
Jan hannunta hajiya saratu tayi"mu shiga ciki" tafiya su ka yi cikin hall din sai faman yan waige waige zahra ta ke yi, fargabanta bata san inda hajiya saratu zata kaita ba.
Su twins ta hango kowan nan su ya ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya kan kujeru, tare da Dr Nawaz, wurin su hajiya saratu ta nufa da zahara wadda tuni gabanta ya soma dakan uku uku, hankalinta ba karamin tashi yayi ba, ganin suna tunkararsu
"Barkan ku da hutawa" a tare suka dago suna kallon ta
"Mom..." zaid ne ya kira sunanta bai karasa ba yai tozali da zahra,
Kallo ɗaya zayn yai mata ya kau da idonshi yaci gaba da danna wayar hannun shi, har kwara dr nawaz da dan fara a face din shi
"Yawwa ajiya na kawo maku, zahra ki zauna a wurin su, dan Allah ku kula mun da ita" amsa mata zaid yai da toh tare da nuna ma zahra kujera"have a seat," jikinta na kerma kerma ta zauna duk tasha jinin jikinta, sam ba ta so hajiya saratu ta kawota cikin maza ba, Ina laifin wurin ƴan matasan matan family din duk da tasan ba lallai ta samu shiga a wurin su ba.
Cikin kulawa hajiya saratu tace"Idan kina buƙatar wani abu, ki faɗa masu zasu sa akawo maki, pls ki saki jikin ki, Idan aka kammala taron zanyi magana dake kafin ki tafi gida' amsa mata tayi da toh
Bayan tafiyar hajiya saratu, zaid Ya soma jan ta da fira.
"Kamar naso na gane ki" murmushi ta ɗanyi tare da cewa"ina ɗaya daga cikin interior designers din da suka yi aiki lokacin birthday din ku dana baba obie"
"Oh yes, I remember now, What's your name"?
"Zahra"
"You look absolutely beautiful today" still face din ta da murnushi tace"thank u"
Dr nawaz ya dube ta daga ƙasa har sama farat ɗaya ya gane ba ƴar masu kuɗi bace sai dai akwai kyau ko dan saboda wannan zai ɗan daraja ta.
"Bimillah malama zahra" ya fada tare da miƙa mata glass na ruwa me sanyi
ya haɗa mata da plate din chicken kebabs, godiya tayi mashi, harta kai hannu zata sauki glass din zayn ya ɗago da sexy eyes din nan nashi wani kallo ya jefa mata mai kama da harara, gaba ɗaya ta rikice ta fasa ɗaukar komai, ta duƙar da kanta ƙasa.
"Are you okey? Ki ci mana" zaid ne ya fada yana ɗage mata gira.
Dr nawaz yace"na lura kamar hankalin ta bai kwanta ba, Bari nayi magana da faryat inyaso sai ta koma wurin su ta zauna may be tafi sakewa'
Har cikin ranta taji dadin maganar dr nawaz, wayar dake a hannun shi ya shiga dannawa ya kira layin faryat kusan sau uku batayi picking ba, a kira na huɗu ne ta ɗaga.
"Ina son ganin ki yanzu ki zo ki same ni" ya fada yana bin hall din da kallo Can Ya hangota, Cikin su Hindu sun zaƙe sai fira sukeyi kowaccen su hannunta ruƙe da glass na lemu.
Cikin takun yanga da kwarkwasa Faryat ta nufo wurinsu, tana karasowa ta ruƙe qugu tana fadin"Gani"
da gira zaid Ya nuna mata zahra"bakuwar mommy ce, pls ki tafi da ita wurin ku"
Wani kallon shaƙiyanci tabi Zahra da shi kafin Ta miƙa mata hannu"let's go" miƙewa zahra tayi faryat ta ruƙo hannun ta suka nufi wurin Ƴan uwanta.
"Faryat ina kika kwaso mana wannan" Yusrace ta fada tana nuna zahra da hannu, baiwar Allah jikinta duk yayi sanyi duk zumudin da takeyi na son zuwa ya ragu
"Bakuwar mommyne, Yaya zaid ne yace in kawota wurin mu" wani kallo suke bin ta dashi daga ƙasa har sama alamar ba'ajinsu bace,
"Barka da zuwa ƴan mata, Zo ki zauna kusa dani," zulaihat ce tayi maganar fuskarta da fara'a, Hakan ba karamin sanyaya zuciyar zahra yayi ba, gefen zulaihat ta zauna, Hindu tace da ita"kina bukatar wani abu naci ko sha"?
Ɗaga kai zahra tayi alamar eh, saboda yunwa take, bata ci komai ba kafin ta baro gida
Magana tayi da server din dake a kusa da su tasa aka kawo ma zahra lafiyayyan abinci, tare da juices masu sanyi
"Zaki iya ci kona baki abaki"? murmushine ya kubce mata jin abun da zulaiha tace
Da sauri ta girgiza kai"a'a zan iya ci dakaina, nagode da kulawa"
Hindu tace"kada kiji komai, ki saki jikinki, Ki ɗauka kamar kina a jirgi ne mai ya kare" dariya sukayi gaba dayansu cikin raha, zahra har ta fara sake wa
"Meye sunanki ne"? Yusra ce ta tambaye ta
"Zahra"
"Masha Allah, family status fa"? Ras taji gabanta ya fadi aranta ta ayyana komai ya kawo maganar family status?
Jin tayi shiru yasa yusra cewa"dake magana"
Cikin sanyin murya tace"ɗan iya family" kallon juna su ka yi alamar basu ta6a jin sunan ba, hakan na nufin ba ƴar kowa bace, ta6e baki yusra tayi
"Ni sunana yusra, ƴar gidan His excellency abdul razak, Jikar baba obinna, nayi karatu a U.S, na kammala degree dina a 6angaren medicine and surgery, ke fa"? Da izgilanci takeyiwa zahra magana
ganin abun nata na neman wuce gona da iri ne yasa Zulaihat yin saurin tarar nunfashin ta da cewa"look Yusra, Ki ƙyale bakuwar tamu ta huta mana, ko ruwa bata sha ba, kin fara tsareta da tambayoyi kamar ƴar jarida" dariyar shakiyanci yusta tayi idonta acikin na Zahra tace"am sorry fa, kawai ina so ne musan juna, amma bakomai, nayi shiru"
Kasa cin abincin zahra tayi, gabanta nata faduwa, sam jin kanta takeyi bare a cikin su saboda tarbar da wasu sukayi mata.
"Companyn ku ne sukayi decoration din nan ko"? Zulaihat ce tayi mata tambayar jinjina kai zahra tay alamar eh
"Masha Allah, gaskiya kuna da kwararrun interior designers, na jinjina maku, nima idan lokacin birthday dina yayi zan gayyace ku"
Murmushi zahra tayi har cikin ranta taji dadin yadda zulaihat ta sakar mata fuska ita da hindu daga gani sun san darajar ɗan adam ba kamar Yusra da faryat ba.
Sautin kiɗane Ya soma tashi, Mc yaci gaba da kiran Su daya bayan ɗaya suke shiga filin Taron suna taka rawa ta ko'ina sautin shewarsu ne da Dariya yake ya tashi, Bakomai ne Ya burge su ba face yadda mukarraban hateem na kasar canada suka hau kan dance floor suka dinga tiƙar rawa dama sun sha sun bugu har takai masu karo, ga abokin baba obie shima yana tangyal tangyal ya shiga tsakiyar filin Ya dinga tiƙar rawa, Nan fa ƴan mata suka dinga shiga suna yin rawa tare da su.....
Tun da aka fara taron Nazli ke a zaune saman wata kujera ta alfarma, ta daura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, fuskarta babu annuri, a tsanake take danna wayar hannunta, lokaci ɗaya ta dakata tana kallon message din da aka tura ma chief owais ta layinta, nan take fuskarta ta canza zuwa tsantsar 6acin rai, tasan bakowane zaiyi mata haka ba face Yazrin, A hankali ta ɗago kyawawan idanunta tana bin hall din da kallo a kokarinta nata gano inda Yazrin ta shiga, Cikin rashin sa'a ta sauke idanunta akan chief owais dai dai lokacin ya ɗago suka haɗa ido da shi, kasa janye idanunta tayi daga kan shi, wani irin kyau taga ya ƙara mata musamman daya sanya shadda a jikin shi, kau da idanunsa yayi daga kan nata, itama ta janye nata, kamar wasu makiyan juna
Text ta tura mashi
_sakon da aka tura maka ta layi na bani na tura shi ba_
Reply yai mata da cewa"I don't know what message you're referring to_.
Shiru tayi tana tunanin me yake nufi? Ko dai bai ga sakon ba.
Wani sakon ne ya kuma shigowa wayarta
_"Why did you send me a video of you on WhatsApp? Nace maki ina ra'ayi ne?
Wani irin bugu kirjinta yayi, cikin sauri ta shiga whatsapp don ganin inda gaske an tura mashi video tana shiga ta taras da aika aikan da Yazrin tayi mata, Dafe kai tayi da hannu ɗaya, ji tayi tamkar ta fasa ihu tsabar takaicin zubda mata ajin da Yazrin tayi
_"I didn't send you any video! You know I would never do such a thing. This must be Yazrin's doing!"_
_"I don't care about the excuses, I already understand that you're missing me. If you miss me so much, you know where to find me"_
ya rubuta text din tare da yi mata sending kafin ya ɗaura wayar kan table din gabanshi.
Ta wutsiyar idanun shi yake hangota, runtse idanunta tayi tare da cije pink lips dinta, hakan ba karanin ƙayatar da shi yayi ba.
Kifa kanta tayi kan laps dinta, yatsun hannunta har kerma sukeyi tsabar 6acin rai.
Shin Ina Prime minister?
Tun bayan shigarsu resting room, gimbiya mujeedat ta soma tarairayarshi tana kwantar mashi da hankalin shi, ganin yadda yake zubda gumi yasa ta taimaka mashi wurin cire rigar shi, Ya rage daga shi sai yar singlet, atsaye suke gaban mirror suna fuskantar juna.
"Fada min meke damun ka"? Ta fada cikin kulawa tare da daura palm din hanunta kan wuyan shi.
Har wani jiri yake gani a cikin idanun shi abu kamar jaraba ƙaunar Danish na neman zautar da shi, hatta tempereture din jikin shi ya ɗauki zafi rau kamar mai fama da zazza6i.
Sam yakasa fada mata gaskiyar abun da ke damun shi saboda jin kunyar furtawa yake yi
"hankalina bazai kwanta ba in har baka fada min ba, kasan tsakanina dakai babu 6oye 6oye, "
Ɗaura head dinsa yai kan shoulder dinta, ya daddafe waist dinta da tafukan hannayensa
Yana faman fitar da nunfashi da sauri sauri
"Idan baka da lafiya zanyi magana a kira doctor ya duba min kai"
da sauri ya furta"lafiyana lau,"
"Taya zan yadda da maganarka? Lokaci ɗaya ka canza kafin mu shigo dakin taron nan babu abun da ke damunka fuskarka da annurin farin ciki amma lokaci ɗaya ka canza mana meyasa? Hatta yanayin jikinka ya dauki zafi rau.... " fuskarta a yamutse tayi maganar
Ɗago da fuskarshi yayi tare da kallon ta, ya sanya palms dinsa ya tallabi fuskarta dake asanye da gold chain
"Ki kwantar da hankalin ki, kinsan dai bazan maki karya ba, kamar yadda na fada maki babu abun da ke damuna, zuciyata ne ke bata min dadi"
Wani kallon kauna ta jefa mashi"ban yarda ba, Ko dai akan wannan Yaron ne na wurin owais"?
Da mamaki ya kalle ta jin ta gano abun da ke damun shi
"Ai ina lura da duk wani motsin ka, Jiya saboda shi baka runtsa ba ka zauna yi mashi nafila ko ba haka ba" ta fada tana binsa da kallon na kamaka
Kamar wani mara gaskiya yayi shiru yana kallon ta
"Har hotunan shi ka ajiye awayarka, lokacin da naje tada ka daga bacci naga hoton shi da kake kallo a wellpaper na wayar ka, mijina anya kuwa kana da lafiya?
Ta faɗa fuskarta da tsantsar Al'ajabi
Lumshe idanun shi yayi bai san amsar da zai bata ba
"Akan yaron da bakasan ko wanene ba kake nema ka rasa sarrafa zuciyarka? What kind of crazy love is this? Na ruɗe please ka fahimtar dani' ta fada tana zare mashi kyawawan idanuwantaBest gifts for your loved ones
"You don't know who he is, you have no connection to him, so why would you cause yourself so much pain for loving him" Cikin tausasa murya tayi maganar, bawan Allah yayi shiru yana sauraranta ya rasa abun fada.Best gifts for your loved ones
"Hankalina ya tashi hubby, kwara mubar kasar nan tunkafin In rasa kanka, Maybe if we distance ourselves from him, you'll be able to forget about him.... " cikin karyayyar murya tai maganar, fuskarta duk ta yamutse.
"Idan ma akan rashin haihur ɗa namiji da baka samu bane yasa kake son shi, nayi maka alkawarin zan dage da addu'a akan Allah ya bani ciki na ɗa namiji nima na haifa maka ko hankalin ka ya kwanta, zan kira mahaifina in fada mashi yasa ayi min addu'a...." tuni idanunta sun cicciko tab da kwalla, nan fa hankalin shi ya tashi don ko kadan baison 6acin ran gimbiya mujeedat gaba ɗaya yake rasa sukuninsa, da sauri ya janyota jikin shi.
ya rungumeta sosai yana lallashinta,
"Na gane kuskure na, ki yi hakuri gimbiyata, nima bayin kaina bane bansan ya akai na kamu da kaunarsa har haka ba, amma tun da baki so na daina, zanyi kokarin mantawa da shi arayuwana....' lallashinta yaci gaba da yi har sai da yaga ta dan saki jikinta kafin ya ɗago da ita.
chain mask dinta Ya gyarata mata ganin ya karkace, bayan ya gama suka kalli juna lokaci ɗaya suka saki murmushi, yatsun hannun ta ya ruƙo ahankali ya daura mata soft lips dinsa hadi da sumbatar su, ya kuma dagowa ya sumbaci forehead dinta, sai da ya tabbatar ya faranta mata almost 15 mins, tukunna ya mayar da rigarsa, kafin Yaja hannun ta suka nufi kofar fitowa daga room din, Jami'an dake a bakin door suna jiran su, ganin sun fito yasa suka take masu baya.
Suna gab da zasu ƙarasa ga mazaunin su, ba zato ba tsammani Hasken Hall ɗin Ya ɗauke gaba ɗaya duff ko'ina Yayi duhu sai hasken candles din dake a kunne, Hankalin jama'a ba karamin tashi yayi ba, Kowa Ya ruɗe sautin muryoyin su Ya cika hall din Kowa sai tambaya yake yi ya akai aka dauke wutar hall din ko an samu matsala ne
"Jama'a wai meke faruwa ne? Meyasa za'a ɗauke mana hasken Hall? Ba'aji ina magana ba ne"! Hajiya saratu ce take ta faman surfa masifa Sautin muryarta yafi na kowa
Faryat Har ta fara Fasa masu ihu saboda lalurar dake gare ta na rashin son duhu gaba ɗaya take firgicewa ta dinga kuka tana iface iface, Jazz na jin sautin ta jiki na bari ya shiga laluban ta cikin duhu cikin sa'a Ya cafko hannunta ta ƙanƙame shi tana kuka....
"Wannan wani irin rainin wayau ne za'abar mutane cikin duhu? Hajiya laurat ce ta faɗa atsiwace ran kowa Ya harzuƙa, Hankalin zahra ba karamin tashi yayi ba fargaban ta kada ace Aikin decoration dinsu ne Yajawo matsalar, tuni ƴan hanjin cikin ta suka kaɗa ido ya raina fata, harta fara tunanin zuwa prison.
_Kwatsam ba zato ba tsammani, A lokacin da kowa Ya gama rikicewa wani Haske mai ƙyalƙyali daga saman ceilling Ya soma baiyana A hankali Ya ke haskaka bakin ƙofar shigowa Hall din, gently ya dira ƙafarsa kan Polished marble floor din wurin A matuƙar ruɗe suka kai idanunsu kan mai shigowa yayin da zuciyoyinsu ke harbawa da ƙarfi ƙarfi_
(Mu hadu monday idan Allah ya kai mu da rai da lafiya in sha Allah)
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 12 Complete
by
Novels Elite Admin
May 28, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
12
سجن القدر💋✊🔥
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Gently ya dira ƙafarsa kan Polished marble floor din wurin A matuƙar ruɗe suka kai idanunsu kan mai shigowa yayin da zuciyoyinsu ke harbawa da ƙarfi ƙarfi.
Lokacin daya ƙarasa shigowa ciki, Gaba ɗaya Suke bin shi da kallo mai cike da tsantsar ruɗani, idanun kowa akan zazzafar surar jikin shi, kasancewar ya sanya face mask hakan ya 6oye ainihin suffar fuskarsa, wato wata hadaddiyar Emirati thobe ce a jikin shi yar ubansu launin Black gold, yadda kasan a jikin shi aka ɗinka ta saboda yadda ta bi shape nasa, ta baiyanar da surar shi mai matuƙar jan hankali, Musamman sick packs din kirjinsa ya fito 6aro 6aro, da murɗaɗɗan damtsensa, abun ka ga dogon namiji komai nashi is exraordinary, farar fatarsa kuwa har wani salƙi take tana walwali, yadda kasan namijin hurul aini tsabar kyau da daukar ido, wrist din hannun sa na asanye da agogo ƙirar Rolex sai ƙyalli take, face mask din dake lullu6e da fuskarshi dai dai ƙasan idanunsa ya rufe kyawawan sexy eyes dinsa waɗanda ke a kewaye da lallausan long eye lashes dark brown sun ƙara ƙawata kyawun idanunsa, yalwatacciyar sumar kanshi kuwa tasha gyara har ƙyalli take, gaba ɗaya gashin an tattare shi an ɗaure yasauka har kan gadon bayan sa, Wani irin sanyayyan ƙamshin turare ne ke fita daga jikin shi mai narkar da zuciya,
Hankali fa gaba ɗaya ya tashi da ganin ɗan tahalikin nan, tun kafin ma ya buɗe fuskarshi sun gama girgiza da kyawun shi, kowannansu sake sake yake a zuciyarsa wanene wannan? Daga ina Yake?
Zuciyoyinsu ba su gama kiɗima ba, sai da su ka yi tozali da kyakkyawar matashiyar dake shigowa hall ɗin ta bayan shi, wohoho zo ka ga yadda idanu suka koma kanta, from head to toe suke kallon ta, ta ɗauki wankan Embroidery Open front baya, launin black anyi mata adon gold stone works da zanan Red flowers, rigar tayi masifar yi mata kyau, ta yi rolling mayafi akanta, itama fuskarta asanye da face mask take, ƙafafuwanta kuwa Highhills ne jigunanu, Tsabar ruɗani Ya hana kowa na hall din furta magana sai dai su bi da idanu kamar kurame, ko da shigowarta daga gefen shi ta tsaya, Jim kadan suka cigaba da shugowa kowan nan su da face mask, matan cikin shiga ta abaya mazan kuma Emirati thobe ne a jikin su, sai da suka cika su goma sha ɗaya cuff tukunna suka dakata suna kallon kallo atsakanin su da mutanan hall din, ga dukkan alamu bakin su ya mutu, saboda babu alamun zasu furta magana, lamarin ya ruɗar da su, mamakin su ina aka samu wadannan matasan yan matan da samari? Daga gani dai ba yan nahiyar su bane saboda komai nasu is exraordinary, dai dai da yanayin tsayuwarsu abun kallo ne kamar a shirin drama.
A ƙalla an shafe tsawon Mintuna ana jifar juna da kallon ƙurulla, daƙyar Hajiya saratu ta samu ƙwarin giwar buɗe baki ta furta"Su wanene ku"? Ta jefa masu tambayar tana mai zare idanu
"Bayin Allah daga ina ku ke? Wanene Ya gayyace ku dinner din nan? Meyasa ku ka rufe fuskokin ku da face masks? Hajiya Madina ce tayi maganar a ƙagare da son jin amsarsu
Gaba ɗaya mutanan hall din suka matso gab da su, kamar sunga sabbin halittu daga wata duniyar
"To ko dai mutanan boye ne? Wai ba zakuyi mana magana ba, kuntsaya kuna kallon mu kun bar mu a cikin duhu"! Da tsiwa hajiya laurat ta faɗa tana tada jijiyoyin wuya.
"Anya kuwa waɗannan ba mutanan 6oye bane? Nifa wlh hankali na bai kwanta da su ba, akan me zaku faɗowa mutane ɗakin taro babu sallama? mun tambaye ku su wanene ku kun yi shiru ba ku tanka mana ba, ko dai turo ku akayi ne don ku tarwatsa mana taron mu"! A faɗa ce Hajiya saratu ta kuma yin magana, Hankalin fa kowa Ya tashi wasu sun harzuƙa, su kan su tsabar fargaba ne ya hana su buɗe baki suyi masu sallama, duk sun sha jinin jikin su.
Baba obie da Manyan mutanan canada sunyi kasaƙai Suna Kallon su tamkar a shirin drama, sam babu alamun sun tsorata da ganinsu saboda sun san akwai jami'an dake tsaron gurin dole akwai wanda ya gayyace su, sai dai zallar mamakin dake shimfiɗe a kan fuskokin su.
Ƴan matasan family din maza da matansu sunyi cirko curko suna kallon su, cike da son sanin su wanene wadannan bakuwar fuskan da suka faɗo masu a hall!!!
Mc da ke atsaye ya ruƙe mic sai mazurai yake yana fadin"ga dukkan alamu mun samu baƙi daga jinsin aljanu, suma sunzo taya mu jimamin tafiyar prime minister Hateem, wannan abun mamaki ne da al'ajabi, lallai prime minister ba karamin mai farin jini ba ne......." sai sambatu mc yake yi yana dubansu babu alamun wasa akan fuskarshi, bilhakki dagaske yake koro jawabi, su sir mubarak kuwa jira kawai suke suga iya gudun ruwan wadannan bayin Allahn da suka faɗo masu bagatantan babu sanarwa.
Sannu A hankali sautin takalman prime minister ya karaɗe tsakar filin, babu fargaba ko kaɗan Ya nufi inda suke har ya ƙarasa gaban matashin nan daya fara shigowa kafin yaci burki yana bin shi da kallo tun daga sama har ƙasa, hakanan ranshi ya dinga bashi cewar yaron daya jima yana kwaɗayin sanyawa a idanun shi ne, zuciyarshi ce ta soma azalzalar shi da son tabbatar da abun da yake hasashe, a hankali Ya juyo baya ya dubi chief owais dake a can gefe ɗaya ya goya hannayensa bisa ga kirjinsa tamkar baisan meke wakana ba
Haɗa ido su kayi da prime minister, cikin sanyin murya ya furta"shi ne...?
*WAIWAYE A DON TAFIYA*
Abun da ya faru, lokacin da Chief ya dawo gidan bai samu kowa a falon ba,, har su naufal da suka zauna sun koma daku nan su, direct Ya nufi bedroom dinsa bayan shigar shi, tsayawa yayi agaban mirror zuciyarsa a cike fal da tunanin ta wace hanya zai iya taimaka ma Uncle dinsa! Saboda yaji tsantsar tausayinsa ganin irin halin da ya shiga na kaunar yaron, bai da burin daya wuce danish ya farka ko dan Ya faranta Ma daddy hateem kafin yabar nigeria....
Yayin da ya ke wannan tunanin Yana safa da marwa a tsakar ɗakin sa Ya shafe kusan Mintuna ashirin, Batare daya samu mafita ba, Yanke shawarar kiran layin ɗaya cikin drs dinsu yayi don azo aduba lafiyarshi wata'kil adace, duk da shiekh Imam Ya ce basai sun kira likita ba saboda rashin lafiyar tasa bata asibiti bace, kawai a lokaci Ya ƙosane daya farkan shiyasa ya yi deciding kiran likita.
A firgice ta farka daga gajeran baccin da yayi awon gaba da ita tun bayan kammala sallar azhar, Hannun ta dafe da saitin zuciyarta dake yi mata wani irin bugu tamkar ana dakan sakwara, wani irin faɗuwar gaba ta soma ji, Hankalin ta sam ba'a kwance yake ba, tarasa gane dalilin jin bugun da zuciyarta take yi mata da rana tsaka, kuma ita ba mafarki tayi ba, saukkowa tayi daga kan gadon su, batool dake a kwance babu alamun zata farka, Cikin sauri ta fito daga room dinsu zuciyarta na azalzalarta da taje ta ƙara duba danish dinsu don tana ji aranta wani abu ne ke faruwa da daya daga cikin su shiyasa taji wannan faduwar gaban, kuma bakowa ne ya fara fado mata aranta ba face shi din dama da tunanin shi ta wuni.
Gudu gudu sauri sauri ta nufi second floor, ko da ta shiga falon babu kowa.
Tana ƙarasawa bakin ƙofar ta sanya hannu biyu ta dafe ta da karfi har sai da ta buɗe kafin ta faɗa a fujajen shigarta keda wuya, idanun ta su kayi mata tozali da abun da Ya figitar da ita, da wani irin faduwar gaba take kallon shimfidar shi.
Wata irin zuface take tsastsafo mashi tun daga cikin sumar kanshi take gangarowa har izuwa saman fatar wuyan shi, kyakkyawar fuskarshi ta jiƙe sharkaf da gumi, hatta jallabiyar jikin shi ta manne ma fatarshi saboda ruwan zufar daya jiƙe ta, muryart na kerma ta soma kokarin ambaton sunan shi.
"Dad...da..nish" bata ƙare maganar ba, ganin yadda yatsun hannayensa dana ƙafafuwansa suka fara kerma tamkar na wanda sanyi ya kama.
Kasa samun nutsuwa tayi, har batasan sa'adda ta haura saman gadon nashi da rarrafe ta ƙarasa saitin inda kanshi ya ke, ta zuba mashi ido tana kallon shi da tsananin firgi ci.
Cikin lokaci ƙanƙani, Ilahirin Jikinsa Ya jiƙe sharkaf da gumin zufa, lamarin yayi matuƙar ɗaure mata kai.
Tsabar Yadda Jikinsa ke kakarwa Har gadon kerma yake yi ita kanta jikinta ya kama kakarwa, tun zuciyarshi na bugawa a hankali har ta fara bugawa da matsanancin ƙarfi kamar zata fasa kirjinsa ta fito waje, sautin numfashinsa mai haɗe da gurnani ya gauraye bedroom dinsa, da karfi Yake Jan shi tamkar babu wadatacciyar iskar da zai shaƙa.
Ko wani sashe na jikin shi tuni ya soma motsawa, Unaisah dake kallon shi idanunta azazzare duk tabi ta rude ta firgice Lokaci ɗaya tsoro Ya cika ta, Zabura tayi da niyar ta watsa aguje gudun kada Ya cutar da ita don ta fahimci kamar baya hayyacin sa ...
Sai dai kafin tayi wani yunkuri juyawa yayi wani kwakkwaran juyi tamkar mayunwacin zaki haka Ya damƙo sumar kan nan nata daya sha gyara gaba ɗaya ya dawo da ita jikin sa, Yana huci ya matseta kamar zai tsinkata biyu, Ji tayi tamkar an daureta da igiyoyin kaca, hucin zafin jikinsa har anata jikin take jin shi, Zuciyarta ce ta bata shawarar ta hankaɗe shi ta gudu, kafin yai yunƙurin cutar da ita, Cikin ƙarfin Hali ta daddage ta fusge kanta daga ruƙon da yayi mata, gaba ɗaya ta kundumo saman tiles kanta ya daku, Harta zabura zata mike da niyar ta watsa a guje taji ya damƙi ƙafarta ɗaya, ta ƙarfi ya janyota kamar ɗiyar roba ya dawo da ita saman gadon, runtse idanunta tayi da sauri tana ambaton La'ila ha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin.
Dogayen yatsun hannayensa dake kerma ya ɗaura saman wuyanta, ya shaƙeta sosai tamkar zai tsinka wuyan, radadin azabane ya ziyarce ta, ta kware baki ta fasa wata irin ƙara mai sautin gaske, sai faman kiciniyar kwace kanta take yi amma ta kasa saboda ƙarfin dake gare shi tamkar zaki a haka ma don bai da koshin lafiya da tuni yajima da kashe ta cikin rashin sani. Radadin da tajine yasa ta fashe da matsanancin kuka mai sautin gaske
Adai dai Lokacin Ummi ta fito daga room din ta, don taje ta fara shiryasu ganin lokacin dinner din Ya kusa Cika
Har ta nufi stairs zata hau, kunnuwan ta suka soma jiyo mata Gunji gunjin kukan unaisah, Lokaci ɗaya taji gabanta yai mugun faɗuwa, tsabar rudanine akan fuskanta, fasa sauka tayi cikin takun sauri take bin hanyar da take jiyo sautin kukan cike da was wasin kodai kunnuwanta ne suke jiyo mata badai dai ba
A hanzarce takarasa Bakin kofar, ta soma bubbugata tamkar zata 6alleta, muryarta da sauti mai karfi take ambaton sunanta"Unaisah!! Unaisa!! Unaisah"
Kofar tamkar an datse ta da key taki buɗewa ta rufe gam, kware murya ummi tayi tana ambaton ba kowa ne akusa? Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un unaisah idan kinaji na ki yi min magana! Meke faruwa dake ne'?_
Ta faɗa jiki na tsuma ta zura hannu ɗaya ta dauko wayarta daga cikin aljihun skirt dinta.
Layin boss man ta danna ma kira bugu biyu yayi picking ko sallama babu tace"yalla6ai kazo gida an samu matsala, na fito daga daki na na ji yo sautin muryar unaisah a dakin danish tana kuka na tashin hankali, nayi kokarin buɗe kofar ta datse..."
Muryarshi a ruɗe Ya furta"Chief bai dawo ba"? Yarfa hannu ummi tayi "bansani ba, yanzu na fito daga daki.... bai bari ta ƙare maganar Ba, Yayi rejecting kiran ranta ne ya 6ata cewar zai zo, tsayawa tayi abakin kofar Idanun ta sun kaɗa jawur ta tsorata dajin ihun unaisah, lokaci daya taji shuru babu ihun nata nan fa hankalinta ya kara tashi tadinga buga kofar da hannu da kafa Tana Ambaton"Unaisah dan Allah Kiyi min magana? Danish Ya farkane? Me yake yi maki? Meyasa kike kuka, Nashiga ukuna, Unaisah kada ki bari Ya cutar dake, Kiyi kokarin kare kanki! Unaisah kina jina? Naji kinyi shiru inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un..." hawaye har sun fara wanke fuskar ummi saboda ta gama gigita Zuciya da sake sake gani take kamar Danish Ya kashe ta ne shiyasa tajiyo shirunta.
Kamar an jeho shi Ya faɗo falon A fujajen, wuyan jallabiyar shi ma akarkace take sam baya a hayyacinsa, da gudu Ya falfala Ya haye up inda ummi take atsaye tana faman buge bugen ƙofa, yana karasawa Ya daddage da iya karfin shi na karshe Ya bangaje ta da kafadarsa nan take kofar Ta zuge kanta da gudun gaske, Tsabar saurin su shiga suga meke wakana har suna bangaje juna shi da ummin america, duk wannan budurin da ake sauran yan uwan su basu san meke faruwa ba.
Shigar su keda wuya, suka taras da abun da ya daure musu kai, Yana azaune bakin gadon Ya duƙar da kanshi kasa, Sumar kanshi Ta lullu6e fuskar Unaisah wadda kanta yake abisa cinyoyinsa' basa iya ganin fuskarta sai ƴan kafafuwanta, cike da fargaba da karyewar zuciya boss Ya furta Sunan shi"Danish! Unaisa meya faru ne? Ka yi mata wani abu ne? Haƙiƙa sun yi mamakin farkawarsa babu wanda yayi tsammanin zai tashi a cikin ƴan kwanakin nan.
Adabarbarce ya kare maganar, tamkar yayi magana da bango babu alamun danish zai saurare su duk sun bi sun rude mutun kamar Ifritun aljani gashi ya damki yarinya a hannun shi
Cikin shessheƙar kuka Ummi take rokonshi akan Ya saketa, kada ya kashe masu ita.....'
Karfin Hali taj yayi da sauri Ya nufi gefen gadon inda su ke a zaune Ya miƙa hannayenshi biyu da niyar ya kawar da ita, Damƙar hannunsa Danish yayi tare da dagowa yana faman lumshe idanun shi tamkar na wanda yasha giya, muryar shi da kasala Ya furta"ina bukatar ruwan da zan yayyafa mata" kusan atare ummi da Taj suka sauke ajiyar zuciya, saboda sunyi tsammanin baya ahayyacinsa ne.
juyawa ummi tayi da sauri ta fita daga dakin sai gata ta dawo hannunta ruƙe da robar ruwan da ta ɗauko a fridge ta miƙa ma taj, shi kuma Ya kar6a ya Miƙa ma danish, a hankali Ya sanya hannu ya kar6a bayan ya cire murfin ya tarfa hannunsa dake ɗan kerma Ya ɗebi ruwan ya watsa mata akan fuskarta, lokaci ɗaya ta zabura zata fara buge buge da sauri boss Ya damƙi hannunta, tare da dago da ita ya zaunar.
Wani jiri jiri take gani a idanunta, hannu tasa ta dafe makoshinta tana fadin ruwa ruwa zan sha.
Kwafa mata ruwan yayi abaki ta rurruke robar duka ta shanye shi, ta dago da luhu luhu idanunta wadanda suka kada jawur da su Sam ta manta a ina take zaune, gani take kamar amafarki lamarin Ya afku, Kwata kwata bata lura da danish ba, wanda ke a gefenta kuma shi ya bata ruwan da ta sha.
"Unaisah, are you okey? Ina fata bai ta6a lafiyar jikin ki ba"! Cikin kulawa ummi keyi mata magana
Kallon ummi tayi murya na ɗan rawa ta furta"nayi mafarki danish Ya farka, Har Ya shaƙe min wuyana" ta faɗa tana shafa wuyanta
"Ba mafarki ki ka yi ba, dagaske ne Ya faru, danish Ya farka sai dai baya a hayyacinsa ne lokacin daya shaƙe ki" boss ne ya bata amsa, da wani irin Hanzari ta dubi danish da ke gefen ta, idanunsa suna a lumshe numfashin sa na fita a hankali.
Lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kukan farin ciki, ta kamo yatsun hannayensa acikin nata, Muryarta cikin shessheƙar kuka take fadin"My man...kana lafiya? jinjina mata kai ya danyi alamar eh.
"Alhamdulillah Ya Allah, Alhamdulillah..." sakin hannunsa tayi ta sauko daga kan gadon ta zube saman gwiwowinta tare dakai goshi kasa tayi sujjada tana mai nuna godiyarta ga Allah.
Murmushi taj ya soma saki yana kallon danish, Wani irin farin ciki ne Ya lullu6e shi mara misaltuwa Yaji dadin farfadowar nan tashi, Har ya fara tunanin haduwar shi da Prime minister.
Har yanzu Danish babu fara'a akan fuskar shi, jefi jefi Ya ke kallon su da lumsassun idanunsa, ganin lokaci na shirin kure masu yasa ummi ruko hannun unaisah tace su tafi su fara shiryawa, kamar karta baro dakin tana tafiya tana waiwayon danish gani ta ke kamar in ta fita zai koma yar gidan jiya, har sai da boss yace mata zai kira chief yanzu awaya tare da sheikh imam tukunna ta ɗan samu kwarin gwiwar barin dakin.....
Batare da 6ata lokaci ba, Taj Ya kira chief awaya ya sanar da shi dangane da farfaɗowar danish, A lokacin chief Har Ya kira likitan da zai duba shi, yayi murnar jin zancen tashin danish, kafin ma karasowar su dakin sai da ya Kira Shiekh Imam suka jira Ya zo falon Kafin suka sauko shi da likitan dayazo duba dashi a tare suka nufi dakin shigar su keda wuya Chief owais ya nufi danish, tamkar dan uwansa na jini Ya miƙa mashi hannu ya taimaka mashi ya sauko daga kan gadon gaba ɗaya yayi hugging dinsa a jikin shi, ya ɗaura hannayensa abayansa yana dan bubbuga shi, har rada yai mashi a kunna ya furta"nayi farin ciki da samun lafiyar ka, Ina fata babu abun da ke yi maka ciwo ayanzu..." ya fada tare da dafe kafadun danish ya dago da shi.
Babu wanda baiyi farin ciki acikin su ba, Musamman sheikh imam Ya ambaci kalmar alhamdulillah tafi sau a kirga, ya ɗaga hannayensa sama ya dinga zubawa Allah kirari Haɗi da nuna godiyarsa ga nasarar da suka samu, Bayan ya gama ya janyo danish din duk da bai sakar masu fuska ba wannan bai shafe su ba, dama su burinsu ya farfado kuma Alhamdulillah kwalliya tabiya kudin sabulu, Rungume shi shiekh imam yayi tamkar zai mayar dashi cikin sa, ya dinga shafa sumar sa yana karanto addu'o'i yana shafe mashi ko'ina na jikinsa.
Ko da likitan ya duba danish baiga komai ba sai ma wani abun ban mamaki daya gano wato Lafiyar dake gare shi, har ta wuce wadda hankali zai dauka, babu ko ciwon kai a tare da shi.
Bayan tafiyar likitan shawarwari suka tsaya sunayi atsakanin su, kafin daga bisani chief ya raka shi bathroom don yayi wanka, Kafin ya fito aka shirya mashi lafiyayyan abinci a daki aka shigo mashi da shi, atare da chief suka ci abinci, gwanin ban sha'awa kamar wasu yan uwan juna sai daya tabbatar danish Ya cika cikinsa tukunna ya samu kwarin gwiwar sanar da shi dangane da uncle dinsa dake son ganinsa, ya nemi alfarmar yana so su tafi atare, shiru danish yayi mashi dama yaƙi furta masu magana tun da ya farka kamar wani kurma sai dai yabi su da ido.
Tarairayarsa suka dinga yi suna lalla6a shi, duk don ya amince, amma ɗan tahalikin nan yai shiru, dabara ce ta fadowa taj da sauri yace mashi a tare da su unaisah zamu tafi da sauran ƴan uwan ka, kuma duk sun amince zasu je.
Jin ya ambaci zasu tafi da su unaisah ne yasa shi saurin amince masu ta hanyar jinjina masu kai, domin kuwa bazai bari su tafin masa da yan uwansa ba, Murmushi sukayi gaba dayansu ganin sunyi nasara akanshi... Nan fa suka fara shirya shi, kamar wani yarima.
Lokacin da su sajeed suka ji labarin Farkawar danish, Aguje suka watsa da gudu suka nufi bedroom dinshi, Tsabar farin ciki maimakon suyi dariya saima suka fashe da kuka suka dinga rungumar shi, Dadi kamar zai kashe su, Shi kanshi yayi farin ciki da ganin su duk da yaki tanka masu sunyi sunyi dashi akan ya bude baki yayi masu magana amna yakiya sai dai fa kallo ko irin sakin fuskarnan babu
Hakan bai wani dame su ba, tun da ya farka falillahil hamdu, duk wannan mai saukin ne, dama sun riga da sun san halin kayan su, bayan sun gama murnar samun lafiyan dan uwan nasu, Ummi ta tattarasu suka koma dakunansu, kowan na su yayi wanka, Suka soma shiryawa cikin kayan su cike da zumudi, bayan haka dangane da abun da ya faru a hall na kashe Hasken lantarki aikin chief owais ne shine ya tsara komai, tare da interior designers da sukayi decoration na hall din saboda yana son yaga reaction din family nasa, bayan ya gama tsara komai, Shi yafara halartar dinner din, ya riga su Unaisah tafiya kamar yadda ya tsara saboda yana son ya fara yi masu hanyar shiga batare da an samu matsala ba, tun da wurine mai tsaron gaske, su boss da big guy ne da wasu daga cikin jami'an isod sukayi jigilar daukar su Unaisah a cikin motocin su, suka kawo su bakin hall din, bayan tafiyar su tuni Ummi ta shirya saboda ta samu amincewar chief akan fitar da za ta yi, taje ne ya nema mata alfarma, Jami'in isod ne yayi driving dinta zuwa gidan da tace zata je na kawarta.
(Wannan shine abunda ya faru kafin zuwansu dinner hall din)
(CIGABAN LABARI)
Haɗa ido su kayi da prime minister, cikin sanyin murya ya furta"shi ne...?
Jinjina mashi kai chief owais yayi alamar eh, wata nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, fuskarshi dauke da wani irin annurin farin ciki mara misaltuwa da tafukansa ya tallabo fuskarshi yana bin shi da kallo mai nuni da tsantsar ƙaunarsa, kasa jurewa yayi baisan sa'adda Ya janyoshi zuwa ga faffadan kirjinsa yai huggin insa tightly kamar zai mayar da shi cikin cikinsa, hannayensa biyu dukansu ya tallabe bayan danish dasu, yayin da zuciyoyinsu ke harbawa da bugu mai tsanani, wani irin yanayi mara misaltuwa....
Hakan ba karamin ɗaga hankulan mutanan dake a hall din yayi ba, gaba ɗaya sun ƙara rudewa da ganin rungumarshi da prime minister yayi.
Muryar Hajiya saratu tamkar zata fashe da kuka ta furta"wai ba zakuyi mana bayanin su wanene ba? Kun barmu atsaitsaye cirko cirkon kamar sakarkaru" ta fada tana kallon chief owais don ta fahimci yasan da zamansu tun da taji Pm hateem ya tambaye shi shine....
"Owais su wanene wadannan Yaran! "? Baba obie ne ya furta maganar
Sai lokacin chief Owais ya soma takowa yana tunkaro wurin da su ke atsaitsaye, cikin dakakkiyar muryarsa ya soma magana genlty
"A gafarce ni, nayi laifi ban sanar da zuwan su ba....' ya faɗa awayance yana bin kowan nan su da kallo.
"Idan ba zaku manta ba, na ta6a baku labarin Yaran da Sojin america suka tsinta a evil forest, suka damƙa case dinsu ga hukumar mu ta Isod, ga wadanda basu san da zaman su ba, to ga su nan, sune yaran da nake ruƙo a hannuna, na gayyace su ne don su gana da dangina saboda sun zama tamkar ƴan uwa agare ni"
Lokacin da ya ƙarasa maganar, hajiya saratu ta zabga salati tana huci ta furta"wlh baka isa ba Owais! Ka haukace ne? da Zaka kwaso mana tsintattun Yaran da ba'asan asalin su ba, ka kawo mana acikin dangi? Anya kuwa kana a hayyacin ka? Rai amatuƙar 6ace tayi maganar, Hankalin su Unaisah ba karamin tashi yayi ba, Masu tsoro acikin su har sun fara Ja da baya jiki na kerma...
A matuƙar firgice Senate Lateef Yace"kana nufin ƴan uwan yaron nan da ya rikiɗa ya koma maciji"? Wannan maganar da senate lateef Ya furtane Yaja hankulan mutanan Hall din, Tashin hankali ne tsantsa akan fuskokinsu, Muryoyinsu a kidime suke maimaita kalmar maciji ga wadanda basu san da zancen faruwar lamarin ba, nan take Pravin yayi wuf ya kwashe komai daya faru ya sanar da su, Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un shine abunda suke furtawa a bakunansu....
Prime minister sam baya gane me su ke cewa saboda idanunsa sun makance, Ya kurmance baya ji baya gani tunda ya rungumi danish a jikin shi bai ƙara ɗago da kanshi ba, Kamar daga sama yaji an damƙi damtsen hannunsa da ƙarfi aka raba shi daga jikin danish wanda bakowa ne yayi hakan ba face Senate Lateef, ya janye shi gefe guda, Yana faman zazzaga masifa"wlh bazamu lamunta ba! Don Na fahimci bakasan ciwon kan ka ba, taya zaka kwaso mana mugun abu ka kawo mana a cikin dangi? Wannan wata iriyar masiface? So kake ka tarwatsa mana farin cikin mu? Ko kuwa so kake ka ƙarar mana da dangin mu ne!? Wai ma wanene ya baka shawarar ka kawo su wurin nan....."?
Tunkafin Senate lafeef ya kare maganar, sautin shessheƙar kukansu Ya soma karaɗe hall din, sun girgiza da jin munanan kalamin da ake fada akansu, bayin Allah da farin cikin su da zumudi su ka zo ganin dangin chief owais sunyi tsammanin suma zasu sosu kamar yarda shima yake son su ashe ba haka bane......'
"Wallahi sai dai ka za6a, ko dai ka tattara su ku koma can gidanka, ko kuma mu mu fita mubar maka hall din ka ƙare dinner din tare da su, don wlh baka isa ka jazamana masifa ba, wannan ay annobace ka kwaso mana" acewar hajiya saratu ta faɗa tana watsa hannayen ta.
Chief owais dake sauraronsu ɗaya bayan ɗaya yake binsu da kallo daman yasan za'a rina ba lallai su wanye lafiya ba, sai gashi ta tabbata, kowa da abun da yake tofawa, mutane ƙalilan ne basu tanka ba.
Hankalin Hateem yafi na kowa tashi, ganin za'a raba shi da muradin ranshi, Ga samu ga rashi, Ji yake tamkar Ya fasa ihu, ƙiri ƙiri su Senate lateef sun rurruƙe hannayenshi gudun kada Ya ƙara tunkarar Danish.
Security advisor din Hateem ne ya tambayi meke faruwa ne? Muryarsa a bubbuɗe yasha ya bugu baya gane komai sama sama yake jin kan shi, Kasancewar basa jin yaren hausa basu san takan zancen ba, da sauri pravin uban Ƴan zigi Ya buɗe baki da niyar Ya sanar dasu, wata irin tsawa mai kama da saukar aradu chief owais Ya sakar mashi, wadda tay matuƙar gigitasu a hanzar ce yaja baki ya yi shiru.
Dalilin dayasa ya yi mashi hakan gudun kada ya sanar da su, don muddin sukaji da zancen Yaron daya rikida ya koma maciji to kuwa nan take zasu sa a dakatar da taron bayan haka zasu sanya jami'ansu su kori su unaisah don ba zasuyi ganganci da rayuwar hateem ba...
Cikin sanyin murya prime minister yayi ma mutanansa bayani da yaren da zasu gane ya kwantar masu da hankalin su, da cewa family issue ne kuma in sha Allah zasu shawo kan matsalar yanzu, iya abun da ya fada masu kenan, dama kuma ba ahayyacin su suke ba, shiyasa abin yazo masa da sauki da tuni sunsa an tada taron gaba ɗaya.
Da kakkausar murya chief owais Ya soma magana babu annuri akan fuskarshi.
"ni ne silar dana kawo su wurin taron nan, bawani ya bani iznin in gayyace su ba, kuma basu suka nuna suna son zuwa ba, face don ni nake so su zo...." bai ƙare maganar ba, Hajiya saratu tayi yunkurin dakatar dashi aikuwa a fusace Ya ɗaga mata hannu alamar tayi shiru, Waro idanu waje tayi ba ita ba hatta sauran mutanan hall din sunyi mamakin rashin kunyar da owais yayi.
"Suma ya'yane kamar kowa! Yaro kuma da bashi da lafiya, Bayin kanshi bane, Aljanu ne suka shafe shi, kuma ya samu lafiya bayan da shiekh Imam ya dau kwanaki Yana duba shi.....' bai ƙare maganar ba, muryar sheikh imam ta karaɗa kunnuwansu a yayin da yake shuowa dakin taron.
"Tabbas maganar owais gaskiya ne, Yaran nan ba masu cutarwa bane, mutanene kamar kowa, kuma abin a tausayamawa ne....." a tsanake cikin hikma sheikh imam ya fayyace masu komai dangane da halin da danish yake a ciki, wasu sun fahimta yayin da wasu sam kamar kurame basa gane komai.
Gaba ɗaya hall din Ya rikice da maganganunsu, wasu suna hura wutar akore su daga hall din yayin da wasu sukayi shiru basu tanka ba irin su mai girma sharafudden, sun natsu suna bin duk wani mai magana da kallo, ga dukkan alamu akwai abun da suke jira shiyasa suka yi shiru.
Cikin sanyin murya prime minister yace"dan Allah kowa yakwantar da hankalin shi, Idan har saboda ni aka shirya dinner din nan, to ina rokon alfarmar ku bar su na yau kawai su zauna, in sha Allah ba abinda zai faru" idanunshi akan danish ya ƙare maganar, wanda tun shigowarshi hall din idanunsa suke alumshe tamkar ma baisan sunayi ba, su batool daine suka ruɗe jikinsu sai kerma yakeyi bayin Allah sun firgita.
"Meye amfanin kawo su wurin nan? Inace an shirya dinner din nan ne saboda mu ƴan family ba bare ba! Don haka afitar mana da su idan ana son zaman lafiya, idan ba haka ba mu zamu tattara yanamu yanamu mubar masu hall din" rai a6ace hajiya laurat tayi maganar tana faman haɗe rai.
Runtse ido chief owais ya yi, har cikin ranshi baiji dadin irin tarbar da akayi ma yaran ba, zuciyarshi ta raunana duk sai yaji dama bai sa anzo da su ba.
_Cikin sanyin murya mai ratsa zuciya Unaisah ta soma magana"dan Allah ku yi hakuri idan mun 6ata maku rai, wlh ba mu zo da niyar mu cutar da kowa ba, hasalima ba da son ranmu mu zo ba, face don chief ya nuna yana son mu ziyarci danginsa, ba ku san mu ba, muma bamu san ku ba, bai kamata kuna munana mana zato ba, akan
abun da baku da tabbas akanshi_
tun da ta fara magana hankula suka dawo kanta, Idanu zuru zuru cike da mamakin karfin halin ta.
_A hankali ta sanya hannu ta cire facemask din fuskarta tare da jefar da shi gefe ɗaya, Tabarakallahu ahsanul khalikin, Hankalin maza ya tashi da ganin kyakkyawar fuskar unaisah wadda take a jike sharkaf da hawaye_
_Cikin murya kuka taci gaba da cewa"Idan bakusan ganin mu ba sai kun kore mu ba, zamu tafi da kafafuwan mu,' kalamanta sun sanyaya zuciyoyin wasu daga cikinsu, Hakika unaisah ta tafi da imanin wasu daga cikin su, Har mamaki sukeyi yarinya karama ga iya tsara kalami uwa uba gata kyakkyawa da ita_
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 13 Complete
by
Novels Elite Admin
May 29, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القدر💋✊🔥
~Takun Ƙarshe🔥~
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Cikin muryar kuka taci gaba da cewa"Idan ba ku son ganin mu ba sai kun kore mu ba, zamu tafi da kafafuwan mu,' kalamanta sun sanyaya zuciyoyin wasu daga cikinsu, Hakika unaisah ta tafi da imanin wasu daga cikin su, Har mamakin ta su ke yi yarinya ƙarama ga iya tsara kalami uwa uba gata kyakkyawa da ita, ba karamin jan hankalin su Captain yasir tayi ba, sun kafe ta da idanun su kamar za su haɗiye ta.
Fashewa da kuka Jemimah tayi muryarta da gunjun kuka ta ke fadin
"wallahi babu inda zamu je, don baku san wahalar da mu ka sha ba mu ka yi gayu hada gyaran gashi saboda mu nuna maku, shi ne ma zaku kore mu, to wlh ba zamu tafi ba... " a faɗa ce ta faɗa tana nuna su da yatsan hannun ta, Hankulan su gaba ɗaya ya koma kanta, ƴar ƙarama da ita sai masifa, idanun ta sun yi jawur da su, ta harzuƙa, dama ya lafiyar giwa, tsana da tsangwama da zuluncin da akayi masu arayuwarsu ya ɗan ta6a lafiyar kwalwarsu, silar maganganun da ake fadi ayanzu ne ya fara motsa haukan kansu, da sauri Unaisah ta janyo jamimah ta ƙanƙameta a jikin ta cike da fargaban kada ta ja masu jaraba.
Dafe goshi Azeeza tayi da hannun ta dake kerma kerma cikin wani irin yanayi na jin tsoro da fargaba ta soma magana muryarta da shessheƙar ku ka
"Inna... lillahi wa'inna ilaihirraji'un Ni dai mu koma gida, ku mai dani gida, ba su san mu, ba su son ganin mu, za su iya cutar da mu....' ba ta ƙare maganar ba, Sajeed yai hanzarin janyota tare da rufe mata fuskarta jikin laps dinsa.
Sautin shessheƙar kukan su ya cika hall din, mazan cikin su ne kadai ba su karaya ba, sai dai hankulansu ba a kwance ya ke ba, Mom Turai sarkin tausayi zuciyarta ta karaya ita da Hajjaty har sun fara sharar kwalla saboda tausayi ne da su, ga kaunar yaran da ta ɗar su a zuciyoyin su, da ace suna da damar da zasu ja su a jiki su rungume su da kuwa sunyi hakan.
A hankali unaisah ta ɗaura idanunta akan chief owais, mutumin da bata jima da sanin fuskarsa ba, duk da babu kwanciyar hankali atattare da ita sai da taji ya kwanta mata arai saboda jajircewarsa akan su.
Kamar yarda take kallon shi haka shi ma yake kallon ta, har cikin zuciyarsa bai ji dadin zubar hawayen su ba.
"ba laifin ka ba ne, abun da akayi mana, sai dai inaso ka sani bakowane zai fahimce mu ba ko ya kaunace mu kamar yadda ku kayi mana, zamu tafi kawai....." ta ƙarasa maganar ƙananun la66anta na kerma ta ruƙo hannun batool da na jemimah har zasu juya muryar Sir mubarak ta dakatar da su.
"Duk da bansan su wanene ku ba, ni dai kun kwanta min araina, kun sace min zuciyata, don haka ban gaji da ganin ku ba, ina yi maku maraba da shigowa family din mu...." a ruɗe su hajiya saratu suke kallon Sir mubarak, wanda fuskarsa take ɗauke da murmushi yayin da yake kallon su.
Pravin dake ta faman mazurai, jin maganar sir mubarak yasa shi jin bakin ciki da takaici tamkar ya fasa ihu haka ya ke ji, kwata kwata babu kwanciyar hankali a tare da shi, duk ya rasa sukuninsa kamar wanda yayi ma sarki ƙarya, burin shi a kore su daga hall din.
Sheikh Imam dai lamarin nasu ba karamin mamaki yake ba shi ba, kallon su kawai ya ke yi, Sam baiji dadin halin da su ka jefa yaran ba.
"Meye ribar ku idan kun 6ata ran wadannan bayin Allahn? Farin ciki ku ka yi ko bakin ciki da kuka sanya su zubar da hawayen su? Idan ya'yan ku ne a irin halin da ku ka jefa su za ku ji dadi ne? Daga ni har ku bamu da tabbaci akan abunda muke zargin su da shi, don haka yakamata mu kyautata masu zato, sannan shiekh imam yayi mana bayani, babu wanda baisan wanene sheikh imam ba, kuma mun yarda da maluntarka sa, bai kamata mu musa ma maganar shi ba, bayan haka owais jinin mune bazai ta6a kawo abun da zai cutar da ahlinsa ba, idan ma saboda kuna fargaban kada su cutar da ku ne to ku sha kuruminku owais shi ya ke da alhakin da duk wani abu da zai faru"
cike da ƙwarin gwiwa Mai girma sharafuddeen yayi maganar babu wasa akan fuskar shi, tuni wasu sun fara shan jinin jikin su.
Matsawa Chief owais yayi kusa da baba obie wanda tun ɗazu bai tanka ba, ruƙo hannunsa yayi acikin nashi, a hankali Ya ɗago suka haɗa ido da juna
In a calm voice ya furta"banji kace komai ba baba, umarninka kadai nake jira, In har ka nuna bakason su zauna zan koma da su, Idan kuma ka amince babu wanda ya isa yasa subar wajen nan, sai dai mutun ya tafi" ran shi yakai maƙura awurin 6aci
Lumshe idanu baba obie ya yi yana nazari, na ɗan lokaci yana yanke shawara da zuciyarsa kowa ya ƙagara yaji ta bakinsa domin kuwa shi kaɗai ne zai zartar da hukunci kuma dole ayi biyayya......
Komai dake faruwa akan idanun zahra, tsoro duk ya cika ta ganin rikicin dake shirin 6allewa, tun ɗazu ta 6oye kan ta a bayan su hindu dake a tsaitsaye, jikin ta sai kerma ya ke yi saboda batason tashin hankali arayuwarta...
Pravin Allah Allah ya ke baba obie yaki amincewa da zaman su a hall din ji yake tamkar ya shiga zuciyarshi don ya samu damar tunzura shi akan kada ya bar su, jikin shi sai tsuma ya ke yi.
Chief owais dake kallon shi amsar shi kawai yake jira, cike da fargaban kada Ya kunyata shi a bainar jama'a duk da yasan abune mai wuya baba obie yayi mashi hakan saboda baya son 6acin ransa.
Gyaran murya yayi hankali gaba ɗaya ya dawo kan shi, kafin ya soma magana yana duban kowan nan su
"Bana son abun da zai cutar da ahlina, sannan bana son duk wani abu da zai kawo rashin zaman lafiya a zuri'a na...." tunkafin ya kare maganar, munafuki pravin ya soma sakin shu'umin murmushin farin ciki don yasan karshen zancen zai ce ne a kore su.
"Bawai don bana son yaran bane, ɗa na kowa ne, sai don ina son mu ƙare dinner din nan lafiya, zaman su acikin mu, ba lallai ya zama alkhairi ba, tun da wasu sun nuna basu buƙatar ganin su,......" da tsantsar mamaki chief owais ya ke kallon fuskar baba obie, hajiya saratu da su laura har sun fara sakin fuskokin su sai kace akan su za su zauna....
Chief bai tsaya jin karashen zancen ba, saboda zuciyarshi ta karaya, a raunace Ya sakin hannun baba obie, ya juya ya kalli prime minister wanda tuni ruwan hawaye sun kwanta luff a idanunsa...
Cikin sanyin murya ya furta"am sorry uncle, banyi tsammanin abun zai kai haka ba, dana san ba za a kar6e su ba da banyi gigin zuwa da su dinner din nan ba, dama nayine saboda farin cikin ka" ya faɗa yayin da yake mayar da idanunsa kan baba obie
"zan tafi tare da su....'
yana ƙarasa maganar cikin takun sauri Ya nufi su unaisah, wani irin murmushi ne ya bayyana akan fuskar pravin da su hajiya saratu.
"Owais"!! Har Ya kusa kaiwa bakin kofar muryar Baba obie ta katse shi, Cak ya tsaya da tafiya, dama da biyu yayi hakan don yasan baba obie bazai iya jurar 6acin ranshi ba.
"Meyasa ba zaka tsaya kaji karashen maganata ba"? A hankali Ya juyo yana duban fuskarshi, Nan take murnar pravin ta koma ciki.
Matsawo yayi kusa da shi, fuskarshi dauke da murmushi yace"kamar yarda kayi saboda farin cikin Uncle dinka, Ni kuma saboda farin cikin ka, na amince su shigo ayi shagalin dinner din nan tare dasu, sannan bana so na sake jin wani ya fadi abun da zai 6ata ransu, Umarni ne wannan!!
Yana ƙarasa maganar shi, Chief owais ya nufeshi, gaba ɗaya yayi huggin dinshi.
rai a6ace hajiya saratu ta nufi hanyar fita daga hall din.
"Karki kuskura ki fita! Dawo ki zauna" muryar Sir mubarak Ce ta katse ta, tana faman haɗe rai ta dawo ta tsaya hannunta dafe da ƙugu.
Damƙo hannun hajjaty pravin yayi, yana faman fitar da huci Yace mata ta biyo shi subar hall din, sam ya manta da hajiya saratu dake kallon shi, ga alama ya fita hayyacinsa, jikinshi duk yayi zufa sai kace babu a.c a hall din
Muryar hajjaty da tsantsar tashin hankali ta furta"pravin meke damun ka ne? Agaban mutane kake ruƙe hannu na? ina zaka kaini ne? bayan ba agama dinner din ba, dan Allah ka kyale ni" ta fada tana kokarin cire hannunta daga mugun ruƙon da yayi mata.
Da karfi hajiya saratu ta furta sunansa"pravin!!" ko kallo bata ishe shi ba, ƙoƙari kawai ya ke yi yaja hajjaty don su bar hall din, ita kuma ta dage akan bazata bi shi ba, gaba daya hankulan mutane ya dawo kan su.
"Nashiga uku pravin, dan Allah ka kyaleni, nace maka bazan bika ba....." gigitacciyar tsawa hajiya saratu ta daka mashi da kakkausar murya mai haɗe da zafin kishi ta furta"ka fara haukane? Agabana kake ruƙe hannun ta? Anya kuwa kana acikin hayyacin ka"
Ɗagowa ya yi da idanunsa waɗanda suka kaɗa jawur ya dubi hajiya saratu da masifa ya furta"Bai shafe ki ba!" har sai da taji gabanta ya fadi, Su hajiya laura sun saki baki da hanci suna kallon ikon Allah, hatta su Hajiya malikat da su sir mubatak mamakinne ya kamasu yadda ya rufe ido yana jan hajjaty da tsiya yake son fitar da ita daga hall din.
Alhazawan canada suna ta kallon ikon Allah abu kamar a drama, anbarsu a duhu sun kasa gane meke faruwa...
Tsawar da Sir mubarak Ya daka mashi ne yasa shi saurin shiga taitayinsa, A fadace yace"wannan wani irin shashanci ne? Baka da hankali ne? Ina ruwanka da ita? Tun da ta nuna batason tafiya ka ƙyale ta mana!"
Kallon hajjaty pravin yayi idanunshi jawur yana huci ya furta"idan har baki bini mun koma gida ba ranki zaiyi mugun 6aci, wlh kada ki bari na riga ki fita daga hall din nan" yana fadar hakan Ya juya tamkar mayunwacin zaki Ya nufi kofar fita hall din cike da sa ran hajjaty zata bi bayan shi, sai dai har ya fuce babu alamun zata bishi, kamar an ruƙe ƙafafuwanta, hakanan taji ba ta son tabi shi, taji kunyar abun da yayi mata, agaban jama'a, tasan dole adasa masu ayar tambaya, ita kanta a ruɗe take batasan dalilin dayasa pravin ya rikice mata ba, Hajiya saratu yau taga abunda yafi karfinta, tamkar a mafarki take ganin komai, akan idonta pravin ya ruƙe hannun hajjaty bainar jama'a batare da ya ji tsoronta ba, lallai zai fuskanci horo mai tsanani daga gare ta, har ta ita kanta hajjatyn yaja mata bala'e domin kuwa bazata ƙyale ta ba, ransu twins su yayi mugun 6aci musamman zayn shi da yafi zuciya......
Bayan hatsaniyar ta lafa, senate lateef ya dubi su unaisah "tun da mahaifinmu ya yanke hukunci akan ku zauna, ba mu da ja, ya zamar mana wajibi mu tarbe ku, amma kafin nan ku sauke facemask dake akan fuskokin ku" ya fada yana nuna faces din su.
Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyoyin su.
"Kamar ka shiga zuciyata, nima abun da nakeso nace kenan, gaskiya ba zamu bari ku shiga da wannan face mask din ba, yakamata mu ga fuskokin ku," tun da aka fara rikicin nan sai yanzu his excellency abdul razak ya sanya baki,
His excellency deen yace"to nima dai abuɗe min inga fuskokin nan, ko hankalina ya kwanta" ya fada da ɗan murmushin kan fuskarsa.
A hankali Batool ta ɗaura yatsun hannunta da ke kerma ta ruƙo face mask din ta yaye shi daga kan fuskarta, Har saida gabansu ya fadi da ganin kyawun fuskarta, wato wani guntun murmushi da tayi ta sunnar da kanta kasa ba karamin tafiya yayi da imanin su ba, wasu tuni sun fara danasanin sanya su kuka da su ka yi.
Bayan batool ta cire nata, Sajeed Ya zame face mask din fuskarshi, tsabar kiɗima da ganin fuskarshi yasa hajiya laura ɗan zaro idanunta ga dukkan alamu akwai wani abu da ya ruɗe ta da shi, kyawun sajeed ba ƙaramin tafiya yai da imanin su ba.
"Saura ku, Ku cure naku mu gani" Zaki ne ya fada yana nuna sauran
Sajeed ne ya taimaka wurin Cire ma Azeeza nata, Duk tabi ta ƙanƙame shi, fuskarta tayi sharkaf da hawaye har wani zazza6i ya lullu6e ta, ganin fuskar Azeeza ya yi matuƙar razana Sir mubarak har sai da ya kalli fuskar Mom turai, ba shi ba, hatta Dr jazz da su Ibad kusan a lokaci ɗaya suka jefa wa junansu kallon kallon mai nuni da tsantsar mamaki da al'ajabi.
Jamimah dake a maƙale jikin angel, babu alamun zata motsa, ruƙo hannunta Angel tayi tare da cire mata mask dinta, fuskar ta 6aci da hawaye hada majina hakan yasa basu samu damar ganinta da kyau ba.
Kusan atare Javed da Haris suka tu6e nasu face mask din, Kallon kallon aka komayi atsakanin Iyalan obinna kowa da abun da ya ɗaure ma shi kan shi.
"Parveen ku cure naku" cikin sanyin murya Unaisah tayi masu magana
Batare da 6ata lokaci ba, Parveen ta cire nata mask din, wani irin bugu zuciyar hajiya saratu tayi, haƙiƙa ta razana da ganin kamannin ta dana yarinyar, har sun 6aci kamar tayi kakin ta, banbancin su launin fata, ba ita ba harta sauran matasan family din da iyayan mamakine tsantsa akan fuskokin su...
Lokacin da Naufal ya cire mask din fuskar shi, wata irin firgita hajjaty tayi, har sai da ta dafe saitin zuciyarta da ke yi mata wani irin mahaukacin bugu, tagaza yarda da abun da idanuwanta suke gane mata, gani take tamkar mafarki ne ba gaske ba, domin kuwa ita dai tasan wanda ya mutu baya dawowa, harta su Hajiya Muhibbat sai da suka saci kallon fuskar hajjaty da ta naufal saboda wani abu daya ja hankalin su....
Gaba ɗaya sun rikice Sun ruɗe, sun gaza gasgata abunda idanunsu ke nuna masu
Tamkar an kulle masu baku nan su, Sun kasa magana, Lamarin ne yafi karfin tunanin mai tunani, mamakin su tayaya akai yaran suke bala'en kama da ƴan family din su?
_Ba zata juri bugun da zuciyarta ke yi mata ba, da azalzalarta akan son ganin fuskar yaron da hateem ya kwallafa rai akanshi, tabbas tana son ganin shi, kowa na gurin burin shi Danish ya cire mask din fuskar shi, sunyi matuƙar ƙagara da son ganin sa, walking gently gimbiya mujeedat ta tako ta tsaya gab da inda danish yake atsaya kamar mai wani nazari abu akanshi, idanunshi na kallon kasa sam bayason hada ido da kowa_
Sanya hannu tayi ta cire mask din dake akan fuskar shi............
Kiris ya raga zuciyar gimbiya mujeeda ta daina bugawa saboda razanar da tayi, gaba ɗaya hankulan su ya dawo kan shi, Wani irin mugun bugu zukatan su suka soma yi, yadda kasan ana dakan sakwara, Gaba ɗaya suka zazzare idanunsu gami da buɗe bakunansu saboda tsabar kiɗima kamar sun ga wani mugun abu, wato Sun gigita sun razana da ganin wanan abin al'ajabi da yai matuƙar Ɗaga hankulan su, Afirgice Chief Of Staff Na canada Ya dubi fuskar Security Advisor da wani irin ruɗani akan fuskokin su, at same time su ka yi saurin kallon Prime minister Hateem, Baba obie kuwa kusan suman tsaye yayi da ganin wannan Kama ta ban al'jabi, Senate lafeef da su His excellency sai faman jinjina kan su suke yi sam sun gaza magana kamar kurame, sai yanzu suka gane dalilin dayasa hateem ya firgice ma su da kaunar yaron ashe shi yasan abun da ya gani, Kai kowama dake a wurin ya rasa lissafin kwalwarsa saboda ganin fuskar Danish, Wai shin Ina Nazli? Ay tun da tayi tozali da danish tsabar firgici da ruɗani yasa har batasan sa'adda ta saki wayar hannunta ba, gaba ɗaya ta kife kan flloor, Jikinta ya kama kerma kerma tana faman zazzare eyes din ta akan fuskar shi yadda kasan twin brother din ta.
saboda ruɗu tunani su ka yi ko dai Nazli ce ta koma inda danish yake atsaye hakanne yasa sukayi Saurin kai idonsu inda take atsaye don suga idan tana nan, Ganinta yasa suka ƙara rikicewa.
Security adivisor ya kasa samun nutsuwa saboda al'ajabin da ya kama shi, Muryar shi na rawa rawa yana tangyadi cikin harshen turan ci yace" dama prime minister yana da wani ɗane da ba mu san da shi ba, ko kuwa ƙaninsa ne? Ko dai giyar dana sha ce takai mun karo? Pls ku yi min bayani yadda zan fahimta.
Senate lateef ne ya bashi amsa da cewa"ba su haɗa alaƙar komai ba, kama ce kawai" babu alamun za su gasgata maganar shi.
"Abun da ɗaure kai, amma ya ya akai su ke bala'in kama har haka? Kamar an yi photo copy din fuskar Hateem, ko ma ince Nazli" his exellency Deen ne yayi maganar, Yazrin sam takasa samun nutsuwa Sai kallon shi take yi ko ƙyaftawa babu, wato danish ya girgiza su da kyawun shi, Hankulan su Faryat ya tashi haikam tsabar yadda su ke kallon shi kamar za su haɗiye shi, yadda kasan irin kura taga naman nan.
Haƙiƙa sun rudu da prisoners, babu wanda bai yi mamakin sanyin kyan su ba, da al'ajabin kamanceceniyar su da ƴan uwan su yadda kasan ya'yan cikin wasu daga cikin su tsabar yadda kamannin su ya bayyana da juna...
Ganin kallon nasu ba mai ƙarewa ba ne gashi sunbar yara atsaitsaye, da sauri Ziyad ya ce
"Lokaci yana tafiya, yakamata acigaba da shagali"
kafin Ya ƙare maganar sautin waƙa mai ratsa zuciya ya karaɗe cikin hall din, Ɗaya bayan ɗaya Suka juya suna nufar wurin zaman su kowa da abun da yake saƙawa a cikin zuciyar shi.
Hateem kamar jira yake yi a samu maslaha, jiki na rawa ya nufi danish ya ruƙo hannun shi acikin nashi, burin shi su haɗa ido don su kalli juna dakyau amma yaƙi bashi damar hakan, murmushi ne dauke akan fuskar sharafudeen sai faman kallon su ya ke yi, yaji dadin ganin hateem a irin wannan yanayin.
Da zolaya yace irin wannan kallo haka? Ka da fa ka lashe mana yaro" ƴar dariya hateem yayi,
Chief owais da ke kallon su ba karamin kwanciyar hankali ya samu ba ganin ya faranta ran uncle din sa
"Uncle ka tafi da shi, zaman shi anan bazai yiwu ba, saboda baya son hayaniya, kuma baya son ana kallon sa, From now until nightfall, I entrust him to your care" wani irin farin ciki ne ya ƙara lullu6e prime minister, kamar wanda akayima albishir da gidan Aljanna, cikin sanyin murya yake fadin"nagode owais, wlh ka gama min komai, bazan ta6a manta alkhairin ka a gare ni ba, Allah ya faranta maka kamar yadda ka faranta min" addu'o'i ya dinga zuba mashi, bai manta da sheikh imam ba wanda ke atsaye tun dazu murmushine akan fuskar shi.
"shukran jazeelan Ya sheikh, Allah ne kadai zai iya biyan ka, saboda babu wasu kalmomi da zan iya yin amfani da su wurin yi maka godiya" ya faɗa yana ruƙo hannun sheikh imam gaba ɗaya wani irin annurin farin ciki ne akan fuskokin su.
Unaisah da ke ta sauraron su aranta Allah Allah take Danish ya amince da buƙatar chief yabi prime minister don tasan halin shi da kafiya ba kowa ke iya tankwara shi ba.
Kafin ta ƙare zancen zucin nata ba, da mamaki taga danish yabi prime minister hannun su ruƙe cikin na juna suka nufi hanyar fita daga hall din ko irin ya waigo ya kalle su baiyi ba, ajiyar zuciya ta sauke, sarai ta fahimci masu satar kallon ta.
gimbiya mujeedat sai bin su da kallo take yi, tarasa ma wani irin tunani zatayi game da bawon Allan nan mai tsantsar kama da Nazli, kasa jurewa tayi da sauri ta bi bayan su, ita ma Yazrin ta bi su, Nazli ce kaɗai ba tayi yunkurin bin su ba, kwata kwata babu annuri akan fuskarta, Ita bakomai ne damuwarta ba face abu biyu, na farko yaron da ke kama da ita! arayuwarta ta tsani ace wani yana kama da ita, saboda izzarta, tafi so mai nata ya kasance ita kadai ke da shi, bayan wannan sai Unaisah! Hankalin ta bai kwanta da ita ba, saboda wani kallo da taga sun jefa wa juna a tsakanin ta da chief owais nan take taji bata son ganin yarinyar, Nazli tana da zafin kishi, izzarta ce ke hanata bayyanawa.
Fuskarta babu annuri ta kai hannu ta dauki wayarta dake kan floor, da wani irin takun qasaita ta juya tabar wurin su.
Mom turai da ke ta kallon su tun ɗazu take son tunkararsu ganin babu dama ne yasa ta yi shiru tana kallon badaƙalar da ake yi, yanzu kuwa da ta samu dama, Da sauri ta nufi wurin Azeeza saboda sun bata tausayi da suna kuka, hanky ta zaro daga purse dinta, ta zuƙunna agaban ta tare da sanya shi kan fuskarta ta shiga share mata hawaye
Cikin kulawa tace "Stop crying kin ji ko? everything is over now, we are welcoming you to our family" wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyoyinsu har sun fara ɗan sakin jikin su.
A hankali Sir mubarak Ya nufi Jemimah dake a maƙale da Angel ta cukuikuiye mata rigarta zukunna yayi agabanta, ya ruƙo hannayenta a cikin nashi yana rarrashinta ganin har yanzu tana shesshekar kuka.
"Sorry baby girl, share hawayen ki...."
muryarta na rawa ta furta"wlh baku son mu, shiyasa ku ke korar mu, ni dai gida zan koma Allah" a fadace ta faɗa tana faman zabga masu harara, ƴan kumatunta sunyi jawur da su.
Ba zato ba tsammani Taji Sir mubarak Ya dauketa dungurum Ya daurata kan kirjin shi, wuƙi wuƙi tayi da idanunta.
"Sai mu ga da wasu kafafun zaki koma gida, ay tun da ki ka shigo wurin nan sai mun ci abinci dake, idan kuma mutun yace zaiyi min rigima zan sanya bindiga ne in har be mashi tsakiyar kan shi"
Ya fada Yana daura yatsan shi akanta, Murmushi kowan nan su ya dan saki.
"Bismillah ku shiga daga ciki mu zauna, ko baku gaji da tsayuwa bane"
Zaki ne yayi maganar Yana nuna masu cikin hall din, su kansu so suke su zauna kafafuwansu har sun fara ruƙewa kawai suna fargaban shiga ne.
Ganin hakan yasa zaki matsawa ya ruƙo hannun Sajeed Dana Naufal Ya shiga da su cikin hall din, Da sauri Dr Jazz Ya matsa Cikin su ya ruƙo hannun javed dana haris yayi ciki da su.
Bayan mom turai ta gama sharewa azeeza hawayenta, ruƙo hannun ta tayi suka nufi table din su.
babu wanda yayi tsammanin Hajiya malikat zata tanka, don tunda aka fara rikicin bata sanya baki ba, sai yanzu data matso kusa da su ta ɗan saki fuskarta tana fadin"naga kowa dan uwansa yake dauka nima bari na dauki nawa" ta fada tare da ruƙo hannun Unaisah, ta haɗa dana batool dake a gefenta"mu shiga ciki Ƴan mata," wani irin farin ciki ne ya lullu6e su, da sauri suka bi bayan ta, chief owais dake atsaye ya goya hannayensa kan kirjinsa sai kallon su ya ke yi, hankalin ya kwanta babu sauran damuwa.
"Toh, ni ma dai bari na dauki nawa ƴan matan" hajiya madina ce tayi maganar da fara'a akan fuskarta ta ruko hannun Parveen da na hannah, ta nufi wurin zaman su da su, gaba daya sun koma ciki, hatta su Hajiya saratu kowa Ya koma mazaunin su wasu suna daga tsaye har yanzu hankalin wasun su bai kwanta da yaran ba, Abunne ya daure masu kai sun gaza samun sukuni a fakaice su ke satar kallon su.
Tuni Daddy sharafudden yayiwa sheikh Imam mazauni a wurin su, umarni aka bawa servers din dake awurin akan su kawo masu abin da zasu ci, nan fa suka fara aikin jera masu abinci kala kala da abin sha shaƙe da table...
Wata irin nauyayyar zuciya jemimah take ta faman saukewa, mom turai da sir mubarak sun tasa su agaba sai faman tarairayarsu su ke yi, kamar ƴa'ƴan cikin su.
"Me ku ke son ci"? Cikin kulawa tayi masu maganar.
Jemimah ce tai kokarin bude baki tace"komai ma muna ci" murmushi mom turai tayi, ba karamin burgeta su ke yi ba,
"Ko kin lura yaran nan suna kama da ke? Kamar ƙannan Jazz saboda sunyi kama da shi kan shi" murmushi tayi tana kallon Sir mubarak da yayi maganar.
"Nima nayi mamakin kamannin mu" ta fada idanunta akan fuskar Jemimah da azeeza, wadan da tuni suka fara cin abincin da aka kawo masu.
6angaren Su Hajiya saratu kuwa, sun kasa sun tsare sai jifar Parvin take yi da wani kallo mai wuyar fassaruwa, dama su biyune hajiya madina takai su tebur din su, ita da hannah wadda jikin ta keta kerma
"Baki da lafiya ne"? Hajiya laurane ta jefa mata tambayar fuskarta a yamutse, girgiza kai Hanna tayi, ta6e baki tayi"to meye kike ta kermar jiki! Tun da kun riga da kun samu wurin zama, ay sai ku saki jiki kuma ku kwashi arziki" ta fada tana hura hanci.
"Please ni ban kawo su nan da agaya masu magana ba!" Hajiya madina ce ta fada tana mai nuna 6acin aranta, kafin ta mayar da dubanta ga su parveen
"Ku ci abinci mana" da sakin fuska tayi masu magana, parvenn kamar jira takeyi aikuwa ta dauki glass of juice ta fara sha, tana shanyewa ta soma cin fruit salat, bayan ta gama ta koma tana cin spring rolls, ɗan zaro idanu hajiya saratu tayi tana kallon ikon Allah, yadda kasan irin kwancen yunwar nan,
Hajiya laurat tace"ba banza ba naga tayi kama dake ashe itama din acici ce" ta fada da zolaya tana yar dariya, parveen dai ko kallo basu ishe ta ba, ta dage damtse komai ci take, har kwara hannah a hankali take dan cakura tana ci
"Wai ni ka ɗai ce nake mamakin kamannin yaran nan da family din nan"? Hajiya madina ce tayi maganar,
Hajiya saratu tace"hmmm, ay ni abun ya gama ɗaure min kai, har yanzu zuciyata ta gaza samun nutsuwa, na ruɗe musamman dana ga yaron nan mai kama da hateem" lumshe ido Hajiya laurat tayi tunawa da surar shi don ba karamin tafiya yayi da imaninta ba.
Hajiya muhibbat tace"na girgiza da ganin shi, lokacin da mujeeda ta cire masa mask din fuskarshi araina sai da nace wannan kyau haka kamar ɗan sarkin aljanu? Dariya su kayi gaba dayan su
"Ay tun da nayi mashi kallo ɗaya na kau da ido, saboda wannan kyan nashi kadai ya isa yasa mace fadawa ga halaka" acewar Hajiya laurat
"Ina kananun Yaran nan ƴan mata masu kama da tagwaye, wlh yadda kukasan Hajja turai tayi kakin su, Ƙaramar fuskarta da komai kalar nasu ne, sai kuma wani mai kama da hajjaty kamar anyi photo copy din fuskarta acewar Hajiya mudeena.
"Nima na lura da su, amma fa ni duk ba wannan ba, Yarinyar nan ta burge ni, kwarin gwiwarta ya tafi da imani na....".hajiya muhibbat ce ta yi maganar tana kallon can cikin hall din inda su unaisah su ke
Duk wannan suratan da su ke yi, akan kunnan su Parveen sai dai sam basa ganewa hankalin ta na kan abinci ci, hajiya saratu sai faman satar kallon ta ta ke yi afakaice, tun parven bata lura ba har dai ta gano ta, da zarar ta ɗago suke haɗa ido da juna.
_________________________💞
Gyaran murya Zaki yayi masu, a tare su ka dago suna kallon shi,
"Kunyi shiru baku faɗa mana sunayen ku ba"
Murmushi sajeed ya ɗanyi
"Ni sunana sajeed, shi kuma ɗan uwana Sunansa Naufal"
"Masha Allah, It's a pleasure to meet you both, I hope you will feel at ease with us, sannan ku dauka tamkar ƴan uwan ku ne mu" jinjina mashi kai su ka yi alamar eh.
"Okey, Yanzu ina so ku bani mamaki, ku cinye wannan abincin da nasa aka kawo maku" dariya su ka yi gaba ɗayan su, har cikin ransu sunji dadin tarbar da zaki yayi masu.
Nan fa suka saki jiki suka soma cin abinci.
Ɗagowa zaki yayi tare da kallon Su captain, yayi mamakin ganin yadda suke dogon wuya suna leƙen table din su unaisah.
Da zolaya yace"kun dai ji kunya wlh, ina ajin naku yake"?
dariya ziyad yayi yana fadin"wlh yarinyar ce ta tafi da imanina, ni ka gane bawai sonta nake ba, wannan ay tafi karfin ɗan jarida, kawai dai kamar nasan fuskarta, sai dai narasa gane a ina nasanta, abun ya shige min akaina...."
Daƙyar captain Yaseer Ya janye idonsa daga kan fuskar Unaisah.
"Nifa ina ji zan canza sheƙa ne, wlh ko da dukiyata zata ƙare ne akan neman waccan yarinyar saina jaraba sa'ata..." justice na murmushi yace"karka soma wlh, domin kuwa iskace zata wahalar da mai karan kara, ay ni tun daga kan kallon dana ga chief yanayi mata raina ya bani cewar da akwai wata aƙasa"
Kwa6e fuska captain yayi"kana nufin yana sonta"? Dage mashi gira Justice yai.
Yatsina fuska yayi"again, bayan ya kwace nazli, ga kuma wata, mata biyu kenan zai aura!"
"Ni duk ba wannan ba ma, ganin yaron nan mai suffar lu'u lu'u yaɗan girgiza ni, wai ku bakuyi mamaki ba? Ziyad ne ya fada.
"Ay mamakinne yasa ka ji munyi shiru da zancen shi, domin kuwa kwakwalwa zata iya daina aiki" dariya su ka yi jin abun da Justice yake fadi.
"Gaskiya nayi mamaki ace wai yaron nan a daji aka tsince shi, ay hankalima bazai dauka ba, kai daga ganin zubin halittarsa ɗan wani ne, shiyasa nifa gaba ɗaya na ruɗe da lamarinsu, kaina a duhu yake, kamanninsa sun 6aci da Uncle Hateem kamar yayi kakinsa kuma gaskiya ina kishi da shi Allah" captain ne ya fada.
Sajeed dake sauraran su murmushi ne dauke akan fuskarshi, Naufal Kuwa gaba ɗaya ya rasa nutsuwarsa saboda kallon da hajjaty take mashi, Da zarar Ya ɗago da idanun shi karaf suke sauka acikin nata, saboda shi ta baro wurin da take ta dawo kusa da table din dake fuskantar nasu ta zauna tana ta kallon shi, ko kyaftawa babu.
Cikin muryar raɗa yace da sajeed "waccan matar sai kallo na take yi kamar zata haɗiye ni, taƙi bari naci abinci cikin kwanciyar hankali, bansan me na tsare mata ba, ni fa duk na tsorata" da sauri sajeed ya saci kallon inda naufal ke nuna masa ganin hajjaty yasa shi yi ma naufal rada"ka kwantar da hankalin ka, saboda kana kama da ita ne shiyasa take kallon ka" ya fada yana ƴar dariya, shi dai naufal hankalin shi yaƙi kwanciya, kamar anyi mashi dole ya kalle ta.
Hakanan take jin shi a zuciyarta, komai nashi sak kalar na yaron ta, bazata ta6a mantawa da suffar shi ba, abinne ya daga hankalinta, ya kuma tada mata tsohon Ciwon dake kwance a cikin zuciyarta, bakomai take tunawa ba face yaronta da ta rasa tun farkon zuwan su nigeria wannan wani labari ne wanda sai nan gaba kaɗan zamu ji shi...🥺
Dr jazz sai Rawar kai yake yi da su Haris, kamar kannansa, Ya tasa su agaba shi da ibad sai fira suke jan su da shi.
"A cikin ku wanene Haris"? yai tambayar yana duban su, da yake yana fuskantar su, da sauri Javed Ya nuna haris," ɗan zaro idanu Dr jazz yayi"masha Allah, kaine haris kenan"? Jinjina mashi kai haris yayi alamar eh, da biyu ya tambaye shi saboda yasha jin labarin shi awurin deeja, tana yawon yin sambatun sunan shi idan haukan ta ya motsa.
Ruƙo hannun shi yayi a cikin nashi yana fadin"kun burgeni, ina kaunarku, ganin ku kawai da nayi kun kwanta min arai na" murmushi kowan nan su ya saki.
"Wlh nima Na kamu da kaunarsu, dan Allah ku dawo gidan mu da zama, dama ni bani da abokai a nigeria" ibad ne yayi maganar da yar shagwa6ar shi.
"Kun ƙi sakin jiki damu, ko dan baku san mu bane" kallon juna haris da javed su ka yi, sufa basu saba mu'amala cikin mutane ba.
"Okey, yanzu bismillah mu fara cin abinci"
Atare suka soma cin abincinsu, jefi jefi Dr jazz yake satar kallon Haris Aranshi ya ayyana duk ranar da khadeeja ta yi tozali da shi ba karamin hauka zatayi ba.
"Yaya jazz, wadancan twins din sunyi kama da mommy da kai," ya faɗa yana nuna su azeeza.
Murmushi jazz yasaki shi kanshi ya kamu da kaunsarsu, tun dazu yake ta faman satar kallon su, ji yake tamkar kannansa na jini.
"Please Ya jazz mu yi wa daddy magana, akai mana su gidan mu, ni wlh bana so suna kuka, kaga mom saratu da waccen tsigai din ko ina ruwansu da rayuwarsu, ni fa shiyasa bana son zuwa nigeria saboda su, ko gajiya da masifa basayi, ina ruwan su da ƙaddarar rayuwarsu? Su ne suka tsara ma kan su ne? Ni fa kaganni ya jazz ba ruwana da shiga sabgar wani ko in wulakanta sa, wai don basu da asali, sai kace an gaya masu daga sama suka fado, mutun dai ay sai an haife sa yake xuwa duniya ba daga sama aka wurgo saba, balle ace da rashin asali aka haife su," Rai a6ace ibad yakeyin maganar da zallar shagwaba.
Su haris sun saki baki suna kallon shi, komai nashi burge su ya ke yi, ganin suna kallon shi ne yasa shi dakatawa da maganar yana yar dariya yace"na cika ku da surutu ko"? Girgiza mashi kai su ka yi alamar a'a.
Hankalin Zahra Yaƙi kanciya, bakomai ne yajawo hakan ba face Unaisah, ko kwanto takeyi kamar tasan ta, sai dai takasa gane a ina tasan fuskarta, sai yanzu ta samu damar kare mata kallo daga inda take azaune, duk wani motsin unaisah akan idon zahra, ta kwallafa rai akan son yin magana da ita dama kawai take jira....
Batasan ya akai ta tsinci kanta da jin nauyin haɗa ido da chief ba, tun da suka zauna ta sunnar da kanta tana wasa da yatsun hannayenta, ƙamshin turarensa gaba ɗaya ya cika mata hanci, duk wannan abun da take yi chief owais na lura da ita, da yake suna fuskantar juna da shi, wayarsa ce ruƙe a hannunsa da yake daddanawa cikin nutsuwa.
Ga jerin kayan abinci da aka shaƙe masu table da shi amma takasa ci, ga yunwa tana ji.
Gyaran muryar da Hajiya Malikat tayi masu ne yasa suka dago a tare suka kalle ta, tana daga zaune gefen chief
"Nasa an kawo maku abinci kun ƙi ci, meyasa?"cikin kulawa tayi ma su maganar.
Murmushi suka dan saki suna faman noƙe kai.
"Ko dai Kunyar Chief ku ke ji" kamar ta shiga zuciyar su, murmushi tayi ma su
"Ku ci mana, hankalin shi ba akanku Yake ba"
Batool ce ta fara cin abincin ganin zata sanya hannu yasa hajiya malikat cewa"ki ɗauki tsokali" muryarta na dan rawa tace"ban iya ci da shi ba"
"Okey, nagane ki sanya hannun"
Hannu tasa ta soma ci, unaisah kuma ta ɗauki glass na lemu tana ɗan kur6an shi sama sama take satar kallon fuskar chief owais da zarar taga zai ɗago da idanunsa take yin saurin kau da nata gefe ɗaya, bakomai ne yaja hankalin ta gare shi ba, face kamanninsu da Danish, kusan komai nasu iri ɗaya banbancin su kaɗan.
Mai girma sharafudeen ne ya nufo wurin su, fuskarshi da fara'a Ya samu wuri ya zauna yana dubansu, da sauri suka gaishe shi cikin girmamawa ya amsa masu.
Duban owais yayi"baka cika min alkawari na ba" ya faɗa yana ɗan haɗe fuskarshi.
Dagowa chief yayi tare da kallon daddyn nasa, da alama bai fahimci me yake nufi ba
"Maganar da mu kayi dakai ɗazu da safe"
Sai yanzu ya fahinci inda zancen daddyn nasa ya dosa.
A hankali ya ɗaura idanunsa kan Unaisah dake kur6ar lemu.
Murmushi hajiya malikat tayi
"tubarakallah Masha Allah, nagode ma Allah da ya nuna min wannan ranar da raina da lafiyana, gani ga second in-law ɗina, yarinya mai hankali da nutsuwa, ni dai surukan nawa duk kyawawa ne, ubangiji Allah ya tabbatar mana da alkhairin sa...." amsa mata yai da ameen.
Ga dukkan alamu unaisah bata fahimci takan zancen ba, ta dai ji ana zancen suruka, Ruƙo hannunta daddy Sharafuddeen yai a cikin na shi fuskar shi dauke da murmushi yace"I'm so happy to meet you, my daughter-in-law, I don't even know how to describe the joy I feel just from seeing you today"
murmushi tasakar masa har dimple din ta lotsa, duk da batasan wanene shi ba, ranta yana bata cewar Mahaifin Chief ne saboda kamannin su da ga gani.
Muryarta cike da jin nauyin shi ta furta"nima naji daɗin haɗuwa da kai,"
"Shekarunki nawa ne"? ya jefa mata tambayar.
"Sha shida amma na kusa shiga ta sha 17"
A wayance Daddy sharafuddeen yace"Wonderful, Now, what about your studies?
Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta ba tare da ta amsa mashi tambayar da yayi mata ba.
"Sorry kada daddy ya takura maki da tambaya ko"? Murmushi ta ɗanyi masa.
"Inaso ne nasan me yakamata mu fara yi don tallafa ma rayuwar ki, ko ba haka ba" cike da rashin fahimtar kalamansa take duben shi, Hajiya malikat dake kallon ta murmushi ne dauke akan fuskarta, yarinyar ta kwanta mata aranta.
Chief owais ya nutsu yana sauraron su.
"Aure ko karatu wanne kika fi so a yanzu" waro mashi gray eyes dinta tayi da sauri ta sanya tafin hannu ta rufe fuskarta alamar taji kunya, hakan da tayi ba karamin dariya ya basu ba, hatta chief saida yayi murmushin gefen fuska.
Hankalin batool gaba ɗaya baya akansu tun da ta samu abinci take ta aikin ci.
"Kinyi shiru baki ban amsa ba" ya ƙara tambayarta, ƙasa ƙasa da murya chief ya furta"dad..." dakatar da shi daddy sharafudeen yayi"no kada ka shiga tsakanina da surukata, baby Angel ke nake sauraro," tayi mamakin jin ya ambaci nickname dinta, ba tare data buɗe fuskarta ba tace"Aure zanyi kafin na cigaba da karatu"
Murmushin fuskarsa ne ya faɗaɗa da zolaya yace"ta kwana gidan sauƙi, yanzu faɗa min kina da saurayin da zaki aura ne ko babu"
da sauri hajiya malika tace"haba dan Allah, kabarta mana, miji ay ta riga da ta samu ko ba haka unaisa"? Ɗaga mata kai tay alamarh.
Duk wannan abun dake faruwa a tsakanin daddy sharafudeen da Unaisah akan idanun Nazli wadda tuni tagama cika ta batse ranta yayi mugun 6aci tamkar ta ɗaura hannu bisa kai tayi ihu, wani irin kishine Ya ziyarce ta ganin yadda chief owais yayi zaman shi a wurin yarinyar, tun zuwan su hall din bai tako yazo inda take ba, kamar ma baisan da zamanta ba.....
Bazata juri kallon su ba, miƙewa tayi da niyar tabar hall din kamar daga sama muryar Faryat ta katse mata hanzarinta.
"sister Nazli, Ina zaki je ne bayan ba'a kammala taron ba"!
Ba tare da ta kalli faryat ba tace"bazan juri zama ba, sai nake ga kamar ba don mu aka shirya dinner din nan ba, because everyone's attention is focused on them. Daddy Ya tafi da wani wanda bamusan wanene shi ba and the chief is only paying attention to that girl." ta faɗa tana nuna saitin inda unaisah ta ke da hannun ta.
Ruƙo hannunta faryat tayi a cikin nata" Sister, ba ke ya kamata ki bar hall din ba! They are the ones who should leaves"
Girgiza kai Nazli tayi"no ni bana son hatsaniya, barina shi yafi min kwanciyar hankali"
Ta faɗa tana kokarin kaucewa rukon da faryat tayi mata.
Sai dai taki bata damar tafiya
"Nasan menene ya 6ata maki rai sister, ba ke kaɗai ba, mu ma ran mu ya 6aci da zuwansu saboda babu alkhairi atattare dasu, gaba ɗaya hankali Ya koma kansu, Amma ni na maki alkawarin zan kawar da yarinyar can daga hall din nan, indai hakan zai kwantar maki da hankalin ki, amma bai kamata ki tafi ba, ba zamu ji dadi ba" shiru Nazli tayi na ɗan wani lokaci kafin ta ɗan sauke ajiyar zuciya.
"What are you going to do to her I hope you won't hurt her."?
Shu'umin murmushi faryat tasaki,
"Don't worry sister, I won't hurt her. I'll just keep her out of sight until the dinner is over."
"Bana so a samu matsala faryat!"
'kawai kibar komai a hannu na, abun da nake so dake da zarar kinga babu yarinyar kiyi kokarin jan hankalin Yaya owais"
A hankali Ta furta Okey, fasa fita tayi da sauri ta juya ta koma wurin zaman ta.
Faryat kuwa ba karamin dadi taji ba, dama ta tsani ganin unaisah, tun farkon shigowarsu taji bata yi mata ba, da sauri ta koma wurin su Yusra tana jiran ta samu damar da zata aiwatar da mummunan kudurin ta........
Bayan kammala cin abinci, Mc Ya Kira su ɗaya bayan ɗaya suke hawa saman step suna taka rawa, sautin kiɗa Ya karaɗe ko'ina na hall din, Ta ko'ina hasken camera ne ke Ƙyalli, sai daukar hotuna sukeyi, abun ba karamin burge prisoners yayi ba, Ay tuni Sajeed Ya miƙe dama ta samu tun da ya shiga filin Ya fara taka rawa hankalin kowa ya dawo kan shi, harta su baba obie da suke atsaitsaye hankalin su na akan shi, abun a jininsa yake da zarar yaji kiɗa bai iya jurewa kamar ana kada mashi mazari, In har baiyi rawa ba hankali sa bazai kwanta ba, wakar da aka sanya tana ƙarewa wakar calm down ta shiga, aiko jiki har rawa yake yi su Parveen suka shiga fili suka dinga tikar rawa, gaba ɗaya suka ja hankulan mutanan hall din, sunyi matuƙar burgesu in ka cire su Yusra dake jin haushin su badan komai ba, sai dai saboda sun hana su rawar gaban hantsi, Hankalin unaisah ba karamin tashi yayi ba, ganin yadda suke rawa da alama sun manta a ina su ke ne, daga ita sai batul ne ba su shiga filin ba, Manyan mutanan dake a wurin ne suka soma yi masu liƙin kuɗi, tamkar ana yayyafa masu ruwan sama.
Hajiya turai da Hajjaty suma suka shiga filin suna tayasu yin rawar, kusan gaba ɗaya suka shiga cikin su, cikin raha da nishaɗi suka taka rawarsu.
Jemimah ta dage duk wanda ya lika mata kuɗi sai ta kwashe su ta tura a aljihun rigarta, ta tarasu dayawa har a hammata take saƙe wasu, tayi zaton abun wasan yara ne.
Mutanan dake harin Unaisah dama jira suke ta miƙe, a lokacin chief Owais Yabar wurin su, Ya tafi amsa kiran da akayi mashi awaya.
Miƙewa ta yi tana tafiya a hankali yayin da idanunta ke akan dance floor din, da alama itama so takeyi tayi rawar ta ɗan gagije jikinta.
"Baiwar Allah sannu" jin muryar mutun abayanta yasa tayi saurin dubanta, zahara ce fuskarta dauke da murmushi, Mayar mata da martanin murmushin unaisah tayi.
"Yawwa"
"Tun ɗazu nakeson yi maki magana ban samu damar yi ba, saboda mutanan da kike atare da su...." da ɗan mamaki take kallon bakuwar fuskar da tayi mata magana.
Miƙa mata hannu zahra tayi don su gaisa, A hankali unaisah ta ɗaura hannunta a cikin nata.
"Sunana zahra ke fa"?
"Unaisah"
"Banyi tunanin zakiyi saukin kai har haka ba,"
Murmushi unaisah tayi mata.
"meyasa kikace haka"?
"Raina ne ya bani haka" girgiza kai unaisah tayi
"Kin burge ni, idan badamuwa inaso muyi hoto a tare"
Bata kawo komai aranta ba, ta amince ma zahra.
Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin curo wayarta daga cikin yar purse dinta, ta dinga daukar su hoto da unaisah, A kalla zahara ta dauki hoto sama ashirin, Tsabar iyayi na zahra harda rungumeta sukayi hoto amanne da juna kamar kanwarta....
"Kinga yanzu na samu wanda zan dinga kallo awayana," ta faɗa bayan sun gama
"Ko zan iya samun layin wayarki? Ina so mu dinga gaisawa.
"Ban haddace number dina ba, kuma wayar bata a hannuna"
Shafa gefen fuskarta zahra tayi"ba damuwa, ay ina zuwa estate din nan zamu dinga haduwa...." wayar zahra ce ta soma ringing da ɗan sauri tace ma unaisah yanzu zan dawo ana kirana" amsa mata tayi da toh, har zahra tabar wajen Unaisah bata daina bin bayanta da kallo ba, hakanan taji ta burgeta, aranta ta ayyana wato duk yadda wani yaƙi ka, to wani zai so ka ne.
Murmushi tayi, tare da juyawa da niyar tabar wurin cikin rashin sa'a ta bange ɗaya daga cikin servers din dake safa da marwa wurin raba abinci, Gaba ɗaya tray din lemun da matar ta ɗauko ya 6are a jikin abaya dinta, glass cups din suka rikito kan floor, hankalin ba karamin tashi yayi ba ganin ta 6ata mata wankanta don ma Allah yasa rigar baka ce
Muryar matar na rawa ta soma bata hakuri.
Shiru unaisah tayi tamkar bazata tanka mata ba tace"bakomai, ay ba laifin ki bane, Ni ce na bangaje ki, bansan da mutun abayana ba"
A ruɗe matar tace"akwai rest room ki zo muje ki wanke rigarki please, idan ba haka ba za'a hukunta ni ne idan wani yaga ruwan lemun nan a jikin rigar ki"
Girgiza kai unasah tayi"a'a bani buƙatar zuwa, Ki tafi kawai, ay rigar baka ce babu wanda zai gani"
Magiya matar tadinga yi mata akan tazo su tafi ta wanke mata rigarta, ganin tasa naci ne yasa ta amince mata, da sauri matar ta zukunna ta kwashe glasses din ta mayar a tray, kafin ta juya Tayi gaba unaisah tabi bayanta, babu wanda ya lura da abun da ya faru saboda sautin kiɗan daya karaɗe hall din hankalin kowa na akan dance floor,.
Wani corridor suka shiga a inda jerin rest rooms din suke ta nuna mata ɗaya daga cikin su, ki shiga zan jira ki anan" amsa mata tayi da toh.
Unaisah kamar kada ta shiga haka take ji saboda hankalin ta bai kwanta da matar ba, buɗe kofar tayi shigarta ke da wuya taji alamun an datse ƙofar, sai dai ranta bai kawo mata komai ba, agaban sink ta tsaya ta kunna tap ruwa ya shiga karanyowa ta soma wanke inda lemun ya 6ata, bayan ta gama ta tsaya tana kallon fuskarta ta cikin mirror bakomai take tunawa ba face fuskar chief Owais hakika Yaja hankalin ta, musamman a lokacin da aka so aci mutunci su ya kare masu martaban su,
Murmushi tasaki har dimple din ta ya lotsa, can kuma ta juya akalar tunanin nata ga garkuwarsu, tasan duk inda yake ayanzu yana cikin koshin lafiya don ta fahimci prime minister ba karamin kaunarsa yake yi ba, tabbas zataso taga yadda zai tarairaye shi.....
_Sam ta manta a rest room take, tunawa da yan uwanta yasa tayi saurin juyawa zata fuce sai dai me? Tana jan ƙofar taji kamar ta damƙi dutse, bata kawo komai aranta ba, ta soma knocking tana fadin"pls kibuɗe min kofar na kasa" shiru taji mata bata amsa mata ba, kusan sau uku tana neman taimakonta amma shiru, bata amsa mata ba, gaba ɗaya taji ta takura hankalin ta ya fara tashi, bubbuga ƙofar tadinga yi tana cigaba da fadin pls bakowa ne akusa ku buɗe mun kofa, tun tana sa ran za a buɗe mata har ta fara fidda rai, zuciyartace ta soma raya mata gaya can za'a cutar da yan uwanta aikuwa da karfi ta soma bubbuga ƙofar kamar zata balle ta, har kafa take sanyawa tana harba jikin ta, babu alamun zata buɗe, tana nishi ta ja da baya ta watso da gudu ta bangaji kofar duk don ta samu ta buɗe amma duk abanza, Lokaci ɗaya tafara burkicewa dama brain ɗin su da rauni acikin ta, gaba ɗaga rayuwar kullan da su ka yi a gidan kurkukun ƙaddara ta fara dawo mata a cikin kanta, sautin dariya dariya ta soma ji da shessheƙar kuka yaran da muryoyin wadannan tsaffin da suka ta6a bata naman mutun ta ƙarfi suka sanyata dole ta ci, runtse idanuwanta tayi tare da sanya tafukan hannayenta ta daddafe kanta dake wani irin mahaukacin sarah mata, wani irin tsoro da firgici ne ya soma ziyartarta, rushewa tayi da kuka tana bugun kofar muryarta da shessheƙar kuka take fadin"Wayyo Allahna ku buɗe mun kofa! na shiga uku, zan mutu kaina, Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'in Boss ka buɗe min kofa zasu kashe ni, Danish kana ina kazo ka taimake ni, nasan bazaka bari a cutar dani ba, nashiga ukuna sajeed naufal Batool wai baku jina nane so kuka na mutu.... cikin fitar hayyaci take yin sambatun tuni mayafin dake akanta ya zame ƙasa, duk tabi ta yamutsa gyaran gashi da akayi mata tamkar mahaukaciya haka ta koma, jikinta duk ya raunata saboda bugun kofar da take yi tana faman ciccije la66anta, ga ƙarancin iskar dake a wurin ta fara affecting dinta, gwanin ban tausayi baiwar Allah, jan numfashi ta cigaba dayi tana ganin jiri jiri a idanunta kamar daga sama taji zubar wani abu a tsakankanin cinyoyinta da wani irin matsanancin ciwon mara na fitar hayyaci nan take wata juwa ta kwashe ta gaba ɗaya ta kife kan floor sumar kanta ta tarwatse har ta saman fuskarta, hannayenta daddafe da cikinta dake ta murɗamata yanayi mata zogin azaba, muryar ta adisashe take ambaton Allah.............._
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Mu haɗu jibi Alhamis Idan Allah yakaimu da rai da lafiya*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
S
kukun Kaddara Takun Karshe Page 14 Complete
by
Novels Elite Admin
May 31, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
_cikin fitar hayyaci take yin sambatun tuni mayafin dake akanta ya zame ƙasa, duk tabi ta yamutsa gyaran gashi da akayi mata tamkar mahaukaciya haka ta koma, jikinta duk ya raunata saboda bugun kofar da take yi tana faman ciccije la66anta, ga ƙarancin iskar dake a wurin ta fara affecting dinta, gwanin ban tausayi baiwar Allah, jan numfashi ta cigaba da yi tana ganin jiri jiri a idanunta kamar daga sama taji zubar wani abu a tsakankanin cinyoyinta da wani irin matsanancin ciwon mara na fitar hayyaci nan take wata juwa ta kwashe ta gaba ɗaya ta kife kan floor sumar kanta ta tarwatse har ta saman fuskarta, hannayenta daddafe da cikinta dake ta murɗamata yanayi mata zogin azaba, muryar ta adisashe take ambaton sunan Allah da daƙyar daƙyar, zufa ce ta soma tsastsafo mata ta ko'ina na jikin ta, kafin wani lokaci jikinta ya saki tamkar matacciya ko yatsanta bata iya ɗagawa ta gama fita hayyacin ta............_
*Shin Ina prime minister ya tafi da garkuwa?*
Lokacin da suka fito daga Hall hannun su ruƙe cikin na juna, Yayin da gimbiya mujeedat da Yazrin suke a biye da bayan su, gaba ɗaya hankalin Jami'an da ke tsaron wurin Ya dawo kansu, da wani irin tsantsar mamaki da Al'ajabi suke kallon fuskar Danish da ta prime minister, Musamman jami'an Canada sun yi matuƙar girgiza da ganin shi, sun ruɗe sai faman Kallo ƙurulla suke bin su da shi.
Wata danƙareriyar mota Suka nufa, irin motar da a mafarki kaɗai talaka ya ke iya ganin ta, da sauri Wani gabjejen Soja Ya buɗe masu murfinta, Cikin motar yadda kasan bedroom tsabar haɗuwarta ga wani sanyin A.c dake sanyaya zukata, a tare suka shiga ciki ba tare da sun raba hannun su daga cikin na juna ba, Gimbiya mujeedat da Yazrin motar dake a jere da tasu suka shiga, zuciyoyinsu cike fall da al'ajabin Danish....
Kusan a tare motocin suka soma tafiya A hankali, Yayin da sojoji ke take masu baya, da kafafuwansu suke tafiya ta gefe da gefen motocin nasu.
Lumshe idanu gimbiya mujeedat tayi yayin da brain din ta ke tariyo mata fuskar Danish, bata san ya akai ta tsinci kanta da jin tsantsar kaunarsa ba, farat ɗaya taji ta kamu da son shi ya kwanta mata aranta, batasan ma ya zata mistalta yadda take ji azuciyar ta ba.
Ita kanta Yazrin zuciyarta ta tsunduma a kogon kaunar matashin da bata san wanene shi ba, jin shi take tamkar ɗan uwanta na jini......
"Mommy, fatana Allah yasa ba mafarki na ke yi ba" can cikin kunnanta ta tsinkayi maganar Yazrin da tayi magana cikin harshen larabci.
Numfasawa ta ɗanyi muryarta da wani irin sanyi ta soma magana da yaren su na larabci
"ban ga laifin mijina ba, yanzu nake danasanin maganar dana gaya mashi ɗazu da mu ka shiga restroom, ban ta6a tsammanin zanga yaron haka ba, ay dole ma ya nemi zaucewa, Ni ko a tarihi ban ta6a jin labarin kamanceceniya irin wannan ba"
"Abun da yafi ɗaure mun kai shi ne, ba mu haɗa alakar komai da shi ba, bamu ta6a ganin ba, ba mu ta6a jin labarin shi ba, sai yau da Allah Ya haɗa mu.....
Fuskokin kowan nan su da tsantsar al'ajab
Slowly motor su ta ratsa katafaren entry way na shiga gidan hateem dake a tsare da security, basu nufi ko'ina ba sai cikin Ƙawataccen Lambun gidan.
Bayan sunyi parking, da sassarfa sojojin dake safa da marwa su ka ƙaraso tare da buɗe ma su marfin motor.
A hankali Prime minister Ya dira kafarsa Ya fito tare da ruƙo hannun Danish, Lokacin daya fito daga motar kusan suman tsaye jami'an dake tsaron gidan su ka yi, sai faman yin dogon wuya suke yi suna leƙen fuskar danish, Sun saki bakunansu kamar lehen sakarai, ƙasa ƙasa da murya sautin raɗar da sukewa junansu ta soma baiyana
"Abun mamaki bai ƙarewa"!
"Kodai idanuwana ne suke nuna min badai dai ba?
"Dama prime minister Yana da ɗa Namiji ne?
"To ko dai 6acewa yayi ne sai daga baya aka gano shi? In ba haka ba ni dai a iya sanina ya'yan sa biyu mata....."
Murmushin gefen fuska prime minister ya ɗan saki jin tseguminsu, aranshi yana mai jin wani irin annushuwa.
sai bayan da suka soma tafiya tukunna motarsu gimbiya mujeedat ta ƙaraso, sam bai son sun biyo su ba, saboda ya makance idanunsa danish kadai su ke iya gane masa, Fitowa su ka yi a tare suka bi bayan Su prime minister, wanda Ya miƙi hanyar shiga wurin shaƙatawarsa da ke a cikin garden.
Yayin da suke tafiya wata irin ni'imtacciyar iska ce ke ratsa fatar su hakan bakaramin ƙaimi ya ƙarawa yanayin ba, danish Ya nutsu Yana bin furannin dake a garden din da kallo, dama can shi ma'abocin son furannine da alama dai Garden din ya burge shi...
Hateem sai satar kallon shi ya ke yi kamar zai lashe shi, shi kuwa wanda akeyiwa kallon bai ma son anayi ba.
Su Gimbiya Mujeedat da Yazrin suna a biye da su ba tare da sanin su ba.
Sauke idanunsa yayi akan Peacocks da ke yawo a garden din sun bubbuɗe Tail feathers dinsa gwanin ban sha'awa, ba karamin burge shi su ka yi ba..
Wani ƙawataccen wuri suka nufa, inda akayi shimfiɗa ta alfarma irin ta sarakuna, a kewaye yake da furanni launuka daban daban, Ga wata lumbutsetsiyar Round mattress mai tudu lallausar gaske, an kewaye ta da matassan kai masu laushi.
"Bismillah mu zauna" muryar Hateem ce ta dawo dashi daga kallon gardeen din da yake yi, A hankali suka zauna saman shimɗidar.
Daga inda suke a zaune suna fuskantar swimming pool tamfatsetse, launin ruwan da ke a cikinsa blue sky ne pure, ga wasu fararen agwagi saman ruwan suna ta shawagin su.
A ƙalla sun dauki tsawon mintuna babu alamun danish zai mayar da hankalinsa akan prime minister, ya nutsu sai kallon agwagin ya ke yi.
Yayin da shi Hateem din gaba ɗaya ya tattara nutsuwarsa da hankalinsa akan danish, wani irin kallon kurulla yake jifar shi da shi mai dauke da zallar kaunarsa, Jin shirun yayi yawa yasa shi yin gyaran murya, hakan Yaja hankalin Danish zuwa gare shi, slowly ya juyo tare da ɗaura fararen idanunsa akan fuskar minister, a karo na farko kenan daya fara kallon shi, nan fa suka fara jifawa juna kallon kallon, ko ƙyafta ido ba sa yi, sai da suka kusa shafe mintuna batare da sun kau da ido ga juna ba, su gimbya mujeedat dake a tsaye can gefen wata bishiya mai yalwar rassa da ganyayyaki sun kura ido suna kallon su, Ita da yazrin dake a gefen ta.
Wani irin ƙwarjini Danish yayi mashi, da sauri ya katse kallon da suke jefawa juna ta hanyar yi mashi magana
"Sorry ban gabatar maka da kaina ba, Ni sunana Prime minister Hateem Obinna, kai fa"? Ya faɗa yana duban shi har lokacin danish bai daina jefa mashi kallon ba, babu alamun zai tanka mashi kamar akwai wani abu daya ja hankalin da yasa shi kallon nasa.
"Ka yi shiru baka ce komai ba," kamar kurma haka danish yayi mashi.
Dafe kai Hateem yayi muryarshi da kasala ya furta"please ka yi min magana, ba ka son yadda na ƙagu da son ganin ka samu lafiya ba, na damu da kai kamar yunwar ciki na, dan Allah ka saki jiki dani, kada ka azabtar dani da kaunar ka...." fuskar shi a yamutse yake yi mashi magana.
"Ina fata babu inda ke yi maka ciwo yanzu"? Ya jefa mashi tambayar, lumshe mashi idanu danish yayi alamar eh.
"Ya Ilahi, ba zaka yi min magana ba, sai dai ka yi min nuni da ido, ni bana so ka daure ka yi min magana, Inason jin muryarka ko hankalina ya kwanta, namanta ban faɗa maka ba, gobe da asuba zan bar ƙasar ba lallai mu sake haɗuwa ba, shiyasa nakeso ka bani haɗin kai mu more lokacin nan da muka samu...." cikin sanyin murya ya ƙare maganar.
Har lokacin kallonsa danish ya ke yi, abun ya ɗaure mashi kai, Ya rasa gane ma'anar kallon nan.
"Ko dai kana mamakin kamannina dakai ne"? shiru yayi mashi.
"Wayyo Allah na, to ko dai baka jin harshen hausa ne inyi maka da turanci ko larabci ko french wanne yare kafi ji a cikin wadannan"? A ƙagare da son jin amsar shi ya faɗa yana kallon la66ansa burin shi ya motsa su don yayi magana.
Ƙiri ƙiri danish yana neman ya zautar da prime minister, zuciyarshi a jagule yace"nayi maka uziri tun da ba ka jima da farkawa ba, may be har yanzu baka gama dawowa normal ba, a hakan ma na samu kwanciyar hankali, ganin ka da nakeyi ba karamin faranta raina yayi ba" ya fada yana ɗan murmushi sama sama.
"Nasan kana jin yunwa bari nayi magana akawo mana abinci" wayarsa ya zaro daga aljihunsa har time din yana lura da kallon da danish ke jefa mashi har ya fara jin shakkar ko dai ifritan dake jikinsa ne suka motsa, dauriya ce kawai irin ta Hateem
"Namanta ban tambayeka ba, wani kalar abinci kake son ci"? Shiru yai masa, hakan yasa shi yamutsa fuska "Okey,Tun da baka iya yi min magana kar6i waya ka rubuta min ta text message sai in karanta" ya faɗa tare da miƙe ma danish wayar, baiyi tsammanin zai kar6a ba, sai gani yayi yasa hannu ya kar6a, Ya soma daddanata, Wani irin dadine ya lullu6e hateem, abun mamaki ya dauki lokaci yana yi mashi dogon typing har mamaki ya kama Hateem sai da ya mula yasha iska tukunna Ya miƙa ma Hateem wayar, Cike da zumuɗi ya kar6a don ganin me ya rubuta mashi
Har saida gabanshi ya ɗan faɗi ganin jagwalgwalon da danish ya rubuta mashi, irin wanda yara sukeyi idan suka damƙi waya.
da sauri ya dago suka haɗa ido da juna, baisan sa'adda dariya ta kubce mashi ba, ya dinga 6a66aka dariya har fararen hakoransa suka bayyana masu kyan gaske.
Shi duk a tunaninshi dagangan Danish ya rubuta masa jagwalgwalo awaya, alhalin shi baisan amfanin wayar ba, Shi bai ma ta6a ganin waya ba sai da suka shigo duniyar mutane, sannan bata ta6a zuwa hannunsa ba, yadai san ana daddanata da yatsun hannu shiyasa ya kar6a ya yi mashi abun da zai iya.
"Please meke damunka ne"? Bayan Ya tsagaita da yin dariyar ne yayi mashi maganar, shiru yayi bai tanka mashi ba.
Yanke shawarar kiran Chief Owais yayi saboda ya tambaye shi dangane da Danish don kada a samu matsala tun da shi baisan ya rayuwarshi take ba, yana son yaji ko kurma ne.
Bugu uku Chief yayi picking call din
"Uncle yanzu nake shirin kiranka, Don inji ko lafiya"?
"Owais baisan ya zanyi da shi ba, dama ka fada min yana da wuyar sha'ani, wallahi tun ɗazu yaƙi yi min magana sai dai kallona da yake ta yi, na rasa gane kanshi, har waya na bashi don ya rubuta min abunda yake son ci amma a karshe sai ma ya rubuta min jagwalgwalo, Ko dai kurma ne"?
muryarshi tamkar zai fashe da kuka yayi maganar.
Da buɗar bakin chief sai cewa yayi"ina fata akwai sojoji a kewaye da ku"? ya fadi hakanne gudun kada lalurar Danish ta motsa musamman yanzu da yaji halin da suke a ciki.
"Babu, Mu kaɗaine"!
"Uncle ka sanya sojoji su yi maku ƙawanya saboda yaron ba shi ɗaya bane, bana so asamu matsala"
"In sha Allah ba za'a samu matsala ba, kafin mu zauna nayi mana addu'a, kuma nayi imanin babu abun da zai cutar da ni ko shi bi'iznillahi" da kwarin gwiwa prime minister yayi maganar
Yana iya jiyo sautin ajiyar zuciyar owais.
"Uncle, ba kurma ba ne, abun da nake so da kai, ka ɗauka tamkar Jiriri ne sabon haihuwa, saboda bai son komai ba, wayar da ka bashi baisan amfanin ta ba, please ka bashi kulawa yadda ya dace sannan ka ƙara haƙuri da shi, A hankali zai fara sakewa" amsa mashi yai toh, kafin yai katse kiran.
Danish nata kallon sa bayan ya gama, har zai kira don a kawo masu abinci, ya jiyo motsin tafiyar mutane da sauri yakai idanunshi kansu, Hadimai ne su biyu sanye da uniform na ma'aikatan gidan, kowaccensu hannayenta na a ruƙe da faffaɗan faranti, daga saman su anjera kayan abinci nau'i daban daban, wannan ba aikin kowa bane face Gimbiya mujeedat, itace tayi tunanin zasu buƙaci abinci shiyasa tayi saurin kiran landline na gidan ta isar da sakon a kawo masu abinci.
Ya ɗanyi mamakin ganin su da abinci, bayan bashi ya bada umarnin su kawo ma su ba, kwata kwata baisan da zaman gimbiya mujeedat da yazrin ba, har yanzu bai gan su ba, saboda bai son sun biyo su ba.
Cikin girmamawa hadiman suka russina har suna hada baki wurin furta"sannu da hutawa yalla6ai" suna magana suna satar kallon danish kamar kwayan idanunsu zasu faɗo ƙasa.
"Wanene ya bada iznin a kawo mana abinci"?
Da sauri sukace"umarni ne daga wurin gimbiya mujeedat"! nuna masu tsakiyar shimfiɗar yayi, anan suka ajiye masu kayan abincin kafin suka juya zasu bar garden din suna tafiya suna waiwayon Danish har da tuntu6en su tsabar gulma da kitsibibi.
ta riga tasan halin hateem bai cika yarda ba, hakan yasa ta tura mashi tezt message.
_I ordered them to bring you food because I was worried about you, tun da muka shiga dinner hall baka ci komai ba_
Murmushine dauke akan fuskarshi bayan ya gama karanta sakon nata, yai mata reply da cewa"Nagode Gimbiyata"
Tuni ƙamshin soye soyen da aka kawo masu ya buɗe hancinansu, shi kanshi danish din yunwa yake ji, tamkar baici abinci ba.
Farantin farko yana dauke da banƙararrun kaji anyi masu jar suya sai maiƙo sukeyi, ga tsiren nama daban kuma, yaji kayan lambu dana kamshi, ga wasu luxury warmers daga gani abinci ne a cikin su, ɗayan tray din Glasses ne da ke dauke da exotic sodas Fresh coconut water, premiun juices and coconut milk, sun haɗo masu da silverware and tissue box duk wani abu dai da zasu buƙata......
'Bismilla me zamu fara ci ko in za6a mana"? Cikin kulawa yayi maganar yana duban danish dake ta faman haɗiyar yawu.
Bai jira amsar shi ba, Ya zuba masu sakwara with egusi soup, taji uban naman ganda manyan yanka ta dahu tu6us.
Ya lura bai da alamar ci, Hakan yasashi yanke shawarar bashi abaki,.
Wanke hannunsa yayi a bowl kafin ya zura shi a plate din ya debo sakwarar da miya yakai mashi saitin bakin shi, bai yi tsammanin zai ci ba, ganin ya damtse bakinsa can kuma ya ɗan buɗe kananun la66ansa a hankali hateem ya sanya mashi abaki, yadda yake tauna tamkar baisan ci nan da nan ya haɗiye, cigaba da bashi yayi abaki yana ci, kamar wani karamin yaro, shi kuwa hateem dadi yake ji yana bashi abinci yana ci, Ba zato ba tsammani yaga danish ya sanya hannun shi ya ɗebo sakwarar ya miƙa mashi don yaci shi ma, yaga tun dazu yake ta bashi shi baici ba...
Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyar Hateem, bakomai ne ya faɗo masa a ransa ba, face maganar Owais da yace yaci gaba da bashi kulawa a hankai zai saba da shi, tabbas kuwa hakane.
Buɗe baki yayi danish ya sanya mashi ya soma ci, yayin da suke kallon juna, tuni yaji hawaye sun cika idanunshi sai dai bai bari sun zubar masa ba, da sauri yayi kokarin danne su...
Cigaba da bama juna abinci su kayi, su gimbiya mujeedat dake kallon su ita da yazrin, murmushi ne ɗauke akan fuskokinsu, tsabar Jin dadin yanayi yasa suka samu wuri saman wasu kujerun shan iska suka zauna...
Bayan sun gama da plate din sakwarar, Tsiran naman suka fara ci, Idan ya bashi shima sai ya bashi abaki, suna ci suna kallon juna.
Saboda tsantsagwaran kauna da zarar abincin ya 6ata ma danish gefen bakinsa da sauri yake cirar tissue ya goge masa bakinsa, daga shi har danish din sun jima basu ji abinci mai yawan gaske ba irin nayau, kusan rabi da kwatar abincin saida suka cinye shi, bayan sun gama suka koma suna shan coconut milk da fresh juice.
Sauke farantan hateem yayi can gefe ɗaya ƙasa, kafin ya mayar da hankalinsa akan danish, rungumo shi yayi ajikinshi, hannun shi ɗaya dafe da bayan shi, ɗayan hannun yana ruke da wayar shi, Camera ya shiga don ya yi masu hotuna ko ya samu waɗanda zai dinga gani yana ɗebe kewarsa, da sauri Danish ya runtse idanunsa alamar baya so, kokari yake ya buge wayar gaba ɗaya hakan ba karamin ɗaga hankalin hateem yayi ba, cikin sanyin murya ya furta"pls ka bari nayi mana hoto mana, inaso na samu wanda zan dinga kallo bayan na koma ƙasa ta," cikin sigar lallashi yake yi mashi magana akan ya buɗe idanunsa, dakyar ya samu ya ɗan buɗe su, maimakon ya kalli camera din sai ya dinga kallon fuskar hateem din, babu yadda baiyi dashi ba akan ya kalli camera amma yaƙiya kamar wani karamin yaro, A haka hateem yadinga daukarsu hotuna idanun danish akan fuskarshi, wasu hotunan ya rufe idanunsa, hada video yayi masu mai ɗan tsayi, ya kwantar masa da kanshi saman kafadarsa, da wanda ya sumbaci forehead dinsa, kamar wani ɗan cikinsa, A kalla ya dauki hotunansu sunkai Talatin, bayan video da yayi masu kusan goma.
Kafin ya gama ɗauke ɗauken hotunan, kwatsam Yaji danish Ya ƙanƙame shi da hannayensa da farko ya ɗan ji fargaba amma daga bisani da yaga yana lumshe idanunsa sai yaji hankalin ya kwanta, wani baccine mai daɗi yayi awon gaba dashi, kanshi asaman shoulder din hateem, A hankali Ya gyara mashi kwanciyarshi, ya rungumo sa, kamar zai maidashi cikin shi, hannayen danish na abayan hateem ya ƙanƙamesa kamar wani yace zai ƙwace masa shi.
Wani kallon so da kauna hateem yake binsa dashi yayin dayake yin baccin, A hankali ya soma shafa bayan shi da yatsun hannayensa kafin ya zura hannun cikin sumar kansa tamkar yanayi mashi susa, harta numfashin danish sai da ya canza saboda daɗin da yaji na abunda Hateem ke yi ma sa.
Bakinsa yakai saitin kunnan danish, cikin muryar raɗa yayi mashi magana.
"Do you feel what I feel about you?"
Ya faɗi hakan batare daya sanya ran danish zai tanka masa ba, a tunaninsa yayi zurfi a baccin nasa.
Kamar daga saman yajiyo daddaɗar muryarsa tamkar ana busa sarewa ta ratsa kunnansa da cewa "Yes, I do. I feel more than you might think"
wayyo Allah dadi prime minister tamkar zai zauce tsabar murna da jin maganar danish, Cigaba da kallon fuskarsa yayi tamkar zai haɗiye sa.
"Nakasa yarda cewa kaine kayi min magana da bakin ka, ko dai kunnuwana ne suke jiyo min ba dai dai ba"? da biyu ya fadi hakan saboda yana son ya ƙara jin muryar shi.
"No, ni na maka magana" danish ya bashi amsa idanunsa a rufe, har time din basu raba jikin su daga na juna ba
"Meyasa ka damu dani"? Danish ne ya jefa mashi tambayar
Murmushi hateem yayi kafin ya furta"tun lokacin da nafara Yin tozali dakai, Naji na kamu da matsananciyar kaunarka, duk da bansan wanene kai ba, amma naji ka kwanta min araina, ka sace min zuciyata, babban abinda yafi jan hankalina gare ka shine kama da muke da juna, Ina jinka tamkar ni na haifeka, Allah ne kadai yasan son da nake maka Danish, wallahi bana son rabuwa dakai, bana son in tafi in barka, don bani da yarda zaniyi da natafi da kai" Kalaman da yake furtawa daga cikin zuciyarsa suke fitowa, abunda ke ransa ne yake bayyana masa ko ya rage radadin da yake ji na kaunarsa .
A hankali danish ya ɗan buɗe idanunsa yana satar kallon fuskar hateem dake a dab da tashi, wani irin kallo yake jifar shi da shi mai wuyar fassaruwa batare da prime minister Ya ankara ba.
"Bansan su wanene Iyayenka ba, bansan dalilin dayasa sukayi watsi da rayuwarka ba, amma bana tsammanin akwai wanda zai samu ɗa kamarka ya jefar sai dai idan da wani dalilin"
Runtse ido danish yayi sam baya son anayi mashi maganar iyayen sa.
Muryarshi na dan rawa ya furta"ka daina yi min magana akan iyayena, bana son su bana son duk wani abu daya shafe su, If I could see them, I would kill them."
A ruɗe prime minister ya dubi fuskar danish da tsantsar mamakin yadda kalaman suka fito daga bakinsa, har kokwanto yayi anya shi yayi maganar?
Ko da yai yunkurin tambayarshi meyasa yace haka, sai jinshi yayi shiru alamar wani baccin ya dauke shi....
Haƙiƙa furuncin da ya yi akan iyayen su sun tada masa hankali, sun tsaya masa a ƙahon zuciyarsa, duk da baisan dalili ba amma yaji fargaba aransa, musamman da ya ambaci Idan ya gansu zai kashe su .......
Lumshe idanunsa yayi, tare da ƙara janyo danish ajikinshi, yaci gaba da ɗan bubbuga bayansa kamar mai lallashin ƙaramin yaro a haka harshima baccin yayi awon gaba dashi, wata irin iskace mai ni'ima taci gaba da kaɗa wurin da suke.......
gaba ɗaya abun da ke faruwa akan idanun Yazrin, sai dai basu samu damar jin komai da suke tattaunawa ba atsakanin su saboda akwai tazara.
Nannauyar ajiyar zuciya Gimbiya mujeedat ta sauke tare da kallon Yazrin dake a gefenta"gwanin ban sha'awa, sun burgeni, a yadda suka kwanta kamar Uba da ɗansa, ban ta6a jin zafin rashin ɗa bamiji ba sai ayau dana kalli Hateem da yaron nan, wallahi sunyi min kyau sun tafi da imanina ......." Cikin sanyin murya Gimbiya mujeedat tayi maganar.
Jikin Yazrin yayi sanyi lakwas tamkar wadda aka zarewa laka, idanunta sun ciko tab da kwalla ta soma magana ba tare data janye idanunta daga kan shimfiɗarsu Hateem ba.
"Daddy ya bani tausayi, na tausaya masa mommy, daga shi har matashin nan, Ina kaunarsa Ina jinshi kamar ɗan uwana na jini... " da raunatacciyar murya tayi maganar.
"Mommy abun da yafi ta6a zuciyana, yaran ba su da kowa a daji aka tsince su kamar yarda naji akhi owais Ya faɗa, wallahi banji dadin yadda Su oum saratu suke jifarsu da munana kalamai ba, ni abun da ya daure min kai Yaran sunyi kama da family din daddy sosai"
Jinjina kai Gimbiya mujeedat tayi ba tare da ta iya furta komai ba, Ta yunƙura ta miƙe Cikin takun nutsuwa Ta nufi shimfidar su hateem, Yazrin na zaune bata bi bayanta ba, bakomai zuciyarta ke tariyo mata ba, face lokacin data haifi baby boy din su da suka rasa, haƙiƙa taji bakin cikin da bata samu damar ganin ko da gawarsa bane, taso ace ko da fuskarsa ne ta gani, tuna wannan yasa taji hawaye sun taru cikin idanuwanta
Adai dai bakin shimfiɗar ta ɗan zuƙunna tana kallon danish from head to toe, yayin da zuciyarta ke azalzalarta da kaunarsa, sai kallon shi takeyi babu kyaftawa, ranta ne ya raya mata wani abu da bata da tabbaci akanshi, hakanan taji tana son ta jaraba gwadawa, Miƙewa tayi da sauri ta zagaya ta dayan bangaren da farantan abincin da aka kawo masu suke, ta zaro ƙaramar wuƙa ta yanka fruit, ta dawo bangaren inda danish Yake ta zuƙunna duk akan idon Yazrin da mamaki yagama cikata, zuciya da sake sake arude ta furta me mommy zatayi wuƙa"? hankalin ta yadan tashi tsoron ta kada ta aikata wani abu duk da tasan hasashenta bazai ta6a zama gaskiya ba...
A hankali ta ɗaura ziraran yatsun hannunta kan sumar danish ta ruƙo ƙasanta, Cike da fargaban kada su farka, tana yi tana kallon fuskokinsu cikin kwanciyar hakali suke fitar da numfashinsu, bacci yayi dadi
Yatsun hannunta na kerma ta yanki sumar kan danish da wuƙar, ajiyar zuciya ta sauke tare da miƙewa ta mayar da wukar cikin kayan abincin kafin ta juya tana faman sauke ajiyar zuciya ta nufi Yazrin tunkafin ta ƙarasa yazrin ta miƙe tana tana fadin"mommy! Meyasa kika datsar mashi gashin kai"! Idanunta azare ta fada tana nuna ziraziran gashin danish da gimbiya mujeedat ta cira daga kanshi
Fuskarta dauke da murmushi tace "Ki kwantar da hankalin ki, kinsan dai mom dinki ba matsafiya bace," dariya yazrin tayi"ina kyautata maki zato a koda yaushe Rabin raina" lumshe ido gimbiya mujeedat tayi"ki ajiye min gashin nan a wurinki, Idan muka koma gida zan tambaye ki shi" da sauri Yazrin ta kar6i gashin daga hannun mom mujeedat, ta cire cover din wayarta ta ɗaura gashin abayan wayan kafin ta mayar da cover din sosai ta matse shi ta yadda bazai ta6a faɗowa ƙasa ba.
"Yanzu ki zo mu koma dinner hall, kada aji shiru babu ni babu hateem bayan saboda mu akayi taron" amsa mata yazrin tayi da toh" a jere suka nufi hanyar fita daga garden din, suna tafiya Yazrin na waiwayon shinfidar su danish, har saida ta 6ace ma ganinta tukunna ta dauke idanunta daga gare shi.
*Dinner Hall*
Bayan zahra ta kammala yin wayar, Jiki na rawa ta dawo Ciki tana nema unaisah, kamar zata zauce sai ƴan waige waige take yi babu ita babu alamarta, kusan sau uku tana zagaye tsakar hall din wurin neman unaisah amma babu ita, zuciyarta ba ƙaramar karaya tayi ba, Har cikin ranta bata ji dadi ba, saboda taso su sake ganawa da juna, Yarinyar ce ta kwanta mata aranta, musamman yadda ta sakar mata fuska har ta amince mata su kayi hutuna, dabara ce ta faɗo mata, ganin ɗaya daga cikin matasan ƴan matan a tsaye tana kallon masu yin rawa akan dance floor sai murmushi take saki, da sauri Zahra ta nufe ta, muryarta da sanyi ta furta"sannu baiwar Allah" firgigit batool ta dubeta da alama ta razana don bata tsammaci jin muryar wani a kusa da ita ba
"Kiyi haƙuri na baki tsoro ko"? da fara'a zahra tayi mata maganar, batool kuwa sai kallon bakuwar fuskar takeyi taƙi tanka mata, gani take kamar zata cutar da ita ne tun da ta fahimci basa son su
Miƙa mata hannu zahra tayi"ni suna zahra, ke fa"? Cike da rashin yarda ta furta"batool" muryarta da ɗan rawa tayi maganar, ba tare da ta ɗaura hannunta asaman na zahra ba, nan take zahra ta fahinci tsoron ta take ji hakan yasa tace"ki kwantar da hankali yar uwata, Bana ɗaya daga cikin waɗanda suka ci muku mutunci ɗazu...." still bata saki fuskarta ba
"Shikenan, yanzu ki faɗa min ina ƴar uwarku Unaisah? Muna cikin magana da ita ɗazu aka kirani awaya sai naje amsa kiran kafin nadawo na taras bata nan, Ko kinsan inda take"!?
Sai da ta ambaci sunan Unaisah batool tafara kyafkyafta idanunta tana bin dakin taron da kallo, sai yanzu ta tuna da tsawon lokacin da bata ga gifcin unaisah ba, kuma bata cikin masu yin rawa, nan fa hankalin Batool Ya fara tashi ta fara ƴan waige waige fuskarta a yamutse babu nutsuwa
Ganin yadda ta ɗaga hankalinta ne yasa Zahra cewa"ko kema bakisan inda taje bane" ɗaga mata kai batool tayi muryarta adabarbace ta furta"ban..bansani ba, bamu jima da rabuwa da juna ba, atare muke zaune can mu da su chief kafin tashin ta" ta fada Tana nuna mata wurin..
Ruƙo hannun batool zahra tayi "zo muje mu nemo ta," da sauri batool tabi zahra suka soma bi sako da lungu na hall din suna neman Unaisah, ba tare da sun fada ma kowa ba ...
____________________________💋✍️
Jin ta ruƙo hannunshi yasa shi yin sauri fusgewa Yana bin ta da kallo mai cike da fargaba
Jikinshi har kerma yake yi saboda matar bata kwanta mashi aran shi ba,
Murmushi ta ɗan sakarmashi cike da fargabansa ta furta"kayi haƙuri dan Allah, bawani abu zanyi maka ba, Inaso mu yi hoto ne" ta fada tana nuna masa i phone din hannunta, maƙe mata kafaɗa naufal yayi muryarshi da yar tsiwa tamkar zai fashe da kuka yace"banso, Ni ki ƙyale ni, kuma wallahi ki daina kallona," Ranshi a6ace yayi maganar, arude hajjaty ta soma lallashin shi gudun kada ya janyo hankalin mutane gare su.
"Dan Allah ka yi hakuri, Idan na bata maka rai, alfarma ɗaya nake nema a wurinka, Ka fada min sunanka"?
Harara naufal ya wurga mata, Yana faman haɗe rai yace"sunana Sajeed"
Tuni yanayin fuskarta ya canza, tayi zaton zataji irin sunan ɗanta,
Gyaɗa kai tayi"masha Allah, Allah yayiwa rayuwarka albarka, amma baka ga muna kama da juna ba"? ta faɗa da fara'a akan fuskarta, Ta6e baki naufal yayi alamar ta takura masa hada ɗan bubbuga kafafunsa"Ni bani kama dake, bansanki ba, dan Allah ki ƙyale ni, In shaƙi iska" yanayin yadda yayi maganar yaso bata dariya,
"Naji zan ƙyaleka, ka shaƙi iska but pls ka bari na dauki hoto dakai"!
Juya mata ƙeya yayi atakure yace"sai dai ki ɗauki bayana" dariya tayi sosai tana kallon bayan shi.
"Kaga dan Allah ka juyo na dauki fuskarka, Ita nakeson gani, Harma In nunawa Mijina shima yaga mai kama dani" maƙe mata kafaɗa naufal yayi alamar a'a.
Magiya tadinga yi mashi amma yaƙi juyawa, ta rasa ya zatayi da shi.
Sajeed da ke ta kallon su, baisan me suke tattaunawa ba, A hankali Ya nufo su,
"Bro, meke faru ne"? Ya faɗa yana kalon fuskarshi dake a daure
Da yatsan hannu ya nuna mashi hajjaty dake abayn shi"matar nan ce ta ɗazu da take ta kalllona, shine ta biyu ni wai dole sai ta dauke ni hoto ni kuma nace mata bana so"
Ɗagowa naufal yayi su ka haɗa ido da Hajjaty, harta bude baki zatayi mashi magana sai kuma ta fasa, saboda ganin suffar Sajeed kamar zaifi naufal din taurin kai, a tunaninta amma ga mamakinta sai ji tayi yace mashi"to meye aciki? Ba hoto kawai ta buƙata ba"? Ɗaga mashi kai naufal yai, Ruƙo hannunshi sajeed yayi" dallah juya kaje ku ɗauki hoton, In ba haka ba bazan ƙara taimaka ba wurin koya maka karatu" ba don yaso ba, ya juya yana jifar hajjaty da harara kwayar idanunsa kamar zasu faɗo ƙasa,
"Nagode sosai, Kai meye sunanka"? fuskarta dauke da murmushi ta tambayi Sajeed, Kafin yai yunkurin bata amsa naufal yai sautin cewa Sunan shi Naufal, Wani kallo Sajeed Yayi mashi da ruɗani akan fuskarsa jin Ya canza mshi suna, da ido yai mashi alamar da nan take ya gane me yake nufi wato Ya faɗa mata sunan sa amatsayin nashi, shine yace shi sunansa Naufal
Jim ta ɗanyi har cikin zuciyarta sunan ya dake ta, Taso ace mai kama da itan ne yake da suna Naufal sai dai kash shi sunan shi Sajeed.
"Kawo wayar nayi maku hoton" da sauri ta miƙa ma sajeed wayar ya kar6a, ya soma daukarsu hoto, Hada kokarin Jan naufal Ya matsar dashi jikin hajjaty gaba ɗaya ya takura mashi, duka hotunan sunyi bala'en kyau kamar ɗan ta, sai dai fa babu fara'a akan fuskar naufal har ya kammala daukar su, hajjaty ta kar6i wayar tana yi masu godiya.
Suma su jamimah anyi masu hotuna tare da Sir mubarak da Mom turai, harta su Zaki sai da su kayi hotuna da su, kamar ƴan uwan juna.
Haka zalika Su Haris da Javed suma hada su akayi hotunan, kowa ya yi kyau ana ta kwasar shagali.
Hajiya saratu dake ta faman satar kallon parveen duk in da tayi akan idonta, ta sanya mata ido sosai, tsabar ji da kai ne ya hana ta nemi alfarmar ta su dauki hoto atare, sai ta koma tana daukarta a fakaice da wayar hannun ta ba tare da ta ankara ba.
Hankalin Batool ba karamin tashi yayi ba, Ko'ina sun duba ita da zahra babu Unaisah, Jikin ta har Ya fara kerma tsabar tashin Hankali, sune har wajen hall din neman Unaisah, Dawowa ciki su kayi cike da fargaba, can zahra ta tuna da akwai restrooms a dakin taron, ajiyar zuciya ta sauke tare da kallon batul tace su ɗan jirata, watakil ta shiga toilet ne, zama sukayi a table daya ita da batool suna jiran unaisah ta fito.. ..
*Chief Owai*
A tsaye yake a wani area dake a hall din, Ya juya bayansa, hannunsa ɗaya ruke da phone dinsa yayin da dayan hannun ya zuba sa a trouser pocket dinsa, bai jima da kammala yin wayar da ta yi silar tada sa daga wurin zaman sa ba.
Layin boss Ya danna ma kira bugu ɗaya yayi picking.
Muryarsa ƙasa ƙasa tamkar ta me yin raɗa ya furta" ina fata ka same su lafiya"?
On the other hand muryar boss ta karade kunnansa"tun dazu na shigo gidan, suna nan cikin koshin lafiya yalla6ai, yanzu haka ina atare da salsabeel sai fada yake min wai jiya hankalinsa ba akwance yake ba, sun ji shiru Dr jazz bai leƙo su ba, sannan mu ma bamu kira ba kamar yadda muka sama"
Daga can cikin wayar yajiyo muryar salsabeel yana fadin"ka fada masa jiya ko isasshen bacci ban samu ba, deeja ta hanamu sukuni daga ni har ƴan uwanta daƙyar na samu yarinyar nan tayi bacci".
Lumshe ido yayi ahankali Ya furta" Please tell him I'm sorry. It won't happen again. We were busy with dinner preparations yesterday. in sha Allah, cikin kwanan nan zasu baro anguwar nan su dawo cikin ƴan uwan su"
Taj yace"amma naji dadi Yalla6ai, saboda bani da burin daya wuce inga an haɗa kan yaran nan, su gana da ƴan uwansu, hankalin su sai yafi kwanciya"
Sun ɗan jima suna yin wayar, kafin daga bisani su ka yi sallama, tunkafin ya sauke wayar daga kunnansa daddaɗan ƙamshin turarenta ya daki hancinsa har sai da lumshe idanunsa saboda yadda fragrance din Ya ratsa shi, tuni ranshi ya bashi cewar itace saboda haddar turarenta da yayi
Shiru yayi batare daya juya sun fuskanci juna ba, sai ma ya ci gaba da danna wayarsa.
Sautin tarin ta da yaji ne yasa shi saurin juyawa yakai idanunsa saitin inda take, hannunta ɗaya dafe da gefen cikin ta, ɗayan hannun kuma yana ruƙe da Mayafinta da ya zame, lallausar sumar kanta ta lullu6e bayanta baƙa wulik da ita, babu alamun tasan da zaman shi a wurin, yanayin ta kamar bata a hayyacin ta, ganin tana kokarin faɗuwa kan fillow yasa shi yin saurin nufarta, ya sanya hannu ya janyota gaba ɗaya ta fada kan broad chest dinsa, luf ta kwanta masa, ta daddafe waist dinsa da hannunta, yana iya juyo fitar numfashin ta da sauri da sauri, hankalinsa ba karamin tashi yayi ba.
"Nazli! Are you okay? What's wrong? Are you alright?" a ɗan ruɗe ya yi maganar.
Ƙara ƙanƙameshi tayi muryarta da wani irin sanyi da zaƙi ta furta"bana jin daɗi, kaina da ciki na ciwo su ke min, sannan bana son hayaniya, kwata kwata bana son zama awurin nan" yanayin yadda take yin maganar ba karamin narkar masa da zuciya yayi ba, ƙamshin turarenta ya kanainayesa.
"Bana son zama anan, rikicewa nakeyi" cikin wani irin salo take maganar, Nazli karshe ce, babu namijin da zai haɗa jiki da ita batare dayaji sauyi atare da shi ba, koda kuwa zuciyarsa dutse ce.
bakomai yasa shi yadda da kalamanta ba, face sanin lalurarta na rashin son hayaniya, tun da kuruciyarta, daga bayane ta samu sauƙi bayada likitoci suka tsaya tsayin daka don ganin ta dawo normal, tunaninsa abunne ya dawo mata yan zu shiyasa ya aminta da ita......
Yanke shawarar fita yayi da ita daga hall din kota samu lafiyar jikin ta,
"It's okay, Let's go. I'll take you home and you can rest."
maƙe mashi kafaɗa tayi tana fadin"I can't walk. My legs hurt."
Kallon takalman kafarta yayi wasu matsiyatan high hills ne masu tsini na fitar shariya, irin takalman da tafi sha'awar sanyawa kenan, mafi yawan lokutta suna jaza mata ciwon ƙafa, sai da ya fara duddubawa ya tabbatar babu mai kallon su, kafin ya sanya hannu ya ɗauketa gaba ɗayanta Ya nufi second door da ake fita hall din bai bi ta ainihin kofar fita ba, don bayason wani yagansu.
Bayan sun fita, yayiwa ɗaya daga cikin sojojin dake tsaron ƙofar magana akan ya kawo mashi motarsa, bayan ya miƙa masa key, jim kadai sai gashi ya kawo motar, ya fito tare da buɗe masu, a backseat ya shigar da Nazli, sai faman lumshe idanunta takeyi masu kama dana ɗawisu saboda kyau
Cikin kulawa yace"Calm down, He will take you home."
ya fada yana nuna mata sojan daya kawo masa motar, girgiza mashi kai tayi da wata irin kasalalliyar murya tace"I want you to take me. Don't you have time for me?" She bit her soft, pinkish lips.
"Tomorrow, I will leave the country. I am not sure if we will meet again,"
her words touching his heart deeply sai yaji kamar bai kyauta mata ba, a matsayin ta na yar uwarsa rabin ransa kuma jinin jikinsa.
Bai gama yanke shawara da zuciyarsa ba, Yaji ta ruƙo hannunsa baisan sa'adda Ya shige cikin motar ba, sojan da zaiyi driving dinsu Yai wa motar key, driving slowly suka miki hanyar zuwa gidan prime minister.
A lokacin da baiyi tsammani ba, yaji ta ɗaura kanta saman broad shouder dinsa, ta ruƙo yatsun hannayenta a cikin nashi, wani irin sanyi sanyi ne ya ratsa zukatan su, Tsawon Lokaci basa kula juna till to day.
Ranta ne ya bata cewar yana kallon ta, A hankali ta dago da sexy eyes dinta akan fuskarsa karaf suka shiga cikin nashi, cigaba da kallon juna su kayi babu alamun gajiya.
_Unexpectedly, she planted a kiss on his chin. He closed his eyes for a moment, put one hand on her hair, and slowly put his smooth lips on her forehead, gently pecking it._
_Gaba ɗaya sun shiga yanayi, sai dai fa duk da haka babu fara'a akan fuskokin su kamar basa son kasancewa da juna, bayan motar ta isa gidan, bata bari chief ya kubce mata ba, don ta fahimci hankalinsa na akan dinner hall kuma tasan bai wuci saboda yarinyar nan ba, jan shi tayi da ƙaryar ciwo da kisisina har ta samu yabita Part din ta don taji dadin ruƙe sa kamar yadda faryat ta tsara mata.........👀_
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 15 Complete
by
Novels Elite Admin
June 02, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
_Gaba ɗaya sun shiga yanayi, sai dai fa duk da haka babu fara'a akan fuskokin su kamar basa son kasancewa da juna, bayan motar ta isa gidan, bata bari chief ya kubce mata ba, don ta fahimci hankalinsa na akan dinner hall kuma tasan bai wuci saboda yarinyar nan ba, jan shi tayi da ƙaryar ciwo da kisisina har ta samu yabita Part din ta don taji dadin ruƙe sa kamar yadda faryat ta tsara mata.........👀_
(Back to Dinner Hall)
Bayan tafiyar Nazli da Yan Mintuna, sai ga kiran ta ya shigo layin faryat, A lokacin harta koma wurin su Zulaihat bayan ta gama shirya makircin, A hanzarce tabar wajensu ta samu wurin da bakowa tayi picking ta kara wayar a kunnanta.
Muryar Nazli tamkar tame jin bacci tace"faryat, nakira ne nayi maki godiya, yanzu haka muna a gida tare da chief"
"Naji dadin jin hakan sisters, babu godiya tsakanina dake nayi ne saboda farin cikin ki"
"Ina yarinyar nan take"?
Rass taji gabanta Ya faɗi jin abun da Nazli tace, ita sam ta manta da zancen ƴar mutane da tasa aka kulle a restroom.
"Naji kin yi shiru baki ce komai ba"?
"Sister kulle ta nayi a restroom yanzu zanje na buɗe ta"
"Okay, I don't want any problems tun da buƙata ta biya, kawai ki ƙyale ta tafi, i know her relatives will start looking for her as soon as they notice she is not there."
"Okey, bari naje na buɗe ta" sallama su ka yi da juna, tsaye tayi tana bin Hall din da kallo, can Ta hango matar da suka hada baki da ita, Cikin sauri ta nufe ta.
"Ke! Ina son Magana dake ki biyo ni yanzu" da sauri matar tabi bayanta suka ke6e a wani wuri.
"Yarinyar dana sa kika kulle a restroom, ita nakeso kije ki buɗe ta yanzu"
Hannu matar tasa tana laluban aljihun uniform din jikinta, can ta rabka salati tana fadin"Inna lillahi! Nashiga Uku..." idanu azare faryat tace"what"?
Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"Sister, I think I lost the key, ba tare da sani na ba"
Waro idanu faryat tayi cike da masifa tace"amma Baki da hankali! So kike kija min bala'e, kin manta yadda mu ka yi dake ne? Sai da nace maki da zarar kinga kirana kije ki bude mata kofa, shi ne zaki ce wai key ya bata"? ta fada tana zare mata idanu taci gaba da cewa "to wallahi baki isa ba! Kisan yadda za'ay ki nemo shi da gaggawa ki buɗe ta" ta fada tana faman cije le6en ta, da yatsan hannu ta nuna ta"Don't you dare mention my name if anyone finds out what we've done, Idan ba haka ba hmmm kinsan sauran" rai a6ace ta faɗa tare da juyawa har ta fara tafiya ta dan dakata tunawa da CCTV dake a hall din, Hankali A tashe ta ta kuma juyowa ta kalli matar dake a tsaye ido ya raina fata, jikin ta sai kerma yake daga gani tana acikin matsanancin tashin hankali.
Sassauta murya tayi "Kiyi kokari ki gano key din, ki je ki bude yar mutane, kinga akwai CCTV duk wani abu dake faru suna gani, kuma wallahi muddin baki bude ta ba har suka gano kece kika kulle ta, Na lahira sai yafi ki jin dadi" ta karasa tana sakin shu'umin murmushi ta kuma cewa"ni nasan yadda zan fidda kai na, ke ce a ruwa, dama kwadayin abun duniyane yasa kika amince min muka shirya komai, na riga dana biya ki kudinki, shawara ta rage wa mai shiga rijiya, ni kinga tafiya ta" cike da shakiyanci faryat ta juya ta nufi hanyar fita daga hall din don zaifi mata kwanciyar hankali akan ta tsaya ganin rikicin da za'ay na rashin ganin Yar Mutane
Kafin ta fuce ta kira layin Jazz tace mashi ya same ta a bedroom dinta tana son ganin shi, tayi hakanne saboda ta samu damar ke6ewa dashi kafin gobe Subar Nigeria.
Hankalin matar ba karamin tashi yayi ba, wata irin zuface ta soma wanko mata, har ta fara danasanin kudin da ta kar6a a hannun faryat, gaba daya tabi ta firgice sai faman lalube lalube take yi tana neman key din, Sako da lungu bata gan shi ba, ga shi lokacin ana gab da za'a rufe taron dinner din tasan dole a nemi yarinyar, a karshe da taga ba ta da wata manufa, sai ta yanke shawarar guduwa daga hall din.....
___________________________________✍️
"Ai ga irinta nan, Ni dama nasan za'a rina, yadda yake rawar kai akan yaron nan kamar ɗan cikinsa, hakan na nufin yafi kowa mahimmanci awurinsa shiyasa yaja su suka tafi wata uwa duniyar, Allah kadai yasan ina suka je..." senate lateef ne ya fada Yana huci yayin da suke atsaitsaye curko curko
"Ni abunda nake ma fargaba, kada yaron nan ya cutar dashi, don ni wallah hankalina bai kwanta da shi ba, saboda ina zargin ba cikakken mutun bane" His excellency Deen yayi maganar
Abdul Razak Yace"Laifin Owais ne, Ya cika daukar kasada, akan me zai hada shi da yaro, hada karfin halin cewa ya tafi da shi salon Yajaza mana bala'e"
Kwa6e fuska Senate lateef yayi"ay tin farko ubansane ya daure masa wurin zama da duk hakan bata faru ba, Ina kallonsa dazu Ya hakikance akan cewa owais ba zai kawo abunda zai cutar da ahlinsa ba, Idan ma muna jin fargaban wani abu zai faro owais ne ke da alhakinsa, don haka bai kamata muna tada jijiyoyin wuyanmu akan sa ba, Mu zuba ido mu gani"
"Wannan duk ba abun tada hankali bane, In sha Allah zai dawo cikin koshin lafiya, yakamata muna kyautata masu zato, ku kanku fa dazu ku ka gama tsegumin kamannin Yaron da hateem har kuna fadin baku ga laifinsa ba daya kusa zaucewa akan kaunarsa, shine kuma yanzu kuke korafi don kun ji shi shiru" ya fada yana ɗan jifar su da hararar zolaya.
Dakuwa Senate lafeet yai masa"ungo nan, dani kake wannan maganar, ni banma ga wani kamanninsu ba, na dai fadi ne kawai" dariya suka sanya gaba dayansu.
Sir mubarak yace"kaifa ɗan iskan mai raine, Lokaci ɗaya sai ka burkicewa mutane ka hakikance kan abu daga baya kuma ka dawo ka canza magana, daɗina da ɗan siyasa kenan, Haka halin ku yake, Shiyasa dazu na zuba maku ido kunata jaraba saboda an shigo da yara hall alhalin nan kuwa duk kun ƙyasa da ganinsu, musamman shi yaron da kuke magana akai"
Harara suka watsa masa atare, Senate yace"ba ka girmamani mubarak"
"Da dai ba lokaci ɗaya muka zo duniya ba," acewar Sir Mubarak.
"Bari na fada maku gaskiya, wallahi da ace Hateem ya ta6a haihuwar Namiji tsab zan iya dafe alkur'ani ince dansa ne yaron nan sai dai kaffara ta hauni" his excellency abdul razak ne yai maganar.
Deen yace"yadda kasan irin an tsaga kara, Har hancinsu da idanunsu, kai komai fa, ni fa da za'a bi ta shawarata zance ne muje asibiti ayi masu gwajin DNA" wani kallon harara Senate lateef yayi masa da zolaya yace"lallai siyasa tafara haukata ka, in ba haka ba kawai daga ganin yaro tsintacce daga daji sai ka ƙababa ma Hateem!" watsa hannu yayi"ni abunda ke raina na faɗa"
Shiru suka danyi na wani lokaci kafin senate yayi yar dariya yana fadin Yau wani zaici ubansa a hannun shalelen baba obie" gaba ɗaya suka sanya dariya cikin raha don sun gane me Yake nufi
Sir mubarak Yace"na tauyasa mashi, don wallahi nasan bazata ƙyale shi ba, sai ya yabawa aya zakinsa Hmm Allah dai ya kyauta.
Senat yace"yayi banban kuskure na ruke hannun wata mace agabanta, Ni abun da bangane ba, meyasa yayi hakan ne? Ni fa nafara zargin mutumin nan, wallahi babu gaskiya acikin lamarinsa in ba haka ba akan me zai ja hannun baligar mace bazawara a bainar jama'a da sunan zai fitar da ita ta tsiya daga hall har yana ikirarin kada ta kuskura tabari ya riga ta fita......"
His excellency Deen Yace"idan ma akwai wani 6oyayyan sirri atsakaninsa da ita, a sannu zamu gano koma menene ay mu ba'a shiga family dinmu da fuska biyu a zauna lafiya.... Fira suka cigaba da yi atsakaninsu,
Abu kamar wasa har Bayan Magrib ana gab da za'a rufe taron babu prime minister babu Unaisah, Ga mutane sunataso suyi mashi bankwana saboda ba lallai gobe su haɗu da shi, asubar fari zasu bar nigeria, babu wanda bai jaraba kiran layin hateem acikin su ba, sai dai wayar tayi tayin ringing, ba'a picking, Shima owais sun kira layinsa wayar bata shiga, ransu yayi mugun 6aci, sauƙin su ɗaya zuwan gimbiya mujeedat itace ta sanar da su inda Hateem yake, ba tare da 6ata lokaci ba, suka yanke shawarar zuwa can su same shi, kusan gaba daya mutanan hall din suka nufi gidan prime minister don suyi mashi bankwana tun da shi yaki dawowa dakin taron, yana can tare da sanyin idaniyarsa.,
Idan muka koma bangaren zahra da batool lamarin Ya fara Tsoratar da su ganin Har mutane sun fara watse wa babu alamun Unaisah zata fito daga toilet, kwatsam wayar zahra tafara ringing, da sauri ta ɗaga ganin sunan hajiya saratu.
"Meet me outside the hall right now, Zarah!" cikin sanyin murya ta amsa mata da toh, bayan ta katse kiran, Ta kalli batool jikinta yayi sanyi lakwas sam bata so ta tafi tabar Hall din ba tare da an gano unaisah ba.
"Ki yi hakuri sister batool, tafiya zanyi ba don naso ba, matar da ta gayyace ni dinner din nan itace take kirana, shawarar da zan baki, Ki sanar da sauran yan uwanki da kuma jami'an dake tsaron hall din su taimaka maki ku gano yar uwarku" ta fada tare da ruko hannayen batool a cikin nata kafin taci gaba da cewa"kada ki manta idan kun gano unaisah ki sanar da ita cewa na tafi da kewarta" batool ta amsa mata da toh, kamar kar su rabu da juna su ka yi sallama.
Bayan tafiyar zahra, batool tabi yan uwan su daya bayan daya ta sanar da su zancen bacewar Unaisah, nan fa hankalin su yai mugun tashi, su sajeed suka bazama nemanta, tsantsar tashin hankaline da damuwa akan fuskokinsu, babban abunda suke ma zullumi kada ace wani mugun abunne ya faru da ita, dama sun lura bakowa ke son su ba, tsaf za'a iya cutar masu da yar uwarsu, bacci tuni yayi awon gaba da jamimah, Sai dai haris ya goyata abayan shi, itama Azeeza daukarta Naufal yayi abayanshi sbd lalurarta, Parveen da su Hanna idanu sunyi jawur ga bacci suna ji ga kuma tashin hankalin rashin yar uwarsu, babu wanda Ya lura da halin da su ke a ciki saboda babu mutane sai jefi jefi wasu suna bakin hall wasu kuma sun tafi gidan Hateem kusan su kadai ne suka rage a hall din sai servers din dake tattara kayan abincin da aka yi amfani da su, da kuma interior designers din da suka fara kwashe kayan decoration din dakin taron.
A lokacin da ba su yi tsammani ba, Sai ga Boss tare da biy guy sun shigo hall din cikin takun sauri, sun zo ne domin tafiya da su ganin lokacin yayi, su parveen na ganin su suka fashe da kuka da gudunsu suka nufe su tare da fadawa jikin boss da big guy suna kuka suka fada masu basu ga unaisah ba, ta 6ace sun nemeta sun rasa.
Da tsantsar tashin hankali Taj Ya furta"wai wata unaisah ne ta 6ace? Ko kuna nufin Angel dina"? Adabarbarce Yai maganar Yana dubansu,
Sajeed Yace"ita muke nufi, tun dazu muke nemanta bamu ganta ba, mun duba ko'ina"
Kallon juna boss da big guy su ka yi a lokaci daya,
wani irin bugun fargabane Ya darsu a zuciyar taj, Jin Angel dinsa ta bata babu ita,
Muryarshi na rawa yace"bata fada maku inda taje bane"?
Hada baki sukayi wurin cewa Eh
Dafa kafadarsa Big guy yai ganin Yana neman rikicewa.
"In sha Allah babu abunda zai same ta, zamu nemo ta, sauƙin ma akwai cctv a dakin taron zamu ga inda ta shiga ne"
Mayar da dubansa yayi kansu batool"sajeed, Ka tafi da su bakin hall din, akwai Jami'an mu dake jiran ku zasu tafi da ku gida"
Muryar batool da shesshekar Kuka tace"ni dai bazan iya tafiya, in ba tare da unaisah ba, zan jira har agano ta ...." kafin ta rufe baki Sajeed Yace"nima bazan tafi ba, kamar yadda muka zo tare da yar uwarmu atare da ita zamu koma"
!
"kwara kubarmu anan wlh ko mun koma gida, hankalin mu bazai kwanta ba, ko runtsawa bazamu iya yi ba, in har unaisah dinmu bata dawo ba...." Haris ne ya fada idanunsu sun ciko tab da kwalla, gaba ɗaya sun turje akan ba zasu tafi ba....
Cikin rauni na murya taj Yace"Ya isa haka! Ku daina zubar da hawayen ku, ku samu wuri ku zauna Yanzu zamu nemo ta," da sauri suka samu kujeru duk suka zauna suna jiran tsammani
Ba su fara zuwa dakin cctv din ba, big guy ne ya bada shawarar su fara bincika restrooms din dake a hall din kafin su fara zuwa can, da sauri suka nufi hanyar da suke, daya bayan daya suka dinga dudduba cikin su ba su ga kowa ba, cikin rashin sani suka tsallake kofar wanda take a ciki ba tare da sun ankare ba, tsabar kidima yasa taj sulalewa jikin bango Ya zukunna, idanunsa sun kada jawur dasu, fuskarshi duk ta yamutse idan harfa ba ganin unaisa sukayi ba to kuwa bazai ta6a dawowa dai dai ba
"Ni nafi tunanin ko dai tabi family din chief xuwa can gidan prime minister" big guy ne Ya fada Yana duban fuskar taj, wanda tuni ya hada gumi duk da sanyin A.c din dake a wurin babban tashin hankalin shi kada Ya rasa yarsa tilo da yake da ita, tabbas zuciyarsa zata iya bugawa.
Ganin bai da alamun motsawa ne Yasa Big guy dafa kafadarsa Cikin kwantar da murya yace"dan Allah ka yi hakuri ka daure ka ta shi, mu shiga cctv room din zaifi sauki muga ina ta shiga"
Zuciyarshi a hautsine Ya cire facemask dinsa tare da jefar da shi gefe daya.
Cikin sanyin murya ta wanda Ya karaya yace"Wallahi tun ina agidan su salsabeel nake jin faduwar gaba, shiyasa nakasa samun nutsuwa na kamo hanya nazo hall din nan ashe abun da zan taras kenan" ya fada tare da kallon big guy"ka tafi ka duba, don bana jin zan iya matsawa daga wurin nan, jiri nake gani a idanuwana"
Dan murmushin gefen fuska Big guy yayi mashi dazolaya yace"duk son nan da kake yi mata ahaka zaka damka ma wani kato ita yaci gaba da kula da ita"
Kallon harara Boss Ya jefa mashi"kaga pls kada ka daura min wani hawan jinin, ka tafi kawai, Ina jiranka"
Yar dariya yayi kafin ya juya ya bar wurin
Dafe kansa yai da tafin hannunsa, wani irin ciwon kaine Ya farmasa, Yana cikin wannan Halin, kamar ance ya dago ya kalli Floor din wurin nan take eye balls dinsa suka sauka akan Stone din rigar unaisah, da alama daga jikin rigarta Ya fadi kasa, mika hannu yayi tare da daukar shi Ya kura ido Yana kokarin tariyo a ina ya ta6a ganinsa, sai da ya zurfafa tunaninsa kafin lokaci daya ya zabura ya mike yana bin kofofin toilet din dakallo saboda ya tuna itace ta sanya abaya me adon gold stones.
Kofar da suka tsallake basu duba ta ba, ita Ya nemo, ganin ta adatse ya kara tabbatar mashi da tana a ciki.
Muryarshi har rawa takeyi wurin ambaton sunanta"Unaisah!Unaisah!My Angel" shiru ba'a amsa mashi ba, nan fa hankalin shi ya kara tashi, Ga shi Ya duba babu key jikin kofar, Karfi yasa wurin bangaje ta da kafadunshi sai dai ko gizau kofar batayi ba, Ja baya yayi kafin Ya nufeta da iya karfin shi na karshe yayi mata wani irin bahagon bugu, nan take kofar ta saki, shi kanshi bai yi tsammanin Yana da karfin da zai Iya bude ta, batare da key ba Allah ne ya taimake sa.
Karasa ture kofar Yayi, a fujajen ya fada cikin toilet din yana faman zubda gumi, shigar shi ke da wuya idanunsa suka sauka kan Unaisah dake kwance saman floor, baiwar Allah ita kaɗai tasan radadin azabar da ta fuskanta, taci bakar wahala ta jigata sosai, zufa ta gama wanke jikinta, Takalmanta ware da ware sun yi gefe guda, Ga mayafinta a kasa, hannunta daya dafe a saitin cikin ta, da wani irin rauni da murya ya furta"My Angel" A sukwane da sanyin gwiwa Ya zube gabanta saman gwiwowinsa, duk irin dauriyarsa baisan sa'adda hawaye masu dumi suka soma sintiri kan kuncinsa ba, yatsun hannayensa na kerma ya daura su kan kafadunta tare da janyota ya dawo da ita kan kirjinsa, ya rungume abunsa tare da runtse idanunsa yaci gaba da shesshekar kuka Yana ambaton sunan ta....
"Am.. sorry my Angel laifina ne da ban zauna a dakin taron ba, da duk hakan bai faru ba....."
Baisan meke damunta ba da yai silar shigarta wannan Mawuyacin halin, baisan Ya akai aka kulle ta a restroom ba.
Yana acikin wannan Yanayin big guy ya shigo da saurin shi, Yana ganin taj rungume da unaisah Ya sauke nannauyar ajiyar zuciya.
Daga bakin kofar ya tsaya don baisan me zai taras ba.
Cikin sanyin murya yace"idonta biyu"?
Muryar taj kasa kasa Yace"bansani ba, kamar ta sumane anan, amma daga gani taci bakar wahala"
Big guy yace"mun gano wacece Ta kulle ta a restroom din, Kuma in sha Allah zamu bincikota sai ta dandani kudarta wallahi" Yana fuci Ya faɗa
Babu alamun taj Ya fahimci me yake cewa hankaklinsa na akan Angel dinsa yace da shi"please Ka koma wajen yan uwanta kada su ji mu shiru, yanzu zan fito da ita" amsa mashi yayi da okey, a hanzarce Ya fice.
Har ya yunƙura zai mike Yaji alamun lemar wani abu a hannun shi, da sauri Ya dago da tafin hannunsa Yana kallon jinin daya ta6o, sai lokacin Ya fara jin karninsa a hancinsa, Idanunsa azazzare yake kallon jinin Hankalin shi yayi mugun tashi, zuciyarshi ta dinga harbawa da karfi da karfi tamkar zata fasa kirjinshi,duk a zaton shi wani mugun abun akayi mata, zuciya da sake sake sai ta dinga ayyana mashi kodai raping dinta wani yayi ko kuma Wuka aka caka mata.
Zuciyarshi na tashi, Yai hanzarin Sanya hannu Ya dage rigar jikinta, santala santalan cinyoyinta tsakankaninsu duk jinin ne daya gangaro mata.
Sai da ya bincika ta sosai, wata irin nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, ganin ba abunda Yake zargi bane, A hanzarce ya fara wanke mata inda jinin Ya 6ata, kafin Ya lullu6a mata mayafinta ya daure mata qugunta da shi, asaman kafadarsa ya rungumo unaisah, yayin da ɗayan hannunsa ke a ruke da rigarta, tuni tajima da farkawa tun lokacin daya fara wanke mata jinin da ruwa sai dai bata iya komai, Jikinta ya sake ga wata irin kasala data mamayeta.
Fitowa yayi da ita sabe a kafadarsa, tunkafin Ya karasa inda su Batool suke, da gudun gaske suka nufoshi, lokaci daya su ka ja burki idanunsa azazzare da tashin hankali suke kallon Taj
Muryoyin su na kerma suke tambayar shi meya faru da unaisah? Bata da lafiya ne? Ko bacci take Yi ne"?
Kokarin danne damuwarsa yayi kafin yace masu"Babu abunda ya sameta, lafiyarta kalou, Ku zo mu tafi gida"
Da sauri Ya wuce gaba suka bi bayan shi, masu aikin dake zarya suna kwashe kayan da akayi amfani da su na hall din sai satar kallon taj suke Yi ganin shi dauke da yarinya kamar ba rai.
Fitowa yayi daga Hall din su Batool suna abiye da shi, Jami'an dake tsaron dakin taron suna ganin shi suka fara tambayarshi meye faru da ita?
Baibi takansu Ba, Ya nufi mota, da sauri jami'insu Ya bude mashi Ya shiga back seat tare da Unaisah, suma su batool suka shiga cikin sauran motocin da aka kawo su, kusan atare su ka bar garden din, da matsakaicin gudu suka nufi hanyar komawa gida
Mutsu mutsun bude idanunta ta somayi wadanda suka kada jawur da su, da kyar ta dan ware su kadan ta kalli fuskar taj dake a rungume da ita, hannayensa duka biyu akan bayanta kamar wani yace zai ƙwace mashi ita.
Idanunta na faman lumshewa dakyar dakyar take kallon fuskarshi ba tare da sanin shi ba, acikin zuciyarta ta dinga ambaton sunan shi daddyna daddyna dama kaine kake boye min fuskarka..." siraran hawayene suka wanke fuskarta, ganin yana kokarin juyowa yasa tai saurin lumshe idanunta, saukar hannun shi taji asaman kanta, A hankali Yake dan shafa mata shi, wata irin ni'ima taji ta saukar mata, jikin ta yayi sanyi ba kamar dazu da zazzabi Ya lullu6eta ba, bakomai take tunawa ba face lokacin da ya jefata cikin ruwa...
Taj sam baisan cewa babu face mask a fuskarshi ba, gashi har unaisah taga fuskarshi, don ma babu kwarin jiki ai da ta tuhumesa nakin bayyanar mata da kanshi da baiyi ba, dama tuntuni ranta yana bata cewar daddynta ne duk da bata ta6a ganinsa ba, amma kulawar dayake bata fiye da ta sauran yan uwanta da yadda yake janta a jikin shi da kuma muryarshi su suka kara sanya ta hasashen ko shine.
Alhamdulillah Taro Ya tashi Lafiya, tuni Kowa ya koma masaukinsa bayan da suka hallara a gidan prime minister inda suka karasa shagalin nasu acan, a 6angaren chief owais tun bayan da suka shiga Part din Nazli, ba tare da sanin shi ba, ta kashe mashi wayar shi don kada a kira shi, bayan haka ta hada baki da daya daga cikin hadiman gidan ta sanya mashi maganin bacci a coffee, duk don kada ya tafi yabarta, Sai wuraren karfe sha daya na dare tukunna chief Ya farka, a lokacin nazli har tafara bacci, bai bi ta kanta ba, da sauri ya fito daga part din ta ya sauko down, Kafin Ya kunna wayar shi, Layin prime minister Ya fara dannama kira don Yaji idan Yasa an mayar da danish gidansa.
Bayan yai picking Hateem Ya fada masa suna atare da shi a bedroom dinsa, bai tsaya bata lokaci ba Ya nufi part din prime minister, dakyar ya raba shi da danish, kamar karsu rabu, na rana daya kawai sun shaku da juna har kyautar zobe ya ba shi mai tsadar gaske saboda ya dinga tunawa dashi, kuma yayi mashi alkawarin kullum xai dinga kiransa suna gaisawa, bayan chief Ya tafi da shi har kwalla saida Ya zubda daboda kewar rabuwa da danish.......
Asubar Fari, Motoci suka dinga tururuwa wurin fita daga Estate din,da wata irin jiniya mai kuwar gaske tamkar zasu tashi sama, kaitsaye suka nufi shantalelen titin da zai sada su da Airport, gaba daya family din obinna ne dashi kanshi obinnan suka yi masu prime minister rakiya, Kamar karsu rabu da juna, musamman mahaifinsa da yan uwansa, duk irin juriyarsu saida suka share kwallar rabuwa da shi, Hajiya saratu tasha kuka kamar karamar Yarinya, shi kanshi hateem din saida Ya zubda kwallar rabuwa da yan uwanshi, Ji yake kamar idan ya tafi ba lallai Ya kara dawowa ba, hakika kowa yayi jimamin tafiyar prime minister da Iyalansa, ko bayan da suka baro Airport din suna akan hanyar komawa estate nasu lokacin da suka jiyo karar jirgin su
Haka suka dinga leken jirgin ta windows din motocinsu, har Sai da ya bace ma ganinsu tukunna suka hakura kowa Ya sanyawa zuciyarsa salama, kusan duk aranar Su his excellency deeen suka bar abuja, harta su Justice kowa Ya koma inda Yake da zama wasu Nan cikin Nigeria wasu kasar suka bari, Zaki ne kadai bai tafi ba, yanzu estate din Ya rairaye ma zauna cikinsa ne kadai suka rage.
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 16 Complete
by
Novels Elite Admin
June 06, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
A hankali ta buɗe idanunta wadanda suka kumbura suntum da su sakamakon kukan da tasha jiya, ƙurawa ceilling din dakin idanu tayi na ɗan wani lokaci zuciyarta cike fal da tunanin meya faru da ita a jiya? tamkar tayi loosing memory ɗinta, da sauri ta sanya hannu ta shafa kayan jikinta, lokaci ɗaya ta yunkura ta miƙe zaune tana faman sauke ajiyar zuciya, ko'ina na bedroom dinsu ta soma bi da kallo kafin ta sauke idanunta akan batool da ke kwance gefenta tana bacci, tayi mamakin ganin kayan bacci a jikinta, ƴar gown ce da bata wuce gwiwarta ba, launin purple colour, ta rude sai faman shasshafa jikinta take yi burin ta ta tunano ya akai aka canza mata kayan jikinta! kamar ma hada wanka akayi mata, hannu tasa ta ɗan bugi kanta a kokarinta nata farkar da kwakwalwarta ko taci gaba da yin aiki yadda ya dace.
Buɗe ƙofar ɗakinsu akayi da sauri taja bargo ta lullu6e kanta, tunkafin ma taga wanene.
Atare suka shigo dakin, boss tare da Ummi da ke abiye da shi cikin shiga ta kimono robe, ta yafa gyale a kafadarta, hannun kowannan su ruƙe da ɗan ƙaramin tray na kayan abincin.
"Barka da safiya daughter" wani irin wurgi tayi da bargon gefe ɗaya ya faɗa kan Batool, ta ɗago tana faman zare mashi idanunta.
Sunyi mamakin ganin yadda ta zabura, ummi tace"ko dai har yanzu jikin ne"? Ko kallo unaisah batai mata ba idanunta na akan taj, wanda ke sanye da facemask, A hankali take tariyo abun da ya faru jiya, lokaci daya ta rushe masu da matsanancin kuka wanda yayi silar farkawar batool.
Hankalinsu atashe su ka soma ambaton sunanta, tare da tambayarta meke damunta! Ko ciwonta ya motsa.
Sauko tayi daga kan gadon ta watsa da gudu ta shige toilet taja kofa ta rufe tana cigaba da yin kukan
Kallon juna ummi da taj sukayi a lokaci ɗaya, fuskokin su dauke da matsanancin damuwa, atare suka daura trays din hannun su kan table suka nufi bakin kofar toilet
Batool dake zaune kan gadon sai faman mutsustsuke idanu takeyi tana ambaton sunan unaisah...
Magiya suka dinga yi mata akan ta buɗe ƙofar
"Dan Allah unaisah Ki fada mana meke damunki? Ko cikin ki ke maki ciwo? Idan akwai inda ke maki radadi ki fadamin Yanzun nan zanje na karbo maki magani, wallahi mun damu dake jiya ko runtsawa bamuyi ba, har sai da muka ga kinyi bacci" cikin sigar lallashi ummi takeyi mata magana.
"My daughter ki yi shiru ki saurare ni, nasan meke damunki, ni nasan dama dole kiji haushi, inaso ki kwantar da hankalin ki, saboda mun riga da mun gano wacece tayi maki aika aikarnan kuma in sha Allah zamu hukuntata, idan ma kinaso zamu kawo maki ita, ki rama abunda tayi maki"
Maimakon unaisah ta sassauta kukanta, jin lallashinta da suke yi mata sai ma takara sautin kukan nata tamkar zata fasa kunnuwansu, da gudun gaske sajeed Ya fado dakin Yana haki daga shi sai gajeran wando bai jima da shigowa ba naufal Ya shigo shima yana tambayar meye faru da angel dinsu?
Shigowa suka dinga yi, daga me hamma sai mai miƙa daga gani basu jima da farkawa daga bacci ba, dama da tunaninta suka kwanta bacci jiya shiyasa suka farka da ita aransu, atare Jemimah da Azeeza suka shigo kowannan su kayan bacci ne a jikin shi, ba su jima da shigowa ba, Parveen ta shigo hannun ta ruƙe da brush, sumar kan nan a haukace gyaran gashin da akayi masu duk ya tarwatse kowa fa hankalinsa Ya tashi matuƙa, Jemimah sai kuka takeyi masu hada tsallanta tana fadin dama tasani mutanan nan sai da suka cutar mata da Angel dinta, wallahi bazata ƙyale su ba dole ta rama mata...
Gaba ɗayan su sunyi curko curko abakin kofar toilet din
"Please ku kwantar da hankulan ku, ku bari muyi kokarin shawo kanta sai muji meke damunta" ummi ta fada tana duban su kafin ta mayar da dubanta ga boss man.
"nifa ina tunanin watakil ko tayi zaton kai ne kayi mata wanka a daren jiya shiyasa take kuka"
Dafe kanshi yai da hannu ɗaya saboda shi ma ya yarda da maganar ummi, cikin muryar lallashi Yace"Unaisah, bani ne nayi maki wanka ba, Aunty umminku ce, bayan na dawo dake jiya na kawo ki gida da taimakonta kika tsarkake jikinki har kikayi wanka.. " kafin Ya kare maganar, cikin muryar kuka tace"ni ba wannan bane damuwana ba, daddy meyasa za ka yi min haka?
Hankali atashe taj ya ɗan zaro idanu Ya dubi ummi babu alamun ya fahimci abunda Unaisah take nufi sai ma cewa yayi"kinyi mafarki ne da daddynki"? A tsiwace tace"ba mafarki nayi dashi ba, a zahiri na ganshi jiya, saboda me zaka dinga 6oye min kanka daddy, ko ka daina sona ne" ta faɗa tana haki
Dariya ce ta kubcewa ummi ganin yadda taj ya daura hannayensu biyu saman kanshi alamar Ya shiga Uku gaba daya yabi ya ruɗe Sai lokacin Ya tuna da abun da Ya faru Jiya, da kanshi Ya cire facemask dinsa Ya jefar da shi saboda baya ahayyacinsa ashe idonta biyu taga fuskarshi
Muryarshi tamkar zai fashe da kuka Yace"am really sorry my Angel, nayi laifi ay min afwa, nasan ban kyauta maki ba, amma dan Allah ki fahimce ni, ki nutsu ki saurari me zan fada maki.." kafin ya kare maganar ta katse shi da cewa"ni bazan saurari komai ba daddy, kawai ka daina sona ne ba ka damu dani ba, kuma ba ka yi kewata ba shiyasa kake 6oye min fuskarka..." ta fada tana jan majina kafin taci gaba da cewa"Daddy, what did I do to deserve this punishment from you? Daddy kasan kuwa irin kalubalan rayuwar dana fuskan ta? Daddy duk halin da na shiga ban ta6a mantawa dakai ba, bana kwana batare da na sanya ka acikin addu'ata ba, kullum zullumina ya rayuwar daddyna ta ƙare? Meya faru da shi bayan Ya jefa ni cikin ruwa, Ya rayu ko ya mutu.... "
Ba ta kare maganar ba saboda kukan daya ciyota, ta kuma fashewa da wani kuka tamkar ana zare ranta, abunne Ya tsaya mata aranta ya 6ata mata rai duk irin kewansa da tayi amma shine ya boye mata kansa.
Gaba ɗaya hankulansu Sajeed Ya koma kan fuskar tajuddeen, kalaman Angel ne suka fahimtar da su wanene shi
Muryar na rawa Azeeza tace"dama kai ne daddyn Angel wanda kullum take bamu labarin shi"?
Da sauri Parveen tace"idan bazan manta ba, duk in muka zauna fira unaisah saita bamu labarinka, itace tafara sanya mana kwaɗayin ganin ka, da zumudin son muje gidan su don muyi rayuwar ƴan ci, har fada mana takeyi daddyn ta zai kar6emu kamar ya'yansa..... Kasa karasa maganar tayi nan take ta fashe da kuka.
Cikin karyayyar murya Batool tace"ashe kai ne daddyn Angel, Ni burin da nake dashi idan Allah yasa na haɗuwa dakai shine inyi maka godiya saboda Angel ta faɗa min kaine ka ilmantar da ita, ka tsaya mata tsayin daka har ta samu ilmin addinin da take da shi, uwa uba kaine silar da Angel tazo duniya...." tana magana hawaye na wanke fuskarta.
"Wallahi ba mu ta6a sanin wanene mahaliccin mu ba, sai a sanadin zuwan Angel GIDAN KURKUKUN ƘADDARA, , In da mu ka yi rayuwar kulle, cikin duhun jahil ci, harta toilet atare muke shiga da ƴan uwanmu maza Angel itace ta tsawatar mana ta fada mana cewa babu kyau mu daina haramunne wani yaga tsiraicin wani......" kuka ne ya kubce ma batool, ummi dake sauraransu a matuƙar ruɗe take ɗan zare idanunta akan fuskokinsu, gaba ɗaya sun jefa ta a cikin ruɗani lamarin yayi muƙar girgiza ta, tayi matukar razana.
Bata gama shan mamaki ba cikin sanyin murya haris Yace"Allah ne kadai zai iya biyanka daddy, zuwan Angel cikin rayuwarmu tamkar baiyanar haske ne a cikin duhu, wallahi baki bazai iya furta irin wahalar da unaisah tayi akanmu ba, duk da kasancewar ta ƙarama a cikin mu amma tana da kaifin basira kuma tana da hankali, Angel ta zama jigo na rayuwarmu, ta share mana hawayenmu a lokacin da muke kukan radadin kuncin rayuwar da muke aciki, Angel uwace agare mu, saboda ta kwatar mana ƴancin mu da aka tauye mana......" zu6ewa haris yayi kan gwiwowinsa hawaye naci gaba da sintiri kan fuskarsa, Gaba ɗaya sun gama kashe ma tajuddeen jikinsa, yayi sanyi laƙwas zuciyarsa ta karaya, wasu irin zafafan hawayene masu ɗumi suka soma wanko fuskarshi yayin da yake kallonsu ɗaya bayan daya, yana mai jin tsantsar tausayin su da kaunarsu azuciyarshi, Angel ta gama masa komai a duniyar nan baisan ma ina zai tsoma kanshi ba tsabar yadda Yake jin mahaukacin sonta na kara nunkuwa acikin zuciyarshi, ba zai iya misalta irin alfarin da ya ke da ita, burin kowani ubane ya sami ƴa kamar Angel wadda zata kare masa martabarsa da kimarsa a idon duniya, wadda zata daukaka darajarsa ta kuma yi silar shigar shi aljanna, hannu ɗaya ya daura akanshi Yana cigaba da kallon su jikin shi har kerna kerma ya ke yi.
Duk wannan abun dake faru a kunnan chief owais da Big guy wadanda basu jima da zuwa bakin kofar dakin ba, sunzo zo ne don su duba jikin Unaisah sai kuma suka ji abunda ba suyi tsammani ba wannan dalilin ne yasa suka dakata suna sauraron su
Cikin shessheƙar kuka Naufal Yace"daddy duk yadda zamuyi maka bayani ba lallai ka fahimce mu, amma wallahi muna kaunarka muna son ka daddyn Angel" wasu hawayen nan suka kuma wanke fuskar taj, idanunshi sunyi jawur da su gaba ɗaya ya rasa bakin magana sai dai kallonsu da yake tayi gwanin ban tausayi
"Unaisah itace take ƙarfafa mana gwiwa, itace komai namu, itace muke gani muji dadi, unaisah ko mun 6ata mata rai bata yin fushi damu ba, sai ma taja mu ajikinta saboda tasan bayin kan mu bane, rayuwa mu ke a cikin duhun jahilci, ....."
gaba ɗaya suka dubi batool da ta dauko maganar hawaye na sintiri kan kuncinta, dakatawa tayi da yin maganar na ɗan wani lokaci kafin taja numfashi taci gaba cewa"ɗaya daga cikin abun da unaisah tayi wanda har a bada bazai ta6a gogewa acikin zuciyata ba, shine musuluntar da yar uwar mu unaiza da tayi, unaisah bata bari unaizah ta mutu a matsayin arniya ba, sai da ta taimaka mata ta kar6i shahada duk don saboda ta tsira a lahira..." muryarta na rawa tayi maganar, kusan atare suka rushe da kuka tunawa da yar uwarsu unaizah, maganar batool ta fama masu raunin dake acikin zuciyoyin su.
zu6ewa su ka yi gaba dayansu saman gwiwowinsu agaban tajuddeen, suna kuka yana kuka babu mai lallashin wani a cikin su, ummi da batasan kan zancen nasu ba tuni itama ta fara matsar ƙwalla cikin rauni na murya tace dan Allah ku fahimtar dani ku yi min bayani tun kafin zuciyata ta buga, saboda hankalina ya tashi na kwaɗaitu da son jin tarihin rayuwarku......."
Lumshe ido chief owais yayi, zuciyarshi ta karaya, wankan suit ne ajikin shi, bai jima da dawowa daga Airport ba wurin rakiyar prime minister.
A hankali Ya dubi Big guy dake a tsaye gefen sa, hawaye ya gani sun cika mashi idanunshi,
Shi kanshi dauriya ce kawai, amma kalaman su sun ta6a ta6a zuciyarsa.
Cikin sanyin murya ya furta"ka kira salsabeel a waya ka faɗa masa inji ni ya shirya sauran yaran, su zo nan gida su sameni, inaso suga yan uwansu"
cikin girmamawa big guy yace"okey, sir." ya faɗa tare da zaro wayarshi ya danna ma salsabeel kira wayar na fara ringing, yayi picking,
"barka da safiya yalla6ai"
"Yawwa barka, Ina fata dai ban katse maka baccinka ba" muryarshi da yar dariya yace"ay bana yin baccin safe saboda khadeeja kasan halinta kamar mai fama da cutar yunwa, tun da safe take tashina, don in shiga kitchen in dafa mata indomie"
"Allah sarki, ka cigaba da haƙuri da ita, Yanzu dai gani tare da chief, yace yana son ganin ka da sauran yaran yanzun nan ku same mu agidansa"
Muryar salsaleen da dan rudani yace"yallabai badai wani abune ya faru ba? Naji kace nazo da yara da sassafen nan"
"Ba wani abu kazo kawai, " amsa mashi yayi da toh, kafin su ka yi sallama Ya maida wayar cikin aljihu...
Angel dake atsugunne bakin kofar toilet din, jikinta ya gama yin sanyi tamkar wadda aka zarewa laka, duk abunda su batool ke fadi akan kunnanta tuni tayi shiru ta dakata da yin kukan, ita kanta bata ta6a tsammanin sun ruƙe kyautatawar da take yi masu ba acikin zuciyoyin su, shiyasa ake son bawa ya kasance yana aikata abun alkhairi arayuwarsa saboda duniya tayi alfahari dashi, al'umma su yi koyi dashi ko bayan ba ranshi, unaisah dai ta bada gudummuwa ta bangarori da dama harta ta bangaren addinin musulunci ta musuluntar kuma ta fadakar Allah ne kaɗai zai iya biyan ta.
Cikin shessher kuka suka soma yi mata magana, muryoyinsu duk sun disashe
"Yar uwarmu rabin ranmu, amadadin abban mu, muna baki hakuri dan Allah ki taimaki daddynmu, Kiyi hakuri ki fito yana son ganinki, daddy ya gane kuskurenshi kuma ashirye yake daya baki hakurin laifin da yayi maki.... " magiya suka dinya yi mata duk don su samu ta buɗe masu kofa
"Unaisah kin manta irin kyautatawar da daddynmu yayi maki tun kina karamarki, lokacin da mommynki ta gudu tabar ki a cikin kwamin wanka, ya daukeki yaci gaba da baki kulawa duk da kasancewar bakyajin magana ahaka yaci gaba da rainonki saboda irin son da ya ke yi maki shi bai tafi yabar ki ba, unaisah da bakin ki ki bamu labarin nan ko kin manta ne......" gaba ɗaya kowan nan su ya ƙosa ta fito saboda ta rungumi daddynta.
Ba zato ba tsammani, suka ga taj Ya dafe saitin zuciyarshi yana ambaton inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un Muryarshi da wani irin sauti na tashin hankali, gaba ɗaya suka zabura da sauri suka rufe shi suna ambaton daddy meke damunka? Baka da lafiya ne...."
Jin wannan maganar yasa unaisah yin saurin miƙewa, yatsun hannunta na kerma ta soma kiciniyar buɗe kofar, a fujajen ta fado dakin, ganinta yasa suka bata hanya, ta faɗa jikin tajuddeen ta ƙanƙame shi tana kuka take fadin daddy dan Allah kayi hakuri nasan nice na bata maka rai, ka tashi ka ji daddyna abun alfahari na, la66anta na kerma takeyin maganar, hawayen fuskarta tuni sun wanke fuskarshi, sumbatar goshin shi tayi, tare da manna masa wani kiss din kan kuncinsa ...." sai da taj ya bari ta gama firgita, tukunna ya buɗe idanunsa fuskarshi dauke da murmushi, fashe mashi tayi da kuka da sauri ya janyota jikinsa suka rungume juna tamkar zasu koma mutun ɗaya tsabar yadda suka matse junan su lallashinta yaci gaba dayi yana fadin"am sorry my angel, ki yafe ni, nasan bankyauta maki ba, wlh kina araina, kamar yadda kike fadin kin yi kewata nima haka nayi kewarki, angel rashinki ba karamin gi6i yayi min ba rayuwata sai da nakusa zaucewa saboda haukan rashin ki a kusa da ni, Angel bana iya bacci batare da nayi mafarkin ki ba, duk dare na Allah sai na tashi nayi salla saboda inyi maki addu'a Allah ya kare min ke duk da bani da tabbacin kina araye ko kin mutu......" dakatawa yai da yin maganar, idanunsa acikin na Angel dinsa, sai da ya fara tattara nutsuwarsa kafin cikin sanyin murya ya fara basu labarin abun da Ya faru dashi bayan ya jefa Angel cikin ruwa.
_______________________________✍️
Abun da ya faru lokacin da wadannan migayun dattawan su ka ƙyasta lighter bayan sun zazzaga mashi fetur a jikin shi, idan ba zaku manta ba, ba su kaiga jefa mashi lighter din ba, har sai da suka kusa shiga motocinsu tukunna suka cinna wutar, sannan ba su tsaya sunga wutar ta kone sa ba, suka shiga cikin motocinsu tare da fusgarsu suka bar dajin a guje, bayan tafiyarsu hucin wutar Ya daki fatar jikinsa wani irin radadin azaba ne ya ziyarci sassan jikinsa, nan take ya farfaɗo daga suman da yayi ko da yaga wutar dake ci, cikin matsanancin tashin hankali ya yi wani irin kwakkwaran juyi da dukkan karfinsa gaba ɗaya ya rubza cikin Kogon ruwan daya jefa Angel, tsulundun Ya rubza cikinsa ya nutse can kasan ruwan kuma nan take ya sake sumewa.
Suna acikin ruwa ɗaya da Unaisah sai dai akwai tazara tsakaninshi da unaisah, wanda silar hakan yasa har danejo ta ceto rayuwar unaisah ba tare da tasan cewa akwai mutun acikin ruwan ba saboda ruwa daya ja shi... A kalla taj ya kwashe tsawon kwana uku acikin ruwan ba tare da ya samu taimako ba.
Ana haka cikin ikon Allah, Wasu fulanin daji dake kiwo daga can wata ruga dake a cikin dajin, su biyu matasa suka koro shanayensu zuwa wurin da ruwan nan yake, Anan suka yaɗa zango, to ɗaya daga cikin su mai suna habu mayen ruwa ne duk in suka zo bakin ruwan sai ya shiga yin wanka, babu irin gargadin da ɗan uwansa garbati baiyi mashi ba akan yadaina shiga ruwa saboda hatsarin dake gare shi amma yai kunnan uwar shegu da shi saboda taurin kansa da kafiyarshi, Abun ne yabi jikin shi tun suna kanana Yake shiga ruwa yin wanka har izuwa girmansa, shi kuma garbati mugun tsoron ruwane da shi, ko kusa da ruwa baison zuwa jikin shi kerma yakeyi saboda Labaran da yake ji daga wurin mutane dangane da mugayen halittun ruwa dake cinye mutun shiyasa yake jin shakkar kusan ta kanshi da ruwa, aranar da suka je bakin ruwan, habu na kokarin cire kayan shi don yashiga yayi wanka, garbati yayi saurin damƙar rigarsa suka soma kokawa a tsakaninsu, cikin harshen fulatanci suke magana garbati yace wlh bazaka shiga ruwan nan ba, ka manta da gargadin da baffa yayi mana akan shiga ruwa? Ko so kake ka mutu ne kafin lokacin ka yayi?
Habu da ya gama hasala Ranshi a6ace yace"Aradun Allah garbati baka isa ka hanani shiga yin wanka ba, ko da kuwa sama da kasa zasu hade saina shiga, idan ma wani abu ya same ni, ni naja ma kaina kai dai naka kallone kawai" duk yadda garbati yaso ya hanashi amma yaki ji, a karshe sai yasa hannu ya hankaɗe garbati gefe daya ya kife kan ciyayi da sauri habu ya bi ta hanyar da ya ke shiga ruwan ta cikin sauki yabi duwatsun dake kewayen da ruwan ya tsunbula cikinsa Ya cigaba da yin wanka yana raira waka cikin harshen fulatanci.
Mikewa garbati yayi zuciyarshi a 6ace yaci gaba da kula da shanayensu yana jiyo muryar habu dake acikin ruwa yana raira mashi wakar habaici har yana kiran shi da ragon namiji, zaifi dacewa ya koma ɗaura zani maimakon wando, har ma ya dinga taya su Inno surfen Gero, ranshi ya 6ace jin wannan maganar, amma saboda hakurin dake gare shi sai ya share shi yaci gaba da kula da shanayensu
Habu yana cikin yin nutso ya shige can kasan ruwan yana shawagi ba zato ba tsammani idanunsa suka sauka akan mutumin dake kwance kasan ruwa rai hannun Allah, kasancewar kasan ruwane idanunsa sunyi mashi biji biji sai ya dinga ganin kamar wata halittar ruwace me girman gaske, bakomaine ya fado mashi aranshi ba face gargadin da garbati keyi mashi akan ya daina shiga ruwa akwai mugayen halittun dake cinye naman mutun, nan fa hankalin shi yayi mugun tashi, zuciyarshi ta soma yi mashi dakan uku uku, Jiki na bari ya soma yin sama ya fiddo kanshi yana ihu na fitar hayyacin tamkar zai fasa makoshin sa, ko da garbati yajiyo ihun Habu abunka ga firgitacce bai tsaya tambayarshi menene ba, ya watsa aguje kamar karan farauta Ya nufi rigarsu.... Ya bar habu acikin ruwa Yana ta Zagba ihu tsabar rudu Ya hana ya fito daga ruwan gaba daya ya gama rikicewa.
Da gudun gaske Fulanin Rigarsu suka nufo wurin ruwan wasu ko takalma babu a kafafuwansu, wasu kuwa hannayensu ruke da makamai saboda su ceto dan uwansu, bayan sun karaso gaban ruwa wasu dattijai daga cikin kakanninsu irin wadanda suka daɗe suna gwagwarmaya ne, basu da tsoro ko miskala zarratin, sun saba da duk wani abu daya shafi daji suna da kwarewa akansa
Basu tsaya bata lokaci ba suka afka cikin ruwan don su ceto rayuwar dan su, ko da suka shiga, Habu Ya kankame kakansu Yana sambatu iri iri, ya dinga nuna masu saitin inda yaga halittar da hannun shi, da sauri ɗaya daga cikin kakannin nasa mai karfin Hali ya kutsa kai cikin don ya kashe halittar, aikuwa yana shiga yayi tozali da mutumin dake a kwance kasan ruwan, lamarin ya daure mashi kai, ganin ɗan mutun acikin ruwa, aranshi ya dinga tunanin mutunne ko aljan? Watakil aljanin ruwa ne" Wasi wasi yaci gaba dayi, har zai tafi sai kuma zuciyarsa ta dinga azalzalarshi akan ya dauko mutumin watakil tsautsayine ya afka da shi... Baiyi kasa a gwiwa ba yaje ya kinkimo tajuddeen abunka ga tsohon kashi na majiya karfi wadanda suke da shirinsu baiji nauyin taj ba akan kafadarshi ya sargafo shi, Ya fito masu da kawunansu daga cikin ruwa, ya ɗaga murya yana fadin"Ta mutunce ba aljani ba," Gaba ɗaya suka zaro idanu waje suna lekensu kowa da abunda yake sakawa aranshi, Bayan sun fito dashi daga ruwanne suka kewaye shi suna kallon shi, anan suka ga alamar bai mutu ba, da ranshi, wani abu daya basu tausayi game da shi, mummunan raunin da suka gani akan tafin kafarsa ta dama, fatar wurin ya rarake yayi rami, ba tare da sun 6ata lokaci ba suka tafi da tajudden can rigarsu, a inda suka cigaba da bashi kyakkyawar kulawa suka ɗaure masa raunin kafarsa bayan sunyi mashi ƴan dabarun su na mutanan daji, tsawon kwanaki baya acikin hayyacinshi, ko bacci yake yi ya dinga farkawa kenan yanayi masu sambatu akan yarsa da ya baro cikin ruwa, sun rasa gane me yake nufi saboda basa jin harshen hausa, wani lokacin kamar zautacce yai ta kuka yana ambaton sunan Angel, a kalla taj ya shafe tsawon watanni ba tare da ya iya taka kafarsa ba, wannan dalilin ne yasa bai samu damar zuwa neman Angel ba, bayan haka ya yi loosing memory dinshi, sunanta ne kadai ya tsaya mashi aran shiyasa yake yawan ambatonshi....
Lokacin da ya fara samun sauki yaci gaba da rayuwa da su yana ta kokarin ya tuna miya faru dashi amma ya kasa saboda lalurar data sameshi a haka ya rayu a rigar su na tsawon shekara biyu cikin ikon Allah a daren wata rana yana tsaka da baccinsa yayi wani mummunan mafarki dangane da Angel dinsa wanda ya yi silar dawowar memory din shi, tun a cikin daren ya fara kokarin barin rigar don yaje nemanta gaba daya ya tada masu hankali duk wani mai bacci sai da ya farka yai ta ambaton sunan ƴarsa da ya jefa cikin ruwa yana ta kokarin kwatanta masu sai dai sun kasa gane me yake nufi, lallashin shi suka cigaba dayi suna kwantar masa da hankali, a dole ya hakura bai fita a daren ranar ba,
A Washe garin ranar da sassafe kakansu habu ya bashi kyautar sandar da zai yi amfani da ita wurin yin tafiya, saboda har time ɗin kafarsa bata dawo dai dai ba, lokacin da su habu zasu tafi kiwon shanu sai yabi bayan su don ya nemo Angel dinsa, sai dai kash ita kuma a lokaci har wannan tsautsayin ya fada da ita, tana acan gidan kurkukun kaddara, kuma bata jima da barin rigarsu Danejo ba, shi kuma yafara zuwa nemanta, tunda yaga kogon ruwan ya ƙafe babu ruwa acikinsa saboda damuna ta wuce, mutun na iya ganin komai dake a kasan ramin, yayi kuka na fitar hayyaci kamar ransa zai fita, har yunkurin fadawa yayi don ya kashe kanshi, da sauri su habu suka rirrike shi tare da jan shi suna lallashin shi, saidai sam baya fahimtar me suke cewa.
Sai da takai ga abakin ramin ruwan yake kwana tun safe har dare ya ritsa da shi baya motsawa anan fulanin suke zuwa kawo mashi abincin da zai ci, tunda ya ƙi komawa rigarsu, yafi son zama bakin ruwa, hakika sunji tausayinshi duk da basu san meke damun shi ba, saboda son da kakansu habu keyi mashi, bukka ya haɗa mashi a wurin saboda yaji dadin cigaba da kwana abakin ruwan, hada bargon lullu6a suka mallaka mashi, da duk wani abu da zai buƙata......
Bayan wani lokaci, awata rana yana zaune abakin ruwan yayi zurfi a cikin tunaninsa, sai ga bafullatanar dajin da ta taimaki Angel, ta koro shanayenta zuwa kiwo, ita kanta bazata tuna rana ta karshe da ta zo bakin ruwan ba tun bayan da angel ta gudu tabar rigarsu bayan ta gama haukan jimamin rashinta gaba ɗaya danginta suka hanata fitowa kiwo, sai dai yan uwanta suka cigaba da yi, sai ranar ta samu suka barta, bata nufi ko'ina ba sai bakin ruwan da yabar tarihi a zuciyarta, tana cikin tafiya ta hango sabuwar bukkar da akayi abakin ruwan ga kuma mutun zaune ya zura kafafunsa cikin ramin, Kamar a mafarki haka take kallon shi, gaba ɗaya hankalinshi baya akanta....
Sautin kukan shanayenta ne suka dawo dashi daga zurfin tunanin daya shiga, firgigit yai tare dakai idanunsa gareta, duk a tunaninsa su habu ne suka zo yin kiwo, ko da idanunsa suka yi masa tozali da fuskar kyakkyawar matashiyar budurwa kamar aljana, da sauri taj ya mike yana kallon ta da tsantsar mamaki akan fuskarshi, babu wanda yayi ma wani magana acikinsu sai kallon kallo da suke jefawa junansu, ita dai danejo kallon sani take yima fuskarshi duk da tayi imanin wannan ne karo na farko data fara ganinshi, yayin da shi kuma tajuddeen baisan dalilin kallon da yakeyi mata ba, ya dai yi mamakin tsantsar kyawun dake gareta.
Jin shirun yayi yawane yasa ta soma yi masa magana da yaren fulatanci"wanane kai? Daga ganin bakuwar fuskarka ba fulanin dajin mu bane" fuskar ta da murmushi tayi maganar tana nuna shi da sandar hannunta.....
Bin ta da ido yayi don bai fahimci me tace masa ba.
Tamkar bazai tanka mata ba yace"bana jin yaren da kikai min magana shi," waro mashi dara daran idanuwanta tayi, wani irin annurin farin ciki ya gani akan fuskarta, cike da mamaki yake kallon ta ganin tana ta murmushi, bakomai ne yasa ta farin ciki ba face jin yayi mata magana da yaren Angel dinta, yarinyar da ta kwallafa rai akan son ta.
Bai yi tsammanin zatai mashi magana da hausa ba sai ji yai tace"Ya sunanka? Wanene kai? Me kake yi a rigar mu" dakyar hausar ke fita irin ta ƴan koyo.
Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya bata amsa da cewa sunana tajudeen, bako ne a rigarku, ban jima da tsintar kaina a cikin ku ba," wani irin bugu taji kirjinta yayi mata, jin sunan daya ambata kamar ta ta6a jin sunan abakin angel, sai dai takasa tunawa
Cigaba tayi da janshi da fira saboda Ya kwanta mata aranta, wunin ranar danejo tana atare da taj, ba laifi ta ɗebe mashi kewar dake damun shi, yawo suka dinga yi acikin dajin suna tafiya suna fira kaɗan kaɗan saboda rashin sabo, da kuma ƙarancin hausar dake gareta, bakomai ne take fahimta ba.
Tun daga ranar daya haɗu da danejo, wata irin shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu, kullum ne sai tazo kawo mashi abinci sau uku arana, wani lokacin gasassar masara zata kawo masu su zauna suna ci suna fira, har dai wata rana ta gayyace shi zuwa rigarsu, duk da ya nuna mata baisan zuwa, roƙansa ta dingayi hada sanya mashi kuka, a dole ya amince mata suka je rigarsu, tashin farko danginta suna ganin taj suka tada 6alli akan basa son ganin shi tare da ita, hankalin danejo ba karamin tashi yayi ba, jin zasu rabata da mutumin da take sa ran zai maye mata gurbin Angel, akan idonshi suka rufe ta da fada kamar zasu bugeta cikin harshen fulatanci inna wuro ke ta faman zazzaga masifa tana fadin ta manta gargadin da sukayi mata akan kada ta kuskura ta ƙara kawo masu wani a cikin rigarsu! So take ta kashe kanta saboda taimakon bare ne? Ko ta manta da irin wahalar da tasha bayan tafiyar yarinyar da ta ƙwalla rai akanta ne?
Babban yayan su bawuro yace"tun wuri ta rabu dashi, idan ba so take su kashe shi ba" fashewa tayi da kuka hada bubbuga kafa tana fadin ita wallahi bazata rabu da shi ba, saboda zuciyarta ta kamu da kaunarshi," jin wannan maganar daga bakinta ba karamin fusata su yayi ba, Inna wuro tace"sai dai ta za6a ko su ko shi," abunka ga mai karancin hankali ga kuruciya dake damunta, da buɗar bakinta sai cewa tayi zata bishi, aikuwa a fusace bawuro ya kifa mata mari, da sauri taj ya dakatar da su ganin abun nasu na neman wuce gona da iri.
Cikin kwantar da murya yace masu su yi hakuri, su daina bugunta indai saboda shi ne yanzu zai tafi yabar masu rigarsu" sam basu fahimci me yake cewa ba, sai ma wani irin kallon tsana da suke jifar shi da shi, har ya juya zai tafi danejo ta ruƙo hannunsa, a fusace gidado ya ruƙo hannunta, suka riketa don kada tabi shi.
Sautin kukanta ba karamin karya mashi zuciya yayi ba, shi kanshi baya son rabuwa da ita, ba don yaso ba sai don ba yadda zaiyi ne...
Har yayi nisa da tafiya, ya ɗan dakata zuciyarshi na raya mashi ya juya ya kalle ta, watakil bazai sake haɗuwa da ita ba, har zuwa lokacin da zai bar dajin,
Juyawar da zaiyi keda wuya, kwatsam idanunsa suka sauka akan rigar Angel dake shanye kan ɗaya daga cikin bukkokin su, daga gani wanke ta akayi aka shanya don ta bushe, da farko bai tantance abunda idanunsa ke nuna masa ba, sai da ya ɗan kara ƙura idanunsa tukunna Ya shaida itace rigar baccin da ke a jikin Angel aranar da ya gudo da ita, sune kayan jikin ta, was wasi yafara yi a cikin zuciyarsa tayaya akai rigar unaisah tazo dajin a hannun fulani? Ko dai suma suna da irin rigunan gayu ne"? Farat ɗaya zuciyarshi ta bashi amsa da cewa me zai kawo irin wannan suturar a hannun mutanan da ke rayuwa a daji? Sai dai idan tsintar ta su kayi...' muryarshi na rawa ya furta"idan har dagaske ne abunda nake hasashe tabbas Wani ya ceto rayuwar Angel ɗina bayan na jefata a cikin ruwa tun da gashi har rigarta ta bayyana...
Ba zato ba tsammani, suka ga mutumin da suka kora ya watso da gudu ya dawo wurin rigarsu, har sun har zuƙa zasu fara dukanshi da sandunan su sai kuma suka fasa ganin Ya damƙo rigar da danejo ta shanya kan bukka, ruƙe rigar yayi a hannunshi zuciyarshi na bugawa da matsanancin karfi ya soma ambaton sunan Angel Angel, Lokaci ɗaya su bawuro da su hasiya suka kalli juna da mamaki jin yana ambaton sunan yarinyar da danejo ta tsinto a cikin ruwa, tambayar shi suka soma yi wanene shi? Ya akai yasan yarinyar?
Hawaye na zuba daga idanunsa ya dago rigar yana nuna masu yace" wannan rigar ta ƴata ce Angel, da hannuna na jefa ta cikin ruwa, dan Allah ku fada min a ina kuka samu rigar? Ko dai kune kuka ceto rayuwarta....." kukane yaci karfinsa, gaba daya ya rikice masu, su kansu so suke son san me yake cewa don suji ko shine mutumin nan da yarinyar take nema don bazasu ta6a mantawa ba da irin kukan data dinga yi masu tana kaisu bakin ruwa donsu nemo mata daddynta tun basu fahimtar me take cewa har suka gane cewa wani nata ne take nema..
Danejo ce kaɗai ta fahimci me Yake cewa, nan take ta fashe da kuka Cikin harshen fulatanci ta sanar ma sauran ƴan uwanta abun da taj Ya ke faɗi nan suka gane cewa shine mahaifin Angel, yarinyar data tsaya masu aransu, har yau har gobe basu cireta aransu ba, hakika sunyi farin ciki mara misaltuwa da ganinsa.
Tsabar farin ciki yasa danejo ta watsa da gudu ta fada kan kirjinsa ta rungume shi tana kuka, ta soma tambayarshi ina Angel? Ko ya ganta"? Hankalin shi ba karamin tashi yayi ba, a ruɗe ya tambaye ta me take nufi? Ba su suka taimake ta ba" cikin sanyin murya danejo ta labarta mashi komai daya faru tun daga lokacin da ta tsintota a cikin ruwa har zuwa time da ta gudu daga rigar su.
Wani irin jiri yaji yana shirin kwasarshi saboda kuncin dayaji, bakomai ne ya jawo mashi jinkirin da yayi ba nazuwa daukarta face loosing memory din da yayi.
Zubewa yai kan gwiwowinsa zuciyarsa a hautsine tamkar zata buga, gaba ɗaya suka kewaye shi, suna kallon shi gwanin ban tausayi, ganin yadda ya ke matsar kwalla.
Saboda son da suke ma Angel yasa suka yi mashi kyakkyawar tarba, a kalla ya shafe wata a rigar su, kafin Yaji bazai iya cigaba da zama a dajin ba, kwara ya koma gida watakil idan yaje can ya sameta ta koma wurinsu Aneelerh.
Ranar da taj ya shirya tafiya, zai bar rigar, ya yi masu bankwana kamar karsu rabu, yace masu zai fara zuwa wurin mutanan da suka taimake shi kafin ya wuce garin su, guzurin tafiya suka hada masa, kowa ya kawo abunda yake dashi, suka bashi sannan sukace mashi idan Allah yasa yaga yarsa angel ya fada mata sunyi kewarta, zuciyarshi cike fal da kewarsu ya kamo hanya zai bar rigarsu, harfa yayi nisa yajiyo takun gudunta sai faman kwala mashi kira takeyi, a hanzarce ya juya yana kallonta, danejo ce hannunta ruƙe da kullin kayanta, hankalin shi ba karamin tashi yayi ba, ganin ta biyo shi.
Karasowa tayi tana haki tace"dan Allah ka tafi dani inason ganin Angel"
Girgiza mata kai yayi"kiyi hakuri bazan iya tafiya dake ba, meyasa kika yarda dani har haka? ki yi hakuri ki koma wurin ƴan uwanki" fashewa tayi da kuka.
Ana cikin haka, yajiyo sautin takalman yan uwanta kusan gaba dayansu ne suka biyota.
Fuskokinsu babu walwala, ruƙo hannunta kakansu yayi tare da mika ma taj, da mamaki yake kallonshi don bai fahimci me yake nufi ba, har saida yayi mashi da kurmanci Ya nuna mashi cewa ya tafi da ita, sun bar mashi ita, saboda tace in har basu bari tabi shi ba, to zata kashe kanta ne, shiyasa suka yanke shawarar kwara su bar mashi ita, don ko sun barta ba lallai su iya shawo kanta ba.
Babu yadda taj baiyi da su ba akan subar yarsu, hankalinsu sai yafi kwanciya idan tana akusa da su amma suka sanya kafiya akan dole ya tafi da ita, ganin ya turje ne yasa suka fada mashi cewa marainiyace, tun kafin ta mallaki hankalin ta iyayenta suka rasu, bata ta6a neman wani abu daga gare su tarasa ba, don haka sun bashi amanarta, yaji tsoron Allah ya rike masu ita amana su je can su yi aure, hawaye ne suka wanke fuskarshi, jiki asanyaye yasa hannu ya ruƙo hannun danejo,yayi masu alkawarin bazai ta6a bari ta nemi wani abu ta rasa ba, zai dauki dukkan wani nauyi nata zai bata kulawa, sunji dadin abunda ya fada masu a karshe sukayi bankwana da junansu, yaja hannun danejo suka nufi rigarsu Habu.
har sun fidda rai da sake ganin shi, tsawon kwanakin da yayi a rigarsu danejo kusan kullum sai sunzo neman shi a yar bukkarsa, sunyi mamakin ganin ya dawo masu tare da yar matashiyar budurwa, cikin harshen fulatanci danejo tayi masu bayanin komai dangane da taj...."
labarin tajudden da Angel ya ta6a zuciyoyinsu, har hawaye suka zubda masa saboda tsananin tausayin shi da suka ji, bayan komai ya lafa ya sanar da su zancen tafiyar shi, ba don sunso ba sukayi mashi fatan alkhairi da addu'ar Allah yasa yaga yarinyarsa, kafin tafiyarsa saida suka hada mashi shatara na arziki, bayan haka suka yi masu rakiya har zuwa bakin titi, ba su tafi ba sai da sukaga ya samu motar hayar da zata shigar da shi cikin garin joss tukunna sukayi mashi bankwana.
Tun da suka shiga motar, danejo ta kankameshi, kamar wani yace zai kwace mata shi, wani irin mugun tsoron mutane take ji, mutun ɗayane ta yarda dashi ta kuma damka amanarta agareshi saboda tasanyawa ranta cewa bazai ta6a cutar da ita ba.
Kafin su karasa cikin garin, tuni bacci yayi awon gaba da ita, a yayin da kanta ke asaman kirjinsa, hankalin taj sam ba akwance yake ba, saboda fargaban kada miyagun da suka kai mashi farmaki su gansu, yasan muddin sukasan cewa bai mutuba, to kuwa zasu nemi hanyar da zasu kashe shi ne kamar yadda suka kashe dan uwansa uzair, mutuwar da tayi matuƙar girgiza shi, dabara ce ta fado mashi da sauri ya sanya hannu ya cire gyalen danejo da take daure qugunta da shi, ya lullu6e fuskarsa, Idanunsa ne kadai suke a bude.
Bayan isarsu joss, motar ta sauke su a tasha, driver yace ina kudin mota, sai lokacin ya tuna da baida ko sisi, sai dai kayan da fulanin nan suka bashi, hakuri ya bashi ya hada shi da katon dawon fura, mai motar baiyi gardama ba ya kar6a, ruko hannun danejo yayi suka soma tafiya atare har ya sama masu abun hawan da zai kaisu unguwar da su ke, kafin isar su tuni dare ya ritsa da su.
Da farin cikinsa Ya zo unguwar, amma lokacin dayaga gidajensu a kulle, nan take murnar ta koma ciki, tunkafin ma yaji abunda ya faru hankalinsa yai mugun tashi, baisan ina zai tsoma kanshi ba, ga yar mutane da yake ta yawo da ita, harta fara yi mashi kukan yunwa take ji, tausayinta ne ya kama shi, da ya san hakan zata faru dabai yi kuskuran tafowa da ita ba..
A bun hawa ya kuma tsaida masu, suka nufi gidan uncle abdalla da ita don ya ga ko sun dawo daga south korea, tunkafin me abun hawan da ya kawo su ya sauke shi ya hango gate din gidan a kulle alamar basa nan, tamkar ya daura hannu aka ya fasa ihu haka yaji.
Tunawa da amininsa muhsin wanda Angel ta ta6a sace ma matarsa waren takalmi yasa shi yanke shawarar zuwa gidan shi tare da danejo, yasan acanne zai ji komai daya faru bayan 6acewarsu
Basu sha wahala ba, cikin sa'a suka same shi agida, tare da matar shi, lokacin dayaji sallamar taj a firgi ce ya mike zaune yana kallon kofar shigowa falon, bai gane shi ba har saida ya cire mayafin danejo dake akan fuskarsa tukunna ya shaida shi, muryarshi na rawa yace taj! Dama kana araye? Tsawon lokaci muna ta neman ku babu kai ba uzair duka an nemi ku an rasa"? A rude yake jefa mashi tambayoyin, matarshi da sauri ta nufi danejo ta ruko hannunta suka zauna kan sofa, kafin ta mike ta shiga ciki ta kawo masu abinci da ruwan shi.
"Dan Allah abban muhsin kabarshi Ya huta, bakasan daga ina yake ba, sannan bakasan meya faru dashi! Idan har bai samu nutsuwa ba tayaya zai iya fayyace mana abunda ya faru da su"? Fuskarta a yamutse tayi maganar, jinjina kai yayi fuskarsa da tsantsar al'ajabi yace da taj su shiga ciki yayi wanka ya canza kayan jikin shi, yaga duk sun jigata kamar na almajirai,
Bayan sun huta, sunci sun koshi, har bacci yayi itama danejo ta dan runtsa, wuraren karfe shabiyu na dare yafarka ya taras da muhsin ya zabga uban tagumi yana kallon shi, mamakine yacika shi.
"Ka yi hakuri taj, kada kaga na takura maka, wallahi na damu da rashin ku, hankalina bazai ta6a kwanciya ba har sai ka fadamin meya faru da ku da har kuka gudu aka neme ku aka rasa......"
Mikewa zaune taj yayi, kafin a tsanake ya labarta masa komai daya faru, wani irin matsanancin kuka mai cin rai muhsin ya fashe dashi, bakomai ya firgita shi ba ya kuma bashi tsoro face mutuwar amininsu uzair ta yi matuƙar girgiza shi, cikin shesshekar kuka ya ke fadin"taj dama abunda ya faru daku kenan? Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un wannan wata irin masiface, Uzair ya mutu, Angel ta 6ace, rana ɗaya an tarwatsa farin cikin zuri'arku, in sha Allah sai Allah ya saka maku wannan zaluncin da akayi maku....."muhsin ya yi kuka tamkar ransa zai fita,
Lallashinshi taj ya somayi yana fadin yayi hakuri komai ya riga daya wuce, yanzu shi damuwarshi ina aneelerh take matar uzair"?
Daƙyar muhsin Ya samu nutsuwa, ya fara mashi labarin abunda Ya faru bayan 6acewarsu,
Yaji dadin jin cewa Aneelerh tana agidan iyayenta, abun da ya faranta ranshi, Yaron da yaji ta haifa masu, tunkafin ma yaganshi Yaji Ya kamu da kaunarsa, kaunar da yake yima uzair gaba daya ta koma akan yaron da bai ta6a ganinsa ba......' acikin labarin da muhsin ya fada masa abu ɗayane bai sanar da shi ba, rasuwar iyayensa gudun kada zuciyarsa ta buga, kwara idan ya samu nutsuwa ya sanar dashi daga bisani.
A daren ranar kafin muhsin yabar dakin taj, Sai da taj ya gargaɗesa akan kada ya sanar ma wani cewa yagansa saboda rayuwarsa tana acikin hatsari, idan mutanan da suka kashe uzair suka san da zaman shi tabbas zasu cigaba da bibiyarsa har sai sunga bayan shi.
Cikin sanyin murya muhsin yace in sha Allah babu wanda zaiji zancen dawowarshi, zai rufa masa asiri yaci gaba da zama a gidansa har zuwa lokacin da Allah zai kawo mashi mafita....
Tsawon wata guda suna agidan muhsin, a cikin kwanakin da yayi baya iya runtsawa saboda damuwar rashin angel, duk daren Allah Sai yayi nafilfili saboda angel dinsa, duk ya fita hayyacinsa sam baya da koshin lafiya ciwon kafarsa tamkar ana fama masa shi abu yaƙi ci ya ƙi cinyewa, muhsin yaso ya bi shi suje asibiti a duba lafiyarshi gudun kada ya rasa ranshi amma yaki yarda saboda bayason wani yaga fuskarshi, ya ƙwammace idan ma mutuwarce ta dauke shi agidan muhsin zaifi mashi sauƙi akan wadannan azzaluman mutanan su kona shi.
A daren wata rana ne, Yana cikin Yin nafilfilin dare, Yajiyo dirar motoci a cikin gidan muhsin, A firgice Ya mike daga kan darduma Gabansa na faduwa, baisan su wanene sukazo gidan muhsin ba, a irin wannan lokacin karfe kusan sha biyu na dare, zuciyarsa na bugawa ya nufi falon gidan don ganin su wanene,
Hankalinsa ba karamin tashi yayi ba, ganin matasan samari masu jini ajika suna shigowa kowannansu sanye cikin shiga ta bakake kaya sun rufe fuskokinsu da facemask.
Bakomai ne ya tsoratar da shi ba face tunawa da wadannan body guards din da suka budewa alhazawannan motocinsu, nan take ranshi ya bashi cewar sune, hakan na nufin muhsin Yaci amanarshi, bayan yayi mashi alkawarin zai rufa masa asiri shine yabi ta bayan fage ya tona masa asiri, zuciyarshi ajagule ya furta meyasa zaiyi min haka! Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, tashin hankalin shi danejo kada suce zasu haɗa da ita su kashe...
A lokacin zuciyarshi ta riga ta gama hasala, Jininsa akan akaifarsa yake, tunkararsu yayi muryarshi a fadace yace"kun biyo ni nan dinma donku kashe ni? Laifin me nayi maku ne? Da ɗaci aransa ya furta maganar, kamar daga sama yaji muryar muhsin daga bayan shi yana fadin"taj, ka tsaya zanyi maka bayani" a sukwane ya juya ya kalle shi a fusace yace"wani irin bayani zakayi min muhsin? haka mukayi dakai? ka cuce ni muhsin, ba zan ta6a yafe maka ba, yanzu dakai za'a hada baki don akashe ni"? Hawaye cike tab da idanunsa yayi maganar, fitowa danejo da matar mushin sukayi daga dakin duk suka tsaya suna kallon su....
Matasan da suka tsaya abakin kofar falon sun harɗe hannayensu akan kirjinshi suna kallon shi, babu alamun zasuyi magana..
"Taj bazan ta6a cin amanarka ba, abun da ya faru da kai ba kai ka ɗai ya shafa ba, hada ni kaina saboda ina jinka tamkar ɗan uwana na, waɗannan matasan da kake gani, ba su zo da niyar su cutar dakai ba, sai don su taimaki rayuwarka, Idan ka basu hadin kai in sha Allah zakuyi nasarar nemo Angel dinka data 6ata, bayan haka zasu tayaka daukar fansa akan mutanan da suka kashe uzair"
"Har yanzu ban fahimci inda zancenka ya dosa ba .." murmushi muhsin yayi kafin yaci gaba da cewa"su ɗin jami'an hukumar ISOD ne, nasan ba zaka rasa sanin CHIEF OWAIS ba, ɗan gidan Sharafudeen Obinna......" wani irin al'ajabi ne ya kama tajudden muryarshi na rawa ya maimaita sunan Chief Owais da tsantsar mamaki yace"muhsin dagaske kake min ko wasa? Tayaya akai ma su kasan da zamana"
Kafin muhsin Ya bashi amsar tambayarshi, Chief owais Ya shigo bakin shi dauke da sallama cikin shiga ta kakin isod, da sauri matasan nan suka buga kafa tare da sara mashi, muhsin kamar zaiyi mashi sujjada tsabar yadda yake washe baki yana yi mashi sannu da zuwa yalla6ai, shi dai taj ya gaza yarda da abunda idanunsa suke gane mashi, kai ko a mafarki bai ta6a tsammanin zai haɗu da chief owais ba, mutumin da a tv kadai yake iya ganinsa, sai gashi yau a zahiri Allah Ya nuna masa shi.
Cike da qasaita, Chief Ya nuna masa sofa alamar Ya zauna" jiki na 6ari taj yaje ya zauna yana ta faman bin shi da kallo a lokacin shima ya zauna kan sofa din dake fuskantar ta shi.
Cikin harshen turanci yace"nasan zaiyi wuya ace baka sanni ba, amma duk da haka zan gabatar maka da kaina, da farko sunana owais sharafudeen Obinna, chief na hukumar Isod...." ya faɗa tare da ɗan dakatawa yana dubansa, tun anan taj ya fahimci ba karamin mutunne bane mai ji da kansa.
"Malam taj, kamar yadda kake mamakin ganina nima haka nake mamakin kasantuwana acikin rayuwarka, ko a mafarki ban ta6a tsammanin akwai ranar da zan hana idona bacci saboda damuwa da mutumin da bansan wanene shi ba...." kalaman chief owais sun girgiza shi matuƙa, har dai ya gaza jure wa yace"dan Allah ka fadamin meyasa ka damu dani bayan baka sanni ba"
da buɗar bakinsa sai cewa yai"ƴarka ce sila" waro idanu waje taj yayi da tsantsar mamaki yake binsa da kallo fuskarsa da rudani yace"meyasa kace haka"?
Numfasawa yayi kafin ya soma magana muryarshi tamkar ana busa sarewa saboda dadin sauraranta....
A washe garin ranar dana dawo Nigeria daga U.S anyi min wani kira da ya tsaya min araina....
Fitowa yayi daga cikin bathroom waist dinsa daure da towel, yayin da dayan hannunsa ke a ruke da wani short towel yana tsane sumar kanshi, a gaban dressing mirror ya tsaya da niyar ya gyara jikin shi, wayarsa dake akan nightstand ta soma ringing, dakatawa yayi da tsane sumar kan da yakeyi a hankali ya nufi wayar ya dauko ta yana duba number din da aka kirasa da ita, yayi mamakin ganin bakuwar number, A matsayin shi na jami'in sirri komai nasu asirrince suke yin shi, harta phone number dinsa special ce, bakowa yasan shi da ita ba, sai mutun yakai yake samun damar mallakar ta, bai yi niyar picking call din ba saboda a ka'idarsa baya ɗaga bakuwar number, ko kiransa akayi indai ba family dinsa bane to baya picking sai anfara neman iznin yin magana da shi......
Amma a lokaci sai zuciyarsa ta kwallafa rai akan son sanin wanene ke kiransa...
Baisan sa'adda Ya danna answer call ba, ko da yai picking ya kara phone din a kunnansa shiru yayi baice komai ba tsabar miskilancinsa jira yake yaji wani isasshen ne ya kira shi batare da iznin shi ba.
Lamarin ya daure masa kai jin anyi shiru ba'ayi mashi magana ba, ko wanene wannan mai karfin halin? Har zaiyi rejecting call din sai kuma Ya fasa calmly ya furta "who is on the line"?
Sautin muryar karamar yarinya yaji ta ratsa kunnansa "Angel ce,"
Yayi mamakin jin muryar karamar yarinya, aransa ya ayyana ko yar wacece ta kirasa,
"kinsan dawa kike magana"?
"a'a," ta bashi amsa atakaice
"Ur age"?
"7yrs" voice ɗin shi da alamun mamaki ya maimaita"7yrs? ina mai wayar yake'?
"Daddyna ne, ya tafi masallaci ni kaɗai ce agidan, shine na hada numbobi na kira don in gaisa da mutanan duniya"
Murmushin gefen fuska yadan saki har dimple dinsa ya lotsa, don ya fahimci ba'asan ta dauki wayar ba, tun daga kan muryarta ya gane irin yaran nan ne masu tsiwa
"Can i call u video"?
Da sauri tace eh,
Nan take ya mayar da kiran Video call, da sauri ya sanya yatsan hannunsa ya rufe front camera din wayar saboda baison taga fuskarshi, baisan ko tarko aka ɗana masa da ita ba, lokacin da fuskar Angel ta bayyana akan faskeken screen din wayarsa wani irin bugu zuciyarsa tayi, bai yi tsammanin zai ganta kyakkyawa ba, fara sol ga manyan idanu launin gray dara dara da su, gaba ɗaya ya kasa kyafta idanunsa daka kallon fuskar ta, a sukwane ya koma gefen gadon shi ya zauna yana ci gaba da kallon ta...
"I can't see u" ta yi maganar tana faman gwale masa ido, murmushi yasaki yana kallon ƙananun la66anta tausasan gaske launin pink, chief Ya shagala da kallonta, tamkar a mafarki yake bin fuskarta da kallon ƙurulla kamar zai haɗiyeta, A can 6angaran Angel taji shiru ba'ayi mata magana ba, a tunaninta rashin network ne, yasa bata ganin shi a video din, batasan cewa shine ya toshe front camera din wayarsa don kada tagansa, da sauri yayi screenshort din fuskarta ba tare da sanin ta ba...
Zuciyarsa ba ƙaramin sosuwa tayi ba, ganin tayi rejecting call din, sam bai gaji da kallonta ba, da wata irin kasala ya kwantar da kansa bisa pillow, Ya bude hotonta yaci gaba da kallon fuskarta....
Baiyi tunanin kiran layin ba, haka ya wuni da tunaninta aranshi, tsawon kwana uku baya iya bacci batare daya kalli hoton fuskarta ba, sometimes a rungume da wayarsa yake kwana, sai da takaiga harta daddynsa da mommynsa sunsan da hoton yarinyar daya kwallafa rai akai, mahafinsa ne Ya bashi shawarar Ya nemo ta idan hakan zai kwantar masa da hankalinsa, Ya ji dadin shawarar daddynsa, maimakon ya tuntu6i layin tajuddeen kaitsaye su yi magana da shi, sai ya fara bincike ta hanyar amfani da phone number din da Angel ta kira da shi, anan ya sami bayanan taj hada shafukansa na social media da yake amfani da su wurin yaɗa aikinsu na ƴan jarida, cikin sa'a ya gano address din gidan radion da taj yake aiki, bai samu damar zuwa joss ba saboda kiran gaggawa da akayi masa tafiya ce ta kama shi zai bar kasar ba don yaso ba.
Gaba ɗaya ya tattara komai ya damka a hannun Big guy, wanda ya kasance ɗaya daga cikin na hannun damansa, amintattunsa, Ya fada masa komai dangane da yarinyar data kirasa a wayar sannan yace mashi yana son yaje har can joss din Ya bincika mashi inda suke rayuwa, saboda yana son sanin komai dangane da ita........
Atakaice big guy shine mutumin da ya siya ma angel piano da kayan zane, a ranar da sukaje kasuwa da su taj ta sanya masu rigima sai ansiya mata su gashi basu da kudi, ashe shine ke bi biyarsu duk wani motsinsu akan idanunsa, chief shine ya bada umarnin komai suke bukata yayi masu shi sannan bayaso su san cewa shine yake bibiyarsu har zuwa lokacin da zai dawo kasar.
Duk wani abu da unaisah tayi sai big guy ya turama Cheif ta wayarshi, hakan ba karamin dadi yake yi mashi ba ....
Kafin chief ya dawo Nigeria wannan tsautsayin ya ritsa da su tajuddeen wanda yayi silar 6acewarsu, hankalin big guy ba karamin tashi yayi ba, lokacin da labarin ya riske shi, har sai da yaji fargaban sanar da chief saboda yasan yadda ya ƙwalla fa rai akan kaunar yarinyar, gashi saura kwanaki kalilan ya rage mashi ya shigo nigeria, Yaci burin haduwa da ita tare da mahaifinta, Allah bai nufa ba . ...
Dakyar Big guy ya sanar da shi abunda ke faruwa na 6acewarsu, tsabar tashin hankalin daya fuskanta na jin mummunan labarin har zazza6i sai da yayi, duk da haka bai karaya ba, yabar komai nashi, ya dawo nigeria bai sauka a abuja ba, kaitsaye ya sauka a joss, big guy ne yaje tarbo su a airport, tare da jami'ansu dayazo da su...
A katafaren gidan da big guy din yake da zama suka sauka, dama chief ne ya biya kudin gidan a lokacin daya tura shi neman gidan su Angel.
Kwana uku da zaman su agidan kafin suka fara nasu binciken, basu tsaya bata lokaci ba suka nemi alfarmar Inspector General of CID da ya damka masu case din su tajudeen a hannun su, tuni suka amince masu saboda sunsan hukumarsu ta musammance, duk wasu bayanai nasu tajudeen saida suka tura ma chief hada makullan gidajensu da suka kar6a.
Muhsin yana ɗaya daga cikin wadanda jami'an isod suka tuntu6a har gida suka kai mashi ziyara don jin cewa shi ɗayane daga cikin aminnan tajuddeen bayan sunyi mashi tambayoyi ya amsa masu wanda ya sani sai kuma sukace mashi ko bayan tafiyarsu idan yaji ɗuriyar tajudeen ko abokinsa uzair yayi gaggawar sanar da su, saboda sunsan zasu iya tuntubarsa tun da shi amininsu ne, contact dinsu suka bashi kafin sukayi mashi sallama kun ji yadda akai har muhsin ya samu damar sanar da jami'an isod zancen zuwan tajuddeen ba tare da shi taj din Ya sani ba, saboda ya fahimci baya son kowa yasan da zamansa, shiyasa bai sanar da shi dangane da jami'an isod dake nemansa ba...
Bayan chief owais ya kammala bashi labarin, saukko yayi daga kan sofa din Ya zube saman gwiwowinsa hawaye nata sintiri akan fuskarshi cikin sanyin murya yace"dama angel itace silar da kasan da zamana"? Muryarsa na rawa ya furta maganar, baisan sa'adda ya fashe da kuka ba, dama zuciyarsa a raunace take,
"Allah sarki angel, ashe da rabon wata rana rashin jin ki ya yi min amfani...." kasa karasa maganar yayi,
Da sauri chief ya ruko hannunsa acikin nashi, cikin sanyin murya yace"ka yi hakuri, ni banzo don na fama maka raunin dake acikin zuciyarka ba, nazo ne don na tallafi rayuwarka, idan har ka bani hadin kai nayi maka alkawarin zan yi iyakar bakin kokarina don ganin na baka kariya, na kuma tallafa maka da duk abunda nake da shi, Allah shine Ya hadani dakai ta silar yarka, Ina jinta tamkar kanwata, muhsin Ya sanar dani komai dangane da abun da ya faru dakai wanda yai silar bacewarku, in sha Allah mutanan da suka yi maku wannan aika aikar sai sunyi danasanin kasantuwarsu a doron duniyarnan......."
kwantar masa da hankali chief ya cigaba da yi har saida yaga ya fara samun nutsuwa tukunna yace mashi zai jira ya yanke shawara...." ai tunkafin ya karasa maganar taj yace mashi ya amince, zai basu hadin kai, babu wata shawara da zaiyi, saboda shi bashi da mafita kwara su tallafa masa ya nemo yarsa.....
Sunji dadin yadda taj ya amince masu batare da 6ata lokaci ba chief, Yace mashi su fara shiri zasu tafi abuja tare da shi, saboda Yana so ya sama masa muhallin da zai zauna akusa dashi sannan yace zai sama masa gurbi a hukumar su ta Isod bayan ya kar6i training dinsu, bayan tafiyarsu tajudeen abuja, rayuwarshi ta sauya, chief owais ya gatanta shi, a cikin gidansa ya ware masa part ɗaya, inda zai zauna tare da danejo bayan haka ya bashi kyautar mota, cin su da suturarsu gaba ɗaya shine yake daukar nauyin su, Kafin taj Ya fara kar6ar training din Isod sai da yafara auran danejo saboda yana son su ƙara kusanci da juna, bayason tayi kewar rashin wani nata.
Big guy shi ne mutumin da ya shiga gidan Uzair, aranar da Aneelerh taje gidan har ya ɗauke mata baby junaid, bayan haka sune jami'an sirrin da suka kaita gidansu har su ka yi mata tambayoyi da suka shafi 6acewar su Angel.
Sauke numfashi yayi bayan ya gama basu labarin cikin sanyin murya yace
_"Kunji yadda akai na tsira daga hannun mutanan da suka so rabani da rayuwana, hakika cheif yayi min halaccin da bazan ta6a mantawa ba, ya kyautata min, ya faranta min a lokacin da gwiwata ta sage na fidda rai da rayuwar duniyar nan, badan Allah ya ƙaddarar haduwata dashi ba, da yanzu bansan awani hali zan tsinci kaina ba"_
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*Buy bestselling books online
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 17 Complete
by
Novels Elite Admin
June 09, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_ *~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋✊~*_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘Best gifts for your loved ones
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
Shessheƙar kukan su ta cika ɗakin, babu mai lallashin wani a cikin su, tsananin tausayin taj ne ya kamasu jin irin kalubalen da ya fuskanta, A hankali unaisah ta ɗaura tafukan hannayenta dake kerma kan fuskarshi ta share mashi hawayen shi, cikin sanyin murya tace"daddy, ka yi haƙuri, ka daina zubar da hawayenka, bana son ganin su, kallonta yai da rinannun idanunsa muryarsa na ɗan rawa yace"My Angel, ni nawa ƙaluban dana fuskanta bakomai bane akan naku! Ku ne kuka ga rayuwa, ku yakamata a jajanta mawa, a kuma tausayama rayuwarku....." gaba ɗaya hankulansu Sajeed na akanshi, da ruɗani unaisah tace"daddy, kasan abun da ya faru dani bayan na gudu daga rugar su danejo"?
Lumshe idanunsa yai hawaye na sintiri ya ɗan jinjina kanshi kafin ya motsa la66ansa"na san abun da ya faru dangane da rayuwar kullan da ku ka yi a GIDAN KURKUKUN ƘADDARA, da kuma irin baƙar izayar da suke yi maku, ranar da mu ka fara ji daga ni har chief duk irin juriyarmu sai da muka zubar da hawayen mu saboda abun ya ɗaga hankulanmu, ya razanar da mu, bazan iya misalta maku halin da muka shiga a lokacin da muka ji labarin abun da ake aikatawa a GIDAN KURKUKUN ƘADDARA.
Kallon kallo Su Naufal suka soma jifar junansu da shi idanuwan kowannansu sunyi jawur da su, saboda kukan da suka sha, bakomaine yasa su kallon juna ba face mamakin yadda akai daddyn Angel Yasan abun da ake aikatawa agidan kurkukun ƙaddara, Unaisah ce kadai batai mamaki ba saboda tasan dama sun sani watakil abakin salsabeel suka ji komai.
Murya na rawa Batool Tace"daddy dama kunsani? Meyasa baku kawo mana dauki ba? Kunsan kuwa irin ƙuntatar rayuwar kullan da mukayi a gidan kurkukun ƙaddara? Ta fada hawaye masu ɗumi suna sintiri akan kuncin ta, muryarsa a raunace ya furta"mu kan mu ba mu jima da sani ba, da ace tuntuni mun san da zaman ku da har rayukanmu zamu iya sadaukarwa don mu ceto rayuwarku"
Ummin dake kallon batool jikin ta har tsuma yakeyi saboda tsabar ƙagara da son jin tarihin rayuwarsu babban burinta taji menene ma'anar gidan kurkukun ƙaddara da taji sunata ambato a bakunansu.
Jan numfashi batool tayi kafin ta ɗaura da cewa"mun rayu tun kafin mu mallaki hankulanmu, bamu ta6a ganin hasken rana ba, babu shige babu fuce, a ɗaki ɗaya muke a kulle, kullum cikin uniform ɗaya, abinci sau ɗaya arana, bamusan dadin rayuwar duniyar nan ba, duk wani hakkinmu na rayuwa an tauye mana shi, mu bamu san dadin iyaye ba, sannan babu mai jin kukanmu, balle a kawo mana dauki, anjuye mana tunaninmu balle musan cewa muma mutane ne masu ƴan ci kamar kowa.... ..." bata ƙarasa maganarba saboda kukan daya tokare makoshinta, tamkar zatayi kakarin amai.
Cikin karyayyar murya Unaisah tace"tsohuwa tamira ta ta6a fada min cewa na jininmu ne kadai zai Iya sadaukar damu, har yau nagaza yarda da maganar nan, Ina kokwanton tayaya za'ay iyayen da su ka yi silar zuwanka duniya ko wani naka ya sadaukar dakai inda za'a azabtar da rayuwarka? Daddy wanene ya sadaukar dani❓
A matuƙar ruɗe ta jefa mashi tambayar tana kallon shi.
Cikin sanyin murya yace"unaisah ni kaina a rude nake, bansan wa zan zarga ba Allah shine yasan wanene mugun da yayi maki wannan aika aikar"
Muryar ummi araunace tace"dan Allah ku fahintar dani, tun ɗazu inata magana kunki bani amsa! Inaso naji meya faru da ku? Sannan Ina ne GIDAN KURKUKUN ƘADDARA"!?
Daƙyar Unaisah ta lallashi zuciyarta dake yi mata radadi, kafin ta ɗaura idanunta akan fuskar ummi"zan fada maki komai da kikeson ji aunty ummi" A hankali ummi ke kallon fuskar unaisah
Lokacin da tafara bata labarin rayuwarsu wata irin zuface ta soma wanke fuskar ummi, jikinta ya hau yin kakarwa saboda razanar da tayi, ko a mafarki bata ta6a jin labari mai matuƙar firgitarwa irin wannan ba tuni hawaye sun soma yar tseral kan kuncinta.
Abunda yafi tsaya mata arai cikin labarin da Unaisah ta bata shine mutuwar Unaizah yar gidan daddy, ba ita ba harta taj Jikin shi Ya gama mutuwa saboda bakomai suka sani ba dangane da rayuwarsu saida unaisah tafara basu labari, chief dake atsaye bakin door yana sauraron su kasa jurewa yayi, wani irin jiri jiri Yake gani acikin idanunsa, zuciyarsa har wani tafarfasa take yi tamkar zata kone kanta tsabar 6acin rai da fusata, jijiyoyin wuyansa tuni sun fito rudu rudu kan goshinsa, juyawa yai da sauri Yabar kofar dakin, A hanzarce big guy yabi bayansa gudun kada zuciya ta debe shi Ya je yai ma kanshi Illa.
Zuciyar ummi dake hauhawa tana harbawa da wani irin mahaukacin bugu na tashin hankali tama rasa ina zata jefa kanta taji dadi gaba ɗaya taji ta tsani rayuwar duniya, Hakika Labarin su Unaiza Ya karya mata zuciya, ya ƙara mata karfin imani sai yanzu ta gane babban kuskuran da tayi nagaza daukar ƙaddarar rayuwarta, cikin shesshekar kuka mai haɗe da gunjin kuka ta furta
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!! Wannan wata irin musibace? Ku fadamin Tayaya akai har kuka Iya jure wannan ukubar da ƙananun shekarun ku batare da zuciyoyinku sun buga ba? La66anta na kerma ta fada tana dubansu kafin taci gaba da cewa "Zuciyata tagaza yarda da abun da kunnuwana suke jiye min! hankalina Ya tashi! Zuciyata ta karaya! Wannan wani irin zaluncine? Su wanene wadannan Fasikan mutanan mugaye azzulamai marasa imani da tausayi, wadanda basu ɗauki ran dan adam abakin komai ba, wai su wanene su dan uban su? Wasu irin dabbobine su jahilai, Masu matattar zuciya, Anya kuwa suna da zuciya a kirjinsu? Anya kuwa mutanene su kamar kowa? Ina kokwanto akansu..." gaba daya ummi ta burkice masu sambatu kawai takeyi kamar sabon kamu ahauka, da alama abun ya razana kwakwalwarta.
Rashin imanin da akai ma yaran ya ɗaga hankalin ta, fashewa ta kuma yi da kuka kafin taci gaba da fadin"sun manta cewa zasu mutu su koma ga Allah? Wai su basa tunanin makomar su ne? Duniya kaɗai suka sa agaba, ko Sun manta cewa duk wani abu da suka mallaka aduniyar nan zasu barshi? Daga su sai halin su za'a binne su!?...."
ɗaya bayan ɗaya take kallon su jemimah dake ta kuka aranta ta ayyana yanzu gaba dayansu nan an lalata rayuwarsu har da yan ƙananan cikin su wani irin yunkurin amai ne yazo mata da gudun gaske ta mike ta fuce daga dakin, Har batool ta yunkura zata bita taj yai saurin ruƙe hannunta,
"ku barta tayi kuka ta hakanne zata samu saukin abunda take ji aranta" jiki asanyaye batool ta zauna.
Shi kanshi bazai Iya misalta irin kunar da zuciyarshi take yi mashi ba
Cikin muryar lallashi Yace da su"Idan na ce kuyi hakuri kamar na cuce ku ne, saidai ba yadda zakuyi hakurin nan dai shine yakamace ku, Allah Baya barin hakkin wani akan wani, wadanda suka azabtar da rayuwarku In sha Allah za su ga mummunar sakayyar da Allah zai masu tun agidan duniya zasu fara ɗanɗana kudarsu kafin su koma ga mahaliccinsu su fuskanci makomarsu......." daƙyar Ya samu ya shawo kansu, kafin ya bi su daya bayan daya yayi huggin dinsu duk don ya kwantar masu da hankalin su, sai da ya tabbatar ya share masu hawayensu tukunna yace
"Dan Allah kada ku sanya damuwa aranku, ku kwantar da hankulanku in sha Allah komai yakusa zuwa karshe, yanzu ku koma dakunanku ku yi wanka ku kwanta ku huta, nasan baza a rasa masu fama da ciwon kai a cikin ku ba, zanyi magana akawo maku breakfast har bedroom dinku"
muryoyin su adisashe suka amsa mashi da toh,
kafin suka mike kamar wadanda aka zarewa laka haka suka nufi kofar dakin suka fuce.
Bayan fitarsu Ya rage daga Unaisah sai batool sai kuma Taj,
Mikewa batool tayi jikinta tamkar na wadda tayi zazza6i ganin ta nufi kofar dakinne Yasa taj yi mata magana"Ina zaki je ne"?
"Ɗakin Aunty Ummi" amsa mata yai da okey, bayan ta fuce ya maida dubanshi ga unaisah, janyota yai tare da kwantar mata da kanta kan kirjinsa hannunsa akan kafadarta
"Ina fata yanzu babu abunda ke maki ciwo"? muryarta kasa kasa tace"eh daddy,"
Da yar zolaya yace mata"ya rashin ji ko da yake naga kin daina Yanzu"? ƙara shige mashi tayi tana yar dariya, bubbuga bayanta yai da hannunshi, kafin ya janyeta, ya mike kan gwiwowinsa ya fuskanci alkibla yakai goshinsa kasa yai sujjada murmushi tasaki tana kallon shi, da sauri itama tayi sujjadar kamar yadda yayi, tsawon mintuna kafin suka dago da kansu fuskar kowan nan su dauke da annurin farin ciki
"Daddy fada min me ka ce acikin sujjadarka"
Numfasawa yai kafin yace"nayima Allah godiyane da ya bayyanar min da ke da ranki da lafiyarki"
"Nima haka" murmushi suka kuma saki gaba dayansu,
"Daddy Inaso na tambayeka, tayaya akai ku ka hadu da su salsabeel? Ko ya fada maku yadda akai suma suka ku6uta daga kurkukun ƙaddara"?
Shiru ya ɗanyi kafin yace"ki bari idan yazo sai ki ji daga bakin shi, yanzu nafiso ki kara samun kwanciyar hankali" amsa mashi tayi da toh
"ki tashi mu shiga toilet ki wanke fuskarki kizo mu ci abinci"
Ya fada tare da ruko hannunta suka shiga toilet, bayan sun wanke fuskokin su suka fito atare
A gefen gado suka zauna Ya bude masu abincin tray din da suka ajiye kan table
Cikin kulawa yake bata abinci abaki tana ci, tsabar dadi kamar ta zuba ruwa a kasa tasha, wai yau gata ga daddynta
"Daddy, Ina aunty Aneelerh da babynta"?
Murmushi Yasaki kafin Yace"suna nan cikin koshin lafiya, kwanakin baya nabibiyi layin wayarta amma ba'a ɗaga ba sai wata rana dana ci sa'a aka daga wayar kinsan wanene ya daga" girgiza mashi kai tay alamar a'a yana murmushi yace"ƙaninki baby junaid," waro idanu waje tayi da tsantsar farin ciki tace"daddy sunan shi junaid" daga mata kai yai alamar eh
"baki ga yaron ba kyakkyawa dashi, ga wayau sai ma in yana surutu.." cike da zumudi tace"daddy inason ganin shi tare da aunty aneelerh, dan Allah ka kaini wurin su nayi missing dinta"
"Zan kaiki in sha Allah, amma ba yanzu ba, ki ɗan ƙara hakuri" tur6une mashi fuska tayi, bakinta cunkushe da abincin daya tura mata, yar dariya yai tunawa da kuruciyarta.
"Banji kin tambayeni danejo ba"!
Sakin fuskarta tay, "tana araina daddy, bazan ta6a mantawa da halaccinta agareni ba, ni dai ba abun da zance sai dai inyiwa Allah godiya saboda Ya hadani da mutanan kirki masu sona tsakani da Allah' ta fada fukarta da ɗan murmushi,
"Yaushe zaka kaini Wurinta in ganta"?
"Ko zuwa anjima idan kika kara jin sauki sai muje ko"? Daga mashi kai tay alamar eh.
Shiru suka dan yi kafin ta kuma cewa"daddy mommy adama fa? da uncle abdallah!! Suna nan suma"?
Daga mata kai yai alamar eh,
"Alhamdulillah Ya Allah" ta furta da matsanancin farin ciki, ashe da rabon in sake ganin yan uwana.
"Ina granny ɗina da sauran mutanan buzaye"
Jiki asanyaye ya ajiye cokalin dake a hannun shi, nan take ta fahimci babu lafiya, muryarta adan rude tace"daddy menene"?
Cikin sanyin murya yace"unaisah sun riga mu gidan gaskiya, mahaifina da mahaifiyata, da kuma kakata kusan duk a lokaci ɗaya suka rasa rayukansu nima sai daga baya naji labari..."
Cikin sanyin murya tace"ubangiji Allah Yajikansu ya gafarta masu, Allah ya jaddada rahama agare su..." amsa mata yayi da ameen
Shiru suka danyi na wani lokaci batare da ya cigaba da bata abincin ba
So take ta tambaye shi dangane da mahaifiyarta sai dai takasa saboda zuciyarta taki bata hadin kai, Har yanzu bata daina jin ɗacin radadin abun da tayi mata ba, ta tsani mahaifiyarta fiye da komai na duniyar nan, tana son ta haɗu da ita ba don komai ba sai don taji dalilin dayasa ta yi watsi da ita, idan ba ta son ta meyasa ta haife ta❓
*HAJJATY 💋*
A zaune take gaban dressing mirror, fuskarta dauke da murmushi bakomai take tunawa ba face fuskar Naufal, ta kasa mantawa da shi, Yaron ya kwanta mata aranta, daren jiya data kwanta bacci har mafarkinsa tayi,
da alama bata jima da fitowa daga wanka ba, duba da towel din dake daure a chest dinta
Tun dazu takasa tabuka komai gaba daya ta shagala da tunanin naufal, ta ƙosa pravin ya shigo donta nuna mashi hoton naufal tasan zaiyi mamakin ganin me kama da ita.
Wayar ta dake ajiye kan mirror din ta dauka ta budo hoton shi tana kallo har zooming din fuskarsa take yi
Jin motsin shigowar mutun yasa tayi saurin juyawa don ganin wanene
Pravin ne ya shigo sanye da farar jallabiya, fuskarshi babu annuri ko miskala zarratin kamar wanda aka fada ma sakon mutuwarsa
Sam bata lura da yanayin shi ba, cike da zumudi ta mike ta nufe shi tana fadin"honey, ina ka shiga tun jiya bansaka a idanuna ba"? Fadawa tayi kan kirkinsa tai huggin nasa kafin ta ɗago da fara'arta tace"ka yi shiru baka ce min komai ba"? Wani kallo ya soma jefa mata mai kama da harara, da alama ta manta abunda tayi mashi jiya shiyasa ta zaƙe tana shige mashi
Ganin baida alamun yi mata maganane yasa tace"fadamin baby, ko dai hajiya saratu ce ta 6ata maka rai"? Banza yai da ita baice uffan ba..
Murmushi tadan saki"nasan itace ta bata maka rai, bari na nuna maka wani abu nasan zakayi farin ciki idan ka ganshi" ta fada da sauri ta nufi mirror
Goya hannayensa yai akan kirjinsa yana jiran karasowarta.
"Baby, duba ka gani, jiya a wurin taro bayan tafiyarka naga wannan yaron mai kama da ɗan mu Naufal kyakkyawan gaske" cikin annushuwa ta mika mashi wayar don ya kar6a ya gani, rai amatuƙar 6ace yakai ma wayar bahagon naushi tayi sama ta ƙundumo kan tiles ta bada wani sauti mai karfi.
idanunta azazzare ta dago tana kallon shi, Huci yake yi tamkar mayunwacin zaki Ya furta"kin manta abunda ki kai min jiya"? Dafe kai tayi da hannu daya idanunta tuni sun cuko tab da kwalla, ranta abace tace"pravin! Meyasa zaka jefar min da wayata? Laifin me nayi maka? Saboda kawai naki bin umarninka? Wai meke damunka ne pravin? Agaban mutane fa ka ruko hannuna kaja ni zaka fitar dani daga hall tayaya bazan ki binka ba? Ko so kake afara zargin mu ?
Kafin ta ƙare maganar Ya daka mata tsawar data firgitar da ita, nuna ta yai da yatsan hannun shi"yi min shiru! Bana son jin komai daga gare ki, ashe harni ban isa in baki umarni ki bi ba! Hankalin ki ya kwanta Kin kunyata ni a idon jama'a..." hawayene suka soma sintiri akan fuskarta, muryarta na rawa tace"pravin ka fahimce ni mana, kasan bazan ta6a kin bin umarnin ka ba, hakanan batare da kwakkwarar hujja ba! Ni nayi hakanne saboda bana so wani ya tuhume mu..." yatsansa ya daura kan la66anta, shiru tayi tana kallon shi
Can kuma ta fashe da kuka tasa hannu ta ture yatsan nasa tana fadin"baka kyauta min ba, Tun jiya nake zumudin in nuna maka hoton sajeed Yaron dake kama da danmu amma shine ka fasa min waya..."?
Ta6e la66ansa yai kafin ya furta"ki yi hakuri rainane ya 6aci, " ya fada tare da zukunnawa ya dauki wayar yana fadin"zan siya maki wata"
"bana so, ni dai ka gyaramin tawa, saboda bana son na rasa hoton sajeed"
Harara ya watsa mata tareda cewa"meye alakarki da shi ne? Kawai daga ganin yaro yana kama dake? Mutun nawa kika sani suna da masu kama dasu a duniya? Kamar kanki farau"
"Ni wannan bai dameni ba, Ina son shi saboda inajin shi kamar ɗana dana rasa"
Rai a6ace ta fada kafin ta juya ta koma kan gado ta zauna, tana cigaba da matsar kwalla
Murmushin gefen fuska pravin yasaki Yana dubanta,
Komawa gefenta yai ya zauna bayan ya ajiye wayar ya ruko hannunta acikin nashi
"Look, bana so ki sanya damuwa aranki, idan har rashin naufal ne ke damunki, nayi maki alkawarin nan bada jimawa ba zaki haifi wani babyn, sai ki sanya mashi sunan naufal din"
Wani kallo ta jefa mashi batare da tace mashi ƙala ba, lallashinta Yacigaba dayi duk don ya samu yashawo kanta.
HAJIYA SARATU
_safa da marwa take yi a tsakar dakinta, zuciyarta cike fal da tunanin abunda Pravin yayi mata jiya a dakin taro, tun jiya abun ke ci mata tuwo akwarya, abun sai nanuƙarta yakeyi, zuciyarta ta gama hasala, wai har ita pravin zai kunyata gaban yan uwanta da abokananta? A ina ya samu ƙwarin gwiwar yi mata haka? ruƙe qugu tayi da hannu ɗaya fuskarta babu annuri_
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 18 Complete
by
Novels Elite Admin
June 12, 2024
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
__________________________✍️
💫HAJIYA SARATU💫
_safa da marwa take yi a tsakar dakinta, zuciyarta cike fal da tunanin abun da Pravin yayi mata jiya a dakin taro, tun jiya abun ke ci mata tuwo akwarya, abun sai nanuƙarta yakeyi, zuciyarta ta gama hasala, wai har ita pravin zai kunyata gaban yan uwanta da abokananta? A ina ya samu ƙwarin gwiwar yi mata haka? ruƙe qugu tayi da hannu ɗaya fuskarta babu annuri_
Maganganun da suka Tattauna jiya ita da su Har excellency ta soma tariyo bayan fitowarsu daga hall kafin su nufi gidan prime minister.
"Meyesa pravin zai ja hannunta abainar jama'a? Menene alakarsu? Wai ku ba ku zargin wani abu atsakanin su"? Hajiya laurace ta fada babu wasa akan fuskarta
"Najima ina zargin matar nan, na dai yi shiru ne ban fada maki ba, saboda bana so in shiga tsakanin ki da mijin ki, amma ni kwata kwata hankalina bai kwanta da ita ba, tun daga kan yanayin yadda take daukar wanka zaki fahince akwai wata a kasa ba banza ba, ni ay ban ta6a ganin yar aikin da ta samun ƴanci kamar hajjaty ba"! Her excellency muhibbat ce tai maganar,
Hajiya jamila tace"yanzu wani hukunci zaki yi masu"? ta fada tana kallon hajiya saratu.
Da sauri Hajiya madina tace"please, ku daina tunzurata ku bar ta taji da abun da ke damunta, ni banga abun ɗaga hankali a maganar nan ba!"
Hajiya saratu da ke sauraronsu ɗaya bayan ɗaya sai da ta cika ta batse kafin tace
"Wallahi bazan ƙyalesu ba! Daga ita har shi sai sun fuskanci 6acin raina, sai tayi danasanin kasantuwarta yar aiki a gidan nan"! Ta fada a tsiwace tana huci
"Ni shawarar da zan baki kawai ki kore ta daga gidan ta koma can kasarsu acigaba da bautar shanu, idan ba haka ba Allah kaɗai yasan munaƙisar da take shirya maki, ƙwara tun wuri ki yi maganinta kafin ta jaza maki matsala" Acewar hajiya Muhibbat
Dafa kafaɗarta hajiya laurat tayi"idan da zaki bi shawarata kada ki tanka masu! Nasan yanzu hankulansu atashe yake saboda sun san dole ki tuhume su, abun da yakamata ki yi shine ki manta da zancen hukunta su, ki yi tamkar babu abun da ya faru, za su yi zaton kin kyale su ne, ki bari sai sun shagala tukunna ke kuma ki fara bincike akan su, ta haka ne kadai zakisan meke atsakanin su amma yanzu idan kikace zaki hukuntasu to ba za ki san menene alakarsu ba, kwara ki fara bin diddiginsu har zuwa lokacin da zakiyi nasarar kama su dumu dumu"
Jinjina kai hajiya saratu tay alamar gamsuwa da shawarar Hajiya laurat..
Bayan ta dawo daga duniyar tunanin taja gauran Numfasawa haɗi da ɗan jinjina kanta, cikin takun sauri ta nufi wayarta dake ajiye kan pillow ta dauka ta kira landline na kitchen.
Tana fara ringing akayi picking, kara wayar tai a kunnanta.
"Inason ganin Marwa, ta same ni adaki bana son bata lokaci"
ta fada tare da katse kiran ta ajiye wayar
Cigaba da zagaye bedroom din tayi, yayin da take dunkule tafin hannunta na dama tana tura shi ana hagu kamar ƴar dambe.
Knocking kofar da akayi mata ne yasa ta dakata.
"Wanene"?
"Aunty ni ce marwa"
"Okey shigo ciki"
Turo kofar tayi, Jikinta sanye da uniform na ma'aikatan gidan ta shigo, cikin girmamawa ta gaishe da hajiya saratu, bata amsa mata ba, sai tay tamkar ba ta ji me tace ba.
Tuni marwa ta sha jinin jikin ta, tsoranta kada ace wani laifin ta aikata da yasa hajiya saratu ta kira ta don tasan halinta masifaffiya ce.
Muryarta na rawa tace"Am.. Aunty gani, naji kina nemana"
Wurga mata harara hajiya saratu tayi da sauri ta dukar da kanta kasa
Tsawon lokaci bata tanka mata ba, gani ta ke kamar zubda ajine ta nemi taimakon yar aiki, sai dai ba yadda zata yi itace kadai hanya mafi sauki agareta.
Zama tayi gefen gadonta, cike da isa ta dubi marwa"ke zonan"! da sauri marwa ta dawo ta zukunna agabanta.
"Wani aiki nakeso kiyi min, bana so kowa ya sani daga ni sai ke! Na yaba da hankalin ki ne shiyasa na za6e ki saboda nasan zaki Iya......" Tun da tafara magana marwa ta soma zare idanunta cike da fargaba.
"Kafin na faɗa maki, zan gindaya maki sharadi, Idan har na kuskura naji maganar nan abakin wani, ko kika bani matsala wallahi thumma tallahi na lahira sai yafi ki jin dadi...." Wani irin yawu marwa ta haɗiya jiki na bari tace"in sha Allah zan kiyaye."
Ta6e baki tayi kafin ta ɗaura da cewa" me kika sani dangane da head maid din gidan nan? ya mu'amalarta daku take? Sannan Wacece aminiyarta acikin ku? Shin tana fada maku sirrinta"?
Shiru marwa tayi aranta ta ayyana to fa! Ko me hajjaty ta aikata ma aunty masifatu da take neman karin bayani dangane da ita? Watakil watan cin ubanta ne ya tsaya
A fili kuma tace "Abun da nasani dangane da ita, macace mai saukin kai, tana da mutunci kuma tana kyautata mana, ba ta shiga sabgarmu, sannan bata cika zama yin fira da mu ba, macece mai kamun kai bata da surutu, sannan bata da aminiya acikin mu balle har wani yasan sirrinta, wannan shine Iya abunda sani"
Tur6une fuska hajiya saratu tayi, ita ba haka taso taji daga bakin Marwa ba.
"Okey, ki nutsu ki saurareni," jinjina mata kai tai
"Daga yau inaso ki fara shisshige mata, saboda ina zarginta, inason kisan duk wani sirrinta, ki zama aminiyarta, bayan haka duk wani motsinta ya kasance a tafin hannunki, idan har kikaga wani abu ba dai dai ba, to kiyi hanzarin sanar dani," amsa mata tayi da toh
"Idan har na samu abun da nakeso nayi maki alkawarin zan baki mukamin da take da shi agidan nan, bayan haka zanyi maki kyauta ta musamman, kin dai san wacece ni, basai nayi maki bayani ba"
Wani irin farin cikine Ya lullu6e marwa musamman da taji Hajiya saratu ta ambaci zata bata mukamin hajjaty ga kuma kyautar da zata samu, aranta ta ƙudiri aniyar saita yi ma hajjaty kutse koda kuwa bata kama ta da laifin komai ba, ita zata ƙala mata sharrin da za'a sauke ta daga kan mukaminta.
Shu'umin murmushin gefen fuska tasaki.
"Baki da matsala dani aunty, in sha Allah zaki samu abunda kikeso"
"Zaki iya tafiya" mikewa marwa tayi zuciyarta cike fal da murna, dama ta jima tana jin haushin hajjaty saboda yadda tayi masu zarra agidan, komai itace akan gaba, gata head maid ga farin jini awurin mutanan gida, bayan ba wani aiki takeyi ba acikin gidan sune masu wahalar girka abinci, ita aikin ta tsara abunda za'a girka ne da kuma bada umarnin yadda abu zai kasance.
Dole ta ɗana mata tarkon da bazata Iya fidda kanta ba, ko dan ta ƙwace mukamin ta, wannan alwashine ta daukarwa kanta!
Ta fada aranta, yayin da take nufar hanyar komawa kitchen
Bayan fitar marwa, hajiya saratu ta sauke ajiyar zuciya, yanzu ne ta samu kwarin gwiwar shiga toilet yin wanka
Lokacin da fito, A zaune ta same shi gefen gadonta, sam bataji alamun shigowarshi ba.
Tun da ya ɗago suka hada ido da ita yai saurin sunnar da kanshi kasa, wani irin nauyinta yaji, baisan ta ina zai fara shawo kanta ba, Yasan dole ta tuhume shi akan abun da Ya faru jiya.
Kau da ido tai daga kan shi, Ta juya ta nufi closet, jim kaɗan Ta fito har ta sanya riga bubu ta atamfa, gaban mirror ta tsaya tare dakai hannu ta dauki turare ta soma feshe jikin ta da shi, yadda ta share shi kamar batasan da zaman shi a dakin ba.
Shi kuwa gogan Ya kasa dauke idanunsa daga gareta.
Kamshin turarenta ne yakai mashi karo har ya gaza jurewa duk da shakkarta da ya ke ji ƙarfin hali yai wurin furta"Har Yanzu fushi kike dani? Banza tayi da shi
Mikewa yai tsaye ya nufeta, daga bayanta ya dan dakata Yana bin ta da kallo.
Kafin cikin sanyin murya yace "Tun jiya nake ta so na baki hakuri, nasan ban kyauta maki ba, ni kaina ba'a hayyacina na aikata hakan ba, bansan meyasa na ruko hannunta ba, wallahi sharrin shaiɗanne"
Murmushin gefen fuska tasaki, ba tare da ta bari ya gani ba, dama dagangan ta dauki wankar da zai zautar da shi
"Na cancanci kowani irin hukunci daga gareki, a shirye nake dana kar6e shi, ni dai bana son 6acin ranki"
ya faɗa tare da ɗaura kansa saman kafadarta saboda karfin hali irin nashi
Lumshe idanunsa yai tare da shakar kamshin turarenta.
"Kinyi shiru baki ce min komai ba" sai da ta mula tasha iska tukunna Tace"laifin me kayi min"?
"Kin riga da kin sani"
"In dai dangane da abunda ya faru jiya ne to ka manta kawai, bana son tada maganar, ko alokacin abunda yasa raina ya 6aci saboda ina kishin ka ne banji dadi ba, amma yanzu komai ya wuce"
Tsabar mamakin kalamanta yasa shi saurin ɗagowa yana duban fuskarta ta cikin mirror.
"Amma dai wasa kike min ko"? Murmushi ta sakar mashi tare da cewa"na taba maka wasa irin wannan"?
Girgiza kanshi yai"a'a, baki taba min ba, amma dai nayi mamaki, Allah yasa ba mafarki nake ba" juyowa tayi suka fuskanci juna, fuskar ta dauke da ƙayataccen murmushi ta ɗaura hannayen ta a kan kafadunsa.
Lamarin ya ɗaure masa kai gaba daya ta canza mashi kamar ba hajiya saratun daya sani ba.
Cikin sanyin murya tace"hubby, kada ka ƙara maimaita kuskuran da kayi, bana so, kasan inada kishi, akan ka zan iya komai daga ciki har da kisa"
Zaro idanunsa yayi"in sha Allah hakan bazata faru ba, zanyi kokarin ganin na kiyaye duk wani abu da zai bata maki rai"
Ba zato ba tsammani yaji tayi huggin ɗinsa tare da zagayo da hannayenta kan waist dinsa, tuni yafara jin shi awani yanayi.
Sumbatar wuyansa tayi kafin ta dago da bakinta saitin kunnanshi cikin muryar raɗa mai hade da kwarkwasa tace"fadamin me ka ke so nayi maka wanda zai faranta ranka"
"Nagaza yarda da abinda kike fada min, anya kuwa kece? Ko dai aljanune suka shige ki? Nifa ina kokwanto bana so saina shagala ki canza min ainihin kala dinki"
dariya tayi cike da nishadi tace"ka daina kokwanto akaina, ni ce dai hajiya saratun daka sani, matarka uwar ya'yanka"
Murmushi pravin yai cike da jin shaukinta
"Ka yi breakfast ko insa a kawo mana mu yi a daki nima banci komai ba"
"In ban da abunki ay kinsan bana iya cin abinci idan ba atare dake ba, don ma ke dince wani lokaci baki jira na"
"I'm sorry Yanzu bari na kira akawo mana a daki, me kake son ci"?
Yana faman washe baki yace "Duk abin da zaki ci, zabinki ay shine nawa"
Shu'umin murmushin gefen fuska hajiya saratu tasaki tare dakai hannu ta dauki waya ta kira layin kitchen ta isar da sakon akawo masu abinci, bayan abla ta kawo masu atare suka zauna suna ci, kamar sabbin ma'aurata abaki ta fara bashi har sai da suka cinye kafin ta soma jan hankalin shi.
Gaba ɗaya nema take ta zautar dashi da salonta, kasa jurewa yayi da sauri ya ƙara tighting nata a jikinsa.
_________________________________❤✍️
Bayan shigar chief bedroom dinsa a zafafe Ya faɗa Bathroom dinsa don ya watsa ruwa ko ya samu zuciyarsa ta lafa daga radadin da ta ke yi masa.
ganin ya shiga toilet yasa big guy sauke ajiyar zuciya, yayi tunanin zaiyi yadda ya saba ne idan ransa ya 6aci da wuya in bai yi ma kan shi illa ba, wani lokacin mirror yake kaima naushi ya tarwatsa shi har sai hannun shi ya faffashe saboda tsabar zuciyar dake gare shi.
Kafin fitowarshi da sauri big guy ya fita na tsawon mintuna ya dawo hannun shi ruƙe da wooden tray mai dauke da breakfast din chief.
Yayi mamakin ganin shi kwance kan gado, jikin shi sanye da bathrobe ya ɗaura hannunsa ɗaya kan lallausar sumar kanshi, ya lumshe wadannan kyawawan idanuwan nashi, bakomai yake tunawa ba acikin zuciyarsa face tarihin rayuwar prisoners, labarin yai matuƙar ta6a zuciyar shi.
"Allah Ya huci zuciyarka Yalla6ai, ga breakfast dinka, nasan kana jin yunwa" cikin girmamawa yayi maganar
Tamkar bazai tanka mashi ba, sai da ya dauki lokaci kafin Ya furta"ka koma da abincin bana jin zan iya ci"
Cikin sanyin murya big guy yace"ka yi hakuri Sir, kasan ni mai biyayya ne agare ka, bana yi maka jayayya amma yau bazan iya bin umarnin ka ba, saboda na damu dakai, abun da ke damunka nima shike damuna..." ya fada yana cigaba da kallonsa.
"Sir, ƙin cin abinci bashi bane mafita, kana buƙatar kwanciyar hankali da nutsuwa, wanda hakan bazai samu ba sai ka jajirce wurin ganin ka kauda damuwarka, sannan yanzu ne ya kamata mu dage damtse mu yi aiki tuƙuru don ganin mun gano su wanene azzaluman mutanan da suke aikata 6arna a kasarmu"
Daɗaɗan kalamai Big guy ya cigaba da zayyano masa yana kara karfafa masa gwiwa da kwantar masa da hankali, A hankali Ya fara jin saukin radadin da zuciyarsa ke yi mashi.
"Sir, har yanzu kana akan bakanka na bazaka ci abincin ba"? Ya faɗa yana duban cute face din Ogan nasa
Slowly ya ɗan motsa tausasan pink lips dinsa in a low voice ya furta"zan kokarta" gyaɗa kai yai
"Zan tafi yalla6ai, Ka huta lafiya" ya fada tare da sara mashi kafin Ya juya har ya kusa ficewa daga dakin muryar chief ta ratsa kunnansa"nagoda da kulawarka agare ni"
Murmushi big guy yai"kada ka damu yalla6ai"
Har zai fuce ya kuma dakatar da shi"please ka duba dakin Yaron nan, kaga Awani hali Yake a ciki, Idan ya farka a tabbatar Yayi breakfast dinsa, idan ya gama ka tambaye shi me yake bukata in ya fada maka ay gaggawar yi mashi, zuwa anjima sheikh Imam zai zo duba shi"
"Okey, Sir"
Ya fada tare da bude door room din Ya fito waje, dakatawa yayi da tafiya yana tunanin tawace hanya zai faranta ran chief? Don ya fahimci har yanzu akwai sauran damuwa aranshi, tunawa da Unaisah yasa shi saurin zaro wayarsa ya danna ma boss kira, tana fara ringing yai picking Call din
Da zolaya yace"masu Ƴa, halan Har yanzu kana nan maƙale da ita"
Sautin muryar boss da alamun dariya yace"To ɗan sa ido, ka fara tsokanar taka ko"?
Dariya Big guy yayi" inatayaka murna abokina"
"Nagode sosai mutumina, Ina chief ne ina fata yana lafiya"
"Ba lafiya, Har yanzu akwai damuwa aranshi, Kuma kasan halinshi mutunne mai zuciya, yanzu haka ina a kofar dakinsa, na kai masa abinci yace min bazai iya ci ba"
Muryar bos da jimami yace"amma banji dadi ba, pls ka yi kokarin kwantar masa da hankali kafin inzo"
da sauri big guy yace"anya zan iya? Ko dai zaka turo unaisah ko da godiyane tayi mashi, watakil hakan Ya kwantar masa da hankalinsa"
"Nima nayi tunanin hakan, yanzu zan turo ta in sha Allah" murmushi big guy yai kafin yai mashi sallama a hanzarce Ya nufi bedroom diny Danish.
*❤GARKUWA💪*
A kishingiɗe Yake kan gadon shi, Ya hakimce kamar wani basarake, wasu hadaddun sleeping dress ne a jikin sa launin red colour sunyi bala'en yi mashi kyau, hannunsa ɗaya rungume da pillow, lallausar sumar kanshi ta lullu6e gefen fuskarshi, yayin da kyawawan fararen idanunsa ke akan hadadden ceilling din dakin, tun da Ya farka daga bacci bai ta6uka komai ba, gaba ɗaya ya shagala da tunanin Hateem, wani irin kewarsa yake ji, mutumin ya kwanta masa aransa saboda yadda ya tarairayesa ya bashi kulawa kamar wani nashi, bai ta6a tsammanin zaiji tsantsar kaunarsa ba, sai gashi zuciyarsa takasa samun sukuni saboda tunaninsa, da zarar ya lumshe idanunsa fuskar Hateem yake gani dauke da murmushi......"
Yana son ya sake sanya shi a idanunsa, kwata kwata bai fahimci cewa prime minister kasar ya bari ba.
Har Yanzu kamshin turaren daddy hateem bai bar jikin shi ba, saboda rungumarsa da yadinga yi jiya kamar zai maida shi jikin shi, fragrance din Yana da karfi sosai shiyasa ya kama jikin sa.
Kalaman hateem ne suka fara dawo mashi
_zan tafi da kewarka, dan Allah kada ka manta dani, inaso ka ɗauke ni tamkar mahaifinka, aduk lokacin da wani abu ke damunka ka sanar da chief zai fada min, zamu dinga yin waya akai akai, daga yanzu inaso ka dinga kirana da sunan daddynka_
A hankali ya dago da yatsan hannunsa yana kallon zoben da ya sanya mashi ayatsa mai kyan gaske, wannan ne karo na farko daya fara sanya zobe,
Daura yatsan yai kan kananun la66ansa Ya sumbace shi a hankali yanayin fuskarshi kamar zaiyi murmushi.
Knocking din kofar dakin da akaine Ya sa shi daura idonsa kan kofar, bakomai Ya fado masa arani ba face Angel dinsa, yasan ita kaɗaice zata Iya zuwa duba shi awanan lokacin, Idan ba ita ba sai kuma yan uwansa, saukowa yai daga kan gadon bayan ya jefar da pillow hannunsa, da sauri Ya nufi kofar don Ya tarbe ta, saboda yayi kewarta jiya, idanunsa sunyi maraicin ganin ta,, shi kanshi baiyi tsammanin zai Iya mintuna batare da ita a gafen sa ba, sai gashi jiya daddy hateem Ya sace zuciyarsa.
Ko da ƙofar ta bude yai arba da big guy tuni yanayin fuskarshi Ya canza, shi da ya taso da zumudinsa don Ya nuna ma Angel dinsa kyautar zoben da mutumin nan ya bashi, sannan Ya bata labarin abunda Ya faru atsakanin su ashe ba ita bace.
"Barka da safiya danish" big guy ya fada da fara'a akan fuskarsa, ko kallo danish bai mashi ba, Hankalin shi na akan bayan shi, burin shi Yaga Angel don har yanzu bai fidda rai da ganin ta ba
Da mamaki big guy ya waiga baya don yaga me yake kallo sai dai baiga komai ba.
"Ina fata ka tashi lafiya" ya fada aranshi yana mai mamakin Girman Jikin Yaron ga tsawo tubarkalla uwa uba ga kyau kamar shi ya zana kan shi.
"Magana na ke yi maka ka yi shiru ba ka ce komai ba, ko har yanzu ba ka jin daɗin jikin naka ne"?
cikin sanyin murya ya furta"My Angel? Tana Ina"?
Dafa kafadarsa big guy yai"kwantar da hankalinka tana nan cikin koshin lafiya, nasan zata zo dubaka..." kafin Ya kare maganar danish Yace"Ina son ganinta, " ya fada yana kokarin bi ta gefen shi Ya wuce, A hanzarce big guy yai saurin Shan gabanshi, gudun Kada Ya ruguza masa plan dinsa na zuwan angel part din chief.
Wani kallo da danish Ya watsa mashi sai da yaɗan ji fargabansa, Karfin Hali Yai wurin furta"Ka yi hakuri bawai ina son dakatar dakai bane, daga gani yanzu ka farka daga bacci ko wanka ba ka yi ba, a haka zakaje wurinta? Itama bazata ji dadin ganin ba, kaje kayi wanka, kafin ka fito zan sa unaisah ta kawo maka breakfast dinka har daki"
cikin sigar lallashi yakeyi mashi magana, badan Ya yarda da kalaman sa ba, ya amince mashi, juyawa yayi tamkar wanda ya rasa kuzarinsa, harta bugun zuciyarshi ya canza ji yake kamar wani abu na faruwa ko yana shirin faruwa
Bayan ya shiga toilet Ya maida kofa ya rufa, ajiyar zuciya big guy ya sauke aranshi ya ayyana wai Allah daga ganin yaron nan zaiyi kafiya, dole saina mike tsaye idan ba haka ba zai iya zame min matsala.
Ya fada tare da juyawa ya fuce daga dakin, Ya nufi sashen kitchen din su don Ya hada masa breakfast dinsa.
*❤UNAISAH ANGEL💋*
Bata jima da fitowa daga bathroom ba, sai rawar kai takeyi saboda daddynta Ya fada mata zancen zuwa dakin chief don tayi mashi godiya bisa ga irin kyautatawar da yayi mashi, ruwan ido Ya hana ta canki kayan da za ta sanya, tayi tsaye gaban faskeken closet dinsu, sai faman bin jerin kayan take yi da kallo, fuskarta dauke da murmushi tarasa gane meyasa take jin wani irin nishadi da annushuwa kamar wadda akaiwa albishir da gidan Aljanna.
A ƙalla ta shafe mintuna kafin ta fito sanye cikin wasu riga da wando launin pearl pink masu kyan gaske, tsayawa zayyana kyawunta acikin kayan 6ata baki ne, abun sai wanda ya gani.
Takalma ta ɗauko masu tsini launin kayan, ta zura su a kafarta, bayan ta dauko mayafi ta tsaya gaban mirror ta ta soma laga shi akanta.
Ita kanta data kalli madubi sai da ta firgita da ganin wani sihirtaccen kyau daya bayyana akan fuskarta, murmushi tadan saki har dimples dinta suka lotsa.
"Daughter I'm waiting For You, Kin bar daddy awaje Yana ta jiranki"
Muryar taj tajiyo daga waje yana magana, da sauri ta nufi kofar ta fito, waro idanu waje taj yai arude Ya furta"Tabarakallahu ahsanun khalikin! My Angel? Kinga kuwa kyan da kikayi kamar hurul aini" sunnar da kanta kasa tay, fuskarta sauke da murmushi
Ruko hannunta yai a cikin nashi suka nufi dakin chief.
Abakin kofar dakin suka dakata suna kallon juna
Lokaci daya suka sakar ma juna murmushi
Raɗa yai mata a kunnanta"ba'ay mashi rashin jin magana ba kamar daddy bane da aka raina" dariya tayi jin abun da yace.
Sakin hannunta yai"ki kula min da kanki," amsa mashi tayi da toh, kamar karsu rabu yana tafiya yana waiwayonta itama sai kallon shi take yi
Ɗaga murya tayi tare da cewa"daddy kada ka tafi ka jirani in fito"
"Ba nesa zanyi ba, Zanje gidane bazan jima ba zan dawo" ta6e mashi baki tayi kamar zatayi kuka, hakan ba karamin nishadi ya sanya shi ba.
Zuciyarta Cike fal da fargaban haɗuwa dashi tay knocking kofar, Almost 3 times ba'a bude ba, harta fara tunanin ko dai bacci yakeyi ne ko baya a dakin har zata juya kofar ta soma zugewa a hankali ta buɗe, kamshin turarensa ne Ya fara dakar mata hanci har saida ta dan lumashe idanunta.
Kasa shiga tay saboda zullumin hada ido da shi, da kuma jin nauyn magana da shi.
Sai da ta shafe kusan mintuna biyar, tana saƙe saƙe a zuciyarta ba tare da ta motsa ba, kafin ta gama yanke shawara da zuciyarta kwatsam kofar ta soma kokarin rufe kanta, da sauri ta ratsa ta tsakankanin door din da karfi ta faɗa dakin kamar wadda aka jeho, ƙiris Ya rage ƙofar ta datse da jikinta, wannan gangancin nata ba karamin mamaki ya bashi ba, sai faman nishi take yi hadi da sauke ajiyar zuciya, sai da tagama yan kame kamen ta, kafin a hankali kamar maijin tsoronsa ta soma bin dakin da kallon, Lokacin da ta daura idanunta akan shi har saida gabanta Ya fadi ganin surar jikin shi, Har yanzu bai motsa daga kan gadon shi ba, kamar yadda Big guy ya barshi haka ta taras da shi sanye da rigar wanka, ya daura Apple laptop dinsa kan waist insa, Yayin da kanshi ke akan pillow ya dan lumshe idanunsa, tuni kamshin turarenta yakai mashi karo
Yawu ta haɗiya, a tunaninta baya ganin ta cikin sanda ta matsa daga gaban gadon tana faman zare gray eye dinta ta furta"ina kwana, ka tashi lafiya" magana takeyi hankalinta na akan kwantaccen sajen fuskarshi.
"Lafiya" taji ya amsa mata da sanyin murya, tayi mamakin jin voice dinsa irin na danish.
Shiru tayi tana faman wurwurga eye balls dinta, bata ta6a jin nauyin wani dan adam ba sai akan shi, kamar ma kunyar shi take ji
Wasa takama yi da yatsun hannunta, batasan cewa yana kallonta ta cikin laptop dinsa ba.
"Idan kingama tsayuwar zaki iya tafiya" sexy voice dinsa ce ta kuma ratsa kunnanta, muryarta da en ena tace"am.. um. wai Dama daddy ne yace inzo in yi maka godiya"
Shiru yayi yana maimaita maganarta a zuciyarsa kafin ya furta"bake ki kayi niyar zuwa ba? Shiya tursasa maki kizo"?
Dafe kai tay da hannu daya alamar ta kwafsa.
"Mantawa nayi, ni nayi niyar zuwa inyi maka godiya".
Ta6e pink lips dinsa yai na ɗan wani lokaci kafin yace"ba'ay min godiya, duk wani abu da nayi nayine don Allah, ina fata kin fahimce ni" amsa mashi tayi da toh,
shiru suka kuma yi, Ganin yaki sake tanka matane yasa tai kafin halin cewa"tun da bakason ay maka godiya, to ka fadamin wani abu da zan dinga yi maka tunda kaima ka kyautata mana duk da nasan bazan iya biyan ka ba" ta faɗa tana cuke la66anta.
A hankali ya dan ware reddish eyes dinsa, duk wani motsinta akan idonsa sai dai ita batasan Yana kallonta.
"Will you do whatever I tell you?"da kwarin gwiwa ta amsa mashi Eh
"Okey," ya furta tare da sauke Laptop dinsa gefe ɗaya, a hanzarce ta juya mashi ƙeya, Ganin zai mike kuma taga bathrobe ce a jikin shi, murmushin gefen fuska ya dan saki.
Saukowa yai daga kan gadon Ya nufi walk-in closet dinsa, Jim kaɗan Ya fito sanye da thobe launin ruwan toka, tamkar a jikinsa aka dinka ta tsabar yadda ta bayyana surarsa.
Kamar yadda yabarta haka ya same ta atsaye ta juya baya.
Zama yai gefen gadon da alama bata san ya dawo ba.
"Zaki Iya zuba min abinci"? ɗan zaro idanunta tayi kafin ta amsa mashi da toh, juyawa tayi a hankali ta saci kallonsa Idanunsa na akan wayar hannunsa, taji dadin ganin hankalinsa baya akanta
Cikin takun sanda ta karasa daga gaban table din.
"Me kakeso nafara zuba maka"
"Duk abun da yai maki" farfari tayi da idonta hada ɗan gumtse baki alamar mamaki, sam batayi zaton zai kulata har haka ba, kallo ɗaya da tai masa ta fahimci mutunne mai ji da kansa
Coffee ta mika masa yasa hannu ya kar6a A hankali Yake kurbarsa, Angel sai faman satar kallon la66ansa take Yi, ba karamin rudarta yakeyi ba, ga kamshin turarensa dake ta kai mata hari.
Komai ta zuba masa cinye shi yake yi, mutumin da bai cika cin abinci ba, amma yau har saida yaso ya ƙwari cikin sa, ba tare daya ankare ba..
Bayan ta kammala serving nasa tace"ko akwai wani abun da zanyi maka? Ko in gyara maka bedroom din ka"
"Idan kin ji zaki iya" ta6e baki tadanyi kafin tafara tunanin shiga toilet dinsa ta gyara masa shi, watakil kafin ta fito shi kuma Ya fita sai ta gyara dakin
Juyawa tayi da sauri ta nufi toilet din, sai lokacin Ya dago Yana bin bayanta da kallo har sai da ta 6ace ma ganinsa tukunna ya kau da idonsa.
*🤍ZAHRA🤍*
A ƙudundune take kan darduma ta lullu6e jikinta da hijabi, tun bayan sallar asubahi bata farka daga bacci ba.
Shigowa Dakin Aneelerh tayi, hannunta ruƙe dana baby junaid, sakin hannunta yai da gudu ya tunkari zahra Ya faɗa jikinta yana fadin"aunty zahra Ina tsarabar da kika ce zakiyi min jiya! Shine ma baki tada ni daga bacci ba"
Janyo shi Aneelerh tayi tana fadin"meye haka? Ba ka ga bacci take yi ba"? Zahra dake sauraronsu tayi shiru batare da ta motsa ba ashe idonta biyu.
Da shagwa6a baby junaid yace"mommy ay itane tace zata min tsaraba, Ni ta tashi ta bani abuna kamin taci gaba da baccin..." bai kare maganar ba, ta rufe bakinsa da tafin hannunta.
"Yi shiru kada ta farka, mu tafi zuwa anjima sai mu dawo" maƙe mata kafaɗa yayi"nidai ba inda zani Allah, sai ta bani abuna" kwace hannunsa yai daga na Aneelerh Ya fada kan zahra yana kiciniyar tada ta daga bacci, duk yadda taso tayi pretending sai da takasa tana faman fitar da numfashi mai ɗan huci ta sanya hannu ta janye junaid kafin ta mike zaune ta tu6e hijab din jikinta ta jefar da shi gefe ɗaya
Har saida gaban aneerlah Ya fadi ganin jirwayen hawaye akan fuskar zahra, idanunta sun kumbura suntum da su, da alama tasha kuka har ta gaji.
Waro idanu waje baby junaid Yayi "mommy mun shiga uku, aunty zahra kuka tayi wani ya buge ta . " bai kare maganar ba, zahra tai saurin sanya hannu ta dan buge bakinsa"kada na kuskura nasake ji kayi magana," ta6e mata baki yai alamar zai yi kuka da sauri ta janyoshi tare da manna shi kan kirjinta, wani sabon kukan ne ta kuma fashewa da shi.
Hankalin Aneelerh ba karamin tashi yayi ba, tuni yanayin fuskarta Ya canza, matsawo tayi kusa da zahra ta zauna, cikin sanyin murya tace"ni dama tun jiya da kika dawo gida hankalina bai kwanta da yanayin ki ba, saboda na lura da yadda kike kokarin danne damuwarki saboda kada mu gane! Meyasa zahra eyeh? Adan tsawace ta fada tana dubanta
"Ki fadamin me ya faru dake ne? Waye ya ta6a min ke yanzun nan in ɗaura ɗamarar yin yaƙi da shi"! ta faɗa babu wasa akan fuskarta, Cikin shesshekar kuka zahra tace"a.. Aunty Aneeleerh zayn! Na shiga uku! Hajiya saratu ta haɗa ni da masifa, ashe lokacin da ta turamin sakon nan tace min in zabi daya daga cikinsu nayi kuskuran rubuta sunan zayn a maimakon zaid shine fa ta haɗa ni dashi, aunty aneelerh baki ji kalaman daya furta min ba.........' a tsanake tafara bata labarin abun da ya faru jiya bayan da hajiya saratu ta kira ta.
Fitowa tai daga hall din tana ta faman yan kalle kalle can ta hango hajiya saratu tsaye abakin motarta, Cikin girmamawa ta ƙarasa daga gefen ta, bayan sun ƙara gaisawa zahra tace "mommy gani" murmushi hajiya saratu tasakar mata tare da ruko hannunta acikin nata"mu shiga ciki, inaga zaifi muyi magana a tsanake" ta fada tare da buɗe murfin backseat, bayan sun shiga taja kofa ta rufe, Zahra sai faman bin cikin motar take da kallo, saboda haduwarta ga sanyi a.c dake ratsa fatar mutun
Shiru sukayi babu mai magana, Hankalin hajiya saratu na akan wayar hannunta da take ɗan daddanawa,
"Zahra," ta ambaci sunanta, da sauri ta amsa da na'am
"Ina fata kin nishadantu da dinner din nan," tana dan murmushi ta jinjina kanta tare da cewa"Eh mommy, Alhamdulillah, naji dadin gayyatana da kikayi, I can't thank you enough"
Murmushin dattako hajiya saratu tayi"kada ki damu, kin cancanta ne, ni kaina najima ina mamakin yadda kika kwanta min araina, saboda ba kowa nake mu'amala da shi ba, ina da wuyar sha'ani zahra " ta faɗa ba tare da ta ɗago da idonta dake akan screen in wayarta ba.
Zahra sai faman sakin murmushi takeyi taji dadin maganar da hajiya saratu ta furta mata.
"Kinsan meyasa na kira ki"!
"A'a"
"Idan ba zaki manta ba, Kwanakin baya na tura maki hoton twins dina, har nace idan na baki za6i wanne kike so acikin su, ashe kin bani amsa ban samu damar duba sakon ba sai daga baya na gani"
Dakatawa tayi da yin maganar, zahra nata kallon gefen fuskarta burinta ta karasa maganar nata, sai dai ta fahinci bata cika son magana ba.
ba ta zaci zata dago ba, aikuwa karaf suka hada ido cikin na juna, wani irin kwar jini tayi ma zahra da sauri ta dukar dakanta kasa tana wasa da yatsun hannunta
Daura wayar tayi akan laps dinta, ta ruko hannun zahra acikin nata, kafin ta soma magana
"Zahra na yarda dake, Kamar yadda na fada maki kin kwanta min araina, kuma na yaba da hankalin ki, kyawawan ɗabi'unki da halayen ki sune suka sa har nafara kwadayin ki zama wani bangare na rayuwana, Ina nufin ina so ki zama surukata zahra" cikin kwantar da murya hajiya saratu take yi mata magana tamkar ba aunty masifatu ba
Zahra jikinta yayi wani irin sanyi, ga wani annurin farin ciki daya lullu6eta duk da tana jin fargaban wanda za'a haɗa ta da shi Yaki amincewa...
"Naji kinyi shiru bakice komai ba, Ni bazan maki dole ba, kada kiji nauyn fada min abunda ke aranki, saboda nima bazan bari ki auri wanda zuciyarki bata so ba"
Numfasawa zahra tayi fuskarta da ɗan murmushi tace"mommy wa zai ki jinin ki? Ni ay abun farin cikine agare ni, saboda nima kin kwanta min araina, bazan 6oye maki ba, nayi mamakin tayin da kikayi min, saboda ni aganina ban kaiba mommy, ya'yanki sunfi karfi na, sannan inajin fargaban wanda zaki haɗani dashi yakini, tun da bamusan juna ba....." ta ƙarasa maganar idanunta cike tab da kwallar murna.
Jinjina kai hajiya saratu tayi kafin ta furta"kada wannan ya dameki zahra, bana so na sake jin kin furta matsayin ki bai kai ba, ni na za6e ki don haka kada kiji komai, ƴa'ƴana kuma ni nake iko da su, abunda nakeso shi zasuyi don haka ki kwantar da hankalin ki, wadannan hawayen da nake gani ki share su" ta fada tare da zaro mata hanky ta mika mata, yatsun hannun zahra na kerma ta kar6a tafara shaye hawayen ta.
Wayarta ta dauka tare da dannama zayn kira, bayan yai picking cike da bada umarni tace"ka sameni abakin hall yanzun nan Ina jiranka"! Bata jira amsar shi ba tai rejecting call din, tare da mayar da dubanta ga zahra
"Nayi mashi magana yanzu zaizo sai ku fahimci juna" cikin sanyin murya ta amsa mata da toh, sam bata kawo ma ranta zata ga akasin zaben da tayi ba.
Kusan mintuna Kafin akayi knocking, murmushi hajiya saratu ta saki, tare da kallon zahra"ki gyara nutsuwarki, Yanzu zai shigo ku gana da juna" amsa mata tayi da toh, bayan fitar hajiya saratu, da sauri zahra ta bude purse dinta ta curo hanky ta goge fuskarta, ta zaro yar hodarta ta barbaɗa, hada jan baki ta murza ma la66anta, Jin motsin buɗe motar yasa tayi saurin maida kayan kwalliyar cikin purse din.
tun daga kan kamshin turarensa daya daki hancinta tafara jin wani irin fargaba, a wani slow ya zauna kyakkyawar fuskar nan tashi a haɗe Yaci mur, ko kallon inda take baiyi ba balle ma ya nuna alamar yaga mutun a motar, da farko bata gane wanene ba acikin su,
Dakyar ta furta"ina wuni"
Banza yayi da ita, saima ya zaro wayarsa yaci gaba da dannata, nan take ranta ya bata cewar ZAYN ne, Hankalinta a matukar tashe take duban gefen fuskarshi, mutun har mutun ga kyau sai dai babu mutunci ko miskala zarratin, gaba ɗaya tarasa sukuninta tun kan aje ko'ina harta fara danasani, mamakinta tayaya akai zayn ya kasance wanda za'a hada ta dashi bayan zaid ne ta canka ba shi ba? Ko dai hajiya saratu tayi kuskure ne..."
Tayi zurfi a tunaninta muryarshi ta ratsa kunnanta"wani tsautsayine yakai ki amincewa da zancen haɗani dake? Kinsan wanene ni"? Adabarbace tace a'a amma in ranka ya 6aci kayi hakuri ni ma bada son raina ba.."
"Meyasa tun farko bakice mata baki sona ba"! A kausashe ya furta maganar,
Muryarta na rawa tace"saboda bazan iyaba"
"Wallahi idan kina son zaman lafiya ki janye zancen hadani dake da gaggawa idan ba haka ba ciwon zuciyane zaiyi silar mutuwarki, saboda ni nan da kike gani na ba mutumin kirki bane ɗan iska ne ni, sannan bani da mutunci .." Ras taji gabanta ya fadi, tunda yafara magana bai kalle ba, baima san wacece
wani irin wahalallan yawu ta haɗiya, amatukar rude take kallon shi jikinta na kerma
"Nasan bazaki so ya'yanki su yi rashin dacen uba ba, shiyasa nake gargadinki, tun kafin kiyi danasani mara amfani, ke in banda ma haɗama da rashin sanin ciwon kai ina ke ina Zayn pravin obinna? Nayi maki kama da sa'ar auranki? Wai ke yar wacece ma"?
Hawayen dake taruwa a cikin idanunta tuni sun fara wanke fuskarta
Hankalin shi kwance yaci gaba da cewa"Ni nasan ba hakanan kika kyale mommy ba, Allah kadai Yasan me kika kulla da har ta amince zata hada ni da ke, idan ma kwaɗayin abun duniyane ya rufe maki ido to ki fadamin nawa kikeso tun daga miliyan biyar har abun da yai sama zan baki kije kija jari ki rufawa kanki asiri...." sautin shesshekar kukanta ne ya cika masa kunnansa, a zafafe ya juya da niyar ya dauke ta da mari kamar an ruke hannunsa ya dakata cak Yana huci idanunsa akan fuskar zahra da hawaye ya gama wanke ta, bakomai ne yaja hankalin shi ba face kyawun fuskarta ba laifi tana da sura dai dai wadaidai saidai baya jin zai iya kula macen da bata kai matsayinsa ba
Sassauta muryarshi yayi"ke, yi min shiru in ba haka ba zan 6ata maki rai"
yatsun hannunta na kerma ta toshe bakinta, sam takasa kallon cikin idanunshi gashi ya matso kusa da ita kamshin turarensa duk Ya gama kashe mata jikinta
"Idan kinason zaman lafiyar, Kije ki fada mata, baki sona banyi maki ba"muryarya da shesshekar kuka tace"kayi hakuri amma ni bazan iyaba, saboda ina ganin girmanta, sai dai kai ka je ka faɗa mata" dakyar ta kare maganar tana faman jan numfashi
"Tausayinki nake ji bana so kiyi danasani, wallahi bani da mutunci, ni banma shirya yin aure ba, saboda baya agabana, Ni nafi sha'awar inyi sharholiya ta son raina" ya fada yana shafa sajen fuskarsa" yanzu ke kin yarda ki auri dan iska mai mu'amala da matan banza"? Ya fada yana cizon lips dinsa da masifa
Jinjina mashi kai tayi alamar eh, ita kanta batasan tayi hakan ba, batasan ya akai zuciyarta take jin kaunarsa ba, a maimakon taji haushin kalamansa.
Dafe kanshi yai da hannu ɗaya kafin ya furta"look, Idan burgeki nakeyi naji zan baki kaina, amma ki janye batun nan, saboda ni ban shirya ma aure ba, ko auran zanyi bazan auri wadda batakai aji na ba, bana so ki jefa rayuwarki cikin hatsari, kada kiga kamar ina lallashinki mommyn mu kaifi ɗayace idan ta furta magana babu wanda ya isa ya dakatar da ita, shiyasa nake lalla6aki saboda ke kadaice zaki canza ra'ayinta" zahra dake ta faman yin shesshekar kuka muryarta na rawa tace"har abada bazan iya tunkararta da maganar nan ba sai dai kai kaje ka fada mata..." bata ƙare maganar ba ya daka mata tsawar data firgitar da ita
Nuna ta yayi da yatsan hannun shi"Share hawayen kan fuskarki, ki tashi muje ki fada mata baki sona banyi maki ba" muryarta kasa kasa tace"ay na fada maka bazan iyaba..." bata kare maganar ba, taji ya haɗe bakinsa acikin nata, wani irin bugu zuciyarta tayi mata, gaba ɗaya takasa tabuka komai, har sai da Ya gama abunda zaiyi kafin ya zame harshensa, Yai saurin zuge glass din motar Ya tofar da yawun bakinsa.
tsabar wulakanci Ya zari hanky yana kara goge bakinsa kamar wanda ya ta6a najasa, rushewa tayi da matsanancin kuka ganin irin wulakancin da yai mata, abunda yafi ƙona mata rai sanya mata harshe da yai abakinta, arayuwarta ta tsani namijin da ba muharraminta ba ya ta6a ta,
Tsawa yakuma daka mata tuni ta shiga taitayinta.
"Kaɗan kika gani, wannan so mun ta6ine idan har baki janye kudirinki akaina ba, zan cigaba da amfani dake ne" ya faɗa yana mai kara jaddada mata
"Ki share hawayen nan, Ki tashi muje ki faɗa mata kinjanye" muryarta na kerma ta amsa mashi da toh, shu'umin murmushin gefen fuska yasaki, dama yasan zata amince ko dan saboda abinda yai mata don ya fahinci ba yar hannu bace tana da kamun kai shiyasa ya tsorata ta.
Hanky ta zaro ta share hawayen fuskarta, sannan ta daidaita nutsuwarta, kafin ta buɗe motar, ta fito shima ya fito ta ɗayan bangaren suka nufi hajiya saratu dake atsaye can nesa da su.
Tunkafin su karaso ta nufosu, fuskarta da fara'a tace"Son, Ina fata kun sasanta kanku"!
Nunata zayn yai"ki fada mata abun da kika gaya min acikin mota" amsa mashi tayi da toh kafin ta kalli hajiya saratu zuciyarta cike fal da tsoronsa ta ce"Mun gama magana dashi, Kuma mun fahimci juna" a gigice zayn yake kallon zahra jin abunda tace, zuciyarsa ba karamar hasala tayi ba, bai ta6a tsammanin yarinyar zatay taurin kai ba.
"Zahra kin tabbata yayi maki? Amma meyasa naga idanunki sunyi ja"? Da sauri zahra tace"kaina ne keyi min ciwo, har fada masa nayi, shine yace yakamata na tafi gida na huta, zamuyi magana awaya..." da tsantsar mamaki zayn yake kallonta, gashi ba halin Ya karyatata, don ya fahimci ta kama zuciyar mommynsu.
"Naji dadi my son, dama nasan bazaka ƙi tayin da nayi maka ba, da ace zaid ne ba lallai ya amince ba saboda shi na daddynsa ne kai kuma nawa ne, hakika yau ka faranta raina my son, Allah yayi maka albarka, zahra kema nagode maki sosai da kika aminta da tayina in sha Allah ba zakuyi danasani ba, Ina da tabbacin hakan, Ta fada tare da janyo zayn da zahra tayi huggin dinsu tana ɗan bubbuga bayansu, sai faman farin ciki takeyi yayin da su kuma zuciyoyin su suke a kuntacce da bakin ciki.
"Zayn ko zaka kaita, Gida"? Ta fada bayan ta raba su daga jikinta, da sauri zahra tace"mommy kin manta nazo da mota dina"
"Oh eh hakane, na shafa'a, Muje son mu rakata ta tafi gida" atare da zayn suka raka zahra bakin mota bayan ta shiga ta zauna, hajiya saratu tace"surukata, Anya zaki iya driving dinnan kuwa? Ko dai zayn yakai ki" wani irin mugun kallo zayn ya watsama zahra da sauri tace"a'a mommy, wallahi zan iya, ay ba sosai nake jin ciwon kan ba"
"Toh zahra Ki kula min da kanki sannan ki gaishe min da mutanan gidan"
"In sha Allah ngde ssae"
Harara hajiya saratu ta watsa ma zayn"kai bazakai mata bankwanan ba, ahaka zakuyi auren" yana faman yamutsa fuska yace"bye, sai mun yi waya" aran shi ya furta "zakiyi danasani,"
Bayan ta baro estate din har ta hau kan titi tana driving, zuciyarta bata daina tariyo mata kalaman zayn ba.
Uban tagumi aneelerh ta zabga da hannu ɗaya, tana kallon zahara data kammala bata labari
"Zahra kinyi kuskure wlh, meyasa baki ɗauki shawararshi ba kin fada mata baki son shi? Zahra ina guje maki auran mutun mara kunya irin shi! Kowace uwa burinta ta sama ma ya'yanta uba nagari wanda zasu koyi da shi su kuma yi alfahari da shi ba irin zayn ba, sam bai dace dake ba" zuciyarta ajagule tafada, kwata kwata zayn bai kwanta mata aranta ba, tun kafin ma ta ganshi.
Zahra Tana shesshekar kuka ta ruko hannunta"ki tayani da addu'a, ita nafi bukata, Aunty aneeleeh bawai nakasa fada mata bane, Ina son shi ne"
Jinjina kai aneeleeh tayi"inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un! Shikenan, zan tayaki da addu'a Idan alkhairi ne shi agare ki Allah Ya tabbatar mana dashi, idan kuma akasin hakan zan roki Allah Ya shiga tsakaninku, bayan haka dole su mami suji maganar nan"
kwantar mata da hankali aneelerh tacigaba dayi saida komai ya lafa tukunna aneelerh tace"Ina alkwarina? Kince zaki ɗaukar min hotunan dinner in gani, Jiya da su na kwana araina, ganin kin kwaso gajiyane yasa ban takura maki ba"
Murmushi zahra tasaki tunawa da Unaisah, yarinyar data kwanta mata aran ta.
"Aunty aneeelerh, akwai labari, zaki sha kanun labarai, " ta fada tare da janye baby juanid dake langwa6e ajikinta, kamar maijin bacci Yai shiru Yanata sauraronsu.
Gado Ta nufa ta dauko purse dinta ta curo wayarta donta nuna ma aneeleeh hotunan da ta dauka tare da unaisah
Kwatsam wayar ta fara ringing, da sauri tayi picking ganin sunan abie
Barka da safiya abie ina kwana"?
"Lafiyou, zahra, Ina aneeleeh ne"? Da sauri tace gatanan adakina
"Okey ki fada mata, ƙawarta ta turo min da sako ta layina, ta zo ta same ni a daki ina jiranta!" amsa mashi tayi da toh bayan ya kashe kiran ta dubu Aneelerh dake kallon ta, cike da son jin me abie Ya faɗa mata.
"Abie ne ya kira, yace in faɗa maki Kawarki ta tura mashi da sako ta layin shi kije ki same shi adaki"
Da alamun mamaki Aneeleerh ta furta"ƙawata kuma? Anya kuwa abie ya karanta sakon dai dai? In bahaka ba ni wata ƙawace gare ni da zan bata layin abie"
"Aunty Aneelerh kije kawai ki gani, bamusan menene aka turo ba" amsawa tayi da toh a hanzarce ta mike ta bar junaid adakin.
Ruko hannun shi zahra tayi"zonan In nuna maka hotunan dinner,"
Gefen gado ta zauna tare da daura shi kan laps dinta, ta buɗe gallery tana nuna mashi hotunansu, lokacin data buɗe hoton Unaisah, wuff Junaid Ya fusge wayar daga hannunta Yana fadin"Angel! angel! angel"! Har saida gaban zahra Ya fadi, a matukar rude take kallon shi ba tare data fahimci me yake nufi ba.
*SALSABEEL💫*
Zaune Yake kan sofa hannun shi ruke da wayar shi, Har ya kammala shiryawa, sai faman duba agogo Yake yi, Har ya fara gajiya da jiran su, ɗagowa yai tare da kallon su, suna a zaune tsakar falon suna cin abinci, mutun ɗaya ce ke babu acikin su, Khadeeja dake acan cikin toilet tana wanka, a kalla ta shafe kusan awa ɗaya da rabi har yanzu bata fito ba, gashi har yan uwan ta sun kammala shiyawa.
"Dan Allah ku yi sauri ku ƙarasa, kun ga har karfe sha biyu ta buga" amsa mashi sukayi da toh
"Yaya salsabeel, Khadeeja fa? Har yanzu bata fito ba, ko ban da ita zamu tafi" rubeena ce tayi maganar.
"Bansan ya zanyi da ita ba, so take ta 6ata mana lokaci, bari naje na dubo ta" ya fada tare da miƙewa Ya nufi upstairs.
"Wallahi Dama mu tafi mubar ta a gida, kada ta mana hauka, tun da ya salsabeel Yace wurin gasar kyau zamu je kuma in muka ci za'a bamu kyautar wani abu" acewar hibba.
rubeena na murmushi tace"ni zan cinye ma gasar saboda nafi ku kyau" harara hawwa ta galla mata"a haka din? Dubi kumatunki, kuma ay cewa yai sun fi son mace doguwa mai gashi, mara jiki, me dogon hanci" daure fuska rubina tayi rai a6ace tace"wlh indai bani zanci ba sai dai kowa ya rasa" ta fada tare dakai hannu ta dauki robar zuma ta dinga watsa masu akan rigunansu, azabure suka mike suna faman zare idanunsu ganin ta 6ata wankan su.
"Wallahi baki isa ba, Saina rama mana" sarah ce ta fada da sauri ta fisge zumar ta matsa mata a jikin rigarta, fashewa tayi da kuka tana fadin wayyo Allah ya salsabeel sun 6ata min kayana, shikenan ni bazanci gasar kyau ba, zuƙunnawa tayi gaban kayan abincin tana haki ta dauki coke da niygar ta watsa masu, damƙo hannunta Hawwa tayi nan fa faɗa ya kacame a tsakaninsu, daga wadda za'aja ja ma gashin kai sai wadda aka ca6e ma kwalliyar fuskarta, Mubeen dake a zaune yana kallon su sai faman tikar dariya yakeyi
Duk wannan budurin da sukeyi salsabeel bai sani ba, Yana atsaye bakin kofar toilet din dakin su khadeeja, ba irin bugun kofar da baiyi mata ba akan ta fito, amma taƙi ko tanka mashi.
Rai a6ace yace"wallahi idan kika bari nasa kafa nabar dakin nan sai dai ki zauna agida, Babu inda zaki je" muryarta da shesshekar kuka tace"wayyo Allah ya salsabeel ba kaine kace zamuje gasar kyau ba, shine fa nakeso in koma fara" waro ido waje yai jin soki burutsin ta, cike da takaici ya furta"Baki da hankali ne? Tayaya za'ai ki koma fara? Waya fada maki sai farare suke cin gasar kyau? to bari ki ji in fada maki bakake sune suka fi lashe gasar" muryarta da shagwa6a tace"ni dai Allah ba wani nan wayo kakeso kai min don kada inci"
Dafe kanshi yai da hannu ɗaya"ke zaki fito ko ba zaki fito ba" shiru tayi bata tanka masa ba,
Buga kofar yai da karfi"Khadeeja ranki zai 6ace in baki fito ba" still bata tanka mashi ba
Banko kofar dakin akay, Mubeen ne ya fado ciki kamar an wurgo shi, Rigar shi duk ta 6ace da jan bakin su rubina
A ruɗe salsabeel ke kallon shi Yama rasa ta ina zai fara
"Yaya salsabeel, Kaga su rubina sun 6ata min kayana da jan bakinsu, kawai saboda nayi masu dariya suna fada" bai karasa sauraren shi ba yai saurin fucewa da sauri mubeen Yabi bayan shi tunkafin Ya sauko down Ya hango su manne da juna, sun kacame kamar irin kifin gwangwanin nan sai ihu suke Yi,
Wata irin tsawa mai sauti Ya daka masu a firgice suka saki junansu, suna ganin shi suka fara kokarin bare baki zasuyi kuka
Nuna su yai da yatsan hannun shi"kar wadda ta kuskura tayi min kuka" ya fada yana zare masu idanun shi da alama ranshi ya 6aci, Yaji haushin yadda suka 6ata kayan su, abu tun karfe kusan tara na safe ake ta fama yaki ci yaki cinyewa
Sam yakasa yi masu fada, baisan meyasa yake jin nauyin ya furta masu kalma mara dadi ba.
"Yanzu abun da ku kayi kun kyauta"? Sunnar dakai kasa sukai har suna hada baki wurin fadin"dan Allah ka yi hakuri ba zamu kara ba" ta6e baki yai" a haka zamu tafi,tun da kunfi son aganku a haukacen ku"
"Ya salsabeel dan Allah kabari mu canza wasu kayan," harara ya watsa masu, rai a6ace Ya kama hanyar fuce wa daga falon Yana Fadin"ni na tafi sai kun taho"
Watsawa su ka yi aguje suka nufi bedrooms dinsu, Jim kadan suka fito har sun canza kayan jikin su..
Salsabeel Yana atsaye gaban motocin da za su shiga,, Jami'in da zaiyi driving din su Har Ya hallara a mazaunin driver, da gudun gaske khadeeja ta fito hannun ta ruke da takalmanta, har tana bangaje Su Yasmin, kamar a filin Yaki, gaba daya hankalin Jami'an dake tsaron gidan sai da ya dawo kanta, wani burgujejen wando tasanya yadda kasan kafafuwan agwagwa, ga wata yar yaloluwar riga mai hannu daya, Ta dambara jan baki akan la66anta har saman kumatuntu, mascara din data sanyawa eye lashes dinta ya zazzago har kasan idanunta, babu wanda bai firgita da ganin ta ba, Jami'an sai faman kunshe dariya suke yi a bakunansu, ko mayafi babu akanta sai wannan guntun gashin kan nata mai ɗan yawa data fake shi da ribbom Ya karkarce gefe ɗaya.
Ko ta kansu bata bi, Tana isa bakin motar, ta jefa takalmanta cikin car window, kafin ta daddage ta kama glass din Ta zura kanta aciki ta soma kiciniyar kutsawa ta karfi, dafe kai salsabeel yay da hannu ɗaya tamkar zai fashe da kuka, ya ma rasa me zaiyi, su rubina duk sun bude bakunansu asake suna kallon ta.
A hanzarce Ya cafko kafafuwanta, Ya zarota daga tagar, tana ta faman haki ta dube shi idanuwan nan nata kamar na babie sai kyaf kyafta su takeyi
_"Ya salsabeel baka ce nayi kyau ba" Cikin sanyi murya yace"kyawun ne ya ruɗe ni shiyasa nakasa magana" ya fada tare da bude mata murfin motar, ta shiga ciki ta zauna, Bayan kowan nan su Ya shiga, A jere suka fuce daga gidan kai tsaye suka haura kan titi_
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
Mu Haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da Lafiya
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE USNovels Elite
Home
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 19 Complete
by
Novels Elite Admin
June 15, 2024
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
____________________________________✍️
ANEELERH
Bakinta ɗauke da sallama ta shiga dakin abie, yana daga zaune gefen gadon shi sanye da farar jallabiya, idanunsa a manne da farin glass, yayin da hannun shi ke a ruƙe da kur'anin da yake karantawa, sai da yakai aya kafin ya ɗan ɗago yana dubanta tare da amsa mata sallamar da ta yi
A tsanake ta shiga ta zauna daga kasan gadon kusa da kafafuwan shi, cikin girmamawa ta gaishe da shi
Fuskar shi dauke da murnushi yace"oum junaid, kin tashi lafiya" sunnar da kanta kasa tayi fuskarta da murmushi tace"lafiyalou abie"
"Ina jikallan nawa? Maimakon ki tafo min da shi? ko dai rowar ɗan za'ay min ne" cike da jin kunyarshi tace"a'a abie, ni na isa in hana ka jikanka"
Murmushi yayi kafin ya Miƙa hannu ya ɗauko wayarsa dake ajiye kan side drawer ya miƙa mata
"Kar6i nan, Ki duba sakon da aka turo miki" da sauri ta sanya hannu ta kar6a, kafin ta ɗaura idanunta kan screen ta soma karanta sakon
_Assalamu Alaikum, barka da rana abie an wuni lafiya, ya iyali, ƙawar Aneelerh ce benazir matar tajudeen, Ina son yin magana da ita sai dai bani da contact dinta, dan Allah a hadani da ita, nagode sosai, ku huta lafiya__
Lokacin da ta kai ƙarshen Sakon Idanunta azare, baki a buɗe da tsantsar mamaki take kallon screen din wayar, sam takasa gasgata abun da aka rubuta mata, Muryarta ƙasa ƙasa take maimaita sunan Benazir Benazir!
Abie dake ta kallon ta, ganin tayi kasaƙe babu alamun zata motsa ne yasa shi yin gyran murya, kamar wadda aka zungura da sanda a ɗan firgice ta dube shi tana faman zare idanu
"Lafiya? Ko bakisan ta ba ne"?
Muryarta a harmutse tace"abie, na kasa yarda ne da abun da gani, wannan sakon da aka turo min daga benazir ne aminiyar nan tawa, matar da yau tsawon shekara goma sha wani abu da 6atan ta...." kafin ta ƙare maganar abie yace"kina nufin Benazir yar gidan Alhaji ubaid? Wannan ƙawar taki ta ƙuruciya" jinjina mashi kai tai alamar eh.
"To ki kira layinta mana sai ki ji idan itace da gaske" amsa mashi tayi da toh, da sauri ta miƙe ta fuce daga ɗakin a falo ta tsaya kafin ta danna call, jikin ta har kerma yakeyi tsabar zumudin taji idan banezir ce take neman ta. ......
*DAULAR ALHAJI MUSA*
Gaba ɗayan su sun Hallara a kan dining chairs, Tani da lami ne suke dawainiyar yin serving din su, an shake masu table da lafiyayyan abincin breakfast.
Tun da suka zauna babu mai magana acikin su, zeenatu da benazir abayane a jikin su, sun daure kansu da head scarp, yayin da Hajiya sarah ta sanya fitted gown ta atampa, kayan sun bi shape din jikinta, sam babu ɗankwali akanta sai zallar gashin kanta da ya sauko har kan kafadarta, mom layla ma atampar ce ta sanya, Alhaji Ubaid da shureim jallabiya ne a jikin su, Alhaji musa ne kadai ya ɗauki wankan tsadaddiyar shadda launin blue sky, kayan sun zauna mashi abunka ga namijin duniya, yayi kyau sai dai babu annuri akan fuskarshi kamar kullum Ya haɗe rai kai kace bai ta6a murmushi ba, tsabar yadda ya ɗaure fuskarshi yana faman shan kamshi kamar wanda iska ke yi ma wari.
Abinci yake ci kamar baisan tauna shi, hajiya layla dake kallon shi ji take kamar ta shaƙe shi saboda haushin shi da take ji.
Dr shureim dake cin abinci a tsanake ranshi ne ya bashi cewar Ana kallon shi a hankali ya dago da idanunsa kai tsaye suka shiga cikin na zeenatu, murmushi ta sakar mashi tare da kashe mashi ido ɗaya, da ɗan mamaki akan fuskarshi Ya zaro mata ido da sauri ta sunnar dakai kasa tana cigaba da sakin murmushi, girgiza kanshi yayi kafin ya maida hankalinsa akan abunda Yake yi.
Gaba ɗaya Hankalin benazir baya atare da su, ta tasa plate din abinci agaba ta kasa ci saboda tunanin Yarinyar da ta kira ta a daren shekaran jira, tun washe garin jiya take ta kiran layin baya shiga hankalin ta yaƙi kwanciya.
"Benazir Lafiyar ki kuwa? ko wani abu na damunki ne? Tun dazu na lura dake kin kasa cin komai" cikin kulawa mom sarah tayi mata magana.
Sauke ajiyar zuciya tayi kafin tace"ba abunda ke damuna mommy, lafiyana qalou"
"Okey, ki fara cin abincin kada ya huce, ba lallai yai maki dadi ba"
Amsa mata tayi da toh
Spoon ta ɗauka ta soma cin abincin zuciyarta cike fal da tunanin Unaisah
Wayar dr shureim ce ta soma ringing daga cikin aljihunsa, Hannu ya zura ya curo ta yana duban me kiran nasa.
"Ka tsaya ka kammala cin abincin, Inya so daga baya sai ka yi picking call din"
Muryar Alhaji ubaid ce ta katse masa hanzarinta.
"Daddy, kira ne mai mahimmanci,"
"Shikenan je ka daga" mikewa yai a hanzarce yabar dining din
Tafiyarsa keda wuya Hajiya layla ta dubi Alhaji Ubaida dake a zaune gefenta tace"ya maganar da mukayi dakai jiya"?
Murmushi yadan saki Yana duban fuskar Alhaji musa Yace"ay na fada maki, Ki ƙara hakuri"
girgiza kai tayi"bazai yiwu ba, ni bazan cigaba da zama acikin gidan nan ba! Wannan ay abun kunyane ace muna zaune gidan kaninka....." maganar na dira kan kunnan Alhaji Musa Ya ajiye spoon din hannunsa, fuskarsa a murtuƙe Ya ke duban Hajiya layla, yasan tayi maganar ne don Yaji ta.
Gaba daya hankulansu mom sarah ya dawo kanta.
"dan Allah ki yi shiru ya isa haka! Muje ɗaki mu yi magana" galla masa harara tayi"wallahi babu inda zanje, ko na bika bai wuci ka bani hakuri ba, Ni nagaji da zama acikin gidan nan, gaba ɗaya a takure nake, Kai ko gudun surutun mutane ba ka yi? tsawon kwanaki kana zaune agidan kaninka tare da Iyalinka"?
Hankali atashe mom sarah tace"dan Allah kiyi hakuri, mu kammala cin abincin sai muyi magana...." kafin ta ƙare maganar Alhaji musa Ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu tuni taja baki tayi shiru.
Jikin zeenatu harya fara yin kerma saboda batason tashin hankali arayuwarta, abun kaɗan ke rikitata, ita dai benazir ba ta ce komai ba ta zuba ido tana kallom mommyn nasu dake ta faman tada jijiyoyin wuya.
A gadarance Alhaji Musa Yace"Bana son haniya"
Harara ta watsa mashi"ay idan baka fita harkar mijina ba, hayaniya yanzu ka fara jin ta, wallahi bakaso zaman lafiya ba, akan me zaka dinga juya mutane son ranka sai kace wasu bayin ka, komai sai dai ka bada umarni abi, to wlh bazan lamunta ba! Hakuri na Ya ƙare, idan shi ka rufe masa baki to ni baka isa kayi galaba akaina ba!" ta fada tare dakai hannu ta bugi gaban table da karfi, kafin ta yunkura ta mike tare da kallon Alhaji ubaid.
"Ni zan tafi, tun da naga kai baka da niyar barin gidan," mayar da dubanta tayi ga benazir"tashi mu tafi" jiki asanyaye benazir ta miƙe, nan take zeenatu ta fashe da kuka tana fadin"Inna lillahi mom layla dan Allah kada ku tafi, wallahi banso, mommy kada ki bari su tafi, daddy kace masu su su yi haƙuri su zauna, ko kuma su tafi da ni" Hankalin Tani dana lami ba karamin tashi yayi ba, ganin rikicin dake shirin 6allewa.
Wani irin tausayin ta ne ya kama benazir sam batason ta rabu da yarinyar sai dai ba yadda zatai dole tabi umarnin mahaifiyarta.
Da sauri Alhaji Ubaid Ya mike muryarshi da 6acin rai Yace"haba layla menene haka? Yanzu abun ki kai kin kyauta? Mutane suna zaman su lafiya kin tarwatsa masu farin cikin su"
Dakatar da shi Alhaji musa yai, Cike da isa Ya mike tare da kallon fuskar Hajiya layla dake huci.
"Ga hanya nan ki tafi, Allah Ya raka taki gona" bayan ya furta hakan Ya juya azafafe Ya nufi bedroom dinsa Yana shiga ya dauki wayarsa, Call Ya danna tana fara ringing akayi picking
Muryarsa akausashe Yace"kada ku bar kowa ya fita daga gidan nan Idan Har bani na baku umarni ba"!
On the other hand Muryar wani basamuden mutun ta amsa mashi da cewa "Angama Yalla6ai" sauke wayar yayi
"Haba dear, why ba zaka bari su tafi ba, na fa ji kiran wayar da kayi, meyasa zaka rike su? Tun da matar nan ta nuna bata son tafiya to ka ƙyale su su tafi mana," muryar mom sarah a kule tayi maganar tana duban bayan shi...
Tamkar tayi magana da bango, babu alamun zai juyo ya fuskance ta balle harya amsa mata, Rai a6ace ta dawo ta gaban shi ta tsaya idanunta cike tab da kwalla ta furta"magana fa nake yi maka....."
da buɗar bakinsa sai cewa yai"Toh Uwata Ina sauraron ki" ya fada yana ruƙe qugunsa, Idanunsa akan fuskarta, bata san ya akai ta tsinci kanta da jin shakkarshi, sam takasa cigaba da yin maganar.
Gefen wuyanta ya shafa da tafin hannun sa"sau nawa zan ja maki kunne akan ki daina shiga abun da ya shafi dangina!" cikin sanyin murya tace"bazan ƙara ba"
Jinjina kanshi yai, kafin ya ƙara furta wata maganar, Muryar zeenatu ta karaɗe kunnan su.
Shigowarta kenan dakin ko sallama babu, Muryarta da shesshekar Kuka take fadin"daddy dan Allah kada ka bari su tafi, ni ban gaji da ganin su ba, ko kuma ka bari na bi su mu tafi a tare"
Juyawa yayi tare da daura idonsa akan ta, fuskarta tayi jawur hawaye na sintiri kan kuncinta.
Miƙa mata hannu yai da sauri ta nufe shi, hugging dinta yai tare da ɗaura hannunsa kan bayanta yana dan bubbuga shi cikin sigar lallashi.
"Ya isa, Ki daina kuka My daughter, ko dan saboda ke bazan bari su tafi ba, dolensu ne su zauna gidan nan ko suna so ko basa so" sauke ajiyar zuciya zeenatu tayi jin abunda yace, Hankalin ta ba karamin kwanciya yai ba, Hajiya Sarah ta kasa furta komai, Jikin ta yai mugun sanyi musamman yadda Taji Alhaji musa Yana magana da gadara babu ɗa'a a kalamansa....
A fusace Layla Ta nufi dakin ta, bayan tace da benazir taje ta haɗo kayanta su tafi, bin bayan ta Alhaji ubaid yayi kamar zai rufeta da bugu sai faɗa yake yi mata, Ko kallo bata isheshi ba, trolley din kayanta ta ɗauko Ta fara kwashe kayanta dake a cikin closet tana jerawa a akwatin.
Dawowa dr shureim yayi aɗan rude yake kallon dining din ganin babu kowa, da sauri Ya nufi dakin Benazir Yana shiga ya sameta, zuƙunne gefen gadon ta tana kuka, ga trolley din kayanta da ta gama haɗawa.
a ruɗe ya furta Benazir? Lafiya? Meya faru naga hawaye akan fuskarki"?
Jiki asanyaye ta mike tare da kallon shi, fuskarta tayi jawur da ita.
"Yaya shureim bayan kaje amsa kira, mommy ta fara faɗa akan ita bazata cigaba da zama gidan nan ba, shine tace min inzo in hada kayana mu tafi, ni kuma bana son tafiya saboda ban cimma burina ba, na ganin na haɗu da Aneelerh...."
Share mata hawayen ta ya somayi da hannayensa cikin sigar lallashi Yace"kiyi hakuri ki daina zubar da hawayen ki, bana so kina sanya damuwa aranki, amma ni kaina na goyi bayan ku tafi benazir! Ko dan saboda abunda ke faruwa dake agidan nan, Ina jin tsoron na rasa ki, kwata kwata hankalina bai kwanta da zamanki ba'
"Yaya shureim idan na tafi tayaya zan haɗu da Aneelerh"?
Harya buɗe baki zaiyi magana, kwatsam Wayarsa ta fara ringing, a hanzarce Ya duba sunan mai kiran nashi, wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskarshi, arude benazir tace yaya shureim lafiya naga kana murmushi"
"Alhamdulillah, Kiran da muke ta jira ne sai yau Allah Ya nufa zamu gana da su, kar6i kuyi magana, abban Aneelerh ne Yake Kiranki...." Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin picking call din kamar zata zauce tsabar murna
Muryarta da zumuɗi ta furta"Assalamu alaikum Abie Ina kwana...."
Kafin ta ƙare maganar unexpected Muryar Aneelerh ta ratsa kunnanta da wani sauti mai karfi ta furta"BENAZIR!! Mafarki nake ko gaske"? Fashewa da kuka benazir tayi jin muryar aminiyarta da kunnuwanta sukai maraicin ji na tsawon shekaru.
Cikin shesshekar kuka tace"Wallahi nice Aneelerh, nice benazir din da kika sani..."
Kafin ta ƙare maganar, Itama Aneelerh ta fashe da matsanancin kuka tana fadin"Benazir baki kyauta ma kanki ba! Meyasa? Meyasa? Meyasa kika gudu na tsawon shekaru? Idan wani abu ke damunki ba zaki faɗa mana ba? Kinsan irin kunci da radadin da muka ji bayan tafiyarki? Kin kama hanya kin gudu kin bar jinjira acikin kwamin wanka, Da ranki da lafiyarki baki ta6a kira kinji awani hali Yarki take a ciki ba, wai dan Allah meyasa kikayi haka benazir meyasa.....?" kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya sarƙe makoshin ta.
Tsananin tausayin su ne Ya kama dr shureim, tun dazu yana atsaye yana kallon Banazir kuma yana sauraran komai da suke tattaunawa.
"Dan Allah Aneleerh Ki nutsu inyi maki bayani..." Aneelerh bata bari tayi mata bayanin ba rai a6ace tace"me zaki faɗa min benazir? Ni meyasa ma kika kirani ne? lokacin da yakamata ki kira baki kira ba sai yanzu da lokaci ya kure...." hankali atashe benazir ta ke sauraron ta idanunta sun kaɗa jawur da su la66anta na kerma ta furta"meyasa kikace haka"?
Ɗuff taji Aneelerh ta kashe kiran, hawaye na sintiri ta dago tana kallon shureim wanda tuni jikin shi ya gama yin sanyi.
"Yaya shureim ta kashe kiran, dama nasani ba lallai ta kula ni ba..." tsananin tausayinta ne Ya kama shi, hannu yasa ya kar6i wayar, Ya sake Kiran Aneelerh taƙi ɗagowa.
Text message Ya tura mata
_Aneelerh ki ɗaga kiran, Ba benazir bace yayanta dr shureim ne Ina son Yin magana dake_
A 6angaren Aneelerh, Jiki amace ta sulale kan carpet ta zauna dirshan sai kuka takeyi, bakomai take tunawa ba face Angel da tajuddeen, Taji takaicin yadda Benazir tayi watsi da rayuwarsu gashi Yanzu ita benazir din ta dawo su kuma sun 6ata babu su a doron duniya
Muryar Angel ta soma tariyowa kalaman da saba fada mata tuntana yar ƙanƙanuwarta
_Aunty aneelerh wai meyasa Mommyna bataso na? gani yar kyakkyawa dani kowa rububina yakeyi amma ita, bata damu dani ba, shine ma ta haifeni ta bar ni acikin kwamin ka, idan bata sona to meyasa ta haife ni ay da ta sani ta kashe ni acikin ta_
Ƙarar shigowar sakon ne Ya fargar da ita daga zurfin tunanin da ta shiga, zuciyartace ta dinga tunzurata akan kada ta duba wayar ta ƙyale ta kawai, saboda ta bata haushi, Taji zafin abunda tayi.
Wayar sai ringing takeyi taki dubawa, kasa jurewa tayi, saboda ita kanta tayi kewar aminiyartata, bazata taba mantawa da ƙawancensu ba, duk da taci wahalar banezir saboda rashin jin maganarta.
Yatsun hannunta na kerma ta ruƙo wayar ta duba sakon, bayan ta gama karantawa, a kagare ta soma kokarin bin kiran don taji me dr shureim zai faɗa mata, aranta tana mai mamakin bayyanarsu lokaci ɗaya.
Video Call ta kirasu don ta ƙara tabbar da cewa su dinne, bayan sunyi picking call din kallon kallon suka soma jefawa junansu, kowa yasha kuka, hakika sunyi mamakin canzawar da sukayi, duk sun fara manyanta...
Cikin sanyin murya ta furta"ya shureim! Dama kana nan"!
Jinjina mata kai yai alamar eh, kafin Ya soma magana cikin nutsastsiyar muryar shi.
"Aneelerh, inaso ki nutsu ki saurari abun da zan fada maki" amsa mashi tayi da toh, saboda tana ganin girma dr shureim.
"Abun da Ya faru da banezir bayin kanta bane, mu kanmu bamu san da hakan ba sai lokacin da ta dawo, bata a cikin hayyacinta gaba ɗaya alamomin da muka gani ajikinta ya tabbatar mana da cewa Kurciya akayi mata, shiyasa ta gudu tabar yarinyarta batare data tuntu6i kowa nata ba......" atsanake shureim ya fayyace mata komai, Ita kanta benazir din batasan da abun da suke zargin anyi mata ba sai yanzu da taji abakin dr shureim, hankalinta ba karamin tashi yayi ba, aneelerh kuwa jikinta yagama mutuwa, cikin tashin hankali take ambaton inna lillahi wa'inna ilahirraji'un.
Dr shureim Yace"hakuri zamuyi da abunda Ya riga ya faru, bana so muna tuna ba....." nasiha ya cigaba dayi masu har saida Yaga hankalin su Ya kwanta, kafin Ya bar wayar a hannun benazir Ya basu wuri don su gana da junansu
Kamar yau ce rana ta farko da suka fara haɗuwa, sai bin kansu suke yi da kallon kurulla, Allah ne kaɗai Yasan irin kewar juna da su ka yi.
"Benazir bansan yadda zan misalta maki farin cikin da nake a ciki ba, Allah shine shaidata, Naji dadin ganinki da ranki da lafiyarki"
Cikin sanyin murya tace"nima haka Aneeleerh, ashe da rabon zamu gana bayan tsawon lokaci"? Ta fada tana matse kwallar da ta cike idununta.
"Aneelerh, Ina Yarinyata dana bari? Ina mijina Yake? Mommy ta fada min basa kasar nan amma ni ban yarda da maganarta ba, dan Allah ki fada min gaskiya, saboda nasan ke kadaice zaki fada min"
Fuskar Aneelerhh ɗauke da matsananciyar damuwa take kallon benazir dama sai da tayi fargaban tambayar da zatai mata, tuni taji zafafan hawaye sun cika mata idanunta.
"Aneelerh kinyi shiru baki ce komai ba? Pls ki yi min magana wlh ji nake kamar zan zauce saboda ƙagarar da nayi na son ganin su ..." ta faɗa tana dubanta
"Kada ki ji komai, Ki faɗamin kawai ko da ace sun mutune zan rungumi ƙaddara..." cikin karfin hali ta faɗa, tun da tafara maganar Aneeleeh ke kallonta gwanin ban tausayi.
bata jin zata Iya sanar da ita a yanzu, ko dan gudun kada zuciyarta ta buga, ƙwara ta kwantar mata da hankalin ta.
Ƙaƙaro murmushi tayi akan fuskarta
"Abun da mami ta faɗa maki gaskiya ne, suna nan cikin koshin lafiya, sun yi tafiya zuwa south korea inda Uncle dinsa abdalla ke zaune, amma ina ji araina sun kusa dawowa"
Tsabar farin ciki yasa banezir sakin dariya har fararen hakoranta suka bayyana, Aneelerh dake kallonta tsantsar tausayintane Ya ƙara kamata.
"Dan Allah Aneelerh idan kina da hotonta ki turomin inason ganinta, Idan ma kina da number taj din ki bani sai muyi magana da shi, wlh naƙagara da son ganin su"
Murmushi Aneelerh tayi"kada ki damu zan tura maki da hotonta har ma dana yaro na, sai dai bani da layin taj bansan da wanne yake amfani acan kasar ba"
Da mamaki tace"Aneeleerh dagaske kin haihu? Ya'yan ki nawa yanzu"?
"Shi kadai Allah Ya bani, baki ganshi ba, kyakkyawa kamar Angel dinki.."
Muryarta na rawa tace"Allah sarki, Aneeleeh, na tayaki murna, Ina mijin ki ko shima hada shi suka tafi korean"?
"Atare suka tafi" murmushi benazir tayi kafin ta kuma cewa"ki bani labarin Yarinyata, inason jin kuruciyarta, Ina fata dai bata dauko halina ba.." dariya aneelerh tayi da zolaya tace"like mother like daughter, Har tafi ki rashin ji magana," waro idanu banazir tayi hada sanye hannu ta dafe kanta ɗaya"indai kuwa hakane nasan ba lallai ta yi min da sauki ba, watakil ma ta tsane ni, bata son ganina" ta fada tamkar zata fashe da kuka
"Ki ma daina wannan tunanin, taya ɗa zai ƙi jinin uwarsa, ay bata da abu mafi soyuwa da yawuce mahaifiyarta, ni nasan Angel bazata ta6a gudunki ba"
kwantar mata da hankali taci gaba dayi, har ta bata labarin unaisah, taci dariya wani wurin kuma ta matse kwalla.
"Allah sarki tajudden na barshi da dawainiyar yarinya, abunda yakamata ace ni nayi bansamu damar yi ba..." in a cool voice tayi maganar," shiru suka danyi na wani lokaci kafin Aneelerh tace"Har yau babu labarin Aisha! Baiwar Allah taga rayuwa, gaba daya ƙaddarace ke bibiyar rayuwarmu lokaci ɗaya ƙawancenmu ya tarwatse nayi takaicin rasa farin cikin amintarmu' hawayen dake taruwa acikin idanunta tuni sun fara wanke fuskarta....
Shiru banezir tayi zuciyarta cike fal da jimamin halin da suka tsinci rayuwarsu.
"Inaso nazo gidanku Aneelerh, ki kirani da layinki, sai inyi saving contact naki" amsa mata tayi da toh, sunjima suna waya kafin sukayi sallama da junansu..
Meya faru bayan Ummi Ta fuce daga dakin su Unaisah?
Da gudu ta nufi dakinta, tana shiga ta bude toilet ta tsaya agaban Sink tana kwarara amai, idanunta sun kada jawur da su, shatun jijiyoyin goshinta sun fito rudu rudu kamar zasu fasa fatarta, tayi kuka tamkar ranta zai bar gangar jikin ta, komai na duniyar nan ya sire mata, taji takaici da tsanar rayuwar da ta daukarwa kanta saboda takasa hakuri ta rungumi ƙaddarar ta, Sai gashi yau taji abunda Ya jefata adanasani, Yan kananun Yara da basu ji ba basu gani ba, wadannan ma tun suna jarirai suke fuskantar jarabawar rayuwa, Ita kuwa da ilminta da hankalin ta da tunaninta ta faɗa harkar karuwanci saboda ta kasa cinye jarabawarta lamarin yayi matukar gigita tunaninta...
Faucet ta kunna ruwa ya soma shararowa ta tarfa hannu tana watsa shi akan fuskarta, kamar an zare mata karsashin jikinta, da wata irin kasala ta fito jiki babu ƙwari ta faɗa kan gadonta tare da kifa kanta jikin pillow, bakomai take tariyowa ba face rayuwarta ta baya...
Sam ba taji motsin shigowar mutun ba, saboda ta lulu duniyar tunani
A hankali batool take tafiya tana tunkarar gadonta, hayewa tayi kan gadon ta zauna kusa da ummi tana leƙen fuskarta
"Aunty Ummi," kamar daga sama taji muryar batool, a hankali ta buɗe idanunta da suka kumbura ta daura su kan fuska batool.
"Dan Allah ki daina kuka aunty ummi, bana son ganin hawayen ki, bana jin dadi" ta fada muryarta na rawa alamar zata fashe da kuka.
Janyota ummi tayi tare da kwantar da ita kan kirjinta, sosai ta rungumeta ta daura hannunta akan bayanta batare data furta magana ba.
Aranta tana mai mamakin tawakkalli irin Na Yaran, abunne da daure kai, da ace wani mai karancin imanin ne hakan ta faru da shi da tuni yajima da hadiyar zuciya ya mutu amma su a haka suka jure da dadi da ba dadi sukai ta rayuwar ƙunci a kulle tun kafin su mallaki hankalin su.
Numfashi taja, wani irin kaunar yarance taji ta ƙara kama zuciyarta, har ta fara tunanin tawace hanya zata taimaka masu don ganin sun inganta rayuwarsu tun da basu san komai ba .
Bakomai ne ya fado mata aranta ba face zagin da ta ta6a yima batool har ta kirata da sunan jahila wadda bata san komai ba sai ci da bacci... Runtse idanunta tayi sosai tana mai jin takaicin kalaman da ta furta mata, gashi yanzu yarinyar tafi kowa kaunarta
Shafa sumar kan batool taci gaba dayi kafin wani lokaci bacci yai awon gaba dasu arungume da juna kamar zasu dawwama ahaka.......💔
___________________________________✍️
*❤Unaisah Angel💋💝*
Fitowa tayi daga part dinsa bayan ta gama gyara masa shi, A hankali take saukowa down daga kan stairs zuciyarta cike fal da tunanin abubuwa da dama wadanda suka faranta mata rai a yau kamar wata zautacciya sai faman sakin murmushi take yi.
"Daughter i'm back" miryar taj ce ta katse mata zancen zucin nata, kallon shi tayi fuskarta da fara'a, da sauri ta karasa sauko down, mayafin kanta har yana kwancewa daga kanta ya zame ya faɗo kan kafadarta, sumar kanta ta rufa mata bayanta.
Tana ƙarasawa ta fada kan kirjinshi kamar wadanda suka dade basu ga juna ba.
Murmushi yasaki yana fadin"sannu da kokari ina fata kin yi abun da Ya dace"
ɗagowa tayi da kanta ta daura idanunta akan nashi"har gyara masa part din sa nayi, kafin ma na kammala har ya fita ban same shi ba"
"May be ya tafi gidan kakansa ne" acewar chief,
"Kinsan me naje yi agida" girgiza mashi kai tayi alamar a'a.
"Auntynki na faɗa mawa ta hada maki wani abu mai dadin gaske zuwa anjima zatay baƙuwa, amma fa ban gaya mata wacece zata zo ba"
"Naji dadi daddy, kana ji dani"
Mayafin ta dake akan kafadarta ya ruko yana fadin"bari na gyara maki shi" A hankali Ya soma naɗa mata shi, bayan ya kammala ya manna mata sumbata kan kuncin ta kafin ya ɗago da kansa
kwatsam! Ba zato ba tsammani Yaji saukar dundu akan bayanshi tamkar za'a rusa shi, tsabar zafin da yaji ne yasa shi saurin dafe bayan da hannu, tuni ya fara ganin jiri a cikin idanunsa.
Hankalin ta amatuƙar tashi ta wurga idanunta don ganin wane yayi wannan aika aikar saboda itama taji sautin dundun da akayi mashi.
Har saida gabanta Ya faɗi lokacin da tayi arba da shi atsaye yana huci tamkar mayunwacin zaki, tsabar fusata jikin shi har gumi yake fitarwa, magana yakeso yayi amma saboda zafin da zuciyarshi keyi mashi ya kasa sai la66ansa dake kerma.
Harara ta watsa mashi saboda ya bata haushi, zuciyarta ajagule ta ruƙo hannun taj Tana fadin"Inna lillahi! daddy dan Allah kayi hakuri..."_ bata ƙare maganar ba, danish Ya fusgo ta tare da janyota jikin shi, yasa hannu biyu ya rungumeta kamar zai maida ta cikinsa
Lamarin yayi matuƙar ɗaurewa taj kai, idanunsa jawur yake kallon danish Yama rasa me zaiyi, amma tabbas dundun da yayi masa ya kusa yi mashi illa saboda zogin da bayansa keyi mashi kamar an ɗoɗana masa wuta yadda kasan ba hannun mutun bane yayi dundun, yaji zafinsa sosai.
Kiciniyar kwace kanta tafara yi hawaye tuni sun wanke fuskarta ganin baida alamun sakinta ne yasa ta daddage ta gartsa mashi cizo kan kirjinsa, ko gizau baiyi ba, saima ya kara hadeta da jikin shi, zuciyarta har tafarfasa take yi mata saboda 6acin rai.
Kallon kallon suke jefawa junansu tsakanin shi da tajuddeen, kwata kwata bai yi yunƙurin Janye angel daga jikin danish ba, saboda ya fahinci Yaron ba shi kadai bane tun daga kan dundun da yayi mashi ya shaida hakan.
Shigowo Falon big guy da ɗan saurinsa Yana ganinsu Ya nufe su da mamaki Yake kallon Danish daya rungume unaisah
"Lafiya? Meke farune"?
Taj ne yai karfin halin fada masa abun da danish yayi masa
Zuciyarshi ta sosu Harara Ya watsa masa kafin Yace"Sakar ta, tun kafin na 6ata maka rai, kaida bawani koshin lafiya ba har ka fara neman rigima? Ko kunya baka ji ba ka rungume Yarinya gaban ubanta! Idan ma baka sani ba to bari na fada maka wannan da kake gani mahaifinta ne wanda Yai silar zuwanta duniya...." ko ajikinsa bai ma fahimci me Big guy yake nufi ba, sai ma haushin shi da yake ji, Jira yake big guy yakai hannu zai raba shi da ita anan ne zaiga ainihin true colour dinsa...
Atsawace big guy yace"baka ji me nace ba, ka sake mana"!
"Ka daina yi mashi tsawa, Ka kyale shi kawai, nayi mashi uziri saboda baisan komai ba, kuma Yaro ne sai muna lalla6a shi"
Big guy bai tsaya sauraron Taj ba Ya kai hannu zai ja rigar unaisah, wata irin kururuwar tsawa danish Ya daka mashi tamkar saukar aradu, Gaba ɗaya saida suka firgita saboda Yadda sautinta Ya cika masu kunnuwan su, Unaisah dake manne ajikinshi tsabar kiɗima kiris Ya rage ta saki fitsari a wando, saboda firgitar da tayi.
idanunsa sun kaɗa jawur Yana huci Ya furta"kada ka kuskura ka ta6aba, Ranka zai 6aci, zanyi maka abun da baka ta6a tsammani ba, Idan har kayi gigin shiga tsakanina da ita...." ya faɗa yana faman cije red lips dinsa, yadda kasan ba daga bakinsa kalaman suka fito ba saboda girman su.
da gudun gaske Naufal da Sajeed suka fito daga dakunansu, kamar wadanda aka koro tun wannan tsawar da danish ya kwatsa kowan nan su Ya firgita har wadanda ke adaki, kai hatta Ummi da batool sai da suka farka daga bacci jiki na 6ari suka sauko down stairs, ɗaya bayan ɗaya suke fitowa ƙwansu da kwarkwatarsu, hankalinsu gaba daya yana akan Daninsh dake a rungume da unaisah, jikinta sai kerma yakeyi duk tabi ta ruɗe, numfashinta kanshi dakyar take fidda shi.
Kusan atare suka hada baki suna tambayar meya faru? danish dan Allah kayi mana bayani meyasa ka ruke Unaisah ka sake mana ka matseta.. Sajeed ne yai maganar,
Big guy daya gama harzuƙa Har Ya yunkura zai Ƙara kamo rigarta Taj yai saurin damƙar damtsen hannun shi, suka hada ido da juna girgiza mashi kai yai alamar a'a saboda shi yasan mai yaji dakyar in ba sai yayi jinyar bayansa ba.
"Haka zamu zuba mashi ido muna kallon shi? Baka ga yadda Ya matse ta bane? Ko magana takasayi"!
Cikin muryar lallashi Taj Ya dubi Danish dake ta faman zare idanunsa tsabar masifa har ƙanƙance su yakeyi
"Dan Allah kayi hakuri ka sake ta, indai saboda ni ne bazan ƙara taba maka ita ba" Mamaki da al'ajabine Ya kama su Ummi dake kallon Ikon Allah
"Meyasa zaka bashi hakuri? Kaida ƴarka? Tsoron shi kake ji ne"? A harzuke Big guy yai maganar
Taj yace'ba tsoron shi nake ba, fitina ke bana so, idan mukace zamu bi ta karfi da yaji donmu kar6e ta wlh ba zamu iya ba sai dai muja yai mata wata illar kwara mu lalla6a shi' guntun tsoki Big guy yaja, gaba daya haushin danish Ya cika shi, duk da yana tausayin prisoners sai dai ayanzu lamarin danish Ya fara sanya shi kokwanto akansa, gani yake kamar yaron yana da wata muguwar manufa.
Haduwa su Naufal sukayi suna ta yi mashi magiya don Ya sake ta, Amma Ya ƙi sakinta
Suna acikin wannan Halin, a lokacin da basu yi tsammani ba, Sallamar Salsabeel Ta katse su, gaba ɗaya suka dago suna Kallon shi
Ganin shi yasa danish sakin Unaisah tai taga taga zata faɗi da sauri batool ta ruƙota, sai faman haki takeyi tana sauke ajiyar zuciya kamar wadda tasha gudu....
Sunyi tunanin shi kadaine Yazo, kusan atare muryoyinsu khadeeja Ya daki kunnuwansu, tunkafin su karasa shigowa suka fara kokarin tunano su wanene? Saboda sun haddace muryarsu ko tari sukayi za su iya sheda su.
Ɗaya bayan ɗaya suka fara Shigowa bakunansu dauke da sallama, Lokaci ɗaya suka Ci burki suna Kallon su Unaisah dake kallon su, kusan atare zuciyoyinsu ke harbawa da matsanancin karfi, Tsabar rudani da al'ajabi Ya hana su gasgata abunda idanuwansu suke nuna masu, har abada ba zasu ta6a mantawa da muryoyin yan uwansu ba, balle kuma kamannin su da basu ta6a gogewa a idanunsu ba, Kokwanto sukeyi anya kuwa yan uwan sune da suka baro prison ba rai? Ko dai mafarki sukeyi ne? Ko kuwa idanunsu ne suke nuna masu badai dai ba? Tayaya ma haka zata yiwu?
Murza idanunsu suka farayi don su kara tabbatarwa da kansu abun da suke gani dagaske ne ko akasin hakan!
Kamar yadda suke al'jabin ganin su haka suma su Rubina suke kallon su da matuƙar ruɗani akan fuskokin su, babu mai magana acikinsu falon yayi tsit kamar mutuwa ta gifta, har na tsawon mintuna kafin salsabeel Ya fara magana
"Abun da kuke tunani dagaske ne, Ku daina kokwanto, wadannan da ku ke gani ƴan uwanku ne, da kuka baro agidan kurkukun ƙaddara, ni kuma sunana salsabeel ɗan tsohuwa tamira, nasan ba lallai ku shaida kamanni na ba, amma ita Unaisah ta gane ni...." fuskar shi dauke da murmushi ya yi maganar, har lokacin babu wanda ya motsa daga cikin su kamar gumaka, tsantsar tsabar rudani da mamaki ne Ya daure su har suka kasa magana, Hatta khadeeja da take da tabin hankali tayi kasaƙe tana bin su da kallo kamar tana so ta tuna su wanene su ...... .
"Tayaya ma haka zata yiwu? Ni fa nagaza gasgata abun da idanuna suke nuna min, Kaina Ya ƙulle dan Allah ku fahimtar dani, ni dai a iya sanina kafin mu baro gidan kurkukun ƙaddarar amace muka barsu yanzu kuma sai mu gan su da ransu da lafiyar su? dama wanda Ya mutu Yana dawowa ne"? Sajeed ne Ya faɗa fuskarshi da alamun ruɗani
Salsabeel Ya fahimci halin da kowan nan su Ya shiga, In har ba faɗa masu ainihin abunda ya faru yayi ba, toh zaiyi wuya su yarda da bunda suke gani, cikin sanyin murya ya fara ba su labarin abun da ya faru bayan barin su gidan kurkukun ƙaddara......
Waiwaye adon tafiya
Tayaya akai Salsabeel tare da su khadeeja suka ku6uta daga gidan kurkukun ƙaddara!? Bayan a iya sanin mu su deeja sun mutu sakamakon zuciyarsu da ta buga❓❓❓
Bari mu koma baya don jin meya faru?
Suna shiga Cikin Toilet ɗin, Danish Ya datse ƙofar da sihirin shi, ya Janye tukunyar fulawar daga kan ƙofar, nan ta ke ta bayyana duk irin wahalar da suka sha ta ƙi buɗewa shi Bugu ɗaya yayi mata gaba ɗaya ta 6alle murfin ƙarfen ya dare biyu, Sun yi mamaki da al’ajabi yace da su”Ba zai bi su ba, zai tafi da Akwatin kayan su tare da back pack ɗin su, za su tarar dashi a bakin ƙofar da zasu 6ula idan sun ƙarasa” hankalin su bai kwanta da maganar shi ba, gani su ke yi kamar wani mummunan abun zai faru da su idan baya atare da su, ganin sun toge sunƙi tafiya yasa shi Kwantar masu da hankali, daƙyar ya samu su ka Zuƙunna ƙasa tare da kutsa kai ɗaya bayan ɗaya su ke shiga cikin ƙofar da rarrafe, Bayin Allah ga yunwa ga ƙishin ruwa, ga raɗaɗin da zuciyarsu ke yi masu, Ita kanta hanyar da suka biyo Wata uwar ƙura ga yanar girgizo da ƙwari sai hawan masu jiki su ke yi, Amma saboda rashin kwanciyar hankali yasa basu damu da su ba. Babu mai magana acikinsu saboda ƙunar da ran su ke yi masu, Angel ce tai ƙoƙarin tunasar dasu akan suci gaba da ambaton addu’o’in data koya masu ko sun samu sassaucin a wurin Allah, sun ɗau ki shawararta ahaka suka Dinga tafiya da rarrafe babu ƙaƙƙautawa, idan suka gaji su kan ɗan zauna su huta kafin su dasa da wata tafiyar, A ƙalla sun shafe tsawon awanni Takwas suna rarrafawa ba tare da sun kawo ƙarshen Ƙofar ba, a takure su ke Bayin Allah sun ga rayuwa gwiwowin ƙaffuwan su duk sun gurje sun sage, maƙoshinsu ya bushe ƙamas, tun suna ambaton ƙishir ruwa suke ji har sun gaji sun yi shiru.........”😭
A tsugunne yake gaban gawar tsohuwa tamira, yayin da hawaye ke sintiri kan fuskarsa, idanunsa sun kaɗa jawur da su, zuciyarshi ta gama karaya, tamkar baya a cikin hayyacin shi, gaba ɗaya rayuwar duniyar ta sire mashi, duk sai yaji ya tsani kanshi, bai da wani buri daya wuce shima Ya mutu, sai dai baya son ya mutu batare daya gyara rayuwarsa ba, yana da burin wata rana yayi rayuwar yanci, kamar ko wani ɗan adam, yana son yayi sallah ya gana da ubangijinsa, Tun kafin Ya mallakin hankalinsa Rayuwarsa take a cikin gidan kurkukun ƙaddara cikin kunci da takaici, idanunsa sun jima suna gane masa bakin zaluncin da ake aikawata agidan kurkukun ƙaddara, babban takaicinsa mutuwar mahaifinsa tamira batare da ta cimma burinta ba na ganin ta kawo karshen zaluncin shuwagaban nin gidan kurkukun ƙaddara, bai ta6a tsammanin zata riga shi mutuwa ba, yaso ace yacika mata burinta sai dai kash ƙaddara ta riga fata......
Babban burinshi Su Unaisah su tsira da ransu ko dan su kai labarin gidan kurkukun ƙaddara saboda al'umma su san da zaman shi, ko an samu wadanda zasu yi shahada su kawo karahen zaluncin da ake aikatawa.....
Hawayen dake sauka kan kuncinsa a hankali suke ɗiɗɗiga saman gawar tsohuwa tamira....
Gaba ɗaya ya manta da lokacin shi da ke tafiya, sam ya shafa'a ya manta da zancen binne gawarsu da yace zaiyi saboda hankalinsa ya gushe.
Kwatsam yayi zurfi acikin tunaninsa, ba zato ba tsammani kamar daga sama Yajiyo sautin dirar wani abu mai matuƙar razanarwa, harta ginin dakin sai da ya girgiza, lokaci ɗaya ya zabura ya miƙe zuciyarshi na harbawa da karfi da karfi, tunkafin ma yaga menene ranshi ya bashi cewar Giants ne na gidan kurkukun ƙaddara, mutanan da babu ɗigon imani aransu, zuciyarsu tamkar dutse take, kurame ne kuma makafi ne basa ji basa gani umarnin Elders din su kadai suke bi.
Wani irin wahalallan Yawu salsabeel Ya hadiya mai ɗacin gaske, tuni zufa ta soma wanko mashi, gaba daya yabi ya zauce saboda bai da karfin da zai Iya ja da su, sunfi karfin shi nesa ba kusa ba.
Tsabar kidimar da yayi ce ta shi yin zarya a dakin tsohuwa a kokarinsa naya nemo hanyar da zai kubutar da gawawwakinsu gudun kada su wulakantasu ..
Kafin yayi wani yunkuri Ya soma jiyo takun tafiyarsu, A matuƙar firgice Yake kallon fadadan kafafuwansu.
Kusan su uku ne, Wasu irin gabza gabzan samudawa masu kirar Zakuna, kamar fatalwu haka suka fado dakin, from head to toe sun rufe jikinsu da bakaken kaya baka Iya ganin komai nasu.
_Yawu salsabeel Ya haɗiya, ta ko'ina zufa ce ke tsastsafo mashi ta cikin hudojin gashin fatarsa, muryarsa da tsantsar tashin hankali Ya furta"zanyi maku bayani...." bai ƙarasa maganar ba, Muryar wani basamude daga cikin su mai amon gaske Ya furta"Salsabeel ka yi kuskuren ƙetare iyakarka, ka riga da kasan hukuncin wanda Yaci amanar Elders! Sakamakon ka mutuwa ce, zakayi mummunar mutuwa salsabeel zamu kashe ka sannan mu watsa ma karnukan mu naman ka su cinye shi, bayan haka waɗannan ƙasƙantattun gawarwakin da ke a kwance zamu kwanta da su, idan muka gama biyan buƙatarmu da su, zamu cire sassan jikinsu muyi farfesu da su, Kasusuwan jikin su kuma zamu rataye su ne......_ 😳😳😳
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 20 Complete
by
Novels Elite Admin
June 20, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
_AUNTY XEE Thank you for being there for me. Your support has been a lifeline.💋💞_
__________________________E20✍️
Tashin hankalin da ba'a saka masa rana!, Idanunshi azazzare Yake duban su, jikinshi ya soma kakarwa, tsabar kiɗima zuciyarshi tamkar zata fasa ƙirjinshi saboda bugun da takeyi masa, bakomai ne yafi ɗaga masa hankali ya zautar dashi ba face kalmar zasu kwanta da gawawwakinsu, Inna lillahi wa'inna ilahirraji'un wannan wace irin musiba ce? Cikin karyayyar murya yace"Ni yakamata ku hukunta saboda ni nayi maku laifi, na roƙe ku ko dan sanayyar dake a tsakanina daku....."
Wata irin mahaukaciyar dariya suka tuntsire da ita jikinsu har jijjiga yakeyi kamar ana bugun ganguna, wani daga cikinsu ne ya kuma cewa"Ba sani, ba sabo a tsakanin mu, saboda ka tabka babban kuskure salsabeel ka yi ha'inci, don haka dole ka fuskanci hukunci mai tsanani daga gare mu"
Sunan Allah Ya ci gaba da ambato acikin zuciyarshi, duk addu'ar da tazo mashi yinta yakeyi ba ƙaƙƙautawa, har jaraba Yin amfani da sihirin shi yayi don ya ku6utar da kanshi da kuma Gawawwakin amma abun yaci tura, ƙarfin sihirin shi bai kai na su ba, sun riga da sun yi mashi mugun ɗauri na sihiri ba zai iya ta6uka komai ba.
Ja da baya ya soma yi ganin suna tunkaro shi, cikin matsanancin tashin hankali, kafin ya ƙurema bangon ɗakin tuni ɗaya daga cikinsu yai zazzafan taku ya damƙi wuyan salsabeel da kafcecen hannun shi, nan take numfashinsa ya soma ƙoƙarin ɗaukewa, ɗaga shi yai sama tun Yana kiciniyar ƙwace kanshi harya fara gazawa idanunsa sun kaɗa jawur sun fiffito waje, nan take ya soma bleeding ta baki ta hanci, wani irin raɗaɗin azaba ne Ya ziyarci salsabeel tamkar ana yi mashi ɗaskanan wuta a jikin shi, fuskarsa tayi jawur jini ya kwanta a fatarsa, hawaye da gudu suke kwararowa ta cikin idanunsa bakomai zuciyarshi ke tariyo mashi ba A lokacin face kalaman mahaifiyarsa Tamira, Idanunsa na akan gawarta.... Numfashinsa na kiciniyar ɗaukewa gaba ɗaya ya gama jigata har ya fidda rai da rayuwa, a lokacin da basuyi tsammani ba suka jiyo sautin dirar wani abu a bayansu, da sauri giant ɗin daya shaƙe wuyan salsabeel ya sake shi jiki ba ƙwari ya kife ƙasa kan shi Ya daki ƙasa daƙyar numfashin sa ke fita da hucin zafi, kusan atare Giants ɗin suka juya baya don ganin menene Ya faɗo cikin ɗakin da har Ya bada sautin mai kuwar gaske.
Da wani irin tsantsar Al'ajabi suke kallon shi, yadda kasan saukar aradu Haka Ya faɗo masu Yana huci kamar Mayunwacin Zaki, kwata kwata babu riga a jikin shi sai dogon wandon kakin Giant, jikin shi sai tsuma ya ke yi tsabar fusata, ta ko'ina zufar 6acin rai ce ta ke tsastsafo masa, harta tsokokin jikinsa motsi su ke yi, da wani irin hucin zafi numfashin sa ke fita.
Shin Wanene Wannan? To bakowa bane face GARKUWA, dalilin dayasa shi dawowa kurkukun saboda hankalin shi yaƙi kwanciya yasan mawuyacin abu ne Salsabeel ya samu fita daga cikin kurkukun tare da gawawwakin salin alin, ranshi na bashi cewar wani mugun abun zai iya faruwa da Salsabeel ɗin, shiyasa lokacin da su ka shiga cikin makewayin bayan ya buɗe ma su Angel kofa yaƙi bin su yace su fara yin gaba shi zai taho da Akwatin kayan su tare da back pack ɗin su, za su tarar dashi a bakin ƙofar da zasu 6ulla idan sun ƙarasa, yayi hakanne don ya samu damar dawowa ya taimaki rayuwar salsabeel saboda baya son ya rasa shi ko dan saboda halaccin da ya yi mashi a rayuwa bazai ta6a mantawa ba, yaji mutuwar tsohuwa Tamira don haka bazai bari rayuwar salsabeel ta salwanta ba❗
Kallon kallo su ka soma jefawa junan su tsakanin Giants da Garkuwa, wato gaba da gabanta, Aljani Ya taka wuta, banbancin Danish da sauran Giants shi ƙarfin sa Na Evil giants ne masu Star Uku kai ko a cikin su Ya zarce su Power, babban kuskuran da Elders sukayi shine damƙa amanarsu gare shi saboda ya zama garkuwarsu a duk lokacin da za'a kawo masu hari, ba su ta6a tsammanin garkuwarsu zai Iya cin amanarsu ba, shiyasa suka bashi sihirin da ya fi na kowani giant na gidan kurkukun ƙaddara, a halin yanzu babu mai iya karawa da shi sai Elders wato Leaders ɗin su, Danish Yana da kwatankwacin ƙarfin giants ɗari a jikin shi, baƙaƙen shaiɗanun dake a jikin shi wani irin ƙarfi ne da su na fitar shari'a, kuma basa ji basa gani umarnin shi kaɗai suke bi, hatta su kansu elders ba su isa su hana shaiɗanun bin umarninsa ba, kuma su sukayi kuskuren ɗaurashi akan turbar da yake ashe da rabon su yi danasani mai girman gaske,
Duk da Salsabeel baya acikin hayyacinshi Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, ganin Danish Ya dawo! Muryarshi na rawa ya furta "meyasa! Meyasa Danish? Meyasa ka dawo? Ina ka baro su Angel? Sautin muryarshi ko fita batayi shi kaɗai yake sambatun shi ba tare daya iya ɗagowa da kan shi ba, saboda raunatar da yayi.
Ɗaya daga cikin giant dinne Ya ambaci sunan shi"Garkuwarmu"! Yana huci Yace"Ni ba garkuwarku bane! Garkuwar su ne! idan har kuna son zama lafiya to ku ƙyale salsabeel da gawawwakin nan, Idan ba haka ba, zanyi maku abun da baku ta6a tsammani ba"! da kakkausar murya ta majiyi ƙarfi ya faɗa yana nunasu da yatsan hannun shi.
A lokacin kusan suman tsaye sukayi saboda mamakin kalaman shi! haƙiƙa yayi matuƙar ɗaure ma su kai sun firgita da jin furucin sa.
"Amma dai wasa kake mana ko"? Girgiza kai yayi "na ta6a yi maku wasa makamancin wannan!?
"Idan kuwa har dagaske ne, Elders sunyi kuskuren yarda dakai maci amana! Ka bamu mamaki! Ina ka samu ƙwarin gwiwar da har ka Iya gaya mana magana a gaban idon mu ba tare da jin shakkarmu ba?" Shiru yayi baice masu komai ba.
"Tun wuri ka yi gaggawar Janye ƙudurinka, Saboda kai namune baka isa ka juya mana baya ba, har abada kai mallakin gidan kurkukun ƙaddara ne, kuma garkuwarmu, Idanma mafarki ka ke yi to ka farka tunkafin lokaci Ya ƙure maka, duk wani abu da zakai taƙama dashi anan ka same shi, kuma da zarar elders sunji maganar nan, kasan me zai biyo baya......" wanda yayi maganar Ya faɗa yana mai yi mashi kashedi.
"Har abada ba zanyi danasanin bijiremaku ba, Shawarar da zan baku shine kuyi gaggawar barin wurin nan idan kunaso ku tsira da rayukanku saboda ni banzo da niyyar na cutar da wani ba, ɗan uwana kawai nakeso na ku6utar daga sharrin ku."
Babu yadda Danish bai yi da su ba akan subar salsabeel amma suka sanya kafiya, dama su giants basu da tsoro kuma basa karaya sai dai komai zai faru ya faru, Kafin kace me faɗa ya kaure tsakaninsu tamkar a filin Yaƙi, tuni ƙura da kururuwa sun karaɗe cikin daƙin, bakajin komai sai gurnaninsu mai matuƙar firgitarwa, gaba ɗaya sun rikiɗa sun koma dodanni masu ban tsoro sai kaima juna farmaki su ke yi kamar abokan gaba, Kakin Giant ɗin dake jikinsu Ya faffasa saboda garkuwa ne agare su, idan har ba ciresu yayi ba to bazai iya yin galaba akan su ba balle har Ya yi nasarar kashe su, wani irin bahagon naushi ya soma sakar masu akan idanuwansu duk wanda ya nausa nan take ƙwayar idanuwansa ke zazzagowa cikin Jini Ta faɗo ƙasa, gaba ɗaya Ya zautar dasu Ya nakaɗa masu lugudan wahala, Har saida numfashinsu Yabar gangar jikinsu tukunna Ya zuƙunna Yana huci batare daya canza halittarsa ta mutane ba Yabi su ɗaya bayan ɗaya ya farke ƙirjin kowannan su ya 6an6aro zuciyoyin su Ya tura abaki Yana ci saboda Ya ƙara ƙarfin sihirin shi.
Ɗakyar Salsabeel Ya samu ƙwarin gwiwar miƙewa numfashinshi na fita sama sama, muryarsa da rauni Yace "Danish meyasa ka baro su Unaisah Ka dawo don ka taimaki rayuwata, Idan wani abu ya same su fa"?
Danish bai tanka mashi ba, har Sai da Ya gama abunda Yakeyi tukunna Ya girgiza jikinshi ya rikiɗa ya dawo ainihin suffarshi ta mutane.
Ruko hannun salsabeel yayi acikin nashi yana faman fitar da huci Yace"Saboda rayuwarka tana da mahimmanci, bazan bari na rasa ka ba, nasan cewa zasu iya farmakar ka shiyasa na dawo don na ceci rayuwarka, Inaso na cika maka burinka na ganin ka binne gawarwakin su tsohuwa tamira sannan in ku6utar da kai.
Girgiza kai Salsabeel yayi hawaye cike fal da idanunsa yace"Danish ka tafi kawai, Zasu Iya riskarka, wallahi ba zasu ƙyale ka ba, ni kuma bazanso ka ƙara shan wahala arayuwarka ba, Yanzu lokaci ne da yakamata kayi rayuwar yanci Danish, inaso kayi farin ciki kafin kabar duniya, Hakkin ka da aka tauye maka na rayuwa shi nakeso ka samu Danish dan Allah ka tafi, kabarni kawai, ka koma wurin su Unaisah ni basai na rayu ba, rayuwarku tafi mahimmanci agareni nasan zaku haɗa gwiwa don ganin kun kawo ƙarshen elders...." magiya ya dinga yi masa akan ya tafi ya ƙyale shi amma yaƙiya har saida ta kaiga Ya daka mashi tsawa a faɗace Yace"Ka tafi ka ƙyaleni!! nace maka ka tafi! ka tafi !kabarni kawai..."
Cikin sanyin murya Danish yake faɗin "bazan tafi ba salsabeel, Idan kaga na bar wurin nan to na kubutar da kai ne..."
Gaba ɗaya sun Harzuƙa, faɗa ne ya kaure atsakanin su kamar zasu bugi juna, kwatsam a lokacin da basuyi tsammani ba, sautin tarin Deeja Ya cika kunnuwansu, kamar an dasa masu aya suka dakata dayin sa'in sar da suke yi, kusan atare suka kai idanunsu ga duban inda take a kwance da tsantsar al'ajabi, babu wanda yayi zaton akwai me rai acikinsu, da sauri Danish Ya nufe ta Yana dubanta, idanunta a runtse take sambatu cikin fitar hayyaci take ambaton sunan haris da Angel tana faɗin "ku taimaki rayuwata kuna ganin za'a cutar dani........" kallon juna sukayi shida salsabeel, kafin Ya mayar da dubansa ga sauran gawawwakin dake baje ƙasa da sauri yakai hannu ya ɗan ta6a ƙafar Rubina wani iko na Allah nan take Taja Numfashi da ƙarfi ta fesoshi batare da ta bude idanunta ba, sai la66anta dake kerma, ɗaya bayan ɗaya yake farkar da su babu wanda yake a cikin hayyacin sa duk sun jigata sun galabaita, sai sambatu su ke yi suna ambaton ruwa ruwa za su sha, ƙi shi suke ji.
Maimakon salsabeel yayi farin cikin farfaɗowar su, sai ya fashe da kuka yana faɗin "wallahi banso suka rayu ba, saboda bani da yadda zanyi da su, mutuwar ita ce hutunsu, ga shi babu yan uwansu sun riga sun tafi...."
Cikin tashin hankali ya ruƙo hannun Danish yaci gaba da faɗin"ka taimakamin Mu binne su kawai, su ƙarasa mutuwa acikin ƙabarinsu, ni banga amfanin suci gaba da rayuwa a wannan duniyar ba, wahala zasu sha idan mutanan nan suka riske mu zasu kashe su ne bayan sun gama wulaƙanta rayuwarsu....", kafin Ya ƙare maganar Danish Yace"bazai yiwu ba, kamar yadda yan uwansu suka rayu suma haka zasu rayu, bazan ta6a bari su rasa ransu acikin gidan kurkukun kaddara ba, ko da kuwa zan jefa kaina cikin hatsari ne sai nayi musu hanyar da za su gudu" da ƙwarin gwiwa ya furta kalaman tare da fucewa daga dakin tsohuwa yaje ƙasan gadon Batool inda suke ajiye robobin ruwa ya dauko su ya wuce toilets din dakin su ya samo masu ruwan da zasu sha, bayan ya dawo yabi su daya bayan daya ya basu ruwan suka soma sha.
Salsabeel dake kallon shi tsabar ƙululun bakin ciki baisan sa'adda ya fashe da kuka yana fadin "Danish ka tafi kawai, idan har bazaka taimaka min mu binnesu ba, dan Allah ka tafi zaifi min kwaciyar hankali, Ka rigada kasan bamu da wata hanya da zamu iya ceton su...." Cak Ya tsaya da yin maganar ganin babu danish Kamar walkiya Ya 6ace ma ganin shi, Shiru yayi yana faman haɗiyar yawu cike da zullumin ina Danish Yaje? Ko dai Ya tafin ne ...? Tuni ido Ya raina fata sai kace ba shi bane yake korarsa akan Ya tafi ba, wani irin tsoro ne Ya ziyarci zuciyarshi, hankali atashe yake kallon su Dija dake zazzaune a ƙasa cikin fitar hayyaci suke ambaton sunan ƴan uwan su musamman sunan Unaisah da na Danish, gaba ɗaya sun zauce, gawar mahaifiyarsa ya kalla tuni wani kukan ya kuma zuwa mashi cikin matsanancin tashin hankali Ya soma ƙwalawa Danish Kira don Ya dawo ya taimake shi ko ya samu ya binne su.
Jin shiru babu alamun zai dawo ne ya sa shi zubewa kan gwiwowinsa Yana ta faman yin shesshekar kuka kamar ransa zai fita.
Kamar daga sama Yaji motsi a ɗakin, A firgice Ya ɗago da idanunsa azazzare ya kai duban sa ga Bookshelve ɗin ɗakin tsohuwa tamira dake Ta motsi, Kafin yai wani yunkuri gaba ɗaya Ya rikito Ya rubza ƙasa, Jikinsa na 6ari Ya miƙe yana kallon ƙofar da ta 6ullo, da matuƙar mamaki akan fuskar shi.
Ta cikin ƙofar Danish ya fito, fuskarshi sharkaf da gumi Ya dubi Salsabeel.
"Zamu Iya tafiya" wani irin farin Cikine Ya lullu6e Salsabeel.
A ruɗe ya furta"Danish tayaya akai ka gano ƙofar nan? Ban ta6a sanin akwai ta ba, kuma bana tsammanin ko ita tsohuwa tamira tasan da zaman ta" ya faɗa cike da son jin ƙarin bayani.
Yana faman huci yace"Kada ka manta, ka riga ni tsintar kanka acikin kurkukun ƙaddara ni kuma nafi ka sanin komai na cikin sa, duk wata ƙofar sirri dake a kurkukun nan nasan da zamanta, tabbas tsohuwa bata san da wannan kofar ba, tsohuwar hanyace da aka jima da toshe ta, ni da kaina na sake haƙa ta da sihiri na, Idan muka bi ta cikin ta, zata 6ular da mu cikin wani kogon dutse dake wajen kurkukun nan, dalilin dayasa na za6i ku raba hanya da su Unaisah saboda nasan zasu iya farmakar mu idan har suka gano abunda ke wakana, inaso na raba masu hankali ne watakil in mukayi hakan wasu su rayu daga cikin mu"
Bazai iya jure kallon Danish ba, Yaron Ya burge shi, Ya yi mashi abunda bazai ta6a mantawa ba, ya taimake sa a lokacin da rayuwarsa take akan ga6ar salwanta, da sauri ya janyo shi ya rungume shi yana kuka, kafin ya raba jikin su cikin sanyin murya yace
"Amma danish su Angel fa? Yakamata ka koma wurinsu suna buƙatar ka, bana so wani abu ya same su"
Girgiza kai Danish yayi "kada ka damu, babu abunda zai cutar da su, saboda na rigada na ɗaure hanyar da suka bi da sihiri babu wani mahalukin da ya isa ya iya tsaga kofar ya shiga balle har ya cutar da su, kafin nazo nan sai da na kiyasta awannin da za su yi kafin su ƙarasa kofar da zata 6ular da su waje ni kuma zan riga su komawa bayan na taimake ku"
Murmushin farin ciki salsabeel ya saki,
Basu tsaya bata lokaci ba suka yi kokarin taimaka ma su Hibba don su miƙar da su tsaye, saidai mutun biyu daga ciki kafafunsu sun kasa ɗaukar su sakamakon abunda tsohuwa Zafreen ta yi ma su, bayin Allah sai ihun azaba suke saki, da sauri Danish Ya sungumi deeja ya goyata a bayan shi, ya sanya mayafin daya ɗauko a ƙasa ya ɗaureta tamau, kafin ya ɗauki Rubina ya ɗaurata a kafaɗar shi dama su biyune basu iya tafiya.
shi kuma Salsabeel ya yi amfani da bargon tsohuwa tamira ya nannaɗe gawarta aciki ya ɗaurata a kafadarsa.
A haka suka bi hanyar mai duhun gaske ga zafi tamkar ana rura garwashin wuta, sunci baƙar wahala su sarah kamar numfashinsu zai ɗauke. Cikin awanni takwas da su Angel sukayi suna rarrafawa akan hanyar su duk wannan abun Ya faru, baifi awa biyar ba su salsabeel sukayi nasarar fita daga cikin gidan kurkukun ƙaddara hakan na nufin sun riga su Angel ku6uta saboda tasu hanyar batai nisan wadda su Angel suka bi ba.
Bayan su Salsabeel sun 6ula cikin kogon dutsen, Danish Ya sauke deeja da Rubina daya ɗauko, shima Salsabeel ya sauke gawar tsohuwa tamira, su hibba duk suka zube agajiye har lokacin bakunansu basu gushe da ambaton sunayen ƴan uwansu.
Kallon juna sukayi kowan nan su na haki, da sauri salsabeel ya ruƙo hannun Danish, cikin sanyin murya yace "Danish, bazan ta6a mantawa da halaccin da ka yi min ba, kayi min abunda har abada bazan ta6a mantawa dakai ba, kaine silar ku6uta na daga Gidan kurkukun kaddara kuma kaine silar cikar burina na ganin na cika alƙawarin mahaifiyata dana ɗaukar mata akan in rufe gawarta kada in bari ta wulaƙan ta, Danish ko a mafarki ban ta6a tunanin akwai ranar da zan bar gidan kurkukun kaddara ba, nasha jaraba guduwa nida mahaifiyata amma mun kasa saboda karfin sihirin mu bai kai ba, sai gashi a sanadiyar ka nayi nasarar fita...." tuni hawaye sun wanke fuskarshi.
"Danish, Koda ace ban rayu ba, ni ka gama min komai wallahi, koba komai na shaƙi iskar duniya bayan tsawon lokaci da na kasance a kulle" ya faɗa yana duban cikin idanunsa "ni dai burina ka yi rayuwar farin ciki tare da yan uwanka, ubangiji Allah Ya kare min ku ya tsareku a duk inda zaku kasance, bani da tabbacin zamu sake haduwa wataƙil ma ba lallai mu rayu ba....." bai ƙarasa maganarba ya fashe da kuka mai cin rai, da sauri Danish ya janyoshi suka rungume juna sosai suka kankame jikinsu.
Bubbuga bayanshi Salsabeel yai da hannunshi "ɗan uwana, ka kula min da kanka, wallahi ina mutuwar sonka tun farkon ranar da aka kawo ka gidan kurkukun ƙaddara a cikin tsumman ka, naso ka Danish, zan tafi da kewarka, Allah ya rayamin kai Danish, Ina fata wata rana kaima ka zama cikakken musulmi, ka yi rayuwa kamar kowa kayi Aure ka hayayyafa....."
Lumshe idanu Danish yayi cikin sanyin murya yace"ina sonka ɗan uwana, nima zanyi kewarka, ka kula min da kanka, ina fata mu sake haɗuwa" Yana faɗa Ya raba Jikin shi daga na Salsabeel, A hankali ya soma tafiya yana ja da baya yana duban Salsabeel da ƴan uwan shi waɗanda kwata kwata basa a hayyacin su, wasu irin zafafen hawaye ne suka cika idanuwan Danish bai daina kallon su ba har saida yayi nisa kafin Ya 6ace ma ganin su.
Bai dira a ko'ina ba sai a bakin kogon bishiyar da su Angel zasu 6ula, adai dai lokacin su kuma har sun ƙaraso bakin kogon bishiyar suna ta faman ambaton sunan shi.
Bayan tafiyar Danish A cikin Dajin salsabeel Ya samu wuri a gefen wata bishiya ya binne gawar tsohuwa tamira, ya zuƙunna gaban ƙabarinta yai mata addu'o'i yasha kuka kamar ba gobe, har shaida sai da yayi ma kabarin nata saboda yana da burin wata rana ya kawo masa ziyara tare da ƴan uwansa prisoners don su yi mata addu'a.
(Masu karatu kunji yadda akai salsabeel da su Deeja suka ku6uta daga Gidan kurkukun ƙaddara, nasan wasu zasu ce tayaya har suka dau lokacin nan batare da an ritsa da su ba? To idan ba zaku manta ba, shuwagabannin kurkukun ƙaddara basa a ciki, bayan haka an samu tawayar tsaro, sannan babu wanda yasan meke faruwa a sashen su Angel saboda an rikita lissafin Allon tsafin su, su kan su waɗannan giants din da suka shigo sashen har suka ga salsabeel, bawai sun san me suke shiryawa bane, sun zo ne domin tafiya da su Deeja zuwa wani sashe na daban da suke tarasu don su basu ruwan sihiri wanda zai dawo masu da jinin al'adar su saboda su samu damar gudanar da black night ɗin da za'ayi a ƙarshen watan, amma saboda 6arnar da Danish yayi masu yasa duk wani shirinsu ya wargaje, haƙiƙa sunji zafin tafiyar garkuwa da kuma yaran daya tseratar daga tarkon su, wannan ne yasa lokacin da suka yi taron zaman tattaunawa ɗaya daga cikin Elders Yace
_“Wannan ne Karo na farko da muka yi babban kuskure arayuwar mu, wanda idan bamu miƙe tsaye mun nema ma kanmu mafita ba, to tabbas za’ayi nasara akan mu, Ko a tarihi ba’a ta6a samun prisoners ɗin da suka tsira daga kurkukun ƙaddara ba, su ne na farko kuma sune na ƙarshe, da farko sunyi nasarar ƙetare kurkuku da taimakon Garkuwarmu, Na biyu sun ku6uta daga dajin evil forest da taimakon shi, Babu wani mahaluƙin da ya isa ya iya ƙetare kurkuku da dajin evil forest salin alin ba tare da ya Rasa ranshi ba, amma saboda suna atare da garkuwar prison mun rasa cin galaba akansu saboda mu kanmu bamu isa mu Iya ja da shi ba, babu wata muguwar halittar data Isa ta tunkaresu muddin Yana atare da su, rashin baccin da baiyi ba shine Yaja har muka gaza tunkarar su, lokacin da baccin Ya ɗauke shi munyi nasarar yi mashi abunda zai dawo gare mu sai dai wani abun al’ajabi ya ku6uta daga hannunmu Ya koma ma gangar jikin shi_
Kamar yadda suka ce tun tarihin kafuwar kurkukun ƙaddara ba'a ta6a samun prisoners da suka tsira ba sai akan su, kuma ba kowa bace sila face ƙaddarar kurkuku, da ace unaisah ba ta kasance a gidan kurkukun ba, wallahi Danish bazai ta6a yunƙurin taimaka ma wani don ya gudu daga cikin sa ba shiyasa bai ta6a taimakon su Deeja ba bayan yana da hanyar da zai iya fitar da su.
Salsabeel Ya ci baƙar wahala wurin ɗawainiya da su Hibba, babu wanda bai ji jiki ba a cikin su, saboda yankin da su ka faɗo a dajin babu ko kayan marmari da mutun zai sha, yasha jaraba yin amfani da sihirinsa don ya sawwaƙa masu wahalar amma abun ya faska, Saida ta kai ga ciyawa su ke ci ko su ci ganye don suyi maganin yunwar cikinsu, ga Deeja ba hankali tun da tafarfaɗo sambatu takeyi shi kuma Mubeen wasu irin marurai ne masu masifar zafi suka mamaye fatar jikin shi, kullum sai yayi hauka kamar zai rasa ransa saboda raɗadin azaba, ga uwar rana dake ƙwalo masu ta ko'ina ba sauki, ga damuwar rashin yan uwansu sunyi kuka tamkar zasu kashe kawunansu, baƙin cikin da suka ƙunsa baya misaltuwa, hakika salsabeel yayi namijin kokari wurin ganin Ya basu kulawa duk da wani lokacin abun nema yake yafi ƙarfinsa, gaba ɗaya sun jigata sun sha wahala, babban tashin hankalinsu miyagun halittun daji dake kawo masu farmaki, kusan kullum ne sai Salsabeel Ya zubda jinin shi wurin faɗa da su.
Satin su ɗaya acikin dajin suna shan baƙar azabar rayuwa, acikin rana ta takwas suna cikin tafiya agalabaice sunata yi ma Salsabeel kukan yunwa suke ji maƙoshinsu zafi yake yi masu ruwa zasu sha bawan Allah Ya rasa ya zaiyi da su, da gudu Ya nufi Cikin dajin yana neman inda zai samo musu ruwa tun yana tafiya da kuzarinsa har ƙafafuwan sa suka fara sagewa sai da yagama shan wahala bai samu ruwan ba yana kan hanyar komawa wurinsu kwatsam ya faɗa wani yanki na dajin ba zato ba tsammani ya hango gungun Sojojin ƙasar Ghana da suke yin atisayen horaswa a dajin, da gudu ya tunkare su kamar mahaukaci haka suka ganshi Ya faɗo masu, har sun saita shi da bindigu ya zube kan gwiwowinshi ya fara rokon su akan su taimaka mashi da ruwan sha, gaba ɗaya sojojin suka kewaye shi hannunsu ruƙe da bindigu saboda basu yarda da shi ba, sunyi tunanin wani mugunne shiyasa basu bashi taimakon daya buƙataba, tsawa suka fara daka mashi suna tambayar shi wanene shi? Meyake yi a cikin dajin, sam ya kasa ba su amsa, kwatsam ana haka sai ga su mubeen sun watso da gudu iya ƙarfinsu suna neman shi wata dabbar daji ce ta biyo su aguje, a gaggauce sojojin suka harbeta da bindiga tun kafin su ƙaraso nan take suka tarwatsa kan dabbar ta faɗi ƙasa tana birgima, ai koda sojojin suka ga prisoners sanye da jajayen kaya masu numbers a jikinsu sai suka fara zargin salsabeel ne Yayi garkuwa da su tun da shi ne babba acikin su kuma jikin shi akwai zanan tattoo, wanda alama ce ta tambarin wata ƙungiya, ba su tsaya bata lokaci ba suka ɗaure Salsabeel da igiya tamau, su Mubeen sunata kuka suna rokonsu su ƙyale masu ɗan uwansu amman ko ta kansu sojojin ba su bi ba, gaba ɗaya suka sanya su a bayan motarsu ta sojoji, ba su nufi ko'ina da su ba sai cikin ƙasar Ghana.
Bayan isar su, A headquarter suka ruƙe salsabeel wurinsu, su kuma su Hibba Asibiti suka miƙa su ganin muggan raunin dake a jikin su, babu irin bugun da sojojin nan basuyi ma Salsabeel ba don ya faɗa masu me yakai shi daji tare da ƙananun yara amma yaƙi faɗa masu, sai ce masu yai bazai iya tuna komai daya faruwa da shi ba, ya faɗi hakanne saboda bai yarda da sojojin ba yasan ma koya faɗa masu gaskiya ba lallai su yarda ba, A ƙalla ya shafe kwana uku a hannun sojojin kafin ya faɗa masu cewa su ƴan nigeria ne, iya abunda zai iya tunawa kenan a rayuwarsa, ba su sake shi ba har sai da su rubina dake a Asibiti suka samu lafiya sunata tambayar ina ɗan uwansu Salsabeel tukunna sojojin suka gane cewa ba mugu ba ne, ba su tsaya 6ata lokaci ba don sun fahimci al'amarin su babba ne ba kamar rahoton da Asibiti suka bayar, hakan yasa suka tuntu6i hukumar sojin Nigeria don su sanar da su dangane da yaran inyaso sai su miƙa case ɗin wurin su.
Lokacin da saƙon Ya riski su Sir Mubarak, bayan ya duba duka bayanan yaran, nan take ya yanke shawarar kiran chief owais don ya sanar da shi zancen case ɗin saboda yafi dace wa da hukumar Isod, su yakamata case din yaran ya kasance a hannun su saboda abune da ya shafi 6angaren bincike.
Chief Owais yayi farin ciki lokacin da Sir Mubarak ya sanar da shi, dama a lokacin sunata faman bincike kan yadda zasu gano Unaisah, daga shi har taj sunyi tsammanin cikin yaran zasu ga Angel, sai dai ko da sukaje Ghana suka dubasu babu ita aciki, aranar da sukaje basu kwana ba, sai da suka haɗa yaran gaba ɗaya tare da Salsabeel suka tafi da su a privet jet din chief suka shigo Nigeria....
Bayan komai Ya lafa, Sun sama masu gidan da zasu zauna, basu fara bincikar su ba don sun lura da ba'a hayyacinsu suke ba, sai dai suna lura da duk wani motsin yaran sunyi matuƙar yin al'ajabi da irin rayuwarsu, ba su san komai ba, kamar ranar aka haifo su duniya, daga sunci abinci sai bacci, ba zancen yin sallah, ranar da boss ya kunna masu kallo a tv sunga tashin hankali, kuka suka dinga yi ganin baƙon abu da ba su ta6a gani ba, a ƙarshe deeja ce tayi silar mutuwar tv ɗin.
Chief ne ya ɗaukar ma su Jazz a matsayin likitan da zai dinga duba lafiyar su, kafin ya bashi aikin sai da ya gargaɗe shi akan kada ya kuskura ya sanarma kowa ko da kuwa mommynsa ce, shiyasa dr jazz yaƙi sanar ma kowa nashi wanda silar hakan yaja har sir mubarak ya fara zargin shi akan wayar da yake yawan kama shi yanayi ta maganar gidan kaji, matsalar da aka samu shi Sir Mubarak baisan da zancen Aikin da Jazz ya ke yi ma chief owais ba, sannan baisan a gidan da chief owais ya killa ce su ba, amma Yana bibiyar case din yaran don jin wani hali ake ciki game da binciken su.
Bayan wasu yan kwanaki, Su chief suka tuntu6i Salsabeel suka tsare shi da tambayoyi dangane da rayuwarsu, bai 6oye masu komai ba gaba ɗaya ya sanar da su, wa'iyazubillah kusan zaucewa sukayi saboda tsananin tashin da hankulansu suka yi, ba su ta6a jin labarin daya gigita su ba irin wanda Salsabeel ya ba su, abu kamar ashirin wasan kwaikwayo amman wai a zahiri yake faruwa zuciyoyin su sun karaya ainun.
to a cikin labarinsa ne suka ji ya ambaci sunan Angel, sunyi matuƙar girgiza da jin cewa tana a cikin su, kuma sun raba hanya da su, hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba, musamman taj kamar zai zauce jin cewa Angel dinsa tana a cikin su, ba dan zuciyar imani ba da tuni ya haɗiyi zuciya ya mutu, ganin yadda yake kuka kamar ƙaramin yaro yasa Salsabeel tambayar shi meya faru, Chief ne ya bashi amsa da cewa yarsa ce Angel ɗin da ya ke magana akai, wani irin farin cikine ya lullu6e Salsabeel ganin Mahaifin unaisah, jiki na rawa ya ruƙo hannun shi tamau ya fara jinjina mashi yana faɗin ya gode ma Allah saboda yarinyarsa tana da kaifin basira Allah yayi mata baiwar da zaiyi wuya asamu mai irin ta, bayan haka yace da shi ya kwantar da hankalin shi, in sha Allah babu abun da zai faru da su saboda suna atare da garkuwa yayi imanin in har ba lokacin mutuwarsu ne yayi ba to kuwa zasu ku6uta batare da sun cutu ba, abun da ya dace shine su tayasu da addu'a kuma a bibiyi dajin evil forest inda rabon agansu toh, shi kanshi Salsabeel ɗin yayi mamakin daɗewarsu a dajin, amma da yayi zurfin tunani sai ya tuna cewa Danish baisan inda zai kai su Unaisah ba, shi iya rayuwarshi daga gidan kurkukun ƙaddara sai cikin dajin evil forest, bai ma ta6a sanin akwai wasu mutane dake rayuwa a wajen dajin ba, kuma hada ƙarin ba su da taswirar dajin da komai zaifi zuwa masu da sauƙi, saboda dajin evil forest kurman dajine yana da wuyar sha'ani.
Jami'an isod sun yi matuƙar ƙoƙari wurin ganin sun gano su a dajin, kusan kullum ne sai jiragensu sun kewaye shi suna shawagi Allah ne dai bai nufa za su haɗu da su ba.
Babban abun da yaja ma su Angel daɗewa a dajin, Lokacin da Danish ya ke yin amfani da sihirinsa wurin jigilar ɗaukarsu idan dare yayi lokacin sun yi bacci yana yin tafiya mai nisa da su duk don su nisanta da gidan kurkukun ƙaddara silar hakan yaja har suka 6ace hanya suka bar yankin da ya kamata su faɗa, sukai can wani yankin daban.
_Alhamdulillah, Kunji yadda akai Su salsabeel suka ku6uta daga gidan kurkukun ƙaddara, da kuma yadda akai suka haɗu da Chief Owais, kuma cikin ikon Allah daga baya sai gashi suma su unaisah an ceto rayuwarsu, a ranar da sojin america suka tuntu6i chief da case din samun yara yan Nigeria a daji, wani irin farin cikine ya lullu6e su, anci sa'a a lokacin yaje babban burnin america kuma sai ga labarin tsintar su unaisah, tunkafin suga su wanene ransu ya basu cewar sauran yaran ne kuma zaiyi wuya in babu ita acikin su, cikin ikon Allah sai ga hotunansu sun gani wayyo Allah tsabar murna lokacin da chief ya turama taj hotunansu da yake shi yana a Nigeria, ko runtsawa baiyi ba adaren ranar da suka shaida baiyanarta_
_A tsanake salsabeel ya ƙarasa ba su labarin yana duban fuskokin su_
*Mu haɗu Jibi Idan Allah yakaimu da rai da lafiya, don jin yadda zata kaya*
Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 21 Complete
by
Novels Elite Admin
June 25, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
_________________________________E21✍️
A tsanake salsabeel ya ƙarasa ba su labarin yana duban fuskokin su, waɗanda suka jiƙe sharkaf da ruwan hawaye, sautin koke koken su ya cika falon, ta ko'ina shessheƙar kukan su ce, Ni kaina bazan Iya misalta zunzurutun farin cikin da ya mamaye zukatansu ba, saboda baya faɗuwa abun sai wanda ya gani da idanunsa, kamar an ruke kafafuwansu sun kasa motsawa su ƙarasa ga junansu, sai kallon ƴan uwansu suke yi kamar yarda suma suke kallon su, ashe rai kan rai? Ashe da rabon zasu gana da junansu? Muryar na rawa suka soma ambaton sunayensu Deeja Eve Yasmin, Rubina, Hibba, Sarah Mubeen, la66ansa na kerma suke ambaton sunayensu, gaba ɗaya rayuwar su ta prison ta dawo masu sabuwa fal acikin zukatansu wani irin tsantsar tausayin ƴan uwansu ne ya kama su jin irin azabtuwar da su ka yi a daji.
"Ba kuka yakamata kuyi ba, Allah Ya kamata ku gode mawa, da ya sake haɗa ku da yan uwanku da ransu da lafiyarsu..." tun kafin Taj Ya ƙarasa maganar, cikin sagewar gwiwa gaba ɗaya suka zube kan gwiwowin su atare su ka yi Sujudash shukr, khadeeja ce ka ɗai ba tai sujjadar ba, hannayenta ruƙe da takalmanta da ta rungume a ƙirjinta sai faman zare idanunta ta ke yi tana ƙyafƙyafta su, hatta yanayin fuskanta ya canza ga dukkan alamu ƙwaƙwalwarta ce ke ƙoƙarin tariyo mata wani abu da ta yi loosing din shi sai dai kash ta ƙasa tunawa sai ma kanta da ya fara juya mata.
Lokacin da suka ɗago daga sujjadar suna yiwa Allah kirari haɗi da yi mashi godiya, fuskokinsu sunyi jawur da su saboda kuka, da sauri suka fara rungumarsu a jikinsu kamar zasu mayar da su cikin su, ɗaya bayan ɗaya suke hugging dinsu hadi da sumbatar kuncinsu, sautin muryoyinsu masu dauke da tsantsar annurin farin ciki sun cika ko'ina na dakin, Haris sai faman tambayar deeja yakeyi wai fa bai gane ta ba, ba shi ba hatta Unaisah tambayar deeja takeyi suna ta fadin Ina deeja take bamu ganta ba .... salsabeel da ke sauraronsu dariya ce kumshe a bakinshi,
Da hannu ya nuna masu ita tare da cewa"Gatanan tana kallon ku, sai kunyi hakuri da yar uwar taku, ba lallai ta gane ku ba..." tunkafin Salsabeel Ya karasa yi masu bayani haris ya nufe ta da gudu aikuwa ta watsa aguje kamar wadda taga wani mugun abu, bawan Allah kamar zai fashe da kuka saboda ƙagarar da yayi na son ganinta,
Muryar shi da shesshekar kuka yace
"Deeja na kin manta ni? Ni ne fa haris dinki na gidan kurkukun ƙaddara!..."
fashewa tayi da kuka, hankali ya dawo kanta murya na rawa take fadin"wallahi ba kai bane Haris dina ba, ƙarya kake yi min ni bansan ka ba, Haris dina baƙi ne ba fari ba, kuma shi ba siriri bane' gaba ɗaya suka sanya dariya ga hawaye akan faces dinsu
"Deeja ni fa baki gane ni ba"? Unaisah ce tai maganar, tana nuna mata kanta da yatsa, maƙe mata kafaɗa khadeeja tayi"wayyo Allah ni wallahi ban san su wa ne ne ku ba, Wai ya salsabeel ba cewa kai wurin gasar kyau zaka kaimu ba to su wadanda su wanene ni sun wani tsareni da idanunsu" tana kuka ta faɗa.
"Khadeeja baki gane su ba? Ƴan uwanki ne fa" salsabeel ne ya fada yana kokarin fahimtar da ita watakil silar hakan ta dawo hayyacin ta.
"Deeja haris dinki ne fa, abokin kukan ki me share maki hawayen ki, dan Allah ki tuna ni deeja, wallahi bakisan haukan rashinki da nayi ba, nayi kewarki deeja kamar zan zauce, har jinya nayi saboda ke" ta6e mashi baki tayi.
"Wallahi bakai bane haris dina ba, ay shi ba haka yake ba"
Dafe kan shi yai da hannu ɗaya zuciyar shi ajagule yace "Na fahimce ki, nasan na canza kema kin canza khadeeja, Ki kalle ni da kyau ni ne dai wannan haris din naki" harara ta watsa mashi tana faman zumbura bakin ta.
magiya suka dinga yi mata a karshe da sukaga bata da niyar bari su ta6a ba, aiko da gudu suka nufeta gaba daya suka ɗauke ta suka ɗaga ta sama suna jujjuyata, tuntana kuka tana fadin su sauke ta ƙasa, Har dai ta fara tiƙar dariya ba don ta gane su ba, sai don jin dadin abun da sukeyi mata, sauke ta kasa sukai da sauri Haris ya rungumeta ajikinshi suka ƙanƙame juna, ta yi lamo tana faman sauke ajiyar zuciya kamar tana son ta tuna shi sai dai takasa.
Ruƙo hannun Mubeen Angel tayi acikin nata, idanunsu cike tab da ƙwalla suke kallon juna, ta ji tausayin shi, ba zata ta6a manta abun da ya faru lokacin da zasu bar kurkuku ƙaddara ya yanke jiki ya faɗi haka suka haura kafa suka barshi, bawan Allah ashe har ciwo yayi,
Huggin dinsa tayi a kirjin ta, hannayenta daddafe da bayan shi, shima ya dafe ta cike da kaunar junansu,
Hankalin danish bai kai kansu ba, ya basu ya baya, hannayen sa suna acikin na salsabeel sai faman sakar ma juna murmushi sukeyi, wani irin dadi ne Ya lullu6e kowannan su
"Kaine silar komai danish" salsabeel ne ya fada yana dan bubbuga shoulder din sa alamar jinjina
Duk wannan abun dake faruwa akan idon sheikh imam babu wanda Ya lura da shi, Shigowar sa kenan falon Ya taras da abun farin cikin dake faruwa hakan yasa shi tsayawa abakin kofar yana kallon abunda yai matuƙar faranta ransa.
Hatta Taj da big guy murmushi ne ɗauke akan fuskokinsu, kamar waɗanda akai wa albishir da gidan Aljanna babu wanda basu burge ba acikin su, sun tausayawa rayuwar su, ga wani irin son yaran da kaunar su da ya mamaye zuciyoyin su.
Ummin america dake ta kallon su, idanunta sun yi jawur saboda kukan da tasha, dama ba ta jima da gama yin shi ba, gaba ɗaya idanunsu na akan prisoners dake ta tsalle tsallen farin ciki a tsakar falon suka rurruƙe hannayen junansu tare da kewaye kawunansu suka haɗasu guri guda gwanin ban sha'awa yadda kasan fararen furanni a garden tsabar kyan da sukayi.....
Cikin Harshen Larabci sheikm Imam Ya fara karanto masu addu'o'i yayin da yake ƙarasa shiga cikin falon gaba ɗaya hankali ya dawo kan shi, da sauri suka raba kawunansu tare da ɗaga hannayensu sama suna amsa mashi da ameen ameen, mutun ɗayane baya amsa addu'ar sheikh imam wato Danish, har Yanzu bai matsa daga gefen Salsabeel ba.
Bayan ya gama jera masu addu'o'in kowan nan su Ya shafa akan fuskarsa.
Kafin su sauke hannayen su, sautin takalman mutanan da ke shigowa falon taja hankalin su ga duban su
Chefs din dake girka abincin gidan ne suka shigo hannayen su ruƙe da ƙaton Cake stand mai hawa bakwai an ƙawata shi yayi matuƙar jan hankulan su.
Bayan sun sauke masu cake din akan glass table, ba su tafi ba, tsayawa sukai don ayi shagalin da su.
Cikin harshen turanci ɗaya daga cikin chef din yace"muna tayaku murnar haɗuwa da ƴan uwanku, kuma muna tayaku murnar samun ƴan ci arayuwar ku, sannan muna yi maku fatan Allah ya dawwamar da farin ciki arayuwarku" gaba ɗaya suka haɗa baki wurin yi masu godiya.
"Bismillah, wannan na ku ne, chief ne Ya bada Umarnin A haɗa maku Cake, saboda ku ji daɗin yin shagalin murnar ganin yan uwanku" ɗaya daga cikin chefs dinne Ya faɗa, bayin Allah saboda farin ciki hawaye ne suka cicciko idanunsu waɗanda suka kumbura saboda kukan da suka sha.
Hannayen su ruƙe cikin na juna suka kewaye Cake din, Lokaci ɗaya wani abu ya faɗo masu aransu wanda ba komai bane face farkon zuwan Sabbin prisoners gidan kurkukun ƙaddara, ba zasu ta6a mantawa da lokacin ba har abada, ranar da giants suka kawo masu cake sunata murnar yanka shi akarshe majnoon yayi ajalin shi.
cikin shessheƙar kuka jemimah tace"Genie Ina majnoon ɗina? shi bai dawo ba? Yakamata shima Yazo tun da su deeja ma da suka mutu sun tashi"
kumatunta jawur tayi maganar, gaba ɗaya ta karya masu zuciyoyin su.
"Jemimah wanda ya mutu ba ya dawowa sai dai idan dama kwanansa ne ba su ƙare ba, Majnoob Ya mutu ba zai ta6a dawowa awannan duniyar ba, amma in sha Allah zamu haɗu da shi agidan aljanna" yayin da Unaisah take yin maganar bakomai take tunawa ba face fuskar majnoon da unaizah, hakika ba zasu ta6a mantawa da farkon zuwanta gidan kurkukun ƙaddara ba, lokacin da ta sauko kan stairs cikin shiga ta school uniform red colour, ƴar gayu da ita wayayya ta goya back dinta abayanta.
muryarta ce ta soma yi ma unaisah gizo a kunnanta.
_Hi, Am unaizah ƴar gidan daddy, can i know u_
_that's Impossible, ae ni bana sharing soson wanka, Kuma bana wanka in ba a cikin bathtub ba, I can't stay here i wanna go home, cos daddy ba haka Ya kwatanta min school ɗin ba, Yace min fa komai irin na Gidan mu ne, but why naga banbanci_
Runtse ido unaisah tayi yayin da take jin wani irin kewarta a zuciyarta, tayi fatan ace gaba ɗayansu ne suka rayu sai dai kash Allah baya barin wani dan wani yaji dadi.
Siraran hawaye ne suka wanke fuskar Sajeed tunawa da yar uwarsa Gabriella wadda a halin Yanzu ba shi da tabbacin tana araye kota mutu, lokaci ɗaya sautin muryarta ya soma cika kunnuwansa farkon kasancewarsu agidan kurkukun ƙaddara lokacin da za'a raba su da junansu tana kuka tace
_ My twin bro, Ka kula min da kan ka, Duk inda za'a kai ni zan dawo wurin ka_
Kowa da abun da yake tunawa aran shi, ganin jimamin nasu bame ƙarewa bane yasa sheikh Imam Yi masu nasiha mai ratsa zuciya, ya dinga jawo masu ayoyin kur'ani Yana fassara masu har saida yaga sun samun nutsuwa tukunna Ya dakata...
"Waye zai fara Yanka mana cake din"? boss ne ya faɗa yana kallon su don jin za6in su, Har suna hada baki wurin furta"Unaisah"
Idanunta amarairaice ta kalli faces din yan uwanta kafin ta sanya yatsun hannunta dake kerma ta dauki ƙaramar wuƙa, har taj ya yunkura zai ruƙo hannunta don ya taimaka mata ganin hannun ta na kerma, tunawa da danish yasa shi fasawa don har yanzu bayanshi bai daina yi mashi zogi ba.
A hankali ta yanko cake din tare da ɗagowa tana kallon su idanunsu duk suna akanta, tama rasa wa zata fara bama cake din duk da akwai wanda zuciyarta ta aminta da cancantarsa, satar kallonsa tai nan take idanunsu suka shiga cikin na juna,
"Angel ki ba danish, shi Ya cancanta ki bamawa," muryoyinsu sajeed ne suka cika kunnuwanta.
kau da ido tayi daga kan danish ta kalli daddynta, Lumshe mata idanunsa yai alamar ya amince mata.
Murmushi ta ɗan saki har dimples dinta suka lotsa, matsawa tayi kusa da danish, ta miƙa masa cake din ya buɗe ƙaramin bakinsa ta sanya masa, gaba daya suka soma tafa masu, Bayan ta ƙara cirar wani cake din ta miƙa ma daddyn ta Yaci.
daga bisa ni ta miƙa ma Haris Wuƙar, Ya kar6a Ya datsi cake din ya sanya wa deeja abaki, wani irin farin cikine Ya lullu6e su
Bayan ta gama taune na bakinta, ya bata wukar don ta bashi, abunka game tabin hankali, maimakon ta kar6i wuƙar sai ta sanya hannu ta 6allo ƙato ta duma masa abaki har cikin hancinsa ya shiga, gaba ɗaya suka sanya dariya, cike da nishadi.
Kar6ar wukar batool tai, ta ballo cake din ta ba mubeen Abaki Yaci, Kafin Ta sake gutsuro wani ta miƙa ma Rubina itama taci, ɗaya bayan ɗaya duk sai da suka ciyar da junan su cake din.
Tunawa da aunty umminsu dake ta kallon su, yasa batool ta sake kar6ar wukar daga hannun Sarah, ta yanko cake din taje gaban ummi ta miƙa mata, murmushi tasaki tare da ruƙo hannun batool ta tura shi abaki tana taunarsa ɗagowar da zatayi kwatsam suka haɗa ido da sheikh iman dake ta satar kallon ta, duk sai taji jikinta yayi mugun yin sanyi, tuni taji wasu hawayen sun cika idanunta, muryarta na rawa tace da batool"ba ki ba sheikh imam cake din ba" tana fadin hakan tai saurin juyawa ta nufi hanyar komawa bedroom dinta, sam yakasa janye idanunsa daga kallon ta hatta su taj sai da suka lura da kallon ummi da yakeyi sai dai basu kawo komai aran su ba.
Jiki asanyaye Batool ta ƙara yanka wani cake din taje gaban sheikh Imam Ta miƙa mashi, sai da Ya fara ɗaura tafin hannunsa akanta ya ɗan shafa shi ya furta"Allah yayi maki albarka" kafin Ya buɗe baki ta saka mashi cake din'
Murmushi kowan nan su Yasaki gwanin ban sha'awa.
Da zolaya big guy yace"yau an nuna min wariyar launin fata, Ni babu mai bani cake din"?
da sauri sajeed yace zan baka, girgiza kai yayi"I'm sorry Ni mace nakeso ta bani ba jin sina ba" dariya suka sanya gaba dayan su.
Harara boss yadan jefa masa cikin muryar raɗa Yace"kai bana son iya shege fa, halan tazurancin naka ne Ya motsa" ƴar dariya yai har hakoransa suka bayyana.
"Ni zan baka cake din" jemimah ce tayi maganar, da karfin hali fuskarta sharkaf da hawaye, gaba ɗaya suka sanya dariya,
matsawa big guy yai tare da kai hannu ya dauki Jemimah, kafin Ya bata wukar Ta yanka ta bashi abaki, shima ya karbi wukar ya 6allo cake din Ya sanya mata abaki.
Sautin tafin su Ya cika falon, wunin ranar shagali sukayi babu kakkautawa yadda kasan gidan biki.
_______________________________✍️
Safa da marwa takeyi a tsakar dakin ta, fuskarta dauke da tsantsar farin ciki, gaba daya ta shagala da tunanin Yar ta Angel sam ta manta da zancen tafiyar su, zumuɗi Ya hana ta zauna jira take Aneelerh ta tura mata da hotunansu duk tabi ta kosa da son ganin fuskarta
Jin ƙarar shigowar sakonni ta whatsapp din da ta buɗe ne, yasa tai saurin duba screen din wayar dake ruke a hannunta, wayyo Allah dadi, tsabar zumudin ta buɗe sakon Aneelerh yatsun hannunta har kerma sukeyi, lokacin da ta ɗaura idanunta akan hoton Unaisah ƙafafuwanta kasa ɗaukarta sukai, awani slow ta koma gefen gado ta zauna hannunta ɗaya dafe da bakinta take kallon hotunan Unaisah, yayin da zuciyarta ke harbawa da karfi da karfi tun da take a duniyar nan bata ta6a jin son wani ɗan adam fiye da yadda takeson ƴarta, duk da basu taba haduwa ba amma taji wani irin mahaukacin son yarinyar na ƙara shigar zuciyarta.
Hotunan da Aneeleeh ta turo mata na unaisah tun tana jaririyarta nannaɗe cikin farin towel, hada hotunan Birthday dinta lokacin ta cika shekara goma aduniya, sunyi kyau hotunan kamar lu'u lu'u
Wani irin sanyine Ya ratsa zuciyar benazir, a kalla ta shafe mintuna tana kallon hotunanta, kafin ta buɗe na baby junaid din Aneeleeh, Murmushi tasaki tana kallon kyakkyawan yaron kamar sabon fure ya kwanta mata aranta, Bakomaine Ya faɗo mata aranta ba face Fatimar yaya shureim ita kadaice babu acikin su
A hankali ta furta"Allah sarki Aisha ke kadai ce babu jinin ki araye, mun yi babban rashi, Allah yajiƙan fatima Allah Yasa mai ceto ce....." idanunta cike tab da kwalla tayi maganar.
"Benazir zaman me kike yi"? Rass taji gabanta ya fadi jin muryar hajiya layla, a hanzarce ta dago tana duban kofar shigowa dakin, Hannunta ruke da trolley din kayanta, fuskarta babu fara'a sai faman huci take yi, Shigowa dr shureim yayi da sauri yana kokarin shawo kanta"mommy dan Allah ki yi hakuri ki fasa tafiyar nan, kinga daddy bai amince maki ba, Yakamata kibi umarninsa ko dan gujewa fushin ubangiji...." harara ta watsa mashi tana fadin"shureim zan 6ata maka rai wallahi, Idan kai bazaka bi ni ba to ka ƙyale ni in kama gabana, har yaushe ne zan cigaba da zama ana raina min wayau agidan nan? nafa san me nake yi, ni ba shashasha bace..." mai da dubanta tayi ga benazir wadda tuni ta miƙe tsaye damuwa ce tsantsa akan fuskarta.
"Wuce mu tafi, Idan kema ba zaki bi ni ba, to ki zauna tare da su" ta fada rai a6ace.
Cikin sanyin murya Benazir tace"mommy ki yi hakuri dan Allah, kinsan bazan ƙi bi umarninki ba amma bazan iya tafiya ba...." baki asake Layla ke kallon ta.
"Nima ba son zama gidan nakeyi ba, Aneeelerh ce ta kira ni awaya, kiran da muke ta jira, sai yau Allah Ya nufa, dan Allah mami kibarni in hadu da ita inyaso daga baya sai mu tafi"
Girgiza kai hajiya layla tayi"kawai kizo mu tafi, in mun fita zamu fara biyawa gidan su Aneelerhn kafin mu tafi" da ƙarfin hali tai maganar, ita kanta tana jin fargaban zuwa gidansu aneelerh saboda bata so Benazir ta gane karyar da tayi mata nacewa su taj sun bar kasar amma a halin yanzu idanunta sun makance burinta su bar gidan duk abun da zai faru ya faru.
Gyada kai Dr shureim yayi"ki bita ku tafi, Allah Ya kiyaye hanya, Ni zan jira daddy"
Tsoki layla taja, tare da juyawa ta nufi kofar fita daga dakin, da sauri benazir ta dauko mayafi, dr shureim ne ya janyo mata trolley din kayanta, lokacin da suka fito falon gidan, yayi dai dai da fitowar su Hajiya sarah da gudu zeenatu ta nufi benazir tana kuka ta ruƙe mayafinta.
"Aunty benazir kada ki tafi kibarni, dan Allah kada ki tafi, Mami Dan Allah ku yi hakuri ku zauna, Idan wani abu mukai muku badaidai ba zamu gyara, Ni dai banso ku tafi"
"zeenatu zonan"! Muryar Alhaji musace ta katse mata koke koken nata, jiki ba kwari ta saki mayafin benazir ta koma wurin shi ta tsaya, ruƙe hannunta yai acikin nashi, Hajiya sarah kamar an rufe mata baki takasa ta6uka komai sai kallon su da take yi, dakatawa sukai da yin tafiya jin muryar Alhaji ubaid
"Wallahi idan kika sa kafa kika bar gidan nan batare da yawuna ba, to ki sani abakin auran ki"!! hankulansu Dr shureim atashe suke kallon shi har suna hada baki wurin furta daddy meyasa?
Dariyar takaici layla tasaki tana tafa hannu tace"sai me donka sake ni? Ni dama ay najima da gajiya dakai tun lokacin da na gane kai bakomai bane face rakumi da akala, Ina amfanin zama da namiji solo6iyo irin ka"?
Rai a6ace ta faɗa tana kallon cikin idon shi, Kalamanta sun ƙona masa rai, daƙyar Ya iya hadiye yawu mai ɗaci ba tare da ya iya furta komai ba.
Dauke idonta tayi daga kanshi ta kalli Alhaji musa, dake atsaye ya harɗe hannuwansa kan kirjinsa fuskarsa babu fara'a
Harara ta watsa mashi kafin tace
"Hankalinka Ya kwanta Ka shiga tsakanina da mijina, In sha Allah zaka ga sakayyar hakan" wani kallon ƙasan ido Ya watsa mata mai wuyar fassaruwa.
"Shureim Benazir, kada ku bi ta idan har na isa daku, Kubarta ta tafi ita kadai tun da bata jin maganata" acewar Alhaji ubaid.
Murmushin takaici layla tasaki, ba tare da ta ƙara furta kalma ba ta juya a fusace tabar falon
"Ka bar su su tafi" Alhaji musa ne ya fada agadarance.
Da sauri benazir taja trolley dinta tabi mommynta, shima shureim yabi bayanta
A bakin motar shureim ta tsaya zuciyarta a kuntace, batai tsammanin zasu biyo bayanta ba
Dr shureim na ƙarasowa Ya buɗe mata back seat din motar ta shiga ciki, sannan ya sanya masu trolley din kayan su a boot, daga bisani itama benazir ta shiga ciki.
Bayan ya shiga ya zauna a driver's seat, yai ma motar key, zuciyarsa cike fal da damuwar abunda Ya faru, yaji takaicin yadda Alhaji musa ya nuna halin ko'in kula akan tafiyar mamin su, abun da Yafi bata masa rai furucin mahaifinsu yansu shikenan yana ji yana gani auran iyayensu zai rabu"?
"Shureim! Ya akai naga ka dakata da yin driving din"? Cikin rauni na murya yace"mommy Kiyi hakuri mu koma, idan kika tafi ya kike so muyi da rayuwarmu? Ke kanki bazaki so abun da zai tarwatsa farin cikin mu ba...."
Shiru tayi tana nazarin maganarshi, ga dukkan alamu jikinta yayi sanyi lakwas
"Mommy, kina atare damu Ya muka ƙare inaga idan baki nan? Duk wani mai nufin mu da sharri zaiji dadin cutar da rayuwarmu, bayan haka mommy tsawon shekara nawa kuna atare da daddy, auren soyayya kukayi kun tara zuri"a da dadi da ba da daɗi kunyi hakuri kun jure zama da juna sai akan wannan dalilin zaki kashe auranki? Mu kanmu bazamu ji dadi ba dan Allah ki tausaya mana mommy ku dubi girman Allah ki fasa tafiyar nan ko dan saboda mu"
benazir ce tayi maganar tana duban fuskar mami kamar zata sanya mata kuka.
Zancen zuci ta soma yi
_wannan hanyar dana ɗaukarwa kaina ba me 6ullewa ba ce, ƙwara in tsaya in ƙwatar mana ƴancin mu, dole Inyi faɗa ko da kuwa zan rasa raina ne saina shiga tsakanin mu da shi_
Ba zato ba tsammani suka ga ta buɗe motar, wani irin farin ciki ne Ya lullu6e su, da sauri benazir ta fito shima shureim Ya fito suka dauko trolley dinsu dake a boot suka bi bayanta.
Kamar yadda suka bar su hajiya sarah tsaye a falon haka suka taras da su, sunyi mamakin dawowar Hajiya layla, ko kallo ba su isheta ba, Kai tsaye ta wuce room dinta
Da gudu zeenatu ta nufi benazir suka rungume juna suna dariyar farin ciki,
Fuskar hajiya sarah dauke da murmushi ta dubi dr shureim"ta fasa tafiyar ne"?
"Eh mommy," ya bata amsa, Har cikin ranta taji dadin dawowarsu.
Mutumin kuwa murmushin gefen fuska Ya ɗan saki, yayi tunanin security officers din gidanne suka hanata tafiya baisan cewa itace tai ra'ayin kanta ba, fucewa yai daga falon cikin takun isa.
Alhaji ubaid dake kallonsu ajiyar zuciya ya sauke.
"Daddy, dan Allah kuyi hakuri da abunda Ya faru atsakaninka da mommy, ku yi kokari ku sasanta junanku"
Jinjina kanshi yai fuskarshi dauke da murmushi yace"kada ka damu shureim, ni dama ban dauka da zafi ba, itace ke da matsalar, in sha Allah zanje na lallashe ta" ya fada tare dakai hannu yadan bubbuga kafadarsa kafin Ya juya ya nufi dakin layla don su sasanta junan su.
Koda ya shiga ɗakin, ya taras da ita zaune agefen gado, kamar mai jin shakkarta Ya raba ya zauna yana duban ta
kafin yai magana tai saurin katse shi da cewa"basai ka bani hakuri ba, ni yakamata na nemi yafiyarka, ka yi haƙuri idan na 6ata maka rai, in sha Allah bazan ƙara ba, zan bi umarninka in zauna har zuwa lokacin da ka so mubar gidan" da wani irin mamaki yake duban fuskarta, kamar amafarki yake jin kalamanta, Wai yau layla ce da kanta take bashi hakuri har take fadin zata bi umarnin shi?
"Allah yasa ba mafarki nakeyi ba" murmushi tayi tare da dubanshi tace"ba mafarki bane mijina, dagaske ne, abun nayi ban kyauta ba, su shureim sun yi min nasiha nima naga rashin kyautuwar hakan shiyasa na dawo.
Ruko hannayenta yai acikin nashi hawaye tuni sun cika idanunsa
Cikin sanyin murya yace"layla bazan iya misalta dadin da naji ba, kin faranta raina ayau, duk da nasan nine mai laifi amma kiyi hakuri ki yafe min, sannan inaso ki sanyani a addu'arki, Ni kaina bansan meyasa bana iya bijirema umarninsa ba, bana son bacin ran musa, saboda ya kyautatamin arayuwa shine silar duk wata nasara da na samu..." bai kare maganar ba tai saurin rufe bakinsa da tafin hannunta, saboda ta tsani taji Yana yabon musa, saboda ita tasan ba hakanan Ya kyale shi ba shiyasa baya iya ganin laifinsa, amma taci alwashin zata gano ainihin wanene Alhaji musa da duk wani abu dayake takama da shi.
Abun da bai ta6a tsammani ba, Yaji layla ta kwanto da kanshi saman kafadarta, bawan Allah sai Ya kara lafe mata kamar wani karamin yaro.
"Kada ka damu, ni bakai min laifin komai ba, In sha Allah zantayaka da addu'a kamar yadda ka bukata, kaima kuma inaso ka dage dayiwa kanka addu'a" amsa mata yai da toh, cigaba da kwantar masa da hankali tayi, har saida ta cika shi da farin ciki ta dinga zolayarsa tana tuna masa farkon haduwarsu kafin su yi aure.
"Yanzu tun da komai Ya daidaita mu koma dining mu ƙarasa yin breakfast din" cikin kulawa mom sarah tayi maganar tana dubansu.
"Aunty ki tayani murna" acewer benazir
"Fada min meya faru"?
"Aneelerh ta kirani awaya har mun yi magana da ita"
Murmushi hajiya sarah tasaki"masha Allah, ina tayaki murna my daughter, wlh naji dadi yanzu yaushe zaki je can gidan na su"?
Kallon dr shureim tayi wanda gaba daya hankalinsa na akan zeenatu dake a gefensa sai dadi take ji sun fasa tafiya.
"Yaya shureim yaushe zamuje? Ni ko yanzu ma kace a shirye nake Allah" ta fada a kagare.
"Gobe in sha Allah zan kai ki" da sauri zeenatu tace"yaya shureim nima zan bi ku, dan Allah ku tafi dani" ta faɗa a shagwa6e tana kallon shi.
"Kada ki damu ƙafa ta kafarki, duk in da zani je a tare zamu tafi" cikin muryar raɗa yayi mata maganar, dariya murna tasaki.
Benazar tace"kwantar da hankalinki rabin raina, gobe atare zamu je"
"Nagode auntyna"
"Ki daina murna, kin manta da daddyn ki halan, ba lallai ya amince ki fita ba" tur6une fuska tai.
"Mommy pls ki roƙan mun shi yabar ni inje" ta fada tana bubbuga kafafuwanta
"Zanyi mashi magana zuwa anjima nasan zai bari mu tafi da ita" acewar dr shureim
Hajiya sarah na murmushi tace"kunfi kusa ay, nasan kana masa magana zai amince, tun da yana ji dakai na gaban goshinsa" dariya sukai gaba dayan su.
______________________Twins❣
A kwance yake kan katafaren gadonsu idanunsa na fuskantar ceilling, yanayin fuskarsa sam babu walwala ya haɗe rai kamar wanda aka aiko ma sakon mutuwarsa, bakomai ne yake damunsa ba face haɗin da mommynsa tayi masa, ya riga da ya san halinta ba lallai ta canza ra'ayin ta ba, shi fa arayuwarshi sam baida ra'ayin yin auren wuri, yafi sha'awar yai sharholiyarsa son ransa, a yadda ya tsara ma kansa sai yakai 45 years zaiyi aure, bugu da ƙari baya jin zai iya auran yarinyar saboda ba'ajinsa ba ce, jiya kafin ya kwanta bacci sai da yayi bincike akanta ta hanyar amfani da wayarsa har ya gano wanene mahaifinta wato karen ƴan siyasa, aransa ya ayyana tayaya shi da ya fito daga babban gida shahararren family da duniya tasan da zamansa, zai auri wannan yarinyar, Bayan haka mommyn sa minister ce daddynsa Ceo ne na babban companynsu Obi Tech, tayaya zai auri interior designer? Companyn ma da take aiki ba nata ba....
Abu ɗaya daya hana shi sukuni, kyawun fuskarta da surar jikin ta, daren jiya dakyar ya runtsa, ba halin Ya rufe idanunsa sai ya tuna lokacin da ta fashe mashi kuka la66anta na kerma, kissing ɗinta da yayi har cikin zuciyarsa yaji wani irin shauƙi da bai ta6a jin sa a wajen wata mace ba, kawai yayi ƙarfin halin tofar da yawu ne don Ya muzanta ta.
Motsin buɗe toilet ne Ya katse masa zancen zucin nasa, A hankali yakai idanunsa ga duban mai fitowa
Zaid ne ya fito waist dinsa daure da towel, suna haɗa ido da juna Ya sakar masa murmushi
"Bro me kake tunani ne? kamar wani abu na damunka? Banza yayi dashi bai tanka mashi ba
"Faɗamin meya faru jiya bayan mommy ta kira ka awaya"
Yamutsa fuska yayi, tamkar baisan maganar ya furta"zaka iya tuna yarinyar nan da mommy ta kawo wurin mu"?
Shiru zaid yayi yana kokarin tuna ta can yai murmushi tare da cewa"kana nufin Zahra"? Ta6e baki zayn yai kafin yace"oho na manta sunanta"
"Itace zahra, yarinyar ta kwanta min araina saboda ina son mace mai kamun kai daga gani iyayen ta sun bata tarbiya" ya faɗa tare da samun wuri gefen gadon su Ya zauna yana kallon zayn
"Mommy ce ta haɗa ni da ita...." bai 6oye masa komai daga abun da ya faru tsakaninsa da zahra.
Har Ya ƙare maganarsa zaid bai ankara ba saboda zuciyarsa da ta karaya, har ga Allah bai ji dadin hukuncin da mommynsu ta yanke ba na hada zayn da zahra, saboda yasan halin ɗan uwan nasa bai jin magana fiye da shi, yarinya mai kamin kai an haɗa ta da ɗan iska, ina ma ace shi mommynsu ta hada da zahra da ba abun da zai hana ya gyara rayuwarsa saboda samun mace ta gari wadda zuciyarsa ke muradin mallaka...
"Zaid? Naji kayi shiru bakace komai ba? Nasan kana tayani jimami ne"
Jinjina kai zaid yai kafin yace"zayn banji dadin abun da kayi mata ba, saboda ba laifinta bane, mommy ce ta hada ta dakai, ni nasan ba itace ta shirya faruwar hakan ba..." ya fada cikin sanyin murya yana kallon zayn dake faman ya mutsa masa fuska
"Me zai hana ka jaraba amincewa da buƙatar mommy, ni nayi imanin ba zaka ta6a danasanin auran zahra ba, watakil ta zama silar shiriyarka...." kafin ya ƙare maganar zayn ya wurga masa harara tare da katse sa da cewa"kana son ta ne?
"Meya kawo maganar so? Kawai daga na baka shawara amatsayinka na dan uwana" guntun tsoki zayn yaja"bani buƙatar shawarar ka, nayi zaton zaka tayani jimamin abun takaicin daya same ni ashe ba haka bane dakai da mommy kanku ɗaya..." ya fada yana cije la66ansa"har abada bazan ta6a sonta ba, zan amince da ita ne saboda mommy, sannan zan aureta badan ina sonta ba sai don in mayar da ita abun biyan buƙata na amma babu maganar mutunci atsakaninmu muddin ta aure ni taga ma jin dadin zaman duniyar nan" muryarsa a kausashe ya furta maganar
Runtse ido zaid yai har cikin ranshi baiji dadin kalaman zayn ba, baisan ya zaiyi ya shawo kan mommynsu akan ta janye maganar haɗa shi da zahra saboda zayn ba mutumin kirki bane, muddin ya auri zahra bakin cikinsa zaiyi silar mutuwarta, dole ya nema mata mafita tunkafin afkuwar lamarin, Indai daddyn su baisan da maganar ba zaiyi kokarin tunzurasa akan kada ya amince da maganar mommynsa....Saukowa zayn yai daga kan gado daga shi sai yar singlet da short Ya nufi toilet Yana huci Ya shige ciki, zaid dake zaune gaba daya kamar an zare lakarsa shi dai ya damu da zahra baya son mommynsu tayi silar jefa ta cikin wani hali
wayar dake a kan side drawer din su, Yakai hannu ya dauka Ya danna wa landline din kitchen tana fara ringing maid ta ɗauka, ya bada umarnin akawo masu breakfast dinsu, Kafin Yai cutting kiran ya ajiye wayar kan drawer
Badajimawa ba, Abla ta shigo dakin da tray mai dauke da kayan abinci, ta ajiye masu kan drawer bayan ta gaishe da zaid ta juya ta fuce..
________________________Dattijon Arziƙi🤍
A zaune yake kan lallausar darduma, hannunsa ruƙe da cazbaha, a hankali Yake motsa la66ansa, kusan rabi da kwata na hankalinsa na akan chief owais dake kwance saman dardumar ya ɗaura head ɗinsa akan laps din baba obie, kyawawan idanunsa suna a lumshe tamkar na mai jin bacci, su duka biyun daga ka kalle su zaka shaida tsantsar nishadin da suke aciki, musamman baba obie, ransa fari fat tunda owais ya kawo mashi ziraya yau kusan wuni yayi awurinsa duk inda zasuje atare suke tafiya, ba su jima da dawo daga masallaci ba suka shigo garden don su sha iska, sai faman satar kallonsa yakeyi kamar ya haɗiyesa haka yake ji tsabar kaunarsa da ya ke ji.
"Grandpa, wannan kallon na menene"? Idanunsa a lumshe Ya jefa mashi tambayar.
Fuskar baba obie da fara'a Yace"Kallon so da kauna ne rabin raina, wallahi yau ka faranta min rai, gaba daya ka debe min kewar hateem dake damuna...." A hankali chief Ya ɗan bude idanunsa Ya saci kallon fuskar baba obie karaf suka hada ido cikin na juna
"Baba...." Ya fada ba tare da ya ƙarasa maganar ba
"Na'am sanyin idaniyata, Naji ka kira sunana kuma ka yi shiru" gyara kwanciyarsa yayi batare daya bashi amsar tambayar sa ba.
"Duk cikin jikokina babu wanda Ya more ni kamar ka, kaga cinyar nan tawa tun kana ƙarami kake tumurmusarta, gashi har yanzu baka daina taushe min ita ba' murmushin gefen fuska Chief yai masa har chin dimple dinsa Ya dan lotsa.
"Meya fi raina"? Ya fada Yana kallon fuskarsa.
"Ni fa idan ina atare dakai, sai naii kamar an mallaka min komai na duniyar nan, ni dai Allah Ya jarabce ni da sonka kakana ina fata Allah ya dawwamar da farin ciki atsakanin mu zan cigaba da tayamu addu'a Allah Ya Ya ƙara mana tsawaicin kwana ko dan na cika maka burinka akaina......."
tun da yafara magana baba obie ke kallon shi da wani irin matsanancin farin ciki akan fuskarsa, dakatawa yayi da jan cazbahar Ya ɗaura tafin hannunsa kan sumar Owais a tsanake Ya soma shafata kamar yana yi masa susa.
"Kalamanka sun sanyaya min zuciyata, Owais kai na dabbanne, wallahi yadda nake jinka bana jin ko iyayanka, kai tamkar bugun zuciyana ne, wallahi bansan Yadda zan misalta maka kaunarka da nake yi ba....." kafin Ya ƙare maganar, ruwan hawayen da suka taru cikin idanunsa suka gangaro kan fuskar chief, lokacin da yaji saukar su a ruɗe Ya zabura ya mike daga kwancen da Yake, Idanunsa akan fuskar baba obie
da alamun ruɗani Ya furta"baba meyasa ka zubar da hawayen ka? shiru yayi batare daya iya furta masa wani abu
"Fadamin mana, ko dai maganar da muke yi ce ko kuma akwai wani abu dake damunka"? Girgiza kai yai"a'a owais kada ka damu babu abun da ke damuna, kawai bana son duk wani abu da zai shiga tsakanina dakai, Ina jin fargaban duk wani abu da zaisa ka juya min baya, ni dai bana son 6acin ranka......' ruƙo hannayen baba obie yai acikin nasa yatsun hannunsa har kerma sukeyi"baba bazaka iya boye min komai ba, idan har kana da damuwa kallo ɗaya nake yi maka na fahimta, Ina ji araina da akwai wani abu dake damunka dan Allah ka fadamin habibi na, nayi alkawarin zanyi iyakar bakin kokarina wurin kawar maka da damuwarka...." da ƙwarin gwiwa ya furta maganar Yana kallon idanun baba obie da suka kada jawur gray eyes dinsa sunyi ja tsufansa duk Ya ƙara fitowa.
Wani murmushi yayi mai ta6a zuciya kafin yace"Idan na faɗa maka abun da ke damuna zaka 6oye min sirri na ba zaka fada ma kowa ba sannan zaka rufa min asiri" jinjina kai owais yai da alamun rudani akan fuskarsa
kamar baison furta maganar Yace"najima inason sanar dakai, sai dai inajin fargaban yadda zaka dauki abun aranka, ka yi min alkawarin ba zaka fusata ba" ya fada la66ansa na kerma, ba karamin rikita tunanin chief owais Yayi ba, gwiwarsa harta sage In a low voice Ya furta"ni mai rufa maka asiri ne babana, bazan bari kowa Ya sani ba, tona maka asiri tamkar tonawa kaina asirine da zuri'armu" jinjina kai baba obie yai sai da yafara kallon garden Din Ya tabbatar babu mai kallon su kafin Ya matsa gab da chief owais Yayi masa raɗa a kunnansa.
Lokaci ɗaya chief ya ɗan janye kunnansa da tsantsar mamaki Yake kallon baba obie wanda tuni yasha jinin jikinsa, ba zato ba tsammani a lokaci ɗaya suka tuntsire da dariya kamar wasu zautattu, Yaushe rabon da inga chief yayi dariya irin wannan ni kaina namanta, komai nasa mai jan hankali ne.
dariyar tayi matuƙar tafiya da imanina, saboda gaba ɗaya ta bayyana zunzurutun kyan fuskarsa, dimpla dinsa duk sun lotsa, fararen hakoransa kamar auduga tsabar hasken su, sun ɗau lokaci suna tiƙar dariya kafin daga bisani chief ya kifa kansa bisa kafadar baba obie, hankalinsa ba karamin kwanciya yayi ba, da farkon yai tsammanin wani mugun abunne zai faɗa masa ashe ba haka bane
Muryarsa tamkar tame jin bacci Ya furta"Grandpa are you kidding me"?
Baba obie na murmushi yace"Wasa nake maka owais, Ni ina ni inayin aure, tsofe tsofe dani, ga tarin ya'ya da jikoki"
"Wannan ba hujja bace, Indai Kana son Yin auren ka fadamin, in sha Allah I will try to find a righteous life partner for you."
Da zolaya baba obie yai masa dundu akan bayansa tare da cewa"Owais wlh wasa nake maka, kawai don inga reaction dinka ne, kuma nagani tunda gayanan na sanya ka yin dariyar da ka dade baka yi taba"
Sauke ajiyar zuciya chief yai kafin ya sake furta"please ko da nan gaba kaji kana bukatar abokiyar rayuwa ka sanar dani, zan goyi bayanka kuma zan nema maka dattijuwa dai dai da kai" dariya baba obie yayi "Allah ya kiyaye In auri tsohuwa, Haba owais Ina laifin Yar sha takwas mai jini a jika, wadda zata sangarta ni, kasan mu tsoffi munfison adinga tarairayarmu kamar irin new born baby, Yanzu ni owais idan na auri dattijuwa kamana me zata min"? da mamaki chief ya ɗago yana kallonsa kai kace ba daga bakinsa kalaman suke fitowa ba.
Kafin Ya bashi amsar maganarsa, Wayar baba obie Ta fara ringing, da sauri ya zarota daga aljihu tare da picking call in ya kara a kunnansa.
Chief owais sai kallonsa Yake yi har yau yana mamakin tsufan kakan nasa, kwata kwata babu rudin tsufa atare da shi, yana da karfi ga kaifin basira, idanunsa kuwa kona matashi albarka saboda yadda yake gani da su ko bai sanya glass ba, harta sandar da yake rukewa ta gayu ce ba dan ya gaza taka kafarsa ba.
"Alhamdulillah Alhamdulillah, almost 3 time baba Obie Ya furta hakan, Hannunsa ɗaya dafe da saitin zuciyarsa alamar Yaji sanyi aransa.
"Ina fata kun sauka lafiya, Ubangiji Allah Ya huta gajiya, Ina ƴan jikokin nawa da surukar arzikin Ina fata duk suna lafiya"? Ya tambaya yana sauraron muryar wanda suke magana da shi.
"Madallah, naji dadin jin hakan, Hateem ka kula min da kanka, tun da ka haura kabar kasar nan nake ta zullumi duk bayan yan mintina saina duba Onn news inga ko kun sauka lafiya don nasan sune nafarkon da zasu fara buga labarin yadda jirginku yayi landing sai gashi cikin ikon Allah Ka kirani...' yai maganar fuskarsa dauke da murmushi
"Muna atare da owais, watakil Ya manta wayarsa agidane, wuni yayi awurina yanzu haka muna a garden..."
miƙa ma owais wayar yayi"uncle dinka ne ke son magana dakai, kar6i kuyi magana kai masa bangajia jirginsu Ya sauka lafiya...."
da sauri chief Ya kar6i wayar tare da karata a kunnansa
"My uncle, Ykk Ina fata kun sauka lafiya"?
On the other hand muryar prime minister ta amsa da cewa Alhamdulillah Myson, tafiya tayi kyau yanzu haka Ina a bedroom dina dakyar na samu jama'a suka ƙyale ni"
"Sunyi kewarka ne, Kai dinne badai farin jini ba,
Yar dariya hateem yai kafin ya numfasa Yace"Ina yarona? tun ina a cikin jirgi nake ta tunaninsa, owais Yanzu haka da nake maka magana zazzabi nake ji a jikina saboda kewar sa, ina ta kiran layi ka donka bani shi mu gaisa bana samu" dagowa yai ya saci kallon baba obie Ganin sun haɗa iso yasa shi saurin canza yare zuwa larabci saboda baison Yaji me zai furta.
"Uncle, zazza6i saboda shi"?
"Hmm ba zaka gane ba, dan Allah Ka hadani da shi"
Hankalinsa adan tashe Yace"pls uncle, ka daina sanya damuwa aranka, bana jin dadi, na manta wayana agida ne shiyasa baka same ni ba, amma in sha Allah idan na koma zan yi kokarin hada ka da shi ko hankalinka Ya kwanta amma kafin nan pls ka sha magani kada zaza6in yai yawa"
"Owais babu wani magani da zai warkar da zazza6in nan kawai ka hadani da shi, saboda shi kadaine warakana" baba obie dake kallon owais ya kura masa ido ba tare da ya fahimci me suke cewa ba.
"Okey uncle, zanyi abun da kake so"
"Nagode owais, and pls abashi kulawa ta musamman, bana so ya nemi wani abu ya rasa, na yarda dakai kuma nasan zaka Iya min abun da nake so" cikin girmamawa ya amsa masa da toh uncle.
Sun ɗan jima suna waya kafin sukai sallama Ya mika ma baba obie wayar, harara Ya galla masa"fadamin me kuke tattaunawa ne naji ka canza yare don kada naji ko"
Girgiza kai owais yayi"ba haka bane....." bai ƙare maganar ba, sallamar Hajjaty ta katse su, ba karamin dadi owais yaji ba saboda bay da amsar da zai ba baba obie akan tuhumarsa da Yakeyi
Tuni kamshin turarenta Ya gauraye hancinansu, Hannayenta ruke da tray ta shigo garden din, Tea set ne akan tray din tare da fresh fruit, bayan ta ajiye masu fuskarta da fara'a ta gaishe sa su,a mutunce suka amsa mata
"Idan kin shiga ciki, Ki sanar da mutanan gidan su prime minister sun sauka lafiya yanzu ya kirani awaya ya fadamin nasan ba lallai suji ba"
Murmushi tayi"in sha Allah zan sanar da su" ta fada tare da mikewa ta fuce daga garden
"Kana sonta ne? Naga kana kallon ta" muryar chief ce Ta ratsa kunnansa da sauri ya kau da idonsa daga kallon bayan hajjaty ya wurga masa hararar zolaya"dan Allah ka daina wannan maganar, kawai daga na kalle ta? Ta6e baki owais yayi batare dayace komai ba, Ya dauki Tea pot Ya tsiyaya masu a cups, atare suka zauna suna sha gwanin ban sha'awa
___________________________________BossBature✍️
A6angaren Aneelerh wunin ranar da farin ciki tayi shi, babu wanda baisan da zancen bayyanar benazir ba, Harta su mami da abie sai da ta sanar da su, sunji dadi har addu'a sukai mata akan Allah ya ƙara tsareta daga sharrin wadanda sukai mata kurciya da kuma fatan Allah Yasa suma su Taj su bayyana kamar yadda benazir ta dawo.
Tun bayan da ta kammala sallar la'asar ta duƙufa tana kallon hotunan benazir da ta tura mata awaya, kamar yau tafara ganin ta, gaba daya zumudin son ganinta takeyi, akwai abubuwa da dama da take son taji daga gare ta, tana son tasan meya faru da ita bayan guduwarta? Sannan A wani hannu ta faɗa? Murmushi tasaki yayin da take yin zooming fuskar benazir tayi haske jawur ta ƙara jiki ta zama big mama..
"Ya Allah kamar Yadda Ka nuna min benazir da ranta da lafiyarta Ya Allah ka nuna min su Uzair haka, har Yanzu ban fidda rai da su ba, saboda Inaji araina suna araye, Ya Allah ka tsare min mijina da dan uwansa da angel dina aduk inda suke, Ya Allah Idan sun riga mu gidan gaskiya kajiƙansu ka gafarta masu alfarmar annabi muhammd SAW......"
muryarta na rawa ta ƙare maganar saboda kukan daya ciyota.....
"Aunty Aneelerh" muryar zahrace ta katse mata kukan nata, da sauri ta sanya tafin hannu ta share hawayen don batason zahra taga kukan ta, hakan zai iya sanyata damuwa, murmushi ta kakaro akan fuskarta ta dago ta kalli zahra dake shigowa.
"Na'am Sisterna"
"Auntyna Ina ƙara tayaki Murna, Aunty benazir ta bayyana saura Angel dinmu in sha Allah itama zamu ganta, Ni nasan yau dakyar zaki iya runtsawa saboda zumudin haduwa da Aunty benazir" cike da nishadi zahra tayi maganar, tare da samun wuri gefen Aneelerh ta zauna tana dubanta.
"Nagode zahra, ki cigaba da tayani addu'a Allah Ya bayyana su uzair, bana jin zan ma Iya bacci adaren yau, in sha Allah zanyi nafilfili akan su..." ta fada tana ɗan yamutsa fuskarta dake a kunshe da damuwa.
"Lokacin da yayan benazir Ya fada min cewa kurciya akai mata har ta gudu tabar gida, wallahi bakomai ya fado min araina ba face 6acewar su taj, farat ɗaya aka neme su aka rasa, a tsakar dare, zahra baki tunanin suma kurciyar akayi ma su"? Idanunta Jawur ta jefa mata tambayar, shiru zahra tayi jimm alamar tana nazari kafin taɗan jinjina kai tace"nima nayi tunanin hakan, zai iya yiwuwa, amma kada mu dogara akan hakan tunda bamu da tabbaci"
"Kin fadi gaskiya zahra"
Shiru suka danyi na wani lokaci..
"Zahra, dazu muna cikin yin magana bamu ƙarasa ba abie Ya kira ni..." murmushi zahra tayi
"Ni ma sham na shafa'a...." labari ta fara bata na dinner din hateem tun daga farko har karshe ta dire mata.
Bakomai ne Ya tsaya ma Aneelerh arai ba face yarinyar da zahra ta bata labarin sun haɗu har sunyi hotuna.
"Ki nuna min hoton in gani" zumbur zahra ta mike tana fadin inna lillahi na manta wayar a hannun baby junaid tun ɗazu tana a wurinsa, Allah Yasa bai yi min barna ba" da sauri ta fuce daga dakin ta shiga neman baby junaid itace har dakin ummi da mamie duk baya a ciki, har falo bata gan shi ba, da sauri ta nufi dakin abie nan ma babu shi ta dawo ta shiga dakin uncle still ba junaid
Sai da ta gama shan wahalar nemansa har zata juya ta koma daki ta jiyo sautin muryarsa a kitchen shi da Ana suna magana.
"Kinga wannan itace Angel dina aunty zahra ce ta dauko min hotonta"
Adai dai lokacin zahra ta shiga kitchen din kafin Ana Ta kar6i wayar don taga hoton Angel din motsin shigowar zahra ya firgitar da junaid aruɗe Ya saki wayar ta kife kan floor, wani irin bugu zuciyar zahra tayi ba ita ba hatta Ana hankalin ta, sai da Ya tashi idanunsa azare suke kallon junaid wanda tuni yasha jinin jikin shi.
Muryarsa na rawa ya furta"aunty zahra bani bane, Ana ne ta kada miki waya...' yana magana yana girgiza kansa duk yabi ya rude, Jikinta na tsuma Ta nufi wayar ta dauko ta tare da juyo da ita, gaba ɗaya screen dinta ya tsastsage fatsa fatsa baka Iya ganin komai.....
Kamar ta fasa ihu haka Taji tsabar bacin rai, a fadace tace"junaid hankalinka Ya kwanta ko? Ka fasa min waya! daga abun arziki na baka ita don ka kalli hotuna" ta fada tana zare masa ido fuskarta adaure tuni Ya ƙara firgita.
"Sister zahra kiyi hakuri shima bada son ransa hakan ta faru ba, kada ki tsorata shi" Ana ce ta fada cikin kwantar da murya.
Bata tsaya sauraronta ba, Ta ruko wuyan rigar junaid"don kaga ina maka wasa da dariya ko? Shiyasa har ka samu kwarin gwiwar fasa min phone, muje daki yau saika yaba ma aya zakinta ɗan rainin wayau, dallah jibarka ko kunya babu" la66ansa ya fara ta6ewa alamar zaiyi kuka"kar na kuskura naga hawaye a idonka, wayar wuta zan sa maka" shiru yayi can kuma ya fara mata magiya"bazan ƙara ba aunty zahra, dan Allah kada ki buge ni, na tufa Allah" kiris Ya rage ta fashe da dariya ganin yadda Ya tsorata kamar ta ta6a bugunsa Alhalin tun da ya taso babu wanda Ya ta6a bugunsa
Janshi tayi har zuwa bedroom dinta, Ta zaro wayar charger a jikin socket, kafin ta dawo gare shi da gudu ya fuce waje yana kuka, biyo shi tayi aguje tana kwala masa kira.
Bai nufi ko'ina ba sai dakin mommynsa Yana shiga Ya faɗa kan laps dinta Ya ƙanƙameta yana fadin"mommy kice ma aunty zahra kada ta bugeni, bana so..." duk yabi ya dabarbace, a rude Aneelerh ke kallon bayansa Jikinsa sai kerma yakeyi"fadamin kaida wanene"?
"Aunty kibarni da babyn nan, Allah Yau sai yaji ajikinsa, Har ni zai fasa ma screen din waya? daga abun arziki na bashi aronta don ya kalli hoton Unaisah shine zai fasa min phone"
"Amma banji dadi ba junaid, meyasa zakai mata haka? Ka kyauta abun da kaima aunty zahra"? Ba tare daya dago dakansa ba yace"tayi hakuri bajan ƙara ba, mommy ki siya mata wata wayar cikin kudina da nake tarawa a wurin ki" dariya sukayi gaba dayansu jin abun da Yace.
"Aunty aneelerh yanzu ya zanyi? Ni takaicina hotunan da baki gani ba"
Mika mata hannu Aneelerh tayi muga wayar da sauri ta bata, duddubawa tayi kafin tace"zanyi magana da mahboob yakai maki ita wurin gyara, kada ki damu idan an dawo da ita sai ki nuna min hotunan" ajiyar zuciya zahra tadan sauke"shikenan amma duk da haka saina tsala masa wayar nan" ta fada tare da yunkurawa zata zane bayansa fashewa yayi da kuka yana fadin"aunty zahra kada ki bugeni, Allah Yana sama Yana kallon ki..." dariya zahra tayi"kasan da hakan shine ka fasa min wayar"? Muryarsa da shesshekar kuka Yace"ay mommy zata canza maki wata cikin kudina" tuntsirewa tayi da dariya cike da zolaya tace"ban ta6a sanin kai matsoraci bane sai yau, ay ko daga yanzu tun da na gano lagwonka, da zarar kamin rashin ji zan zane maka baya da wayar cazana" maƙe mata kafaɗa yai, ba tare daya tanka mata
*HAJIYA ADAMA🤍*
A hankali tai parking motarta, fitowa tai cikin shiga ta lace, ta yafa mayafi kan kafadarta, fuskarta manne da farin glass, Shopping bags ta ɗauko a back seat na motar, kafin ta Nufi cikin gidan tana gab da zata shiga bedroom din su ta tsinkayi Muryar Uncle abdallah yana waya
"Kayi hakuri nasan ba haka mukai dakai ba, na saba alkawari amma ka dubi halin da nake aciki, lokaci ɗaya na rasa ɗana bayan haka na rasa ɗan yayana tare da yarsa, na rasa yayana da kakata kai kadaine zaka Iya taimakona a halin da nake a ciki, wlh ni zan iya maida maka adadin kudin dana kar6a a wurin ka saboda ka dawo mun da su indai suna araye na ƙwammace na ƙare rayuwata a talauci akan inci gaba da ganin damuwarta akan rashin haihuwa..."
Muryarsa amarairaice yayi maganar kamar zaiyiwa mutun da suke yin wayar sujjada tsabar yadda yake lalla6a shi yana yi masa magiya
Cak Ya tsaya da yin maganar ba tare daya ƙarasa ta ba, sakamakon kamshin turaren hajiya adama da hancinsa ya shaƙo masa, a hankali Yai rejecting call din yana kokarin dai daita nutsuwar shi
"Ba halin ki bane Yi min la6e,"! Taji Ya faɗi fuskarshi ba fara'a
Bata tanka mashi ba, har sai da ta ƙarasa gaban gado ta daura shopping bags din kafin ta juyo ta dube shi da alamun rudani akan fuskarta
"Gaskiya ka faɗa ba halina bane, amma wannan wayar da kayi yanzu ta ɗan ɗaure min kaina, dear wani kudi ne naji kana fadin zaka mayar adawo maka dasu idan suna araye!? Har kake fadin ka ƙwammace ka ƙare rayuwarka a talauci akan ganin damuwana na rashin haihuwa? Su wanene kake yin magana akan su?
da wani irin kallon tuhuma take duban shi.
Hannu Yasa yaɗan shafa keyar shi, daga ganin fuskarsa babu kwanciyar Hankali, tsufansa Ya ƙara bayyana musamman fuskarsa duk tayi tamoji tamoji.
Maimakon Ya bata amsar tambayarta sai cewa yai"Har Kin kammala siyayyar?
Dame dame kika siyo mana ne" A waske Ya faɗa tare da nufar Shopping bags din da ta ajiye kan gado, Ya buɗe Yana dudduba kayan ciki.
Kamar sakarya Haka Ya barta a tsaye Tana kallon Ikon Allah.
"Hajiyata, Yunwa nake ji, pls Ki dafa min abunda zan dan ci"
gyaɗa kai tay aranta ta ayyana koma menene zan bincika duk da ba halina bane amma da buƙatar nasan dawa kake waya akan su wa kake magana
Cire mayafin tayi, ta daura sa kan gadon, Kafin Ta juya tana fadin"Sorry dear, nabarka da Yunwa, bansan lokaci Yaja har haka ba, bari naje kitchen na shirya mana abun da zamu ci"
Bayan fitarta daga dakin ajiyar zuciya ya sauke, kamar wanda Ya ku6uta daga hannun dogarawan sarki, kwantar da kansa yai kan pillow idanunsa sun kaɗa jawur bakomai Yake tariyowa ba face nasihar yayansa Malam Zaheer haƙiƙa yayi babban rashin da har abada bazai ta6a samun makancinsa ba
Agogon ɗakin Ya kalla kusan ƙarfe Biyar Na marece, lumshe idanunsa yayi zuciyarsa nayi masa wani irin radadi daga gani yana acikin matsananciyar damuwa, Muryoyin su Uzair ne suka fara yi masa gezau acikin kan shi bazai ta6a manta ranar da suka shigo ɗakinsa da zumuɗin sanar dashi sun samu matayen da zasu aura.
"Kunyi shiru bakuce min komai ba"
"Taj ka fara fada masa" harara Taj Yai ma uzair ay kai yakamata ka faɗa masa ni kunyar shi nake ji Allah, acikin kunne sukeyin raɗar
Murmushi Uncle abdallah yai sai yake ganin kamar komai A yanzu Yake faruwa.
"Mijin mace ɗaya, abincin Ka Yana jiran ka" kamar daga sama ya tsinkayi muryar Hajiya adama, da sauri Ya mike Ya shiga toilet jim kadan Ya fito Ya nufi dinning din, A tsaye Ya same ta tana karasa jera masu abincin
Murmushi suka sakarma Juna"Bismillah, babyn Hajiya adama" atare suka zauna suna fuskantar Juna.
"Sannu da kokari matar mutun ɗaya, nagode da kulawarki agare ni, Naji dadin girkin nan" ya fada Yana kokarin tura jallop rice din daya debo a spoon"Shiyasa nake alfahari dake saboda kin Iya girki"
Murmushi tasaki Jin Yabon da yai mata"nima ina alfahari dakai," shiru suka danyi kowa yana cin abincinsa can ya ƙara dagowa ya saci kallon fuskarta karaf suka hada ido duk saiya rasa sukuninsa
"Wai lafiya naga kamar wani abu na damunka"?
Girgiza kai yai"ba wani abu, kawai ina tunanin ranar da zamu rabu" ras taji gabanta Ya fadi arude tace"Abdallah? Meya kawo maganar rabuwa? Anya kuwa kasan me Harshen Ka ya furta"?
Ya ɗan tsorata da ganin Yadda Ta ɗaga hankalin ta.
"Kaga In baka lafiya muje nakaika asibiti bawai ka kama Yi min sambatu ba"
babu wasa akan fuskarta tayi maganar.
Cikin sanyin murya yace"kiyi hakuri hajiyata, Nima zolayarki nakeyi, maganar rabuwa da nayi kinsan akwai mutuwa ko kuma wata kaddarar ta rayuwa da zata iya sanyawa mu juyawa juna baya!
Harara ta galla masa, tuni idanunta sun ciko tab da ƙwalla mikewa tai da sauri tana fadin"banji dadin maganar nan ba, eh nasan mutuwa dole ce amma meye na kawo maganar rabuwa muna tsaka da cin abincin mu"? Ta jefa mashi tambayar hawaye nabin fuskarta shiru yayi sam ya rasa amsar da zai bata
"Na rasa uzair da taj, na rasa unaisah, haba kabarni inji da wannan radadin mana, akan me zaka tada min maganar rabuwa...." rai a6ace Ta bar dining din ta nufi bedroom dinta
Da sauri Ya miƙe yabi bayanta jiki na rawa saboda baisan bacin ranta, lallashin ta Ya dinga yi kamar zai mata sujjada dakyar Ya samu ya shawo kanta har ta daina fushin da shi
*💘EX-PRISONERS❤*
Wuraren ƙarfe takwas na dare Gaba ɗayansu sun hallara A main falo din gidan yadda kasan gidan biki ko suna, sai surutu sukeyi suna yin firar yaushe rabo abu Yaƙi ƙarewa kamar Yauce rana ta farko da suka fara sanin junan su, da alama dai gidan Chief Ya zama Gidan marayu kowa ka kalli fuskarsa annurin farin ciki ne, ummi tana azaune kan sofa tare da batool hannun ta ruke da waya video take daukar su ba tare da sun sani ba.
Mutun ɗayace babu acikin su, Unaisah dake a daki Tana shiryawa, kamar yadda sukai da daddynta zai kaita Part dinsa dake agidan, wata hadaddiyar abaya ta sanya launin black and white ta ɗauko mayafi tayi rolling nasa akanta, tabi ko'ina na jikinta ta feshe shi da turare yarinya fa ta zama budurwa wani irin gayu take ji,
Bayan ta sanya takalma, ta soma tunanin Ina ta jefa wayarta, sai yanzu ta fado mata aranta, farat daya tafara tunanin aunty pretty matar da sukai waya shekaran jira da dare gaba daya ta manta saboda lalurar da ta same ta ga kuma baiyanar daddynta da yan uwanta da suka ƙara mantar da ita zancen matar.
_Neman wayar ta soma yi, tun daga kan mirror har cikin closet din su, tsabar ruɗu itace har karkashin gadon su neman wayar, zukunnawar da zatai keda wuya taci karo da kananun hotunan nan, tura hannu tayi tare da janyo su zuciyarta cike fal da tunanin hotunan wanene._
_Kamar a mafarki take kallon fuskokin mutanan dake akan hoton, wani babban mutun ne mai kyan sura ya ɗauki wankan tailored suit a jikinsa, ɗayan hoton baturiya ce fara sol itama suit ne a jikin ta._
_Ƙurawa hotunan ido tayi tana kallonsu ba tare data Iya gane daga ina suka fadowa ba, ko wanene Ya jefa su karkashin gado, to ko dai Aljanune suka ajiye su? ta fada acikin ranta, can kuma ta sake kallon hoton Alhaji sai taga kamar an daura mashi fuskar Sajeed banbancin su sajen dake a fuskar alhajin da kuma manyantakar sa shi kuma sajeed bai da saje a fuskarshi_
*Mu haɗu gobe idan Allah yakaimu da rai da lafiya, Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
1 COMMENTS
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Anonymous
27 June 2024 at 04:14
Dan Allah kurkukun kaddara takun karshe 22
Reply
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 22 Complete
by
Novels Elite Admin
June 27, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
_________________________________E22✍️
Ta jima tana kallon hotunan kafin Ta miƙe ɗauke da su a hannunta, da sauri ta juya ta nufi mirror drawer ta buɗe gida na uku ta saka su a ciki.
Tana ƙoƙarin mikewa sallamar Taj Ta katse mata hanzarin ta daga wajen dakin ta jiyo muryarsa.
"Daddy gani nan zuwa na gama shiryawa, waya ta nake nema banganta ba"
"Ina kika ajiyeta ne"?
Watsa hannu tai kamar tana agabansa na manta daddy
"Jiya naso na ganta a hannun ɗan uwan ku sajeed, bari na tambaye shi" amsa mashi tayi da toh aranta tana mai mamakin yadda sajeed yake da nacin son waya, sam baya gajiya da ita."
Badajimawa ba, taj Ya turo kofar dakin Ya shigo hannunshi ruke da wayar.
Face dinsa da murmushi Ya mika mata"Na lura baki son wayar nan taki, saboda ba ki damu da ita ba, me zai hana ki bar ma sajeed din tun da yafi ki sonta"
Muryarta da yar shagwaba tace"wallahi inason abuna, sai dai asiya masa wata tunda Yana so, dr laura fa ta bani ita taya ma zan bada ita" ta yi maganar tare da kar6ar wayar daga hannun sa
"Kin ta6a kiranta ne kunyi magana"?
"Mantawa nakeyi wlh, amma in sha Allah zan kirata in na samu nutsuwa"
"Baki kyautaba yakamata kiyi kokari ki kirata" amsa mashi tayi da toh
"Daddy dani kadai zamu tafi"?
"Eh, next time suma zan kai su gidan"
Ruƙo hannunta yai acikin nashi, suka fito daga dakin, babu wanda Ya lura da su fira taja hankulan su, tana kallon su Deeja dake ta faman sakin murmushi wani irin sanyi taji aranta, yanzu damuwarta akan sauran prisoners ne wadanda ke AGIDAN KURKUKUN ƘADDARA!
Har sun kusa fita daga falon, Kamar ance ta wurga eye balls dinta kan second floor, kwatsam Ta hango Danish dake kallon ta, cikin shiga ta pajama launin blue sky, tayi tunanin ba ita Yake kallo ba, sai tai saurin kau da idon ta, gudun kada ya ga za su fita, tasan halin mutumin nata.
Suna fita daga falon ta sauke ajiyar zuciya, kasancewar baida nisa part din nashi, A ƙafa suke tafiya suna fira hanyar da suka biyo ko'ina hasken electric bulbs ne tamkar ba dare ba ga wata iska mai ni'ima dake kaɗawa
"Daugher, kina jin sautin da nake Jiyowa kuwa"? da mamaki Tace A'a daddy menene"?
"Akwai mutun abayan mu, baki ji sautin tafiya ba" aɗan ruɗe ta furta mutum kuma? Wanene? bata jira ya bata amsa ba tayi saurin juyawa don ganin waye.
Har saida gaban ta ya faɗi idanunta adan zare take kallon shi, Hannayensa harɗe akan kirjinsa, fuskarsa babu fara'a, kayan baccin da ta gan shi da su sune a jikinsa fararen ƙafafuwansa ko takalma babu.
Juyowa taj yai tare da kallon shi, ashe tunda suka fito Yake biye da su, shi taj yasan da zaman shi itace bata lura ba.
Muryarta kamar zata fashe da kuka tace"daddy, mu tafi da shi kawai"
ƴar dariya taj yai tare da cewa"ya zama dole ay, wa ya isa ya hana shi zuwa"?
"mu tafi My man, nayi zaton kayi bacci, shiyasa ban neme ka ba, dama zamu je part din daddyna ne don in gaisa da Auntyna"
kamar jira yake ta bashi damar yabi su, da sauri ya nufe su, a maimakon ya tsaya gefen ta sai ya shiga tsakaninta da taj, yasa hannu ya raba hannayensu dake ruke cikin na juna lamarin ya daurewa taj kai aranshi ya ayyana wannan wani irin namijin kishine? Uban nata ma bai ƙyale ba inaga idan wani ne daban ba? Tun yanzu ya fara jin fargaban yadda zata kaya tsakanin chief da danish tabbas akwai ƙura.
A haka suka jera har suka ƙaraso ƙofar shiga Part din, Komai nasa shigen kalar na sashen da suke ne banbancin kaɗan ne amma fa Ya haɗu, Ita kanta Angel tayi mamakin katafaren Ginin gidan Chief gari guda An ƙawatashi kamar A dubai.
Dafe kofar taj yai da hannunsa a hankali ta zuge masu, katafaren falo ne an kawatasa da furniture, ga wani sanyin A.c na mai sanyaya zukata
Sai ƙara kallon ko'ina take tana ɗan jinjina kanta, har cikin ranta ta ƙara jin ƙaunar chief saboda kyautatawarsa ga daddyn ta.
"Bismillah, Ku zauna bari naje nayi mata magana" ya fada tare da wuce ya nufi upstairs.
A hankali suka zauna kan sofa, kallon sa tai suka hada ido cikin na juna.
"Baki kewata ba? kin manta da dani jiya ko ki neme ni" yana magana tamkar baisan motsa lips dinsa
"Ni da kai waye mai laifi? Jiya ko kallo ban ishe ka ba, ka kama hanya ka bi uncle din chief inata kallon ka ko waiwaye na bakai ba" ta faɗa tana kwa6e masa fuska
Lumshe idanunsa yai batare daya furta mata komai ba
"Har ciwon ciki nayi jiya kamar zan mutu, ni kadai a restroom na kasa bude kofa har na fadi kasa na suma duk kana ina"?
"Ina atare dashi," atakaice Ya bata amsa
Ruƙo hannunsa tai tana kalllon dogon yatsan hannunsa dake asanye da silver ring, yayi matukar yi mata kyau
"Shi ne Ya baka wannan"? Ɗaga mata kai yai alamar eh,
Da fara'a akan fuskarta tace"Bani labarin abun da ya faru tsakanin ku jiya"?
Sai da ya fara kai soft lips dinsa saitin kunnanta kafin ya fara bata labari saboda bai iya ɗaga muryar shi.
Sai faman sakin murmushi takeyi hakika taji dadin kyautatawar da prime minister yayi masa, kuma ta fahimce shima yaji dadi tun da gashi nan da bakinsa yake bata labari mutumin da be cika surutu irin haka ba.
"My man, Ni dai fatana Allah yasa mutumin nan ya zama alkhairi agare ka, wlh tunda nagansa naji ya kwanta min araina saboda kamannin dake a tsakaninku..."
kafin ta ƙare maganar Sautin takalman daddynta ne Yaja hankalin su ga dubansa, saukowa yai down a hanzarce Ya nufe su Yana fadin"daugher, bacci takeyi auntyn naki, ko zaki je ki same ta adaki, Inaso ki bata mamaki" murmushi tayi tare da mikewa da sauri Danish Ya miƙe zai bita, kallon shi tayi cikin sanyin murya tace"ka zauna ka jira ni, Yanzu zan fito ba daɗewa zanyi ba"
Taj dake kallon su murmushi yai tare da ƙarasawa gefen Danish yace"Idan saboda ni ne, To mu zauna gani ka gaka ita sai ta shiga watakli hankalinka zaifi kwanciya,'
Kamar kuwa yasan sbd shi Ya miƙe zai bita, komawa yayi ya zauna hankalinsa akan Angel dinsa Harta haura kan stairs.
A hankali Ta zura kafarta cikin dakin, tana shiga ta soma bin ko'ina da kallo masha Allah, a hankali ta sauke idanunta kan Danejo dake a nannaɗe cikin bargo sai sharar baccin ta take yi.
watsa wa tayi da gudu ta daddage ta haye kan gadon gaba ɗaya ta ƙanƙameta tana dariya, wata irin firgita danejo tayi cikin magagin bacci take fadin"daddyn Angel, wayyo Allahna kana ina wai wanene ke takura min! Nashiga ukuna"
Yaye mata bargon Angel tayi, tana faman haki ta buɗe idanunta waɗanda suka kada jawur saboda bacci, A hankali ta sauke su kan fuskar Unaisah ta ƙura mata ido tana kallon ta, da tsantsar ruɗani take binta da kallo, Itama unaisah kallonta takeyi cike da kewarta, ba zata ta6a mantawa da fuskar denejo ba, ta ƙara haske fara jawur da ita kamar ba'indiya saboda kyau, ga gashin kan nan nata mai tsayi baki wulik har gadon bayanta..
Muryarta aɗan tsorace ta furta"wacece ke"? Mutun ko aljan"!
Dariya unaisah tayi cike da nishadi tace mata"Baki gane ni na"?
Waro idanu waje danejo tayi da ƙarfi ta furta"ANGEL"
tuntsirewa unaisah tai da dariya tare da faɗa mata ta sake rungumeta, daura hannayenta biyu tayi akan bayanta tana fadin"Ni ce, Angel dinki, ashe da rabon zamu sake haduwa danejo na" mamaki Ya hana danejo magana, da sauri ta tallabo fuskar unaisah da tafukan hannayenta, ta kura mata ido tana kallon ta batare da ta kyafta idanunta ba, ko amafarki taga fuskar Angel sai ta shaida ta, duk da ta ƙara girma a yanzu ta zama yar matashiyar budurwa, tuni taji hawaye sun wanke fuskarta, da sauri ta kwantar da unaisah kan kirjinta, itama kukanne Ya kubce mata, sautin shesshekar kukansu duk Ya cika dakin, a hankali take shafa sumar kanta tana faman sauke ajiyar zuciya, Allah ne kadai Yasan irin kaunar da take Yi mata, taso unaisah, tayi kukan rashinta kamar zata zauce, muryarta kasa kasa ta furta"Alhamdulillah Ya Allah, nagode maka wallahi bazan Iya misalta farin ciki da nake aciki ba, Ya Allah nagode maka daka bayyana min Angel ɗina, Ya Allah nagode maka...." cikin shessheƙar kuka ta faɗa, tama rasa inda zata tsoma ranta saboda murnar ganin Angel.
ɗagowa unaisah tayi tasanya tafin hannu ta goge mata hawayen cikin sanyin murya tace"Aunty Danejo, naji dadi da Allah Ya sake haɗa ni dake a matsayin matar daddyna, I can't thank you enough saboda halaccin da kikai min arayuwa Allah ne kadai zai Iya biyan ki, kin so ni kin kuma kaunace ni tsakani da Allah, duk da bakisan koni wacece ba a lokacin amma kin taimaki rayuwa, kiyi hakuri ki yafe min laifin da nayi maki....' tana faɗa tana matsar kwalla.
"Angel laifin me kikai min? Ni ay baki min laifin komai ba...."
Girgiza kai tai hawaye nabin kuncin ta tace"nayi maki laifi, bayan mun shaƙu da juna, na gudu daga rugarku kina ji kina gani har biyo ni ki ka yi kina kiran sunana don in tsaya amma naki sauraronki, ashe da rabon in sha wahala" idanunta acikin na danejo takeyin maganar
"duk da bana danasanin ƙaddarar rayuwar da ta riske ni saima farin ciki da nakeyi saboda a kowani rashi da nayi toh akwai nasara acikin sa" tun da tafara magana danejo ta nutsu tana sauraronta, har cikin ranta tana mai mamakin girman yarinyar da kaifin basirarta, komai nata na dabanne shiyasa take da saurin siye zuciyar mutune.
"Aunty danejo, Kinga ikon Allah ko? Bayan na tafi sai gashi Allah Ya hada ki da daddy na har kun yi aure, amma baki takura kanki ba babu danginki a kusa, ki bani labari ya kikaji da kika fara shigowa cikin burni" yar dariya danejo tayi kafin ta fara bata labarin irin yadda ta tsinci kanta farkon shigowarta birni, ta tabka ƙauyanci taj ba karamin hakuri yayi da ita ba, saboda tsoro da rashin sabo da irin rayuwar birni.
Gaba daya suka kama yin dariya kamar wasu zautattu, Yadda kasan wasu aminnan juna.
"Amma dangin ki fa? Shikenan ba zaki sake haduwa da su ba"?
"Ay Yayi min alƙawarin zai kaini rugarmu nan badajimawa ba" murmushi Angel tayi"amma naji dadi watakil nima in bi ki muje, in gano su hasiya da bawuro"
"Baki manta da sunan su ba" jinjina mata kai unaisah tayi"ban manta ba, na haddace su akaina"
"Dama kece bakuwar da zanyi"? ɗaga mata gira tai alamar eh.
"Daddynki Ya faranta min raina, naji dadin ganin abun da banyi zato ba, amma lokacin da kika gudu ina kika je ne , tayaya akai aka gano ki? Ta fada cike da son jin karin bayani.
"Ki manta kawai, nadai ci wahala amma komai Ya wuce, bana son tuna baya" jinjina kai tay alamar ta fahince ta.
"Ina daddyn naki yake"?
"Nabar shi a falo su biyu ne tare da ɗan uwana Danish"
Ruƙo hannunta tayi"muje falon" saukowa sukayi daga kan gadon atare suka fito
A lokacin Taj Yana zaune kan sofa tare da Danish, tun bayan tafiyar Unaisah hankalinsa Yaƙi kwanciya, musamman da yaji ta daɗe bata fito ba, taj Yaso Yaja shi da fira sai dai Yaƙi bashi hadin kai, Jin motsin saukowar su down, yasa shi saurin kai idonsa ga dubansu, lokaci daya ya sauke ajiyar zuciya ganin Angel dinsa.
Fuskar taj ɗauke da murmushi yake kallon su, danejo kuwa tun da ta daura idonta kan fuskar danish gaban ta Ya fadi rass har sai da ta ɗan dakata da tafiya saboda taji fargaban ganin masifaffan kyan dake gare shi, ganin ta dakata da yin tafiyar ne yasa unaisah yi mata gyaran murya tare da cewa"Shi ne dan uwana danish, kada kiji komai atare da shi muka zo"
jinjina kai tay kafin ta bi ta suka karasa saukowa down asaman sofa dake fuskantar su taj suka zauna, kowan nan su murmushine akan fuskarshi banda danish wanda hankalinsa ke akan unaisah.
"daddyn Angel, inatayamu murna cikin ikon Allah sai gashi Allah ya bayyana mana ita, amma meyasa baka fada min anganta ba"?
"Saboda inaso na baki mamaki" yar dariya tayi"wallahi ka bani mamaki kuma ka faranta min raina, ubangiji Allah Ya ƙara tsare mana ita daga sharrin makiya da mahassada dama duk wani abun cutarwa" har cikin ranshi yaji dadin kalamanta"ameen ameen, ga dan uwanta nan ku gaisa da shi" tun da tafara magana taki yarda ta kalli danish saboda tsoranshi da take ji, kallo ɗaya da ta masa kafin su sauko down ta gane ba shi kaɗai ba ne.
Muryarta na dan rawa ta furta"eh ta fada min sunan sa danish, ya kake dan uwan angel, Ina fata kana lafiya" muryarsa kasa kasa Ya amsa mata da lafiya, ba tare da ya dube ta ba
"Amma daddy Angel ya kuke da shi"?
Taj yace"yanzu ba lokacin tambaya bane idan na samu time zan maki bayani, tashi muje kitchen mu dauko masu abunda kika shirya masu"
mikewa tayi taj yabi bayanta suka nufi kitchen
A hankali unaisah ta sanya idonta a cikin nashi, Murmushi tasakar mashi har dimple dinta Ya lotsa, sai yai tamkar baisan tana yi ba.
"Ba dai fushi kake da ni ba? Fadamin ko na bata maka rai na"? Ta fada tana ɗage mashi gira wani kallon kasan ido mai kama da harara ya wurga mata
"Na fahimce ka, nasan bai wuci saboda na tafi na barka bane, ni narasa gane kishin da kakeyi akaina, sau biyu kana dukan daddyna, na farko ka jefa masa pillow daga upstair saboda yayi hugging dina, na biyu kuma ka Naushe shi da wannan kafcecen hannun naka saboda ya gyara min mayafina, next time inaga hannayensa zaka karya idan Ya ƙara ta6ani..." ta faɗa tare da ɗaura kafa daya bisa ɗaya tana jifar shi da harara kallon kawai yakeyi bai tanka mata ba.
"Ƙwara tun yanzu ka fara yi masa biyayya kana kyautata masa, saboda daddyna shi yake da ikon mallaka maka ni, Idan ba haka ba wallahi kana ji kana gani zai aura min...."
kasa ƙarasa maganar tayi ganin yana nannaɗe hannun rigarshi, ay tuni tasha jinin jikinta, damtsen hannunsa Ya fito fari sol ga zanan tattoo na tambarin kurkukun kaddara, adan tsorace tace"my man yanzu saika buge ni akan wannan maganar" banza yayi da ita babu alamun zai tanka mata.
Murmushi tayi tare da kai hannu ta ɗauki wayarta dake a jiye kan sofa inda tabar ta, a fakaice ta soma daukar shi video ba tare da sanin shi ba, saboda yayi mata kyau he looks so sexy cikin sleeping dress expecially da ya naɗe hannun rigarsa zanan tattoo dinsa ya bayyana.
A tare Taj da danejo suka shigo falon hannayen su ruke da trays na kayan abinci, kafin su karaso tayi saurin ajiye wayar, ta yi ma danish alamar ya gyara hannun rigar sa, hannu yasa yaja hannun ya rufe damtsen nasa, bayan sun ƙaraso saman lallausan carpet din falon suka sauke masu farantan.
"Bismillah My daugher, inaso ki ba auntynki mamaki, Ki zauna Ki cinye abincin nan ke da dan uwanki Danish" murmushi unaisah tayi kafin ta sauko ta zauna.
"Malam Danish bismillah" ya faɗa Yana nuna masa carpet din, sam baiyi niyar ci ba, amma saboda unaisah Ya sauko Ya zauna, shima taj din da danejo suka zauna suna fuskantar su, tuni kamshin abincin Ya karaɗe hancin su, wani haɗaɗɗen dambun Shinkafa ne ta zuba masu a plate, Yaji kayan kamshi ga nama manyan yanka da ta jera masu asaman dambun, ta tsiyaya ma su juice mai sanyi a cups, tun da suka fara cin abincin, Ta lura da yadda danish yake ci kamar zai fasa ƙaramin bakinsa, da alama dambun yayi masa daɗi, hatta taj da danejo satar kallon sa suke yi su kansu ba suyi tsammanin zai iya cin abincin har haka ba, bayan sun kammala cin dambun ta sake zuba masu farfesun ƴan ciki, kamar masu fama da yunwa haka suka tasa shi gaba suka lamushe, ta kuma ƙara zuba masu gurasa haɗi na musamman taji kuli kuli da kayan lambu da aka yayyanka ga mai dake kyalli asamanta tare da tsiren nama, danish bai ta6a cin gurasa ba sai Yau, kai harta dambun shinkafar yaune karo na farko daya fara cinshi, yaji dadin abincin har ƙwarar cikinsa yayi, Angel dake kallonsa sai faman sakin murmushi takeyi ba tare da ya lura da ita ba, bayan sun kammala cin abincin kowa yayi kulu wash rabu hani'an danejo ta kwashe kayan abincin ta nufi kitchen da su
"Daughter, dare yayi muje na raka ku gida, Kada chief Ya tuhume ni, kinsan yanzu bani da hurumin daukarki tun da a karkashin kulawarshi ku ke har zuwa time da zamu kammala bincike"
"Bakomai daddy, na fahince ka," shafa gefen fuskarta yai, danish dake kallon su tuni ya hade ransa, shi fa har yanzu bai daina kishi da taj ba, saboda baisan alaƙar dake a tsakanin iyaye da dansu ba.
Fitowa danejo tayi daga kitchen, ganin su tsaye yasa tace"ya akai nagan ku a tsaye ku zauna mana muyi firar yaushe rabo"
Taj ya ce"Zasu tafi ne" ɗaure fuska tay"bangane me kake nufi ba, nayi zaton ta dawo gida kenan," girgiza kai yai"ay tana a gidan amma a part din chief suke da zama, zata dinga zuwa kuna gaisawa da juna...." dakyar ya samu ya fahimtar da ita, atare suka raka su unaisah har gida kafin sukayi masu sallama.
Lokacin da suka shiga falon babu kowa har sun koma bedrooms dinsu alamar time din bacci yayi, kamar kar su rabu da danish har saida ta raka shi bedroom dinsa kafin ta dawo ta nufi nasu dakin, tana shiga ta samu deeja kwance kan gadon su sai jan minshari takeyi, murmushi tasaki tana kallon ta, har yanzu kwalliyar dazu ce akan fuskarta duk ta ca6e kamar ƴar mahaukaciya, ta jima tana kallon ta, kafin ta fara cire kayan jikin ta, ta musanya dana bacci, fuskarta dauke da annurin farin ciki, ta hayekan gadon, bata damu da rashin ganin batool ba, tasan bazata wuce dakin aunty ummin su ba, huggin pillow tai, Allah ne kadai yasan dadin da take ji sam ta manta da zancen kiran aunty pretty gaba daya tunaninta akan abun farin cikin daya faru yau ne
______________________________________✍️
Zaune ya ke kan sofa ya ɗaura ƙafarsa ɗaya bisa ɗaya, yayin da idanunsa ke akan laptop din gabansa da yake operating lokaci ɗaya ya ɗan dakata Ya jingina bayansa jikin Sofa haɗi da lumshe idanunsa zuciyarsa a cike take fal da tunanin prettynsa har yau jiran hajiya laurat yake yi don jin amsarta, tun jiya bayan kammaluwar dinner din hateem ziyad ya nemi alfarmar yin magana da ita bayan sun ke6e cikin girmamawa ya gaishe ta, ta amsa masa daga bisani ya fara kora mata jawabi game da bukatarsu, lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya canza zuwa 6acin rai kamar bata son zancen Benazir da yake yi mata, acikin ranta tayi mamakin jin cewa a hannun Zaki ta faɗa ita sam ta manta da rayuwar benazir tamkar ma ba'a halicce ta adoron duniya ba, saboda tun fil azal hajiya laura basa ga maciji da hajiya layla wata irin gaba ce atsakaninsu shiyasa bata shiga shirgin abun da ya shafi layla, a lokaci shi kanshi ziyad ya lura da 6acin ran da take a ciki amma sai ta waske ta ƙaƙaro murmushi tana fadin Allah sarki benazir ashe dama zaki ne ya taimake ta? Alhamdulillah wlh nayi murna ziyad, sai dai abun da ya daure min kaina babu wanda Ya kirani daga gidan Ya fadamin cewa anganta amma in sha Allah zan fidda lokaci inje can gidan da kaina don in tabbatar ta dawo in yaso daga bisani zan tuntu6i shi zaki din...." akan haka suka ƙare magana ziyad yai mata godiya kafin suka rabu.
A hankali Zaki ya buɗe idanunsa Yana kallon ceilling din falon, duk don saboda son haɗuwa da ita, ya ɗaga tafiyarsa canada.
Yayi zurfi a zancen zucin nasa muryar turai ta ratsa kunnansa
"First born barka da hutawa" ta faɗa tare da daura masa mug din coffee kan table, murmushi ya sakar mata, yana ɗaya daga cikin abun da yake burge shi da mommyn nasu in har zata ganshi zaune yana aiki akan laptop sai ta kawo mashi coffee .
"Mom har yanzu baki yi bacci ba"? ya faɗa yana kallon ta.
"Tayaya zan iya runtsawa Jazz bai dawo ba, daddynku bai dawo ba shima, su nake jira su dawo sai in kwanta" tayi maganar tare da ɗaura gwiwowin hannunta bisa ga hand sofa din da zaki yake zaune idanunta akan fuskarsa
"Ko akwai wani abu dake damun ka ne"? Ta fada cikin kulawa
"Babu komai" ya bata amsa atakaice tare da kai hannu ya dauki mug din Ya soma kurbar coffee
"My son, tayaya zaka 6oye min damuwarka, bayan ni mahaifiyarka ce, ta ido kadai ina gane damuwarka, tun lokacin da ka shigo ƙasar nan na lura da damuwa aranka"
Sauke mug din yai kan table kafin ya dubi hajiya turai"nagode da kulawarki agare ni, amma ki kwantar da hankalin ki ba abun da ke damuna"
Gyaɗa kai tay"haka nakeson ji" ta faɗa ne ba dan ta yadda da maganarsa ba tasan baya son taji ne
"Bari na shiga ciki, ka kula min da kanka" amsa mata yai da toh
Bayan tafiyarta ajiyar zuciya ya sauke, bawai baya son fada mata bane yafi son ya fara jin halin da take a ciki in har ta isa gida lafiya, kuma iyayen ta sun kar6eta ba abun da zai hana shi sanar da nashi iyayen labarin ta.
Ƙarfe goma da rabi, jazz da sir mubarak suka dawo gidan lokacin da suka shigo falon tuni Zaki Ya koma room dinsa ba su taras da shi ba,
Hajiya turai na kwance kan gado tajiyo sautin sallamar sa, jikinta har rawa yakeyin wurin saukowa daga kan gadon da sauri ta nufe shi yana atsaye cikin shiga ta kakinsa
"Sannu da dawowa, tun dazu nake ta jiranka nayi kewarka yau kayi dare " cikin nuna kulawa tayi maganar tare da ruko hannunsa suka shiga dakin
"I'm sorry bansanar da ke zan kai dare ba, wani aiki ne mai muhimman ci Ya ruƙe ni" ya faɗa Yana kallon cikin idonta,
"Ba nace ki daina jirana ba? daga kinga nayi dare to ki kwanta kiyi bacci"
Maƙe masa kafaɗa tayi"kai ma kasan bazan iya jurewa ba...." murmushi ya ɗan saki"kinsan me na tuna"? Girgiza mashi kai tay alamar a'a"
"Waɗannan twins din na wurin Owais, ko da yake yace min ba twins bane, ɗaya ta girmi ɗaya" da mamaki hajiya turai tace"ikon Allah, amma nayi mamakin jin hakan komai nasu fa iri ɗaya kamanninsu sun 6ace"
"Zai iya yiwuwa yan gida ɗayane" jinjina kai tay alamar eh
"Yaran sun kwanta min araina, kinsan ni da son ƴa'ƴa mata, duk family dinmu ni kadai ne nake da ya'ya maza ina alfahari da hakan amma inason ya'ya mata, ga hateem nan shi mazan yake so Allah bai bashi ba"
shiru mom turai tayi kamar ta dan shiga damuwa, sam bai lura da halin da ta shiga ba, ya nufi toilet Ya shige jin ƙarar rufe kofar shi Yasa jiki asanyaye ta koma gefen gadonsu ta zauna idanunta sun ciko tab da kwalla..
Ceilling ta ƙurawa ido tana tunano wani abu da ya ta6a faruwa acan lokacin baya shakeru da suka gabata, ta ta6a haihuwa ya'yan suna mutuwa wanda silar hakan Yaja har sir mubarak Ya hanata haihuwar gaba ɗaya gudun kada itama tarasa ranta kamar yadda ya'yan da take haihuwa suke rasa ransu da zarar sun dira a duniya, Allah kadai yasan halin da ta shiga awannan lokacin saboda ta kwallafa rai akan son taga ta haihu da sir mubarak sai dai Allah bai bata ba shiyasa har su hajiya saratu suke yimata gorin sai dai taci ta kasayar
Yunkurawa tayi jiki ba kwari ta mike ta futo daga ɗakin nasu ta nufi bedroom din jazz sai da ta matse kwallar da ta taru a idanunta kafin tayi mashi sallama shiru ba'a amsa mata ba, har ta fara tunanin ko yayi bacci ne, shigarta ke da wuya kwatsam taci karo da wayarsa dake yashe kan floor ga dukkan alamu wurgo da ita yayi, hatta lap coat dinsa anan ya jefar da ita, hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, a razane ta kalli gadonsa a zaune ta same shi tsakiyar mattress, Ya kifa kansa bisa gwiwowin sa, lokaci ɗaya ta rasa sukuninta da sauri ta nufi kayan nashi ta kwashe su ta je ta ajiye masa kafin ta dauko wayar ta nufin gadon nashi ta hau sama ta zauna tana fuskantar shi
"Jazz meke faruwa dakai ne"? ta fada fuskanta dauke da matsananciyar damuwa
Shiru babu alamun zai tanka mata
"Nasan kana ji na jazz, ka ɗago ka kalle ni sannan ka fadamin meke damunka" A hankali Ya ɗago da fuskarsa wadda ta jiƙe sharkaf da hawaye idanunsa sun kaɗa jawur, wani irin bugu taji zuciyarta tai muryarta na rawa ta furta"jazz kuka kake? Meke damunka ne? Ko bakada lafiya ne? Aruɗe ta fada tana shafa fuskarsa
"Jazz dan Allah ka fadamin ko hankalina Ya kwanta" daƙyar Ya iya motsa la66ansa Ya furta sunan faryat, lokacin ɗaya annurin fuskar hajiya turai Ya ɗauke ɗuff, saboda ta fahimci silar shigarshi halin da yake aciki, batasan ya zatai da jazz ba, tayi fama da shi akan ya rabu da faryat amma yaƙiya saboda tasan bazata ta6a auran shi ba, hasalima ma yarinyar bata kwanta mata aranta ba, saboda fitsararta da rashin kunyarta..
"Jazz yaushe ne zaka daina yaudarar kanka akan yarinyar nan? sau nawa ina maka gargadi akan ka fita sabgarta? Na fada maka ba sonka takeyi ba yakamata ka hakura ka nemi wata ay ba ita kadai bace mace a duniya....." kafin ta ƙare maganar ya tarin numfashin ta da cewa"bazan iyaba mommy, Allah ne ya jarabce ni da sonta, wallahi nayi kokarin cireta araina amma na kasa ki tayani da addu'a Allah ya yaye min sonta in ba haka ba zatai silar da zan rasa raina..."
har saida gaban turai Ya fadi jin abun da yace, ta fahimci mahaukacin son da yakema faryat ba lallai Ya fahimce ta ba
"Me tayi maka ne"? labari Ya fara bata na abun da Ya faru tsakaninsu lokacin da ya je wurinta bai 6oye mata komai ba, har nemansa da tayi don ya bata hadin kai,
"Mom kullum na kirata sai ta ci mutuncina, tace wai ni ba namiji bane tunda bazan iya biya mata bukatarta ba, sannan bazata ta6a auran mara asali dan tsohuwar mai aikin gidan su ba...." ya faɗa idanunsa cike tab da kwalla
Ita kanta hajiya turai hawayen ne ke sintiri kan kuncinta, ta tsani taji ana yi mashi gorin asali kamar kanshi farau, ta rasa gane meke damun wasu mutanan sun manta cewa bawa bashi ke daurawa kansa ba? Allah ne Yake kaddara masa rayuwarsa?
"Jazz ta yi kuskure A kalamanta, wallahi sai tayi danasani, saboda ka fi karfinta nesa ba kusa ba, kuma kaine cikakken mai asali tunda kana jin tsoron Allah kuma ka tsare mutuncinka, ni in banda kaddarar so ina kai ina Faryat"? ta faɗa ranta amatuƙar 6ace
"Tafi ni komai tun da tana da asali"
"Kaima kana da asali jazz" da sauri Ya kalle ta
"Mom bangane me kike nufi ba, ke da kanki kika fada min baki da kowa a danginki mahaifina Ya rasu" girgiza kai tayi"na fada maka hakanne saboda ka fidda rai da kowa nawa, bana son maganar jazz ka cigaba da hakuri in sha Allah komai ya kusa zuwa karshe" tun da tafara magana jazz Yake kallonta har yau ya rasa gane dalilin dayasa bata son tayi maganar abun da Ya shafi danginsa, shi dama yasan dole tana da family dinta akwai dai wani abin da take 6oye masa, duk da yana neman ƙarin bayani daga gareta sai dai ya hakura yabarwa zuciyarsa zai cigaba da hakuri kamar yadda ta ce har zuwa lokacin da zata sanar da shi komai....
Shiru sukayi na wani lokaci babu mai magana a cikin su,
"Ina ibad"? ya tambaya yana kallon ta
"Tun bayan sallar Isha' Yai bacci, ya yi jiran dawowarka har fadamin yai ya kira layinka bakai picking ba"
murmushi yayi"Allah sarki ɗan uwana, dama nasan dole ya neme ni, na sanya wayar a silent ne saboda aiki da nakeyi"
"Bari na kawo maka dinner dinka nasan kana jin yunwa, but pls ka shiga toilet ka wanke fuskarka bana son ganin hawayen nan" ta fada tana nuna face dinsa da yatsa amsa mata yai da toh da sauri ya sauko daga kan gadon Ya nufi toilet.
Tana ta bin bayansa da kallo har ya shige kafin Ta mike ta fito daga dakin
Kitchen ta shiga ta shirya masu abinci ta fara kaima jazz a room dinsa kafin ta dauki na sir mubarak ta nufi dakin su
Lokacin da ta shiga a tsaye ta same shi hannun shi ruƙe da wayarshi Yana daddanata har ya sanya kayan baccinsa
"Ina kika je ne" ya fada ba tare daya kalle ta ba
"Na shiga kitchen shirya maku abinci ne," ta fada tare da ajiye masa tray din bisa table, murmushin gefen fuska ya dan saki batare data ankara ba, abun da bata sani ba tun time da ta shiga dakin jazz Ya fito Yabi bayanta gaba daya ya ji maganganun da su ka tattauna har recording voices dinsu yayi a wayarsa, yayi mamaki abun da yaji suna tattaunawa, maganganun sun tsaya masa aransa, wani lokaci turai tana da zurfin ciki, in har ba la6e yayi mata ba ita da jazz bayajin damuwarsu sai in tura takai bango tukunna take sanar da shi.
_______________________________✍️
Aneelerh har tayi shirin kwanciya bacci, sautin ringing din wayarta ya dakatar da ita, A hankali ta kai hannu ta dauki wayar ganin sunan surukar arziƙi yasa tayi saurin picking call din idanunta na akan baby junaid dake kwance kan mattress Yana sharar baccin sa
Cikin girmama suka gaisa da junansu
"Aneelerh kwana biyu? Ya ki ke Ya su mamin"?
"Alhamdulillah, muna nan lafiya lou"
"Ina jikan nawa ko har anyi bacci"
"Yayi bacci tun ɗazu"
"Allah sarki nayi missing nashi, Ya maganar zuwan naku?
"In sha Allah, cikin week din nan zamu zo"
"Allah yakaimu lafiya" ta amsa mata da ameen daga bisani sukayi sallama taso ta fada ma hajiya adama zancen dawowar benazir amma ta bari sai benazir ɗin tazo gidansu sai ta kira ta awaya suyi magana don ta bata mamaki, murmushi tayi tare da ajiye wayar kan nightstand, ta janyo junaid on her chest ta rungume abun ta.
_________________________________✍️
_Dare Mahutar bawa, sai dai bakowa ne ke samun kwanciyar hankalin runtsawa a cikin sa ba, saboda akwai wanda ya manta yaushe rabon da idanunsa su runtsa saboda rashin kwanciyar hankali_
*👹GIDAN KURKUKUN ƘADDARA👹*
Daki ne madaidaici mai fadi da tsayin gaske, irin ginin dutsen nan ne dayai shekara aru aru, daga saman dakin fitilun kwai ne guda uku masu haske idan ka kalli bangon dakin ta ko'ina jirwayen jinine da ya daskare, kai harta iskar dakin ta gauraya da karnin jini da warin jikin mutanan dake rayuwa a cikin sa.
Matasan Ƴan matane zazzaune kan gadajen ƙarfe, kowaccen su tana asanye da guntuwar riga launin ja wadda bata rufe gwiwar ƙafarsu ba sun rame sun ƙanjame fatar jikinsu duk sahun yakushi da kurajen fata kai gaba dayansu sun koɗe baka gane fari acikin su saboda duhun da fatarsu tayi wanda bakomai ne yajawo hakan ba face uƙubar da suke fuskanta, wadannan bayin Allahn babu irin tashin hankalin da ba su gani ba sunga bala'e da masifa tsirararsa, gaba daya an salwantar da rayuwarsu, tun lokacin da aka kaddara masu rayuwa agidan kurkukun ƙaddara amfani ake da su kamar injina, babu wani sassauci.
gaba ɗayansu babu wacce ta haura shekara sha bakwai dukansu matasan Ƴan matane gwanin ban tausayi, dukkan gabban jikinsu sun raunata, ko tafiya ba su iyayi sai dai adauke su akai su inda za'a yi amfani da su in angama a dawo da su😭 zuciyarsu da fargaba take bugawa, numfashin su da tashin hankali suke buso shi, idanunsu sun kumbura suntum sun ƙafe saboda tsabar kukan da suke sha wanda tun sunayi hawaye na zuba har takaiga ruwan hawayen sun daina fitowa sai dai kukan zuciya mai ɗacin gaske, basu da wani burin dayawuce Allah Ya dauki ransu su huta.
Biyo bayan da Garkuwa Ya gudu tare da wasu daga cikin prison haƙiƙa ran Elders yayi mugun 6aci matuƙa sun harzuƙa evil heart dinsu ta hasala, wanda silar hakan Yaja suka fara azabtar da sauran prisoners dake agidan kurkukun ƙaddara, babu imani ko miskala zarratin yanzu ko abinci mai dadi babu a gidan kurkukun ƙaddara babu wani jin dadi ko na daƙiƙa sai baƙar izayar rayuwa, Allah ne kadai Yasan adadin jinin da suka zubda na yaran da suke raino, da kuma Yaran da suka gur6ata ma rayuwa, wani shiri suka fara yiwa kansu saboda suna hasashen akowani lokaci za'a iya kawo masu farmakin bazata, kuma suna da tabbacin asirin su yana dab da tonuwa, basu ta6a fuskantar barazana da tashin hankali irin na wannan lokacin ba!!
_Zaman tattaunawa sukayi a karo na biyu a dakin sirrinsu wanda a lokacin suka yanke shawarar za su ba ɗaya daga cikin Evil giant ɗin da suke da su horon zama prison shield saboda asamu wanda zai maye masu gurbin Garkuwar su da suka rasa saboda sun fahimci yayi masu nisan kiwon da ba zasu iya tanƙwara shi ba, da buƙatar su samu wanda zai zamanto abokin karawar Garkuwa, saboda a halin Yanzu Idan aka kawo masu farmaki tare da shi to kuwa tabbas za'a ci galaba a kansu tun da babu wani giant da zai Iya karawa da shi idan ba su elders din ba, amma Idan suka gurfanar da sabon Giant din su mai ruƙe da mukamin prison shield zai yi wuya a iya rusa su in ba wani iko na Allah ba, sannan shi wannan giant din zai iya aikata duk wani rashin imani da suke so, ba a halicci zuciyarsa da imani acikin ta ba, baƙin mugune kuma azzalumin mutun ne shu'umi mai hadarin gaske, baisan menene tausayi ba, kurma ne sannan makahone bayaji baya gani in ba umarnin ubayen gidansa ba wato Elders, Shi fa wannan giant din baida mararraba da bakin shaidanin Aljani saboda sune suka rinjayi halittarsa ta ɗan adam_
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
Our website uses cookies to improve your experience. Learn more
Accept !
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 23 Complete
by
Novels Elite Admin
June 29, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
_________________________________E23✍️
Baiyanar sa tamkar bainar mutuwa ne, zaiyi wuya mutun ya hada ido da shi ba tare da zuciyarsa tayi yunkurin dakatawa da bugawa saboda firgitarwar dake gare sa, shin wanene Wannan Evil giant din?
Asalin Sunan sa Jeremiah shi tun fil azal mugun mutunne tunkafin zamantowarsa Giant mugunta da zalunci kaɗai yasa a gaba, inaga yanzu da suka fara ba shi horon zama Garkuwar prison abun ba'a magana babban abun da zai baka mamaki ƙarancin shekarunsa dududu bai fi sa'an garkuwa ba amma a halitta basamude ne saboda girman jikinsa.
A yanzu haka Yana a cikin Rijiyar sirihi, wato mataki na ƙarshe da suke ba mutun na horan zama evil giant, ita wannan rijiyar sihirin bata ruwa bace, mazauni ne na bakaken aljanu da shaiɗanu, kwanan watan da za su gurfanar da shi yayi dai dai da lokacin da suka ɗaga na yin black night, aranar za su fiddo da shi saboda rashin imani da zalunci, nayi imanin ko makiyina bazanyi mashi fatan yakai wannan ranar agidan kurkukun ƙaddara ba saboda musifar da zata afku na bayyanar Jeremiah, rayuka ne za'a salwantar bila adadin ba yara ba ba kanana ba ba tsoffi ba hatta jarirai ba zasu ƙyale ba wa'iyazubillah.....
________________________________✍️
Motsin buɗe ƙofar ɗakin ce ta karaɗe kunnuwansu kamar gumaka babu wanda ya motsa a cikin su sai faman zare idanunsu su ke yi, gaba daya sun sha jinin jikin su saboda sun san ba alkhairi ba ne ya ke tunkaro su.
Dattijuwar macace tsohuwa tukuf, gata doguwa kamar Fatalwa, tun daga kasa har sama ta rufe jikinta da doguwar riga mai hula launin Ja, hannunta ɗaya ruƙe da sanda, kafafuwanta suna asanye cikin jajayen takalma, ta rufe fuskarta da mask launin Ja, tsoffin Idanunta ne kaɗai a buɗe, zuciyar mace da rauni aka santa amma ita wannan baiwar Allahn babu zuciyar imani a kirjinta, batasan menene tausayi ba, muguwar macace shaidaniya mai hali irin na kafuran farko, daga gaban rigarta akwai taurari uku masu kyalli daga gani tana ruke da babban muƙami na gidan kurkukun ƙaddara.
A hankali ta zura kafarta sautin takun tafiyarta kamar na dawakai babu sassauci, daga bayanta akwai wasu gabza gabzan Giants dake take mata baya su biyu, ɗaya daga cikin su yana a ruƙe da madaidaiciyar tukunyar ƙasa an rufe samanta da jan ƙyalle, yayin da ɗayan kuma Yake ruke da faranti mai ɗauke da ganye sai ƙananun kofuna da alama ruwa ne a cikin su.
A tsakar Dakin Ta dakata da yin tafiyar, wani kaskantaccen kallo ta soma jefa masu ɗaya bayan ɗaya kafin ta ba giants din umarnin su fara gudanar da abun da Ya kawo su.
Mai ɗauke da tukunyar ne Ya sauke ta ƙasa yasa hannu ya buɗe jan ƙyallen da suka rufe ta da shi, cikin takun majiya ƙarfi Ya nufi gadajen ƴan matan, ɗaya bayan ɗaya ya ke damƙar su da karfi sannan ya cusa yatsun hannunsa tsakankanin cinyoyinsu, wata auduga ce naɗe cikin panties din su yake zaƙulowa jawur da ita, wani sabon salo suka 6ullo da shi idan yaran suka fara yin jinin al'ada sai su sanya masu audugar da suka tsaface ta a cikin panties dinsu, ita amfanin ta jinin al'adar da suke zubdawa ta ke tsanewa ta ruƙe sa a jikinta ko ɗiga baya yi, suna yin hakan ne saboda a buƙace suke da jinin na su wani mugun sihirine suke yi da shi.
Tuni sautin koke koken su Ya cika dakin, Jikinsu sai kerma Yake yi saboda tashin hankali, duk audugar da ya curo a gabansu cikin tukunyar ya ke zuba su,, bayan Ya gama dattijuwar tai gyaran murya, da sauri ɗayan giant ɗin me ruke da faranti Yabi su ɗaya bayan ɗaya ya mika masu kofunan, wani ruwan sihirine a ciki mai kamar jini, ga ƙarni warinsa babu dadin shaƙa, bayin Allah kamar za su zauce a haka suke shan ruwan wasu har sun fara yunkurin amai amma saboda fargaban kada su zubda a azabtar da su yasa suka daure suna sha.
Wani irin ɗaci ne Ya ratsa maƙogwaronsu tuni idanunsu sun kaɗa jawur tamkar garwashin wuta.
"Zaku Iya ba su ganyen" dattijuwar ce ta furta maganar, watsa masu ganyen su ka yi a ƙasa, bayin Allah jiki ba kwari suka sauko kasa kamar dabbobi haka suka kama cin ganyen da aka watso masu ƙasa.
Shu'umin murmushi dattijuwar ta saki ta cikin mask dinta, Har zata Juya kwatsam idanunta suka sauka akan Gado mai ɗauke da number 100, A hanzarce Ta wurga tsoffin idanunta kan Yaran dake cin ganyen rigunansu tabi da kallo masu dauke da numbers from 80 suka fara har izuwa 99 amma babu 100 nan take ta fahimci bata acikin su lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya canza zuwa 6acin rai.
Da kakkausar Murya mai amo Ta furta sunanta
"GABRIELA"! ta faɗa tana zare idanu cikin 6acin rai
"Kada ki kuskura ki bari na sake maimaita kiran sunanki! Ki fito tun kafin ranki Ya 6aci"! Shiru babu alamun wadda aka kira da sunan Gabriela zata fito daga ma6uyarta, ran dattijuwar ya 6aci matuka ta fusata sai faman zazzare idanu takeyi tana bin ko'ina na dakin da kallo, Har yau tana mai mamakin karfin halin Yarinyar da rashin tsoranta, ga kafiyar tsiya abun a jinin ta ya ke..
Kallon sauran yaran tayi"Ina Yar uwarku gabriela take" da tsawa ta furta maganar, muryoyinsu na kerma suka amsa da cewa ba su san inda take ba..
Ɗaga murya ta kuma Yi a karo na biyu ta furta"nasan kina saurarona! Idan har baki fito ba, zakija ma sauran ƴan uwanki! Ina mai baki umarnin ki gurfanar da kanki agabana tunkafin In zaƙulo ki da hannu na" ta fada tana huci kamar zakanya, sarai tasan inda ta 6oya amma saboda karfin izza tafi son ta kawo kanta agabanta.. "
Kallon giant din da ke a gefenta tay, kamar jira yake ta bashi Umarni, azafafe Ya Nufi gadon mai number ɗari, Ya zura hannu Ya damƙo ƙafarta Kamar yar dambe haka tadinga bubbuge shi da kafafunta hada karfin halin naushin sa da hannunta, wurgo da ita yai waje ta gangaro kan floor, yar guntuwar rigarta tuni ta tattare ta haura kan waist dinta da sauri ta sanya hannu ta kamo rigar ta lullu6e mazaunanta, gaba daya nannaɗadɗiyar sumar kanta ta rufe fuskarta.
Yunƙurawa tayi da karfi ta miƙe tare da dunƙule yatsun hannayen ta alamar zatai faɗa sai faman haki take yi tana huci, daga ganin idanunta babu tsoro a cikin su, duk irin azabtarwar da ake yi masu baisa zuciyarta ta raunana ba, duk cikin yaran babu mai irin karfin halin ta.
wani irin gumi ke tsastsafowa ta hancin ta da gefen kanta, Yarinyar ba karamin kyau ne da ita ba, ga dirin jiki tana shape irin na ƙarfafan mata, gaba ɗaya jikinta tabon raunuka ne, gefen goshin ta hada ɗinkin ciwo da aka ta6a yi mata agidan kurkukun sakamakon wani mugun rauni da ta ta6a ji akwanakin baya.
Shu'umar dariya Dattijuwar ta saki tana tafa hannayenta kafin ta jinjina mata da babban yatsa ta ce"sannu da kokari Gabriella, da ace bakiyi min hakan ba da ban shaida ke jinin jatuminki bace, karfin halin ki yana burgeni ina son inga mace haka..." ta fada tana cigaba da sakin dariya mai sautin gaske.
Gabriela dake kallonta tsantsar tsanarta take ji, ta tsani matar fiye da yadda ta tsani kowa a duniyar nan...
Cike da karfin hali Ta furta"muguwa azzaluma.."
kafin ta ƙare maganar dattijuwar ta daka mata tsawa mai razanarwa, a firgice sauran yan uwanta suka koma kan gadonsu jiki na kerma.
Ita kuwa wadda akai ma tsawar babu alamun firgita atare da ita kamar ana tunzurata taci gaba da fadin"kin manta abunda na ta6a fada maki? Ni bana jin tsoronku har bada azabtarwar ku ba zata ta6a sanyani yi maku biyayya ba saboda ku din dabbobine dakikai kuma jahilai sai kun yi mummunan ƙarshe a wulakance zaku mutu...' ta faɗa tana cije la66anta da gumi ya jiƙa su.
Idanu a matuƙar zazzare dattijuwar ke kallonta da wani irin fusata ta kalli ɗaya daga cikin giant din dake take mata baya da ido tayi masa magana, cikin takun majiya karfi Ya nufi gabriella gadan gadan, lokaci ɗaya ta soma ja da baya hankalinta a matuƙar tashe batasan me zai aikata mata ba, babban abun da take jima tsoro kada ta rasa ranta ba tare da ta cika burinta na ganin ta haɗu da ɗan uwanta gabriel, ba ta son ta mutu batare data gana da shi ba, daba don shi ba da tuni ta jima da kashe kanta.
Watsa wa tayi da gudu ta nufi kofar shiga toilet dinsu ta buɗe kofar ta shige taja ta rufe, tana faman jan numfashi kamar daga sama taji dirar mutun a toilet din kamar aljani haka Ya faɗo mata tuni la66anta sun fara kakarwa muryarta na rawa ta soma faɗin karka kuskura ka ta6ani!! kada ka matso kusa da ni, ka ƙyaleni, Idan ka cutar dani dan uwana bazai kyale ka ba sai ya kashe ka..."
sambatu tadinga yi cikin rawar murya mai haɗe da tsantsar tashin hankali da fargaba sam ta manta cewa giant basa ji basa gani, kallonsa take kamar dodo gaba ɗaya inuwarsa ta lullu6eta.
Ƴan uwanta dake zazzaune kan gadajensu tuni zafafan hawaye sun wanke fuskokin su lokacin da suka fara jin sautin kururuwar gabriela ta cika dakinsu da wani irin azababben sautin kuka mai ƙaraji tamkar ana zare ranta nan take suka fahimci abun da giant din yake yi mata, haƙiƙa zuciyar su ta yi matuƙar karaya.
Tsawa dattijuwar ta kwatsa masu babu digon imani aranta
"kar in kuskura in ƙara jin sautin koke koken ku, ko da tari ne bana son ji idan ba haka ba, zansa ay maku abun da akai mata" jin wannan maganar yasa sukai shiru, kukan nasu ya koma na zuci.
Tsawon mintuna goma cuf, Kafin giant din Ya fito daga makewayin sanye cikin kakinsa kamar bai aikata wani abu ba..
Wata irin mahaukaciyar dariya tsohuwar tayi idonta akan giant din ta jinjina masa da yatsan ta.
Kafin ta juya cikin takun izza ta nufi kofar makewayin nasu ta buɗe kofar tasakai ta shiga.
A kwance ta hango ta kamar matacciya babu sutura a jikinta sai faman sakin nishin azaba ta ke yi numfashinta na fita da hucin zafi, ga wani jini dake gangarowa ta tsakankanin cinyoyin ta, baiwar Allah ko ina na jikinta Ya raunata kwata kwata bata acikin hayyacin ta, ita kaɗai tasan tartsatsin azabar da ta sha, cikin fitar hayyaci take ambaton sunan ɗan uwanta gabriel, yayin da hawaye ke tsastsafowa kan kincinta masu ɗumin gaske, idanunta sun juye jawur kamar garwashin wuta, takasa tsaida gangar jikinta sai birgima takeyi saboda zogin azabar da gabanta yakeyi mata.
Zuƙunnawa dattijuwar tayi saitin inda take, muryarta da gadara tace"bakin ki ne Yaja maki! Nayi mamaki da har kika Iya rayuwa, ay nayi zaton zanzo na same ki awargaje babu rai, amma saboda taurin kai har yanzu numfashin ki bai daina fita ba...." ta ƙare maganar tare da tofa mata yawu mai yauƙi kan fuskarta har cikin idanunta Ya shiga.
"Faɗa da aljani ba riba, wannan somun ta6i ne, nan gaba idan kika kuskura kika sake yunkurin yi min rashin ɗa'a farfesun namanki zansa ayi min shashasha kawai' ta faɗa tare da kai hannu ta damƙi sarkar cross din wuyan gabriellah taja ta da karfi ta shaƙe mata wuya, birgima tadingayi cikin fitar hayyaci ta soma kokarin ceton kanta sai dai ta gaza, dattijuwar bata kyale ta ba har saida taga ta daina motsi jikinta Ya saki tukunna ta ƙarasa balle sarkar ta jefar da ita gefe ɗaya, fatar wuyanta tayi jawur saboda shakar da tai mata.....
Mikewa dattijuwar tayi fuskarta babu fara'a ta sanya ƙafa ta naushi cikin gabriela tsabar rashin imani duk da ta sumar da ita hakan bai mata ba...
Fucewa tayi daga toilet din, ta ba giant umarnin ya dauko gabriellah, yan uwanta na kallo ya fito da ita zindir babu kaya ya ratayata kan kafadarsa suka fice daga dakin, kamar jira suke su tafi gaba daya suka rushe da kuka mai cin rai, haƙiƙa sunji zafin abunda Ya faru da gabriela saboda suna sonta, tana taimakon rayuwarsu wurin kwantar masu da hankali idan damuwa ta addabe su sai gashi yau sun gaza taimakonta sunaji suna gani anci zarafinta an wulakanta rayuwarta.
Allah kadai Yasan Ina zasu kaita? Zata rayu ko ta mutu?
________________________Gabriel💔
A firgice Ya farka daga bacci, hannunsa dafe da saitin zuciyarsa dake harbawa da karfi da karfi, fuskarsa ta jiƙe sharkaf da gumi.
La66ansa na kerma ya soma ambaton inna lillahi wa inna ilaihirraji'un.
zuciyarsa ce batay masa dadi, kuma yana ji aransa wani mugun abunne ya faru da yar uwarsa dake acan gidan kurkukun ƙaddara, saukowa yai daga kan gadon su, yakai hannu ya kunna switch din dakin haske ya gauraya ko'ina, idanunsa sun cika da kwalla, gaba daya ya rasa meke masa daɗi.
A hankali yake yin tafiya kamar wanda aka zarewa laka sam babu karsashi a jikinsa, toilet ya shiga bayan ya fito ya nufi closet dinsu ya canza kayan jikinsa da jallabiya, kafin ya tsaya kan darduma ya fara jera nafilfili saboda yai mata addu'a.
Bayan ya kammala jiki asanyaye ya ɗaga hannayensa sama ya fara addu'o'i hawaye na wanke fuskarsa
Shesshekar kukansa ce ta farkar da naufal, tunkafin ya bude idanunsa kunnansa suka soma jiyo muryar sajeed Yana fadin"Ya Allah kada ka bari acutar min da ita, Ya Allah ka kare min ita daga sharrin duk wani abun cutarwa...
Da wata irin kasala naufal ya sauko daga kan gadon yaje gefen prayer mat din Ya zuƙunna Yana dubansa.
"Sajeed meke damunka ne naga kana kuka"?
Idanunsa jawur ya kalle sa"Naufal bana jin dadin zuciyata, ina ji araina wani abu Yana faru da gabriela, kwata kwata banyi bacci mai dadi ba"
Dafa kafadarsa naufal yai cikin kulawa da nuna tausayawa yace"meyasa baka ta da ni munyi sallar atare ba"?
"Bana so na takura maka" girgiza kai naufal yayi"babu takura, nima yar uwata ce sajeed, zan iya hana idona bacci don muyi mata addu'a"
Kallonsa kawai yai ba tare daya ce masa wani abu ba.
"bro ba ka tunanin Danish zai Iya taimaka mana? Da alamun ruɗu sajeed ya furta"bangane me kake nufi ba"
Naufal yace"ina nufin me zai hana mu nemi taimakonsa akan ya ɗauko mana yar uwarmu, tun da yana da ƙarfin da zai iya yin hakan"
"tayaya zai iya zuwa gidan kurkukun ƙaddara Ya taimake ta? ni bazan Iya tunkararsa da maganar nan ba, saboda bana so ya sake shan wahala, Za su Iya cutar da shi idan Yaje......." Ya faɗa Yana faman matse kwalla, kafin wani Ya kuma furta kalma sautin motsin buɗe kofar dakin su Yaja hankulansu ga duban door room din, kusan a tare suka zabura suka mike tsaye suna kallon shi babu wanda Yayi zaton shi ne, saboda bai ta6a shigowa bedroom din su ba, watakil Yana ɗan zagaye gidanne Ya jiyo sautin muryoyin su shiyasa ya shigo dakin na su
Har suna baki wurin gaishe da shi cikin girmamawa.
Bai amsa masu gaisuwar ta su ba, gaba daya hankalinsa na akan fuskar sajeed, farar jallabiya ce a jikinsa ta kamasa.
"Meke faru ne"? Ya jefa masu tambayar, da sauri naufal Ya nuna sajeed da yatsa"shi ne ke kuka"
takawa yayi a hankali Ya karasa gaban sajeed yakai hannu ya dafa kafadarsa
"I'm sorry nayi maku la6e, ba hali na ba ne, na fito ina zagaye gidanne sai najiyo voices ɗinku kuna magana, bakomaine Yaja hankalina ba, face sautin kukan ka, fadamin meke damun ka" da wata irin sanyayyar murya mai haɗe da kasalar bacci ya furta maganar
Sajeed bai 6oye masa komai ba, dangane da Sister dinsa, ba zato ba tsammani yaji chief Yai huggin dinsa da hannu biyu kamar kaninsa, tuni yaji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarsa kamar an yaye mashi damuwar shi, a hankali chief ya daura hannu daya kan bayan sajeed Yana ɗan bubbuga masa bayan cikin sigar lallashi muryarsa kasa kasa kamar tameyin raɗa ya furta"ka cigaba da yi mata addu'a, Allah Yana atare da su, kuma Yana sane da duk wani hali da suke a ciki, in sha Allah komai yazo karshe, In har sister dinka nada tsawaicin kwana zata rayu ne kamar yadda kuma kuka rayu bayan wahalar da kuka fuskanta....." daɗaɗan kalamai chief ya cigaba da furta masa, ko a mafarki ba su ta6a tunanin chief zai shigo bedroom dinsu balle har ya rungumi ɗaya daga cikin su, sun kara ganin darajarsa da kimarsa a idanun su, sunyi mamakin hakan sosai, mutumin ya ƙara siye zuciyoyin su.
Sai da ya tabbatar Ya kwantar masa da hankali kafin ya raba jikin su daga na juna.
Fuskarsa da damuwa ya furta"time din sallar asuba yayi, ina jiranku a falo ku shirya mu tafi masallaci, ku sanar da sauran yan uwanku maza" amsa masa sukai da toh, gently ya juya har Ya kusa fita daga dakin muryar sajeed ta ratsa kunnansa.
"Nagode chief, kamar yadda ka faranta min rai, kaima Allah Ya faranta maka naka"
Ba tare daya juyo ya kallesa ba Ya furta"Ameen, but ku kira ni da sunana Owais, zanfi jin daɗi"
Murmushi suka saki atare suka hada baki wurin furta"Yaya Owais" jinjina kansa yai kafin Yasakai Ya fuce daga dakin, wayyo Allah dadi kamar jira suke Ya fita, da sauri Sajeed Ya ruko gaban rigarsa ya soma shinshina kamshin turaren chief.
"Naufal shinshina kaji" shinshinawa naufal yayi sai dadi suke ji
"Wallahi baka ji dadi ba daya rungune ni, sai naji kamar an wanke min damuwana, mutumin Yana da mutunci sosai komai nasa yana burgeni....." santin chief suka cigaba dayi.
Kafin daga bisani naufal yace"yana fa jiranmu zamu tafi masallaci, mu yi sauri mu shirya"
💘UNAISAH ANGEL💋
kiran sallar asubahin farko, wayarta ta fara ringing kamar zata fasa kunnuwan su, cikin duhu ta farka tare da laluba hannu ta damƙo wayar dake ajiye kan nightstand ta ɗago da ita ba tare da ta duba sunan mai kiranta ba tai picking
"Unaisah! Ina kika shiga inata jaraba kiran layinki bana samu" wata irin zabura tayi aɗan ruɗe saboda bata gane wacece ba.
"Nasan baki gane mai magana ba, Aunty pretty ce"
Ajiyar zuciya ta sauke muryarta da kasalar bacci ta ce "Yanzu na gane, Ina kwana kin tashi lafiya"
"Ki yi hakuri na katse maki baccin ki, na damu da son jin awani hali kike a ciki kwana biyu ba ki neme ni ba"
Muryarta adidashe Tace"ba komai, nima kina araina"
"Ban yarda ba, meyasa baki kara kirana ba? Ni ay fushi ma nake dake, kin manta dani" muryar benazir da alamun 6aci rai tay maganar.
"Ba haka bane wallahi ban manta dake ba, nayi rashin lafiya ne amma yanzu naji sauƙi, wayar ma bata a hannu na sai jiya na kar6e ta"
Tana jiyo sautin muryar aunty pretty tana zabga salati gaba daya ta ruɗe jin bata da lafiya
"Inna lillahi! Yanzu ya jikin naki? da sauki?
Murmushi unaisah tayi jin yadda ta ruɗe"ay na fada maki da sauƙi yanzu"
Tana jiyo sautin ajiyar zuciyar ta
"Har naji sanyi araina, Allah ya ƙara maki lafiya, wallahi baki ji yadda naji ba saboda na damu dake, dan Allah Idan nan abuja kuke da zama, ki bani dama inzo gidan ku, dama yau nakeson fita anguwa"
waro idanu unaisah tayi da sauri tace"a'a ni ban ma ta6a zuwa abuja ba, a kano mu ke"
"Allah sarki, kinyi min nisa, in sha Allah wata rana zan kawo maku ziyara"
"Nagode da kulawarki a gare ni" sun jima suna waya kafin daga bisani su ka yi sallama, ta ajiye wayar tana faman sauke ajiyar zuciya, ita kanta tana son haɗuwa da matar sai dai tasan ba abune mai yiwuwa ba, na farko batasan wacece ita ba? Idan har dagaske number da take amfani da ita ta sajeed ce me zai biyo baya?
da wannan tunanin ta sauko daga kan gadon ta kunna hasken dakin nasu
a hankali ta sauke idonta kan Deeja dake bacci tana jan minshari kwatsam taga ta fara mirginawa zata faɗo ƙasa daga kan gado, cikin zafin nama ta yi hanzarin tallabota a hankali ta wurga ta kan mattress din
Murmushi ta dan saki kafin ta juya ta shiga toilet, har yau tana mamakin jinin daya dauke mata tun bayan da ta sha bakar wahala bai dawo ba, har cikin ranta bata ji dadi ba, saboda taji ance alamun girma ne ga mace, kuma idan tanayi boobies ɗin ta zasu kara cukowa sannan hips dinta zai ƙara faɗaɗa komai ma na jikinta zai canza ta zama cikakkiyar budurwa, a gaban sink ta tsaya tana lalubar wurin don taga idan za'a samu ko da alamunsa ne sai dai bata ga komai ba...." fuskarta ayamutse ta kalli mirror kamar zata fasa ihu haka take ji, ita da take son ta zama house wife idan har bata fara wadannan abubuwan ba ina ita ina iya zama matar aure? ta faɗa aranta, kafin ta sa hannu ta zame wuyan rigar baccin ta, ta soma leƙen kirjin ta, murmushi tayi ganin sun ƙara girma ba laifi, wani irin dadi ne Ya lullu6e ta, har yau bata bari danish ya gan su ba, saboda kullum in zata sanya kaya sai ta ɗaure su tamau don karsu fito.
jujjuyawa ta yi agaban mirror din tana kallon qugunta, ni dai na rasa me angel take ma zumudi, da alama batasan meye ake azaman auran ba.
Gaba ɗaya matasan gidan sun tafi masallaci, bayan sun kammala sallah shiekh imam ya zaunar da su don suyi karatun da yake biya masu kullum.
Fitowa yai daga bathroom, waist dinsa daure da towel fari, gaban dressing mirror Ya tsaya zuciyarsa cike fal da tunanin halin da sajeed ke aciki, saboda Ya damu da yaran musamman wadanda ke acan gidan kurkukun ƙaddara sun tsaya masa a zuciyarsa, ayanzu baya da wani buri da ya wuce su kai masu ɗauki, shaf shaf Ya shirya kanshi cikin dark jeans tare da v neck shirt ta ɗame fatarsa.
Hayewa yai kan gadonsa ya daura kansa bisa pillow, hannunsa ruke da wayarsa, layin Boss Ya danna ma kira bayan yai picking suka gaisa da juna
"Inason ganinku, tare da salsabeel a room dina" amsa mashi boss yayi da toh"
Bayan wasu ƴan mintuna, wayarsa tai alert, unclock Ya danna a hankali kofar ta buɗe suka shigo su uku, cikin girmamawa suka gaishe da shi ya amsa masu
"Have a seat" ya fada Yana nuna masu couch, zama sukai suna fuskantar sa... Ya ɗan dauki lokaci kafin ya dan bude idanunsa dake a lumshe ya dubesu daya bayan daya kafin ya tsayar da idanuna akan salsabeel
"me yakamata mu yi? bana son abun yadau lokaci, ko dan saboda sauran yaran dake fuskantar barazana da buƙatar mu kai masu dauki....." babu wasa akan fuskarsa yai maganar
Calmly Salsabeel Ya fara magana"yalla6ai, ni bani da hanyar da zan iya jagorantar mu zuwa gidan kurkukun ƙaddara, saboda garkuwar sihirina ta karye kuma ina da tabbacin daga wajen su ne suka yi min hakan, amma nasan ɗan uwana zai Iya taimaka maku, shi kadai ne yasan hanyar da zai shigar daku Gidan kurkukun ƙaddara amma fa dole mu bi komai asannu kada muyi gaggawa saboda gidane mai hatsarin gaske, wani irin kurman ginine idan har baka da ilmi akansa kai kuskuran shiga kwakwalwarka zata iya ta6uwa"
Jin wannan maganar daga bakin salsabeel Yasa Taj da big guy suka kalli junansu da alamun rudani.
"Amma idan har Garkuwa ne zaiyi maku jagora shi ya san ta yadda zai shigar daku ba tare da kun sha wahala ba, amma fa da wuya danish Ya bamu haɗin kai, mutum ne mai wuyar sha'ani yana da kafiya, kuma har yanzu shi garkuwar su ne zasu iya sarrafa shi daga can kurkukun, ni dai ashawarata tun yanzu ku fara jan shi a jiki kuna koya masa abubuwa masu mahimmanci kamar rubutu da karatu tun da baisan komai ba ta hakanne zai fara sakin jiki da ku har asamu abun da ake so" gaba ɗaya sun gamsu da bayanin salsabeel.
Numfasawa chief yai kafin ya ce"in sha Allah zamu yi ƙoƙarin jan shi a jiki,"
Big guy yace"ni abunda ke ɗaure min kai da yaron kwata kwata baya son mutane su rabe shi in ba yan uwansa ba, kuma baya son wani ya rabi yan uwansa, meyasa"? ya tambaya yana kallon salsabeel
"Rashin sabo ne, idan Ya saba da ku zai daina, amma fa da buƙatar ku guji bata masa rai, in har ya nuna baison abu to kada ayi masa in ba haka ba komai zai iya faruwa, idan ransa ya 6aci evil heart ɗinsa zata iya motsawa abun da bana fata" ta6e baki big guy shi dai har yanzu bai yarda da Danish ba.
Shiru sukayi na wani lokaci
"I understand that dealing with them won't be easy." gaba ɗaya suka maida duban su ga chief da yai maganar
"in sha Allah, zamu yi zaman tattaunawa tare da chief of army, da kuma commender na america, bayan haka za mu tuntubi rassan jami’an ISOD da ke wasu kasashen, saboda taron ya shafi kowa da kowa. Dole ne mu hada kai kafin mu ci nasara a kansu. "
"Haka Yakamata yalla6ai" suka fada atare
Lumshe idanunsa yai gaba daya sun fahimci damuwar abunne ke addabar zuciyarsa
A lokacin da basuyi tsammani ba suka ji ya furta"na rantse da wanda raina ya ke a hannunsa wallahi duk wanda na kama da sanya hannunsa a kungiyar matsafan kurkukun ƙaddara sai ya ɗanɗani kuɗarsa ko da kuwa mahaifina ne bazan raga masa ba, ..., " yayin da yake yin maganar idanunsa sun kaɗa jawur saboda tsantsar 6acin rai
"In sha Allah sir mahaifinka ba zai ta6a zama ɗaya daga cikin su ba..." kafin taj ya ƙare maganar chief yai hanzarin katse sa yana huci yace"nima ina fatan hakan amma nasan mawuyacin abune, boss bana son na zurfafa bincike saboda fargaban kada inga wanda banyi tsammani ba, Ina jin tsoron ace akwai sanya hannun wani a family dina zuciyata zata karaya watakil ma hakan zaiyi silar da zuciyata zata buga...." ba su ta6a ganin tashin hankali tsantsa akan fuskar chief irin na yau ba, kwata kwata babu walwala atare da shi
Hada baki sukai wurin kwantar masa da hankali suna bashi baki, dakyar suka samu ya lafa yana faman sauke ajiyar zuciya ya kifa kansa jikin pillow... Bai sake dagowa ba, kamar bacci ne yai awon gaba da shi.
Miƙewa sukai atare suka bar dakin, zuciyoyin su cike fal da tashin hankali, su kansu tsoron ranar da asiri zai tonu suke yi saboda sun san dole akwai na jininsa, a kwanakin baya ya ta6a basu labarin kiran sirrin da wani bawan Allah yake yawan yi masa akan Ya binciki danginsa akwai bara gurbi acikin su wadanda suke sadaukar da yaran family ɗinsu har faɗa masa yai yaran da ake haihuwar su a mace ba mutuwa sukai ba suna nan da yaransu, bai ta6a maida hankali akan mutumin ba sai bayan da prisoners suka bayyana tukunna Ya fara gasgata maganar mutumin da har yau baisan wanene shi ba..."
Abakin kofar dakin nasa suka dakata da yin tafiya suna kallon junansu damuwa ce ƙarara akan fuskokin su kowa da abun da yake saƙawa aran shi sam sun kasa magana daga bisani suka fuce.
Chief Har ya fara nutsawa cikin baccinsa Wayarsa dake ajiye kan drawer ta fara ringing kaitsaye sautin ya daki kunnansa
A hankali yadan bude idanunsa wadanda ke lullu6e da yalwar gashi ya kalli ceilling din dakin kafin miƙa hannu ya ɗauki wayar
Motsa la66ansa yai tare da furta sunan Uncle hateem.
Picking call din yai
"Uncle am sorry, jiya na shiga bedroom dinsa na taras yana bacci shiyasa ban kira ka,"
On the other hand prime minister yace"Son ka hanani ganin maganin da zai warkar min da zazzabina....."
"Sorry uncle nayi laifi ay min afwa"
"It is okey, yanzu yana ina ya farka daga bacci"?
"Yanzu zanje bedroom dinsa na duba sa"
"Okey, akwai sako da za'a kawo masa daga company.." tun kafin ya ƙare maganar chief ya furta"uncle wani sako kenan"?
"Idan an kawo zaka gani, nasan idan na fada maka ba zaka bari sakon ya iso ba, zaka hana ne"
"Haba uncle, ni na isa in hanaka yin alkhairi..."
"Hakane, amma bazan fada ba" ya faɗa da zolaya
murmushi chief yai"andai hanani jin menene bakomai in an kawo zan gani, bari naje na basa ku yi magana"
"Video call zamuyi zanfi jin dadin ganinsa" amsa masa yai da okey, janye wayar yai daga kunnansa Ya nufi desk ya dauko ƙaramar laptop dinsa Ya sauko down babu kowa sai masu aiki dake zaryar kai abinci kan dining, ta elevator ya hau ta sauke sa second floor........
Abakin ƙofar ya tsaya yai masa knocking, shiru ba abasa iznin shiga ciki ba, yanke shawarar shiga yai a hankali ya tura kofar a zaton sa bacci yake yi, yana shiga ciki yaji alamun motsinsa a toilet, har ya juya zai fita da niyar anjima zai dawo sai kuma yaji an bude ƙofar, fitowa yayi daga ci ki jikinsa asanye da kayan baccin sa
Ganin mutum adakinsa Yasa shi cin burki ya tsaya yana kallon bayansa cike da mamakin wanene ya shigo masa bedroom dinsa...
A hankali chief Ya juyo suka fuskanci juna, nan take danish ya ƙara daure fuskarsa tamau babu annuri.
Takawa yai zuwa gabansa Ya miƙa masa hannu don su gaisa, maƙe hannunsa yai alamar bazai bayar ba,
"Ba ay min haka" ya fada tare da sanya hannu ya janyo danish yayi huggin dinsa kamar zai maida sa cikin sa, kamar wani mugun abu ya rungumesa sai kankame jikinsa yake yi, bayan chief ya raba jikinsa daga nasa ya soma yi masa magana.
"Barka da safiya, Ina fata ka tashi lafiya" shiru yayi bai tanka masa ba, wani kallon ƙasan ido yake jifa masa da ace chief baisan halinsa ba da sai yace ya tsane sa
"Ba magana? Ko da ya ke nima dalili ne Ya kawo ni roon dinka, kar6i nan uncle dina ke son magana dakai" ƙin kar6a yayi,
"Ina nufin uncle dina Hateem, mutumin dana hada ka da shi shekaran jiya, ina fata ka tuna sa" zare masa idanu danish yayi, sarai ya fahimci wa yake nufi abun da bai gane ba ta ina za suyi magana da uncle din nasa?
In a low voice ya furta"yana ina"?
Miƙa masa laptop din yai" anan zakuyi magana da shi ta video call"
wani kallon rainin wayau danish yai masa arude ya furta"tayaya zanyi magana da shi ta wannan abun" ɗan zaro ido chief yayi, can kuma ya saki fuskarsa tunawa da wanene shi
"Oh okey na fahimta lemme show you yadda zaku yi magana" bayan ya kira hateem video call fuskarsa ta cika laptop screen din, juyama danish ita yayi"look at him ku yi magana"
har saida danish Yaso Ya firgita lokacin da ya sauke idonsa kan laptop screen din ganin fuskar hateem mai ɗauke da murmushi, muryarsa cike da nishadi Yace"my baby boy danish, ka tashi lafiya? Ya ka kwana jiya? Ka yi kewana kuwa ko kuwa ka manta dani" yatsun hannun sa na kerma Ya kar6i laptop din daga hannun chief Ya kura ma hateem ido yana kallonsa batare daya furta komai ba, shi mamakinsa tayaya har ya bayyana akan wannan abun?
"Ka zauna ku yi magana" chief ne Ya fada tare da nuna masa gefen gado, jiki na bari yaje ya zauna yaci gaba da kallon hateem dake ta faman sakar masa murmushi
"Ka yi shiru baka tanka min ba, ko dai kamanta dani ne? Fadamin sai in tuna maka" shiru yayi bai masa magana ba, mamakin duniya ya cikasa
Chief dake atsaye ya harɗe hannayensa kan kirjinsa sai kallonsa yake yi zuciyarsa cike fal da tausayin rayuwarsa baiyi tunanin tsayawa ya kammala wayar ba sai ya juya ya fita daga dakin.
"Bazan damu ba, kallon da kake yi min ya tabbatarmin da ka gane wanene ni, shekaran jiyama da muka fara haduwa sai da nasha wahala kafin Ka yi min magana" ya faɗa yana murmushi.
"Nakasa jurewa ka tsareni da wadannan kyawawan idanun naka please ko da zagina ne kayi ni dai burina naji muryar nan taka mai kwantar min da hankali, chief bai fada maka nayi zazzabin rashin ka ba"? Ya fada yana marairaice masa fuska alamar zaiyi kuka...
Yana faman furzar da numfashi Ya dan motsa la66ansa kamar baison furta maganar yace"ina son ganin ka"
"Ba ga ni kana gani na ba" girgiza kai danish yai alamar a'a
"Ka fito kazo nan dakina"
"No bazai yiwu ba, ay bana kasar yanzu ina canada kai kuma kana nigeria, sai na hau jirgi tukunna zan iya zuwa wurin ka" hankali atashe danish Yace"a'a ni dai kawai kazo ka fito daga wannan abun ina son ganinka" waro idanu hateem yai da alamun ruɗani akan fuskarsa.
"Ba yadda za'ae na fito, laptop ce fa, baka ga ƙarama bace taya ni da nake babban mutun zan fito ta cikin ta" kamar zai sanya masa kuka yace"ni dai kazo ina son ganinka" ya fada yana shafa laptop screen din a kokarinsa naya gano kofar da zai buɗe wa prime minister Ya fito waje.....
Chief owais Na awaje Yajiyo sautin fashewar wani abu daga dakin danish....
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
Our website uses cookies to improve your experience. Learn more
Accept ![14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 24 Complete
by
Novels Elite Admin
June 30, 2024
Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_
سجن القد💋🔥💞
~Takun Ƙarshe🔥~
Dedicated to Aunty Kubra💋💞
قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘
An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘
Daga alƙalamin Boss Bature💋✊
Chief na waje ya ji yo sautin fashewar wani abu daga dakin danish, a hanzarce ya tura kofar ya shiga kwatsam ya taras da abun da banyi tsammani ba
Gaba ɗaya ya fasa laptop din, ya raba ta gida huɗu, hakan bai masa ba sai da Ya zuƙunna a gaban pieces ɗin Ya sa hannu Yana tatta6a su kamar wani zararre komai ya kwance masa
Chief Ya jinjina ma lamarin, abun ya ɗaure masa kai tamau, ta inda ya gode ma Allah laptop ba wadda ya ke aiki da ita ba ce, da kuwa yaja masa babbar asara.
"Meyasa ka fasa ta? why pls ? Ko kallo bai ishe shi ba, damuwarsa akan Hateem ne da bai gani ba bayan yasha wahalar balla abun
Girgiza kai chief yayi"da ita ne zaka iya amfani wurin yin magana da shi saboda baya a Nigeria" ɗagowa danish yayi fuskarsa a yamutse gaba ɗaya ya rasa sukuninsa, shi fa ya fasa ne da niyar ya buɗe ma prime minister hanyar da zai iso gare sa.
"It is okey, koma ka zauna kan gadon ka, a hankali Ya koma kan gadon yana faman bin laptop din da kallo
Ƙarasawa chief yai tare da kwashe pieces din ya fuce daga dakin Ya koma bedroom dinsa Yana shiga wayarsa ta fara ringing
Da sauri Ya ɗaura laptop pieces din kan couch kafin Ya ɗauki wayar yai picking
"Owais meya faru ne? Muna cikin yin magama da shi naji ɗuff ya katse kiran"
"Uncle mai kuke tattaunawa ne da shi"?
"Cewa yai yana son ganina in fito daga laptop din, nace masa bayadda za'ay amma ya matsamin shi ne fa naji shiru kiran ya katse"
"Uncle Ya 6alla laptop ɗin, gaba ɗaya ta tashi aiki, Allah Yaso ma ba wadda nake amfani da ita bane ay dayaja min asara"
Muryar Hateem da mamaki Ya furta"what? Ya fasata? Amma meyasa yayi haka"?
"Saboda ka ƙi fitowa, may be yana nema maka hanyar da zaka fito daga cikin ta ne"
Kusan atare suka fashe da dariya daga hateem din har chief din saboda abun Ya basu mamaki da al'ajabi......
Dakatawa sukai da yin dariyar, kowan nan su yayi shiru na ɗan wani lokaci, kwatsam sautin shessheƙar kukan prime minister hateem Ya karaɗe kunnansa lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga saboda jin abun da bai zata ba, aruɗe ya furta"uncle? Kuka kake yi? Ko dai kunne na ne suka ji min badai dai ba"?
Muryarsa araunace Ya furta"Ina tausayin rayuwarsa owais, ya karya min zuciyata yau, mutum har mutun baisan komai ba, da ace ya taso cikin kulawar iyayensa koda ba dan masu hali bane zai samu ilmin addini dana zamani dai dai gwargwado....." yana magana sautin na fita da alamun kuka maitsuma zuciya.
Lumshe ido chief yai kafin Ya furta"pls ka kwantar da hankalin ka uncle, zanyi iyakar bakin kokarina don ganin ya samu ilmi akansa, kamar yadda nayi maka alƙawarin bashi kyakkyawar kulawa..."
"Owais idan zai yiwu ku sanya shi makaranta, Ni zan ɗauki nauyin karatunsa because I want him to be like everyone else. ni wallahi da zaka bani dama zansa akawo min shi nan canada"
Cikin kwantar da murya owais yace"Uncle zuwansa canada bazai yiwu ba, akwai abun da ban fada maka dangane da rayuwar su ba, amma dan Allah kayi min Uziri uncle nan badajimawa ba zan sanar da kai komai....."
Yana jiyo sautin ajiyar zuciyarsa"Toh zan jira har zuwa lokacin, Allah yasa inji alkhairi, yanzu sai yaushe zan sake yin magana da shi saboda bangaji da ganin sa ba"
"Ka bani lokaci uncle, zanyi kokarin fahimtar da shi yadda zaiyi amfani da laptop din"
"Okey, nagode my son, sannan ina mai baka hakuri amadadinsa"
"Kada ka damu uncle, ay ba yin kansa bane rashin sani ne"
kwantar masa da hankali Yaci gaba da yi har ya samu ya shawo kanshi kafin daga bisani su ka yi sallama zama yai gefen gadonsa zuciyarsa cike fal da tunanin abun da ya faru.
_________________________✍️
"Deeja! Deeja" kamar daga sama taji ana ƙwala mata kira, firgigit ta ware idanunta masu ɗauke da bacci ta sauke su kan ceilling da alama batasan daga ina ake kiran ta ba sai faman ƙyafta ƙyafta idanu ta ke Yi, fuskarta ta ca6e da jan bakin ta
"gani anan tsaye ina kallon ki" wurga ido tai kan Unaisah da ke yi mata magana, tana a tsaye ta ruƙe qugu da hannu ɗaya, wata hadaddiyar riga doguwa ta sanya a jikin ta black colour tabi shape dinta ba karamin kyau tayi mata ba, hada light make up akan face dinta, tayi rolling veil ga wani daddaɗan fragrance dake tashi
Zumbur khadeeja ta miƙe zaune fuskar a jagule take kallon ta
"Sorry na katse maki baccin ki, safiya tayi tun ɗazu, ga shi ko sallar asuba bakiyi ba, yakamata kije kiyi sannan ki yi wanka ko kin ji dadin jikin ki"
Yamutsa fuska Khadeeja tay"to ke din wacece ne? Kin cika ni da surutu Ina yaya salsabeel da su rubina"?
Murmushi unaisah tayi"Yar uwarki ce unaisah baki gane ni ba"? Harara ta jefa mata"ni bansan ki ba Allah, ki fadamin ina yan uwana suke"?
Zuba mata ido unaisah tayi da alama zatai kafiya, don ma tasan halin kayan ta.
"Yan uwanki suna nan a cikin gidan nan, amma waye ya kawoki ɗakin mu jiya"?
Sosa ƙeya tayi kafin tace"harisuna, shine Ya rakoni in kwanta"
"Okey yanzu ki tashi ki shiga ga toilet can" ta fada tare da ɗan juyawa ta nuna mata kofar da hannu, saukowa tayi daga kan gadon tana miƙa tare da hamma ta nufi toilet ta shige, unaisah nata bin ta da kallo har ta shige.
"kin canzamin kamar ba deejana ba, naso ace kina acikin hayyacinki komai Ya faru nasan zakiyi farin cikin saurayin rayuwar da muka samu, Allah Ya baki lafiya my sister"
Bakomai take tunawa ba, face ranar da giant ya tafi da khadeeja da kuma lokacin da aka dawo masu da ita taje gaban gadon ta tana shessheƙar kuka ta tada ta daga bacci taja ta suka shiga toilet har take fada mata abun da akayi mata bayan an ɗauke ta
Tuni taji jikinta yayi sanyi lakwas rayuwa kenan, babu wanda yayi tsammanin zasu kai wannan lokacin araye sai gashi Allah ya raya abun shi, dama ance wuya bata kisa sai in kwana sun kare.
Faɗowa Dakin Haris Yayi, fuskarsa dauke da tsantsar farin ciki sai faman sakin murmushi Yake yi, ba don komai ba sai don zumudin ganin deejansa jiya da ita Ya kwana Aransa yanzu haka yazo ne don Ya ƙara ganinta ya kuma tabbatarwa kansa ba mafarki bane abun da Ya faru Jiya.
Unaisah Na ganinsa Tace"ba sallama? Me ma Ya kawoka dakinmu da sassafe"?
Shafa sumar kansa yai"ina deejana"? Aɗan ruɗe tay pretending"deeja kuma? Kayi mafarki da ita ne"!
Hankali atashe Yace"bangane me kike nufi ba, wani irin mafarki bayan jiya sun zo gidan nan har mu ka yi shagali, da kaina ma na rakota dakin ku da tace min tana jin bacci.
Fuska adaure tace"haris? Ko dai ka fara samun ta6in hankali ne? Meya kawo maganar deeja? Bayan ta riga da ta rasu tun a prison"? Yanayin yadda tayi magamar ba karamin kayar masa da gaba tayi ba jikin shi yai sanyi gwiwarsa ta sage
"Kina nufin mafarki nayi jiya" ɗaga masa gira tay"zai iya yiwuwa" shiru yayi zuciyarsa ajagule yake kallon unaisah gaba daya so take ta rikita lissafin ƙwalwarsa ..
"Lafiya ka tsaya kana kallona? Meke damunka ne"? Ƙwalla ce ta ciko idanunsa muryarsa na rawa ya furta"deeja na ta mutu? mafarki nayi jiya sunzo? har ta buɗe baki zata bashi amsa Kwatsam Deeja Ta banko kofar toilet din kamar an wurgo ta da karfi ta furta"Laahh! Haris kaine? Yana jin muryarta a ruɗe Yakai dubansa gareta lokaci ɗaya ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya, da gudu Deeja Ta nufe sa ta ƙanƙame shi tana fadin"wallahi jiya har mafarkinka nayi harisuna"
"Deejana Kin tashi lafiya"?
Tana faman Washe Baki tace"lafiyalou wlh, nima muryarka najiyo ina ga daga Cikin toilet, Har na fara alwala na katse ta"
Unaisah dake kallonsu tana dariya gaba daya mamakin ƙaunarsu ya gama cikata, wani abu daya ɗaure mata kai yadda deeja Ta yarda dashi bayan jiya sukai ta fama da ita akan ta tuna shi amma taƙiya sai gashi da yake kaunar tasu a jini take har sun shaƙu jiya izuwa yau
"Sister kada ki sake yi min irin wannan wasan, zuciyata zata Iya bugawa Allah" Yai maganar idonsa akan Unasah
"Naji romeo, bazan ƙaraba, Yanzu sai kabarta ta koma ta karasa alwalar ko fa salla batai ba" Harara deeja ta watsa mata"waike ina ruwanki dani in ma banyi sallar ba, ay ni ba kullum nakeyi ba sai na ga dama, Ko su hawwa basu min dole balle ma ke da bansan wacece ba' muryarta da shagwa6a take magana hakan bakaramin dariya ya basu ba
Lalla6ata haris yayi"rabu da ita, kishi takeyi da take don taga kinfi ta kyau, " washe baki tayi jin Yana yabonta
"Yanzu ki koma ki karasa alwalar in kin gama ki yi wanka sai ki fito muje muyi breakfast" amsa mashi tayi da toh da gudu ta juya tana fadin Kada ka tafi harisuna ka jira ni in fito Yana murmushi ya amsa mata da toh har ta shige bai daina kallon ta ba
Da zolaya unaisah tace"Hankali Ya kwanta Haris, deeja Ta dawo, No more heartbreak " dariyar farin Ciki Ya saki" ba zaki gane ba, wlh daren jiya bayan na rakota dakin ku ta kwanta dana koma dakinmu har nafila nayi saboda in nuna godiya ga Allah daya sake hadani da ita, Ina son deeja Allah Yabar mun ita har abada, in ma mutuwa zata dauke ni ta dauke mu atare" idanu abude Unaisah ke kallon shi aranta tunani take tsakanin deeja da haris da kuma ita da danish suwaye sukafi son juna tsakani da Allah? anya idan danish Ya rasata zaiyi ciwon zuciya kamar yadda haris yayi akan deeja? Ko kuwa ita idan tarasa shi zatai hauka? tabbas A yanzu bata iya ganewa tun da wani bai ta6a rasa wani a cikin su ba, kuma bata fatan abun da zai raba ta da muradin ranta, her eternal lover
"Haris Ina tayaka murna, Allah Ya nuna mana ranar auranku mu sha biki" da mamaki ya maimaita kalmar aure" yar dariya tay"cikar burin masoya kenan idan time yayi basai na maka bayani ba" murmushi kawai yayi duk da baisan me akeyi a auranba but maganarta tasa shi fara jin son ganin auran nasu.
Ƙarfe tara daidai agogo ta buga, ɗaya bayan ɗaya suke fitowa daga dakunansu zuwa dining Room kowan nan su yayi wanka Ya shirya sunyi kyau daga ganin fuskokinsu zaka shaida Anyi kwanan farin ciki daren Jiya....
Da wani irin ɗaukin junansu suka fara ƴan rungume rungumen juna, gwanin ban sha'awa, ƙaunar su a jini ta ke, harta chefs din dake a dakin cin abincin kallon su sukeyi saboda sun siye zuciyoyin su.
Mutun ukune ke babu acikin su, ummi da batool sai Danish, su kadai ne ba su kaiga ƙarasowa ba.
Sun cika dining room din da surutu Ko zama sun kasa yai,
Gyaran murya chef Yai masu Hankalinsu Ya dawo kan shi
"Barkanku mu da safiya yan mata da samari, ina fata kun tashi Lafiya" a tare suka amsa mashi da lafiyalou
"Yawwa, Yanzu ba lokacin surutu bane, lokacin bama ciki hakkinsa ne, nasan kunyi kewar Juna amma Ku ɗanyi hakuri ku zauna mana"
murmushi Kowan nan su Ya saki, ɗayan Chef din Yace"Amma in ba damuwa zamu iya sanin sunayenku? Don gaskiya bansan sunanku ba unaisah kadai nasani' Ya faɗa Yana nuna ta da yatsa
"Ba damuwa ni zan faɗa maku sunayen su," unaisah ce tayi maganar, kafin ta fara faɗa masu sunayen
"wadannan biyun masu kama da twins sunayen su Jemimah sai Azeeza" ta faɗa tana nuna su da yatsa sai faman sakin murmushi sukeyi.
Ɗaga masu hannu chefs din sukai alamar suna miko gaisuwa
"Sajeed Naufal and Javed" ta nuna kowannansu da yatsa
"Wannan Kuma sunan sa Haris ga deejarsa a gefe, kamar anta da jini suke"
"Kina nufin masoya ne"? Ɗaga masu kai tay alamar eh"
"Wow masha Allah, shiyasa suke bala'en kama da junansu ashe soyayyace atsakani, Muna miƙo maku gaisuwa" chefs din suka fada suna ɗaga masu hannu, washe baki deeja tayi shima haris din murmushi ne kan fuskarsa
"Ita kuma wannan sunanta Hannah" ta nuna hannah dake tsaye gefen parven, ga kuma Parveen acici" dariya sukai don sunsan Halinta na cin abinci"
Juyawa tayi kan su Rubina"rubina, eve and yasmin sai hibba" da sauri eve tace"kin manta jiya na fada maki yaya salsabeel Ya canza min suna hawwa"
"Yeah Na tuna sunanta Hawwa, ga kuma sarah da mubeen" ta nuna su da hannu
"thank You unaisah, kunga yanzu munsan sunan kowan nan ku saura mu saba da juna koba haka ba"? Atare suka hada baki wurin amsa masu da Yeah
"Yanzu zamu fara shirya maku wurin zamanku tun da mun samu ƙaruwa"
Ba tare da 6ata lokaci ba, mutun sha Biyu daga cikinsu suka zauna akan 12-seater dining table din da suka saba cin abinci akan shi, sauran suka samu gurbin akan 6-sitter dama ukune a dakin cin abincin.
Har sun fara cikin abincin, sautin cokulansu Ya cika dining room din kamar a restaurant yanayin yadda suka zauna, chefs din suna daga tsaye suna kallon.
Miƙewa unaisah tayi tare da kallon chefs din tace"zanje na kira aunty ummi da batool" bata jira amsar su ba tay saurin kama hanya don tasan zasu iya tsayar da ita..
Har takusa isa ga stairs, sai ga su sunfito daga daki, Hannunsu ruke cikin juna yadda kasan uwa da ɗiyarta, ummi na asanye da abaya maroon tayi rolling, batool tun kayan jiyane a jikin ta riga da wando na bacci
Suna ganinta a tare suka sakarwa juna murmushi da sauri batool ta saki hannun ummi ta nufi unaisah suka rungume juna kamar sun jima ba su a tare
"Barka da safiya My own sis, jiya ko ki neme ni, aunty ummi ta ƙwace min ke" ta faɗa tare da raba jikin su daga na juna.
"Ni da ke waye mai laifi? jiya kamar zanyi hauka wurin nemanki, ina kika je baki fada min ba"? rai aɗan 6ace tayi maganar suna kallon juna
"I'm sorry, nima bada son raina na tafi nabarki ba, naga kuna firar yaushe rabo kuma bana son in katse ku shiyasa na tafi...."
"Ina kike je ne"? Ummi ce ta jefa mata tambayar
"Part din daddyna dake acikin gidan nan, " da mamaki ummi tace"oh dama anan yake zaune? Ko da yake naga gidan ba karamin girma ne da shi ba, ay ko zan haɗu da shi maimakon ya gayyace mu muje baki ɗaya shine ya ware ki ko"? Ta fada da zolaya
yar dariya unaisah tayi"wlh ba haka bane, yace min next time kuma zai gayyace ku kuje part dinsa wurin auntyna danejo"
Murmushi ummi tayi"ai ko bai gayyace ni ba zanje da kaina, ko dan ingano danejo, inyi mata godiya saboda taimakon da tayi mana wurin ceto rayuwarki"
Fuskarta dauke da murmushi tace"naji dadin maganarki aunty ummi, Allah yabarmu atare" amsa mata sukai da ameen
"angama shirya mana breakfast a dining, naga baku futo ba shi ne nazo don in kira ku"
"Yanzu haka da kika ganmu yunwar ce ta koro mu nida baby girl dina" ta faɗa tare da ruko hannun batool har zata ruko na unaisah donsu tafi a tare tayi saurin cewa" zanje na kira danish ne" amsa mata tai da okey, bayan sun tafi ta nufi bedroom dinsa tana gab da zata shiga taji motsin fitowarsa kusan atare idanunsu suka shiga cikin na juna kwata kwata fuskarsa babu annuri ganinta da yayi ne yasa shi ɗan sakin fuskarsa tun daga kan yatsan kafarta ya fara kallonta ba karamin kyau tayi mashi ba, rigar ta ƙara fito mata shape dinta.
"My man, ina fata ka tashi lafiya," lumshe mata ido yai alamar eh
"Oh ba zaka min magana ba, kasan kuwa yadda na ƙagu da inzo ganinka" ta faɗa tana jifar shi da kallo mai kama da harara irin kallon da ke jan hankalin shi gareta
"Saboda kaga na damu kai ko" ta fada tana ruƙe qugunta
Daƙyar Ya iya haɗiyar yawu Ya furta"kin tashi lafiya"
Ɗaga mashi gira tayi"ina lafiya, pls ka shiga ka canza kayan baccin nan, sauran yan uwanmu suna jiranmu a dining muyi breakfast"
"Mu shiga atare" maƙe masa kafada tai"a'a zanjiraka anan, ka shiga ka fito" batai aune ba taji yaja hannunta cikin dakin, ba yadda ta iya dole tabi shi ciki.
Juya mashi baya tayi bayan ta cire hannunta daga nashi tace pls ka sanya kayan suna jiran..." kafin ta ƙare maganar ba zato ba tsammani taji Yai huggin din bayanta gaba daya ya kwanto da kanshi kan shoulder dinta tare da zagayo hannayensa kan waist dinta, a matuƙar ruɗe ta furta"meye haka"? Ta fada tana kokarin raba jikinta daga nashi, kamar ya ɗaureta da igiyoyi sam ta kasa ƙwatar kanta ƙara tighting nata yai tuni taji wani irin yanayi da bata ta6a fuskantar shi ba, rai a6ace ta fara zazzaga mashi masifa kamar baisan tanayi ba
Muryarshi tamkar tame jin bacci Ya furta"ki taimaka min na sanya kayan" gaba ɗaya nema yake ya burkita mata lissafin kwalwa, muryarta na rawa ta furta"wai meke damunka ne? akan wani dalili zan taimaka maka ka sanya kaya"? A hasale Ta faɗa tare da kamo hannunsa dake akan cikinta tasoma kiciniyar banbare shi bakomai take jima fargaba ba face ɗan mayafin data ɗaure kirjinta da shi muddin ya warware danish zaiga abun da yajima yana jira kuma tasan sauran in har ya gani sai wani abu ya faru.
Kamar zata fashe da kuka tace"danish ka sakeni banaso, Babu kyau! Ka matse min cikina! tsabar masifa idanunta arufe ta furta maganar
Babu akamun zai saketa sai faman goga tsinin hancinsa Yakeyi akan fatar wuyanta wani irin Yanayi da bai ta6a jin makamancinsa ba.
A lokacin da baiyi tsammani ba, Yaji ta gartsa masa cizo A hannunsa, ba don Yaji zafi ba Ya saketa, da wani irin kallo Yabita har ta fuce daga dakin da gudu.....
Fitarta keda wuya Yaji kamar ancanza mashi tunaninshi, lokacin ɗaya yafara tunanin me yasa yayi mata hakan❓
Tun akan stairs jikinta ke kakarwa kamar wadda sanyi ya kama, Gaba ɗaya Ya jefata cikin Yanayi kamar bata a hayyacin ta
Sam bataji takun tafiyar sa ba, har sai da muryarsa ta katse mata zancen zucin ta"Good morning daugher"! Wani irin firgita tayi don sai taji kamar muryar danish ne ganin daddyntane Yasa tayi saurin daidaita nutsuwarta gudun kada Ya fahimci wani abu Ya faru.
Jiki asanyaye ta nufe shi ta fada kan kirjinsa tana faman sauke ajiyar zuciya ta furta"daddy Ina kwana, Ina auntyna danejo, Ina fata kun tashi lafiya"
Dago da fuskarta yai suka hada ido cikin na juna, farat ɗaya yaɗan fahimci wani abu na damunta
"Kamar wani abu na damunki? Ko baki da lafiyane" adan rude ta girgiza masa kai"bakomai daddy lafiyana lau"
Ajiyar zuciya ya sauke
"Auntynki tana gaisheki, Kamar zata sanyamin kuka tun jiya bayan mun yi maku rakiya mun koma gida ta dinga yi min surutu akanki, yau da safe har ce min tai zakizo nace mata aa sai tace min tana son tazo taganki dakyar fa na lallasheta ta hakura' Murmushi unaisah tayi"Allah sarki auntyna. Kada ta damu har sai ta gaji da ganina'
Ruƙo hannunsa tai acikin nata"daddy muje muyi breakfast"
"Am sorry daughter bana Jin yunwa, aunynki ta cika min cikina, but da anjima idan na shigo zamu ci dinner a tare yanzu zan tafi dama na shigo ne don inga sanyin idaniyata" farfari tayi masa da ido yakai hannu ya ɗan ja kumatunta
huggin dinta Ya sake yi kamar karsu rabu
"Ki kula min da kanki, Allah Yayi maki albarka," amsa mashi tayi da ameen daddyna kaima ka kula min da kanka
Bayan sun raba jikinsu daga na juna. har ya juya zai fita sai kuma Ya ɗan dakata tare da waigowa Ya kalleta tana atsaye bata motsa ba itama shi din take kallo
"Kin shiga wurin chief "? Girgiza masa kai tay alamar a'a,"pls ki dinga zuwa kina gaishe da shi, inaso kina kyautata masa dan Allah"
"In sha Allah daddy, zanyi kamar yadda kace"
"Ina wayarki ne"
"Nabarta adaki"
"Okey, zan tura maki sakon contact dinsa, ko da baki samu zuwa wurinsa ba, ki dunga tura masa sakon gaisuwa ko ki dinga kiransa awaya kuna gaisawa" cike da ladabi ta amsa mashi da toh, murmushi suka sakar ma juna kafin taj Ya fuce daga dakin
Gaba daya abunda suka tattauna akan kun nan danish dake tsaye kan stairs Ya ɗaura gwiwar hannunsa na dama akan handrail, fuskarsa kamar jan gauta tsabar 6acin rai, ashe Yaji maganar Taj na cewa tadinga zuwa part din chief lallai kam akwai ƙura mai hayaƙi
Saboda abunda danish Yai mata gaba daya taji breakfast din Ya fita aranta, kamar an dauke mata yunwar cikinta, wani irin fitsari Taji Ya ɗaure mata mara, ba arziki ta nufi dakinsu duk Yana kallonta, tana shiga ta faɗa toilet taja ƙofa.
Tunda tafara sakin shi take ganin wani bakon abu da bata ta6a gani ba, hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, bayan ta yi tsarki, gaban madubi ta tsaya zuciyarta na harbawa da wani irin sauri, In har fa bata gano menene ba hankalin ta bazai ta6a kwanciya ba...
A 6angarensu ummi bayan sun zauna a dining chairs din, cikin girmamawa su rubina suka gaishe da ita, da fara'a ta amsa masu yayin da take kallonsu masha Allah, Gida Yayi albarka, dagowa tayi suka hada ido da chiefs din dake kallonta daga masu hannu tayi"hi sannunku da kokari" amsa mata sukai Da yawwa madam ba tare da sun daina kallon ta ba, ba tun yau ba indai zasu ganta sai sun bita da kallon mayuntaka wato sunga sura..
Gwanin ban sha'awa suke cin abinci, sam babu wanda Yayi tunanin Ina danish da Unaisah saboda firar da suke ɗan tabawa da su rubina taja hankulan su ...
___________________________Hajjaty✍️
Wuraren karfe 11 na safe ta fito daga kitchen hannunta ruke da madaidaicin faranti mai dauke da mug na green tea da kayan marmari
Tuntana tafiya take jin motsin mutun abayanta alamar akwai wanda ke bibiyarta, da zarar ta juya sai taga wayam babu kowa, hakanan ta dinga jin tsoro da fargaba, gashi babu kowa main falo din gidan duk suna a part din su.
Tana tafiya tana ƴan waige waige kamar zatayi tuntu6e, cikin takun sauri ta ƙaraso dakin baba obie, sallama ta fara yi masa daga ciki tajiyo muryarsa ya amsa mata sallamar tare da bata iznin ta shigo
a kishingiɗe ta same shi kan gadon shi, Ya tada kansa a pillow, hannusa ɗaya ruke da cazbaha yayin da idanunsa ke a lumshe, tuni kamshin turarenta Ya karaɗe ilahirin dakin har saida Ya ɗan buɗe idanunsa..
A hankali Ta ɗaura masa tray din kan table
"Barka da safiya baba, Ina kwana, kun tashi lafiya"? Murmushi ya sakar mata kafin yace"lafiylou Alhamdulillah, Ina fata kema haka" ta amsa masa da eh
Mug din ta dauka ta mika masa yasa hannu ya kar6a tare da yi mata godiya'
"Ko akwai wani abu da kake buƙata" ta faɗa cikin kulawa, bakomai ya fado masa aransa ba face maganarsu ta jiya shi da owais lokacin da yace masa ko yana son ta, shi kanshi yana yaba kulawarta da kyautatawarta agaresa matar tayi ta ko'ina, ga iya daukar wanka....jin yayi shiru bai amsa mata tambayarta ba yasa ta ɗan ɗago ta kallesa ganin kamar ya koma bacci yasa tace"baba ko ka koma bacci ne"? Girgiza kai yai alamar eh,
"Idona biyu ke nake kallo" waro idanu tayi waje jin abun da yace da sauri ta sunnar da kanta ƙasa
Ƴar dariya yayi ganin yadda ta ruɗe"kwantar da hankalin ki, ay ba laifi bane don na kalle ki, kinyi min kyau ne" gaba daya ta ƙara kame kanta, dakyar ta kakaro murmushi kan la66anta
"Tashi ki tafi, nagode da kulawarki agare ni"nike da godiya" ta fada tare da mikewa ta nufi kofar fita kwatsam tajiyo sautin takun mutun, lokacin da ta fito bata ga kowa ba, tunani tayi anya ba wani ke bibiyarta ba? ga dukkan alamu anyi masu la6e, tuni tasha jinin jikin ta, da sauri ta miƙi hanya ta koma dakin ta, kamar yadda tabar pravin haka ta same shi kwance ya lullu6e rabin jikinsa da barko.
Zama tayi gefen gadon tana faman sauke ajiyar zuciya.
Jin motsu motsin pravin yasa ta kalli bargonsa, murmushi tasaki ganin Ya fara buɗe idanunsa alamar zai farka, da sauri ta faɗa kan jikinsa muryarta da yar shagwa6a take fadin"babyn baby, tun ɗazu nake jira ka farka, ina fata ka tashi lafiya....." da wata irin kasala Ya ware manyan idanunsa da suka kada jawur saboda bacci ya sauke su kan fuskar hajjaty, manna masa sumbata tayi kan lips dinta kafin ta sumbaci karan hancin sa
"Honey, ina alkawarin da kayi min jiya? ko har yanzu ba agyara wayar bane? ta fada kamar zata sanya masa kuka tsabar shagwa6a
Har ya motsa la66ansa zai furta magana, unexpected sautin motsin ƙofarsu Ya daki kunnuwansu, lokaci ɗaya suka dakata tare da kallon ƙofar dake lilo alamar an ta6a ta...
Hankalinsu ba karamin tashi yayi ba, aruɗe hajjaty ta furta"wanene ke ta6a min kofa" muryar marwa ce ta karade kun nan su"Ni ce marwa" kallon juna sukai ita da pravin cike da mamaki, saboda babu wanda ke shigowa dakinta, tsakaninta da sauran ma'aikatan gidan daga kitchen sai in sun haɗu a main falo ko wani part na gidan, kwata kwata bata sakar masu fuskar da zasu zo dakin ta, balle har suga sirrinta..
Muryar pravin kamar tame yin raɗa ya furta"wannan wani irin ganganci ne"?
Hankalinta atashe tace"wlh ba laifi na bane, bansan meya kawota dakin nan ba, kaima ka sani bazan ta6a gangancin yin hakan ba"
"Je kiji me zata ce maki, kada ki bari ta shigo" amsa mashi tayi da toh, da sauri ta sauko ta nufi ƙofar ta buɗe ta leƙa karaf suka haɗa ido da marwa dake ta faman washe mata baki, da sauri ta ƙara babbake bakin ƙofar don kada ta samu damar ganin meke a dakin
"Marwa! Ta fada da mamaki da sauri marwa tace"am...um..barka da safiya.." bata amsa mata gaisuwar ba, sai cewa tay"ina fata lafiya? Don banta6a ganinki a ɗakina ba..." washe baki marwa tayi muryarta da alamun rashin gaskiya ta furta"dama..um inaso zan fara aikin dinner ne da wuri to na shiga kitchen din sai naga store a kulle kuma babu makulli a bakin kofar, na tambayi abla ko ta dauka shine tace min yana a wurinki" wani kallon tuhuma hajjaty take jefa mata, abun yaso bata mamaki,
Murmushin gefen fuska tayi"hmm marwa kenan, kina abu kamar wadda ta samu cutar mantau, in ba ni ba waye dama yake ruke makullin store? da har zaki tambayi abla ina Yake bayan haka wani girkine zaki fara a yanzu? Bayan breakfast da kuka kammala ko dai baki kalli agogo bane?
Sosa ƙeya tayi"wai da afara dinner din da wuri"
Kaitsaye tace mata"a'a babu bukata, kamar yadda kuka saba haka zakuyi dole sai lokaci Ya cika, sannan pls idan kinason Yin magana dani basai kinzo dakina ba! Ki kirani da landline din kitchen kamar yadda kuka saba kirana ku sanar da ni abu"! Ko amsar marwa bata jiraba, taja kofa Ta datse
Rai a6ace marwa take kallon kofar, dakin wai har ita hajjaty zata ja ma kunne kan karta kara zuwa mata daki? Lallai buri ya yi kama da mutun da alama maganar hajiya saratu zata tabbata matarnan bata da gaskiya Allah kadai Yasan makircin da take kullawa da har batason wani Yazo dakinta, dani kike magana hajjaty saina zame maki karfen ƙafa agidan nan..." acikin ranta tafada Harta fara tafiya zata koma kitchen sai kuma ta dakata tana tariyo abunda Tajiyo adakin farkon dataje tafara yin la6e a kofar, tabbas taso tajiyo muryar hajjaty kamar tana magana da wani sai dai bata kaiga shaida hakan ba
Murmushin mugunta marwa tasaki a fili ta furta"ni da ke ne" tayi maganar tare da kama hanya tabar wurin.
Bayan komawar Hajjaty dakin, a zaune ta iske pravin yana jiran ta fuskarsa a yamutse saboda Ya tsani duk wani abu da zaija asirin shi Ya tonu
"Ta fada maki abun da ya kawo ta"? Ya jefa mata tambayar, zama tayi gefen shi kafin ta sanar da shi maganar da sukai da marwa
"Ni sai nake ga kamar leƙen asiri ta zo yi min saboda babu kwanciyar hanlali atare da ita" ta faɗa tana kallon fuskarsa
Pravin yace bana tunanin haka, just ki bar komai a hannuna idan ta ƙara yi maki wani abu da hankalinki bai kwanta da shi ba ki sanar dani" ta amsa mashi da toh
___________________________ANEELERH✍️
Yau saboda da zumudin zuwan benazir ko breakfast batay ba saboda tafi son idan benazir tazo su ci abincin a tare,
Su uku ne a kitchen suke aikin girka ma bakinsu abinci, gaba ɗaya kamshin abincin Ya cika ko'ina
"Pls ku yi sauri mu kammala ta faɗa min da wuri zasu zo, dakyar ma in basu tafo ba"
"Aunty Aneelerh wacece bakuwar tamu ne"? Ana ce ta faɗa tana kallon ta yayin da take tsaye gaban gass cooker tana aikin soye soye
"Ki bari idan tazo zaki ga wacece, nafi so na baki mamaki" cikin raha ta faɗa
"Allah ya kawo su lafiya, har nakosa na ganta"
"Ameen,"
Kallon zahra tay, gaba ɗaya hankalin ta ba akan su yake ba, tana a tsaye gaban counter, inda ta ɗaura juicer ga kayan marmari shaƙe da bowl da alama ta tafi duniyar tunani, tafi karfi mintuna biyar bata ta6uka komai ba, gaba ɗaya tunaninta na akan zayn, zuciyarta sai azalzalarta ta ke yi akan son ganinsa tayi missing dinsa.
"Zahra! Zahra!!" muryar aneelerh ce ta fargar da ita lokaci ɗaya ta sauke ajiyar zuciya tare da kallon ta
"Me kike tunanine? Naga kamar wani abu na damunki"? Murmushin yake tayi"bakomai auntyna.."
"Kedai faɗa min gaskiya ko dai damuwar rashin wayarki ne"? Da sauri tace a'a wlh ba haka bane
"To menene tun ɗazu kin ƙi motsawa, Na fa faɗa miki da wuri zasu zo watakil ma sun kamo hanya,"
"I'm sorry bari na fara Yanzu zan kammala in sha Allah kafin ma su ƙaraso mun gama komai"
Har sun kusa kammala girkin Mami ta shigo kitchen din tana fadin"wai wai irin wannan kamshi haka? Tun da ga ɗaki nake shaƙo shi, lallai Yau bakin mu zasu kwashi gyara" murmushi kowan nan su Ya saki
"Mami sannu zuwa, me kikeso na zuba maki" zahra ce tay maganar
"Ni iya juice din nan Ya ishe ni, sai dai bansan ko ummi zata bukaci wani abu ba"
Zahra tace"to mami, bari na zuba maku hada snacks"
"Yawwa zahra na, adan sanya min kankara aciki zaifi dadin sha" ta amsa mata da toh
Kallon aneelerh tayi"har su nawa ne zasu zo naji dazu kamar kince hada Yayanta shureim"
"Eh hada shi tare da ɗiyar Uncle din ta"
Mami tace masha Allah, Allah Ya kawo su lafiya, bari na koma falon kada na cika ku da surutu...." har ta kusa fita ta kuma juyowa tana fadin"zahra ina jira"
"Toh mami yanzun nan zaki ganni"
Bata jima da fita ba, zahra taje ta kai masu a falo....
_____________________________✍️
ƙarfe sha biyu daidai benazir tana atsaye gaban mirror ta kammala shiryawa cikin atampha riga da skirt sun kama jikinta, ta tsara make up akan fuskarta wani irin kyawune ya ƙara bayyana ta fito ɗas balarabiyarta, ta kashe daurin dankwali bayan ta gama ta miƙe ta dauko mayafin ta dake a ninke kan mattress ta yafa shi a kafaɗa, jujjuyawa tayi gaban mirror din kafin ta sakarma kanta murmushi kyawawan dimples dinsa suka lotsa..
"Aunty benazir yaya shureim yace in baki fito ba zamu tafi mu barki agida" ta cikin mirror ta hango zeentu da tayi maganar, kamar aljanna ta ca6a uban adon lace launin blue sky mai walwali da daukar ido, ɗan ƙaramin bakinta ta shafe shi da jan baki, ga wani daurin dankwali da akayi mata mai kama da ture kaga tsiya ta sauko da gashin ta, ziririn wuyanta yana asanye da ziririyar sarƙar diamond
A sukwane Benazir ta juyo fuska adaure ta kalle ta har saida tasha jinin jikin ta
Da ƙarfi ta furta"zeenatu? meye haka? Wannan ado sai kace zamu je gidan surukan ki?
Zazzare idanu tayi"ay ni ba su nayi ma kwalliya ba, ta yaya shureim ce amma idan baki son gani na da ita sai na canza wasu kayan in goge kwalliyar"
Yamutsa fuska benazir tayi"da dai yafi saboda baki kyau ba, ko meye na shafa powder wai ke kinga fuskarki kuwa? Kamar wata fatalwa? Kina fara dole sai kin shafa powder? So kike ki zama zabayyana ne"? shiru tayi tuni annurin fuskarta ya fara daukewa muryarta da yar shagwa6a tace"Aunty benazir ay na fada maki mommy ma tana shafa powder in zatay ma daddy kwalliya, kuma kema ay fara ce sol amma kina shafa powder...." kafin ta ƙare maganar benazir tace"naji, amma ay ban kaiki haske ba, bana son jan magana kije ki canza kaya in har kinaso mu je dake"
idanunta ne suka cicciko tab da kwalla benazir dake kallonta aranta ta ce kawai daga zan kara ki mu fita sai ki fini kyau hada wata sarƙar diamond...."
Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi bazan canza kayan ba, ay yaya shureim yace nayi mashi kyau, kuma yace duk inda zaije ƙafarsa ƙafata don haka dole aje dani aunty benazir" ranta yakai makura 6aci juyawa tayi da gudu zata fuce daga dakin cikin rashin sa'a highhills din kafarda suka turguɗe gaba daya ta tafi zata kife ƙasa cikin zafin nama dr shureim Ya ruƙota ta dawo jikinsa babu wanda yasan da zuwansa a cikin su ashe yabiyo bayan zeenatu.
Wankan shadda ne a jikin shi, zeenatu na jin dumin jikinshi ta ƙankameshi tana fada masa abun da benazir tace
Murmushi yasaki yana kallon benazir dake kallon sa
Da buɗar bakinsa sai cewa yai"ke baki gane ba? Kishi take yi dake saboda kinfi ta haɗuwa, itafa tun tana ƙarama in za'aje unguwa tafi so taga tafi kowa kyau don haka kada ki damu dabi'arta ce" jin wannan maganar yasa zeenatu fashewa da dariya har hakoranta suka bayyana.
Ta6e baki benazir tayi fuskarta da dan murmushi tace"yaya shureim yanzu abun da kai ka kyauta? Agaban zeenatu kake fadin hakan? So kake ta raina ni"?
Ɗaga mata gira yai alamar eh, jinjina kai tay"bakomai, na fahimci kafi son zeenatu akaina, soyayya ta rufe maka ido ya shureim ka rasa ma wa zaka so sai wannan ifritun sa'ar ƴar ciki na" ta fada da zolaya tana nuna zeenatu
"Ahaka nakesonta" ya fada yana murmushi, zeenatu sai dadi takeji har wani ƙara maƙala hannunta acikin nasa take
"Mu munyi gaba Ki iske mu a mota" yana ƙare maganar Yaja hannun zeenatu suka fuce, da sauri benazir ta dauko mayafi ta yafa a kafaɗa, hannun ta ruƙe da yar purse ta fito
A falo suka iske su hajiya layla suna fira kamar wani abu bai ta6a faruwa ba, Yanzu ta kwantar da hankalinta tun bayan abun da Ya faru jiya
"Zamu tafi mommy asanya mana albarkar iyaye" dr shurem ne yai maganar, atare suka dago da murmushi akan fuskokinsu
Hajiya sara tace"masha Allah, tabarakallahu ahsanul khalikin kunyi kyau kamar dollars" dariya suka sanya gaba dayansu
Fuskar hajiya layla da murmushi tace"nima naso aje unguwar nan dani amma zan bari zuwa nagaba" ta fada yayin da aranta take jin fargaban abun da benazir zata juyo awurin kawarta aneelerh tasan zaiyi wuya in bata fada mata ainihin abun da ya faru da mijinta da yar ta ba, daga nan zata gane tayi mata ƙaryane, tuna wannan yasa taji jikinta yayi sanyi ji take kamar ta hana au zuwa gidan saboda batason 6acin ran benazir ko kadan, fatanta Allah Yasa aneelerh tayi hankalin boye mata gaskiya.
"Mommy layla ni da aunty benazir wayafi kyau"? Zeenatu ce tay maganar da sokana
"Ay bama haɗi kin fita kyau nesa ba kusa ba" acewar layla da sauri hajiya sarah tace"a'a bana son sonkai Allah, aiko makaho ya shafa yasan wayafi kyau, auntynki tafi ki kyau nesa ba kusa ba, itafa jinin larabawa ce" kwa6e fuska zeenatu tayi jin abun da mommynta tace, da sauri ta kalli benazir dake yi mata dariya zumbura mata baki tayi
"Shureim zata bata maku lokaci, Ku tafi ku kyaleta, dama daddynta dakyar ya amince ta biku," yana murmushi yace"toh mommy mu zamu wuce" atare suka hada baki wurin firta"Allah yakaiku lafiya, ku gaida mutanan gidan"
"Zasuji in sha Allah"
Har sun kusa fita falon hajiya layla ta ce"idan kun isa gidan Benazir ki kirani awaya inason yin magana da aneelerh" amsa mata tayi da toh kafin suka fuce, su zeenatu sai rawar kai akeyi za'aje unguwa...
Abakin motar Dr shureim suka tsaya benazir ta fara daukar su hotuna da wayarta har kusan kala takwas bayan sunyi atare tayima zeenatu tare da dr shureim kafin taba zeenatu wayar tayi mata ita kadai sai kuma tayi atare da shureim......
Shiga motar sukai, Dr shureim yana a driver's seat zeenatu na zaune gefensa, benazir kadai suka bari a backseat.
"yau ni za'a nunawa wariyar, wato zeenatu ce ta gaban mota, ni kuma ta baya babu komai nima idan mijina ya dawo zan koma ta gaban motarsa ne" dariya sukayi gaba dayansu,
Bayan yai wa motar key ya fara driving a hankali Ya nufi gate din gidan babu wanda ya dakatar da su saboda an basu umarnin su barsu su fita.
Bayan motarsu ta haura kan titi kowa Ya nutsu, zeenatu sai satar kallon benazir takeyi ta mirror din motar har gwalo take mata saboda ansanyata agaban mota
Murmushi benazir tayi tare da ɗan girgiza kanta aranta ta ayyana bayan sangarta hada ƙuruciya ke damun ki
"Aunty benazir masu number din nan ba su ƙara kiran layin ba"?
"Namanta ban fada maki ba, me layin ta kirani awaya, yarinya ce kamar ki, ashe ta sanya wrong number ne, ko jiya na kirata awaya mun gaisa saboda ta kwanta min araina"
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 25 Complete
by
Novels Elite Admin
July 05, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English Gyaran Nono
"Nima tunkafin naji muryarta har naji ta kwanta min araina, idan muka dawo gida ki kira min ita mu gaisa pls" a ƙagare tay maganar
"Kamar kinsani, farko da muka fara waya da ita sai da tace min idan ina da ƙanwa kamarta in haɗata da ita, kinga shikenan sai ku ƙulla ƙawance" wani irin daɗi ne Ya lullu6e Zeenatu har ta fara imagining haɗuwarta da yarinyar tunkafin ma su fara magana a waya abunka ga me son ƙawaye,
Gaba ɗaya firar da suke Yi akan kunnan Dr shureim, wanda Hankalinsa ke akan driving din da Yake yi,
Basu sha wahalar gane gidan ba, ta hanyar amfani da address da Aneelerh ta basu har bakin gate din gidan suka iso, da sauri mai gadin gidan Ya buɗe masu gate motar su ta kunna kai ciki,
Tunkafin Dr shureim Yayi parking Aneelerh ta fito da sauri ta nufi motar su tsabar son takai garesu har tuntube takusa yi, kafin ta ƙaraso Benazir tai saurin fitowa da gudun gaske ta nufi Aneelerh suka rungume juna kamar za su koma mutun ɗaya,
Fuskar Dr shureim ɗauke da murmushi ya fito tare da zagayawa other side ɗin motar Ya buɗe ma Zeenatu, fitowa tay daga ciki ta soma bin ko'ina na gidan da kallo kafin ta sauke idanunta kan su Benazir dake a rungume da juna,
"Yaya Shureim wannan itace ƙawar Aunty Benazir ɗin?"
ɗaga mata kai yai alamar eh,
Tsawon mintuna kafin suka raba jikin su daga na juna, fuskokin su sharkaf da hawaye saboda kukan da suka sha,
Cikin shesshekar kuka Benazir tace"A.. Aneelerh! Ashe da rabon zamu ƙara ganawa da junan mu?
Itama Aneelern da muryar kuka tace "Benazir kinga yadda kika koma? Nayi maraicin ganinki, nayi kewarki aminiyata sosae, wlh bakiji dadin da nake ji ba..." daƙyar suke magana saboda kukan da suke yi har lokacin,
Zeenatu sarkin tausayi har ta fara matsar ƙwalla, shi kanshi Dr shureim dauriya ce kawai Yake Yi, amma ba ƙaramin tausayi suka bashi ba, bazai ta6a manta shaƙuwar da ke atsakaninsu ba,
Fitowa Zahra tayi daga gidan karaf idanunta suka sauka akan su Dr shureim da Zeenatu Har saida taji gabanta Ya faɗi ganin irin kyawun mutumin da kamalarsa daƙyar ta janye idanunta daga kansu ta mayar da dubanta ga su Aneelerh,
Murmushi Zarah ta saki saboda taji daɗin ganin aminnan atare,
"Ki daina kuka bana son ganin hawayen ki," Aneelerh ce tai maganar idanunta jawur Benazir tace "Idan kinaso In daina kema ki daina, taya bazanyi kuka ba Aneelerh? Nayi babban rashin da har abada bazan Iya ta6a yafewa kaina ba, laifina ne gani nake kamar nice silar da zumuncinmu ya tarwatse..." da sauri Aneelerh ta sanya hannu ta toshe mata bakinta "ki daina ɗaurawa kanki laifi, saboda bayin kanki bane tafiyar da kikai, kema bada son ranki aka raba ki da danginki damu kanmu ba...." lallashinta taci gaba da yi Zeenatu har ta fara gajiya da tsayuwa dama ita bata saba da wahala ba,
Tana faman jan ajiyar zuciya ta juya ta dubi su Shureim cikin sanyin murya tace"Aneelerh ga Yaya Shureim da Zeenatu ɗiyar Uncle ɗina" da sauri Aneelerh ta nufe su fuskarta da fara'a ta gaishe da Yaya shureim "sannunku da zuwa Yaya shureim ku shigo daga ciki" tay maganar tare da hugging ɗin Zeenatu tace "Yan mata sannunki kuyi haƙuri mun barku atsaye"
Kamar bata son haɗa ido da shureim saboda girman shi da take gani, tun fil azal tana matuƙar jin nauyinshi kuma tana girmama shi,
"Yawwa anaeelerh mun same ku lafiya",
"Lafiyalou Yayanmu" tay maganar tare da ruƙo hannun Zeenatu suka yi gaba Shureim Yabi bayansu tare da Benazir da sauri Zahra ta koma falo tana jiran su shigo don su gaisa,
Lokacin da suka shigo falon Mami da Ummi suna atsaye suna jiran shigowarsu don su tarbesu, koda Benazir tayi arba da Mami wani irin nauyinta da kunyarta ne suka kamata, Mami kuwa fara'a tasaki da sauri ta janyo Benazir ta rungumeta tana ɗan bubbuga bayanta "marhabun lale ƴata, tsawon lokaci munyi kewar rashin ki" lokaci ɗaya Benazir taji hawaye sun sake wanke mata fuska
Muryarta da shessheka ta furta"Ma..mi " sam takasa ƙarasa maganar,
"na fahimce ki basai kinyi min bayani ba, Aneelerh ta sanar dani komai, ki kwantar da hankalinki ba kuka yakamata kiyi ba, godiya yakamata mu yiwa Allah daya dawo mana dake cikin ƙoshin lafiya" Mamin ta faɗa tare da raba jikinsu ta sa tafin hannunta tana share mata hawaye
Kafin ta ɗago ta dubi Dr shureim wanda tun da ya shigo ya sunnar da kanshi ƙasa saboda nauyin Mami da yaji gani yake kamar har yanzu tabon da yai ma kansa zaisa su guje shi,
Daƙyar ya motsa labbansa zai gaishe da ita Mami tayi saurin katseshi da cewa "Allah sarki Shureim kaine ka koma haka? Gaba ɗaya kun canzamin, Shureim Ka yada zumunci ƙiri ƙiri Ka guje mu ka koma Egypt ban ta6a zaton zakai mana haka ba"
Cikin sanyin murya yace"Mami ay min afuwa nima bada son raina ba nayi nesa daku, zaman ƙasar ne Ya gagareni saboda abun da Ya faru, amma wallahi ko bayan da na tafi kuna araina..." bai ƙare maganar ba Mami ta katse shi da cewa "bakomai Shureim, duk abun da Ya faru mukaddari ne daga Allah, bawa bai isa Ya guje ma ƙaddararsa ba, naji dadin ganin ku cikin koshin lafiya sosae..."
"Ku mu zauna" ta faɗa tare da nuna masu sofas, Bayan kowa Ya zauna Ummi da Zahra suka yi masu barka da zuwa
"Muyiwa Annabi salati" acewar Mami gaba ɗaya suka yi atare kafin daga bisani Mami ta dubi Zeenatu dake ta faman zare blue eyes ɗinta, gaba daya tarasa sukuni saboda bata saba shiga mutane ba kamar tana jin tsoron su,
"Tabarakallahu ahsanul khaliqin, Ƴata wacece wannan bakuyi min bayani ba, gata dai masha Allah daga gani ba jinsin ƙasar mu bane" murmushi Zeenatu tayi,
Ummi tace"kin riga ni faɗa, tun da suka shigo ta tsole min ido, kamar in sace ta" dariya sukai cikin raha,
"Sunanta Zeenatu, ɗiyar Uncle ɗina ce" waro idanu Mami tayi haɗi da jinjina kai,
"Masha Allah, sannu Zeenatu" amsa mata tay da "yawwa"
"Dan Allah ki saki jikinki, ki ɗauka kamar kina agidanku ne, don na fahimci kamar kin takura"
Murmushi Zeenatu tayi har dimples dinta suka lotsa,
"Ina su Maminku ina fata duk suna lafiya" cikin kulawa tayi Maganar tana kallon benazir"
"Suna nan lafiya, sunce mu gaishe daku, taso mu zo tare amma tace sai zuwa na gaba",
Murmushi Mami tayi "Allah Ya kawo ta Lafiya in ma batazo ba ni na fidda lokaci inje gidan naku"
Shiru sukayi na wani lokaci, kowa da abunda Yake saƙawa aranshi, Benazir ta ƙosa su ke6e da Aneelerh don su ƙara jajantama junansu.
Fitowa daga kitchen Ana tayi hannunta ɗauke da tray na kayan abincin da suka shirya masu har zata gifta ta ɗan dakata tare da kallon baƙin nasu karaf idanunta suka sauka akan fuskar benazir, tsabar kiɗima da ganin Benazir Ƙiris Ya rage ta saki kayan abincin hannunta Jikinta Ya hau bari da sauri takai abincin Dining ta nufo su, gaba ɗaya ta zube kan carpet tana ambaton sunan Benazir,
Kusan atare suka ɗago suna kallonta duk tabi ta ruɗe muryarta na rawa take faɗin "Aunty Benazir! Kece? Ko dai makuwa nayi ne?"
Hawaye ne suka ciko idon benazir bakomai Ya faɗo mata aranta ba face Irin azabtarwar da tayi ma yar'uwar Ana mai aikin gidanta Janet taci azaba a hannunta in tai mata laifi hada duka take haɗa mata,
Cike da jin kunyar Ana tace"Ni ce Ana, ba makuwa kikai ba, fatan na same ki lafiya? Ina yar uwarki janet"
Matse ƙwalla Ana tayi "Allah Sarki Aunty Benazir Ina nan lafiyalou, Janet tana a Jos tare da Esther ni kaɗai ce anan, Aunty Benazir Ina kika shiga tsawon lokaci bamu ji ɗuriyarki ba..."
Kafin benazir ta bata amsa Aneelerh tayi saurin tarar numfashinta da cewa "Ana kije ki ƙarasa shirya masu abincin, zanyi maki bayanin komai" ta faɗi hakanne saboda bata son ana tayi maganar 6acewar su Angel gudun kada Benazir taji hankalinta Ya tashi,
"Kada ki damu, zuwa anjima kafin mu tafi zan nemeki..." amsawa Ana tayi da toh, Jiki asanyaye ta miƙe tana tafiya tana waiwayon su Benazir tana mamakin Matashiyar da suka zo da ita, aranta ta ayyana watakil itace Yar uncle ɗinsu da taji ance zasu zo da ita...har sai da ta shige kitchen tukunna ta daina kallon su,
Miƙewa Aneelerh tayi tare da kallon Benazir tace "mu shiga daga ciki",
Mami tace "kuyi me? Ba zaki bari su ci abinci ba, salon ki cika ta da surutu"
"Ba daɗewa zamu yi ba Yanzu zamu fito"
Ummi tace"ke ko an daɗe ba'a haɗu ba, tana son su ɗan ke6e ne ay firar yaushe rabo",
miƙewa Benazir tayi suka nufi bedroom ɗinta hannunsu cikin na juna,
"Shureim ya'yanka nawa Yanzu" sunnar dakai ƙasa yai jin tambayar da Mami tayi masa,
Dariya tayi "dan Allah kada kace min bakai aureba"
Cike da jin kunyarta Yace "banyi ba Mami, amma nakusa in sha Allah" tayi mamakin jin maganarsa gashi har ya fara manyanta baiyi aureba koda Yake komai sai Allah Ya nufa,
"Allah Ya tabbatar mana da alkhairinsa" amsa mata su kai da ameen,
Shigowa Ana tayi "Mami na gama shirya abincin"
Mami tace"toh, ku tashi mu ƙarasa Ciki" Dr Shureim Yace"Alhamdulillah, bana Jin yunwa sai dai ko Zeenatu in zata ci"
Maƙe kafaɗa Zeenatu tayi "nima bana jin yunwar ay naci abinci agida" yadda tai maganar yaso basu dariya har sun gane shagwa6a66iyace
"Haƙuri zukuyi ku tashi muje, Nasan baza'a rasa space a cikin ku ba ko ruwan zumunci ne ku sha" lalla6a su Ummi tayi har dai suka miƙe suka bi su Mami zuwa dining..
A 6angarensu Benazir bayan sun shiga ɗaki da Aneelerh, cike da zumuɗi suka zauna daga gefen gado
Sai faman bin juna da kallo suke yi kamar yau suka fada haɗuwa
"Kinga yadda kika canza? Kin ƙara girma kinyi kyau abunki, bani labari bayan kin tafi ina kika faɗa"?
Numfasawa tay kafin tace"Wani bawan Allah ne Ya taimaki Rayuwata, Mutumin kirki, ɗan family ɗin Obinna nasan ba zaki rasa saninsa ba, sunan shi Zaki Mubarak Obinna A ƙasar Canada Yake..." gaba ɗaya Benazir ta bata labarin Yadda suka haɗu da zaki a Abuja bayan ta gudu daga jos da yadda harya taimaketa suka bar kasar atare..
Jinjina kai Aneelerh tayi har cikin ranta taji dadi da rayuwar benazir bata wulaƙanta ba,
"Koma wanene Yayi miki wannan aika aikar in sha Allah sai yaga sakayya, tun agidan duniya, anso a cutar da rayuwarki, da yake Allah ba azzalumin bawansa bane cikin ikonsa kin faɗa hannu nagari",
"Ni inda nagode ma Allah, ban tafi da tsohon ciki na ba, da bansan a Ina zan haife shi ba, ba rabon ƴata tasha wahala wlh banyi zaton zata rayu ba, inaji ina gani nabarta a kwamin wanka tana kuka tana kallona..." kuka ne Ya ci karfinta da sauri Aneelerh ta fara lallashinta
"Ni damuwana wanene yake kokarin ganin ya rabani da dangina? Me na masa Aneelerh? Nasan bana jin magana tun a ƙuruciyata inada jan faɗa da masifa, mutane da dama na sanya su ciwon kai har da masuyi min mummunan fata amma wallahi ban ta6a zaton za'a samu wanda zaiyi min asiri, to waini me nayi masu haka??" idanunta jawur ta faɗa.
Dafa kafadarta Aneelerh tayi"in sha Allah duk wani mai nemanki da sharri kanshi zai koma, ubangiji Allah Ya tona asirin su"
"Ameen Aneelerh nagode sosai da kulawarki agareni, ni wlh banyi zaton zaku kar6e ni hannu biyu idan na dawo ba, ko gida da zan dawo nayi fargaban haɗuwa da su Daddy amma saina ga kowa Yana murnar gani na ba ƙaramin daɗi naji ba, yanzu damuwana ɗaya shine mijina da ƴata ina matuƙar jin shakkarsu saboda nasan da wuya su kar6eni hannu biyu kamar yadda kukai min..."
"Meyasa zaki ce haka? ay su sai sun fi kowa murnar ganinki"
Girgiza kai tay"ba zaki gane ba Aneelerh, bayan tafiyata lokacin ina agidan zaki, kwatsam wata rana saiga saƙon saki daga Taj hakan Ya tabbatarmin da yaji haushin abun da na masa" da mamaki Aneelerh tace"kina nufin bake kika nemi saki daga wurinsa ba?"
Ɗaga mata kai tay alamar eh, shiru Aneelerh tayi jikinta Ya ƙara mutuwa lakwas saboda taj da kanshi Ya ta6a faɗa mata Benazir ta tura masa text message tana neman ya saketa, to kenan wanene Ya shirya wannan tuggun?" Ta jafe ma kanta tambayar da bata da amsarta,
Ruƙo hannayenta Benazir tayi a cikin nata ta damƙe su sosai cikin sanyin murya tace "Dan Allah Aneelerh ki taimaka min Inason yin magana da tajuddeen, naji kince baki da layin da Yake amfani da shi, tun da suna a tare da mijinki dan Allah ki kira Uzair ɗin sai mu yi magana da shi..." Rass Aneelerh taji gabanta Ya faɗi, tuni ta nemi nutsuwarta ta rasa, batasan taya zata shawo kan Benazir ba sam ta manta da jiya ta faɗa mata hada mijinta suna a South Korea,
"Kinyi shiru baki ce min komai" ta faɗa idanunta acikin na Aneelerh, farat ɗaya ta fahimci wani abu daga yanayin da ta nuna, Wani irin kwarjini Benazir tayi mata muryarta da inda inda ta shiga faɗin "am..umm..bani da layin shima uzair...au wayarshi ta lalace zan ce....." bata ƙare maganar ba ta katse ta da cewa "Kada kiyi min karya Aneelerh ba halinki bane, dan Allah ki faɗamin gaskiya ni dama najima ina kokwanton maganar mami, daga baya sai da raina ya bani akwai wani abu da take boyemin don itama lokacin dana tambayeta lambar Taj tunda nasan bata rasata ba kamar da suka bayyana man cewa suke kula da yarinyata lokacin dana dawo amman sai ta nuna man basu da lambarshi ta inda yake, tun nan na fara shakkun maganar ta tunda ko don saboda yarinyar tawa ai ya kamata ace suna da lambar tashi da suke magana, kawai ki faɗamin in da akwae wani abu nayi maki alkawarin bazan tada hankalina ba, boyemin bashi da amfani tunda duk min daren daɗewa zanji ne kuma bazan ji daɗin ƙin sanar man da kuka yi ba...."
Jinjina kai Aneelerh tayi tuni taji ƙwalla ta cika idanunta don har yanzu zuciyarta da ciwon abun,
Numfashi taja kafin ta fara bata labarin abun da Ya faru na 6acewar su Tajudeen,
Tsabar tashin hankali Yasa Benazir saukowa daga zaunan da take a gefen gadon ta dawo kan floor dirshan ta ɗaura hannayenta biyu asaman kanta muryarta cike da tashin hankali take faɗin "INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJU'UN! INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJU'UN......" Misalta tashin hankalin da zuciyarta ta fuskanta ba abune mai sauƙi ba, Idanunta sun kaɗa jawur facial muscle dinta har kerma take gaba ɗaya jikinta ya ɗau wani irin mahaukacin zafi kamar mai fama da zazza6i sai kerma take,
Dafa kafaɗarta Aneelerh tayi muryarta a raunace ta furta "Innallaha ma'assabirin Iya abun da zan iya furta maki kenan, abun da Ya faru Ya riga daya faru Benazir, illa iyaka mu cigaba dayi masu addu'a ubangiji Allah Ya bayyanar mana da su tunda har Yanzu babu labarin suna araye ko sun mutu,
Cikin shesshekar kuka Benazir take faɗin "nashiga uku Aneelerh! Meke faruwa da rayuwata ne? Da farko An rabani da dangina hakan bai isa ba sai da akayi silar da ƴata da mijina suka 6ace! Wai wanene ke bibiyar rayuwarmu ne? Uban me muka masa...." jin Yadda take ɗaga Murya Yasa Aneelerh saurin toshe mata baki da tafin hannunta gudun kada su Mami su jiyota....
A ƙarshe ma sai ta rungumeta saboda ta samu relief ɗin abunda ke damunta
Allah kaɗai Yasan tafarfasar da zuciyarta keyi mata kamar numfashinta zai ɗauke bakomai take tunawa ba face fuskar Taj dana yarta Unaisah yanzu shikenan ta rasa su?
Gunjin kuka taci gaba da yi, kwantar mata da hankali Aneelerh ta shiga yi, suna haka Mami ta shigo ganin halin da suke ciki yasa ta nufosu da sauri tana tambayar lafiya mike faruwa ne ta gan su haka da alamun tashin hankali, zama tayi a bakin gadon ta dafa kafaɗar Benazir tana faɗin "mike faruwa ne na gan ki cikin wannan halin??" Aneelerh ce dake ƙwalla ta faɗi mata dalilin shigarta halin, yanayin damuwa ne ya bayyana akan fuskar Mami tace ma Aneelerh tunda bata sani ba ai da bata sanar mata ba, shiru Aneelerh tayi cikin kuka Benazir tace "Mami nice na matsa mata ta sanar man, 6oye mani baida amfani don koda yaushe ina sa ran haɗuwa dasu ashe ba rabo, an raba ni da mijina da kuma ƴata, Mami suwaye waɗannan azzaluman da suka tarwatsa kan iyalin mu, mi mukai masu ne don Allah" gaba ɗaya ta gama karya masu da zukatansu itama Mami har idanunta sun ciko da ƙwallan, rarrashinta ta shiga yi tana karfafa mata gwuiwa kan inda rabo sai suga sun bayyana tunda har yanzu ba'a da tabbacin ko sun mutu har ta bata misali da ita yadda ta 6ace 6at ba'asan ina take ba tsawon lokaci gashi yanzu Allah ya bayyanar masu da ita don haka ba abunda zasu yi sai suci gaba da yin Addu'a, a tare suka cigaba da rarrashinta har saida suka ga ta ɗan samu nutsuwa Mami tace ta taso suje taci abinci dama shi ta shigo tayi mata magana, idanunta sunyi jawur ta girgiza mata kai kafin cikin disashshiyar murya tace bazata iya cin wani abu ba a yanzu, dole Mami ta ƙyaleta Benazir ɗin ta buƙaci shiga toilet da sauri Aneelerh ta miƙe tana nuna mata toilet ɗin ta miƙe jiki ba ƙwari ta shiga, bayan shigarta Mami ta miƙe cike da tausayinsu ta fita, wanko fuskarta tayi bayan ta fito akan gadon aneelerh ta kwanta kamar ba laka a jikin ta, tsananin tausayinta duk Ya kama Aneelerh tana ta kallonta, bayan wani lokaci ta miƙe taje ta kawo mata abinci da juice don tasha tace mata bazata iya cin komai ba, lalla6ata tay dakyar ta samu tasha juice ɗin, shiru sukai can Benazir din tace "Ina yaronki? Naga bangan shi ba? Ina abie?"
"Bayanan sun tafi unguwa tare da Mahboob ƙanin Zahra, su abie suma basa nan amma nasan zuwa anjima kaɗan zasu dawo gidan"
"Allah Ya dawo da su lafiya" amsa mata tayi da Ameen daga haka bata ƙara magana ba har bacci Ya ɗan dauke ta a ɗakin.
____________________Chief
Around 5 na marece Ya fito daga Gym room ɗinsa, daga shi sai short baƙi a jikinsa, Ya haɗa uban gumi zufa ta ko'ina take tsatstsafo masa, Hannunsa ɗaya ruƙe da short towel da yake goge gumin jikinsa,
Bathroom Ya shiga, within 15 mins Ya fito daga wanka ya nufi walk-in closet dinsa cikin kankanin lokaci Ya kimtsa cikin suit navy blue sunyi bala'en Yi mashi kyau da alama zai fita wani wuri ne, hadaddiyar agogon hannunsa sai salki take, kafafunsa na sanye da hadaddun leather shoe ta ko'ina kamshin turarensa Ya karaɗe ɗakin,
Wayarsa ce ta fara ruri ya ɗauko tare da duba sunan mai kiran sa, hidding number ce nan take Ya gane mutumin nan ne daya saba yi mashi kiran sirri,
Picking call din Yayi tare da kara wayar a kunne,
"Naji daɗi da ka fara yadda da maganata, Yanzu Ya rage naka Owais kai kokari wurin gano su wanene miyagun dake a family ɗinka tunkafin lokaci Ya ƙure maka"
"Sai yaushe ne zaka bayyana min kanka? Ina son sanin Wanene kai?And how did you know everything that's happening with my fam?
Sautin dariyar mutumince ta cika masa kunnansa "sanin wanene ni bai da amfani, idan kuma ka damu da son sanin wanene to ka fara kawo ƙarshen miyagun dake a cikin zuri'arku" runtse ido Chief Owais yai har cikin ranshi bai son jin Ya ambaci miyagu a family dinsa zuciyarsa karaya ta ke yi kalmar bata masa dadi,
Rai a6ace yace "babu miyagu a family dina, ka kiyaye kalamanka," dariya mutumin yayi "shiyasa nake jin tausayin ka Owais saboda ka yarda da kowa na family ɗinka, me zai faru a ranar da ka gane gaskiyar da nake kokarin ganar da kai" a fusace Ya daka masa tsawa baima tsaya ya ƙarasa jin zancen mutumin ba Ya wurgar da wayar kan Gadonsa, Yana faman fitar da huci Ya furta "bazai ta6a yiwuwa ba, na yarda da family dina, babu bata gari a cikin su...." Yana a cikin wannan Halin Wayarsa ta sake Yin ringing, Ko kallonta baiyi ba a zaton shi mutuminne Ya ƙara Kiransa shiyasa bai kulata ba,
Jiki amace Ya zauna kan couch gaba ɗaya Ya rasa sukuninsa zuciyarsa sam bata masa dadi,
Wayarsa sai faman ringing take da zarar kiran Ya katse wani Yake shigowa,
Runtse idanunsa yayi bakomai Yake hangowa ba face fuskar Daddynsa data Uncles dinsa kai harma da Kakansa mutanan kirki masu Daraja a idon duniya, abune mawuyaci ya gasgata maganar mutumin in har ba gani yayi a zahirance ba, to wai wa akeso Ya zarga a cikin su? hakan ma bazai ta6a yiwuwa ba, wannan rashin imanin badai a family ɗinsa ba, sai dai wani baren dake a cikin su,
Knocking kofarsa akai, nan take alert ya shigo masa, kamar bazai tashi ba, a kasalance Ya miƙe Ya nufi wayar Ya danna unclock slowly ƙofar ta buɗe, bai kai idonsa ga mai shigowa ba hankalinsa na akan missed calls din da akai masa daga delivery man na Companynsu, tunawa da saƙon Hateem yasa shi saurin dannawa mutumin kiran bayan yai picking suka gaisa ya sanar dashi saƙone Ya kawo masa tun ɗazu Ya shigo jami'ae sun hana shi ƙarasowa ciki,
"Okey, Gani nan zuwa" ya furta,
Sauke wayar yayi daga kunnansa
Juyawar da zaiyi ke da wuya karaf idanunsa suka sauka akan ƙafafunta dake asanye cikin highhill, sam ya manta da izni daya bada na ashigo dakinsa,
Tun daga ƙasa Ya fara kallonta har Ya sauke idanunsa kan fuskarta, ganin kallon da yake yi mata ne yasa tai saurin cewa "naga kana waya shiyasa ban yi magana ba" muryarta ba ƙaramin sanyaya masa zuciya tayi ba sai yaji kamar yasha pain reliever ne,
Kallo ɗaya da unaisah tayi masa sai da ta fahimci wani abu na damunsa,
"Ina wuni,"
Lumshe idanunsa yai muryarsa da sanyi ya furta "lafiyalou,"
"Idan akwai wani aiki da zan maka ka faɗa min"
"Okey" ya faɗa tare da kallon bedroom dinsa "ki gyara min ɗakin but karki takura kanki" amsa mashi tayi da toh, Fucewa yai daga ɗakin Ya barta ita kadai wani irin dadi taji, sai da ta 6ata lokaci wurin shaƙar kamshin turarensa daya cika dakin kafin ta fara gyara mashi gadon shi,
A sitting room dinshi Yasa aka shigo mashi da ɗan sakon, da sallama Ya shigo hannunsa ruƙe da wata katuwar shopping bag mai ɗauke da logo na Obie tech,
"Barka da warhaka Yalla6ai, fatan na same ka lafiya" yana daga zaune kan sectional sofa Ya amsa mashi da barka da zuwa,
"Yawwa Sir, ga saƙon" da hannu Ya nuna masa gaban sofa ɗin da Yake mutumin Ya ƙarasa Ya sauke jakar kayan Kafin sukai sallama Ya juya ya fuce,
Ko minti biyar ba ayi ba wani senior agent Ya shigo sitting room ɗin hannunsa ruƙe da mug din coffee, cikin girmamawa ya gaishe da shi kafin Ya ɗaura masa cup din kan table din gabansa,
Da hannu ya nuna masa shopping bag din "fito min da kayan dake a ciki"
"Okey sir" zuƙunnawa yayi agaban Jakar Ya fara zaro Apple laptop sabuwa gal, tare da phone box na Iphone 15pro max, A hankali Ya ɗaura su kan rug din gaban sofa din kafin ya ƙarasa curo sauran kayan, Apple ipad da headphone tare da watch box and eyeglass case" bayan ya kammala curo su, chief Ya ɗan jinjina kansa kafin yace da shi ya maida su ciki ya amsa mashi da Okey Sir, mayar da su ciki yay sannan Ya miƙe Ya sarah mashi da hannu yay mashi alamar yaje ya juya ya fuce,
Har cikin ranshi Yaji dadin kyautar da Hateem yayi ma yaron kaya masu kyau da tsada, aransa ya ayyana zaiyi amfani da wannan damar wurin ganin Yaja shi a jiki,
Cup ɗin Ya dauka Ya fara kurbar coffee a halin Yanzu Baya buƙatar kowa a kusa da shi shiyasa Ya ke6e kansa don Ya samu damar Yin nazari,
A 6angaren Unaisah dake gyara masa bedroom dinsa, har ta gama da gadon ta dawo gaban dressing mirror ɗinsa tana jera masa perfumes ɗin yayi amfani dasu,
Tunkafin tagama take Jin kamar faɗuwar gaba, kamar ance ta ɗago ta kalli madubin kwatsam idanunta suka sauka akan shi, Rasss! taji gabanta ya faɗi, a matuƙar firgice ta juyo tana kallon shi ya harɗe hannayensa kan ƙirjinsa fuskarsa kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa, ko tayaya akai ya shigo ɗakin bayan kofar tana da security? in badai Chief ɗin bai rufeta ba, anya kuwa shi ne? Ko dai iskokan dake ajikinsa ne? Taya akai ma Yasan tana a dakin Chief?,
Yawu ta haɗiya daƙyar zuciyarta na harbawa da matsanancin bugu ta furta"..My man"
Wani kallon tuhuma Ya wurga mata tare da ƙara haɗe girarsa,
Muryarta da inda inda tace "um..ka gane, wai dama ina ɗan gyara masa dakinsa ne kaga ya taimaki rayuwarmu shiyasa nake son kyautata mashi....." kamar mara gaskiya haka ta fara kora masa jawabin da bai tambayeta ba, har wani gumi ta fara haɗawa akan fuskarta duk da sanyin A.c din dakin,
"You don't want peace" da kakkausar murya taji Ya faɗa,
"Me kake nufi?"
"Abunda kunnanki Yajiye maki"
Yai maganar tare da takawa yaje gabanta ya damƙo hannunta ya jata da karfi ya nufi ƙofar, kokarin ƙwacewa ta dinga yi tana fadin "dan Allah ka sake ni, ban kammala Yi masa gyaran ba, Daddyna ne yace na dinga kyautata masa...." ko ta kanta baibi ba har sai da Ya fito da ita daga ɗakin ya nufi bedroom dinsu da ita, A kan gado Ya wurgar da ita ta mirgina tana faman maida numfashi,
"Kada ki kuskura ki ƙara zuwa ɗakin shi idan ba haka ba Kinsan zan iya komai akanki, har Daddyn naki bazan ƙyale sa ba saina ja masa kunne akanki in har yana son zaman lafiya dani" waro idanu waje tayi tare da ɗagowa tana kallon shi, Ya haɗe rai kai kace ba daga bakinsa maganar take fitowa ba,
Harara ya watsa mata kafin ya juya zai bar ɗakin, durowa tayi daga kan gadon jiki na 6ari tayi saurin shan gaban shi Ya tsaya yana kallonta,
Wani irin kwarjini yayi mata a ido, cikin sanyin murya tace"tunda bakaso bazan ƙara ba, amma dan Allah kada ka ta6a min Daddyna wallahi ina son shi bana son wani abu ya same shi, kuma ay shi baisan alaƙar dake a tsakanina dakai ba shiyasa yace haka..." marairaice masa fuska tayi kamar zata sanya mashi kuka
wani irin kallo taga Yana bin ta da shi, tunawa da abunda Ya faru ɗazu ne Yasa tayi saurin matsawa ta bashi hanya don Ya wuce,
Yana fita daga ɗakin ta sauke ajiyar zuciya, tsoki ta dan ja abun na shi ya fara bata takaici, Wannan wani irin kishi ne? "Jarababbe kawai" ta faɗa tare da samun wuri gefen gadonsu ta zauna tana faman haɗe rai, ta ƙudiri aniyar sai ta koma ɗakin chief yi masa aiki ko ba yau ba sai dai Ya haɗiyi zuciya ya mutu, saboda shi bazata ƙi bin umarnin Daddynta ba duk da tana jin tsoron yace zaiyi mashi wani abu don ta fahimci ba kaine da shi na,
_______________Mahboob
Shigowa gidan yayi bayansa a goye da Baby Junaid, tunda yayi sallama idanunsa suka sauka akansu Zeenatu dake a falon har kusan firgita yayi da ganinta saboda kyanta da yaja hankalinsa, Aneelerh na ganinsa ta miƙe tana faɗin "Oyoyo Baby junaid ɗina, mahboob Ina ka kai min shi tun safe sai Yanzu fisabilillah, halan koma abinci baici ba" ta faɗa tare da kar6ar Junaid ta rungume shi a jikinta, sam babu kuzari a jikinshi kamar bacci ma yakeyi ya farka
Muryarsa tamkar zai fashe da kuka Yace"Mommy, Yaya mahboob bai da tausayi sai da nace masa ni ya dawo dani gida amma yaƙi ya dawo dani, kuma wallahi Allah bazan sake binsa unguwa ba" idanunsa aruntse yake masifa, gaba ɗaya mutanan falon Suka kwashe da dariya hada Benazir da bata jima da fitowa ba, Yaron ba ƙaramin burgesu Yayi ba musamman Zeenatu, duk rashin sakewarta jiki na rawa ta miƙe ta nufi su Aneeleeh tace "Aunty ki bani shi in dauke shi"
Murmushi Benazir tayi "Allah yasa ya yarda rigima ne da shi" miƙa mata shi tayi, abun mamaki jikinshi har 6ari Yake wurin Miƙa ma Zeenatu hannu don ta ɗauke shi Ummi na dariya tace "ɗan ƙwal uba yaga farar fata, da mu mukace masa yazo yadda ransa ya 6aci ɗin nan wlh ba zuwa zaiyi ba" dariya sukai baki ɗaya,
Rungumesa Zeenatu tayi har wani ƙara ƙanƙameta yakeyi, komawa tayi kan sofa ta zauna hannunta akan sumar kan shi
daga bisani mahboob Ya gaishe da su Dr shureim fuskokinsu da fara'a suka amsa mashi, gabatar masu da shi Aneelerhtayi kamar yadda ta gabatar masu da Zahra a matsayin ya'yan uncle dinta,
Sunji dadin karramasu da akayi, ko da lokacin salla yayi Mahboob ne Ya raka Dr shureim masallaci sukayi sallah atare,
Har wuraren karfe shida na marece suna agidan, Dr shureim yaso su tafi Mami ce ta tsaida su saboda abie ya kira waya yace in sunzo su jira su dawo gidan don su gaisa, Bayan dawowar su Abie a falo suka zauna wata sabuwar firar suka soma yi cikin raha hada Uncle ɗan Iya Ya dinga basu labaran ban dariya gaba ɗaya suka cika su da farin ciki, baiwar Allah Benazir daurewa kawai takeyi duk don kada su gane halin da take a ciki, Aneelerh ce da Mami kadai suka san meke damunta, da zarar sun haɗa ido da Aneelerh take yi mata alamar tayi haƙuri, har bayan sallar magrib suna gidan
Lokacin da zasu tafi har bakin motarsu suka rako su baki ɗaya Kamar kar su rabu da juna, musamman benazir da Aneelerh, haka itama Zeenatu da Junaid yaron Ya kwanta mata aranta, har hotuna tayi masu da wayar Dr shureim, ko time ɗin da zai ci abinci ita ta bashi abaki, bayan sunyi sallama da junansu suka tafi, su mami basu daina kallon motarsu ba har suka fuce daga gate din gidan kafin suka koma ciki.
______________
Tun cikin mota Zeenatu ta lura da Yanayin Benazir ta haɗe rai sosai fuskarta tayi jawur Ko magana bata son yi, Ita kaɗai tasan raɗadin da take ji ta ƙosa su koma gida saboda taji zafin 6oye mata gaskiya da Mami tayi,
Motarsu na ƙarasa shiga gida Kamar jira take Dr shureim Yayi parking azafafe ta hankaɗe murfin motar ko yar purse dinta bata dauka ba ta nufi falo,
Hankali a tashe Dr shureim Ya fito Yabi bayanta, Itama Zeenatu ta fito hannunta ɗauke da purse ɗin Benazir ta bi bayansu,
Da karfi take ambaton sunan Mami kamar maƙoshinta zai 6allo, ko sallama batayi ba,
Jiki na 6ari Hajiya layla da Hajiya Sarah suka fito daga dakunan su,
Tunkafin ma tayi magana Hajiya layla ta fahimci meke damunta abun da take gudune Ya faru, dama tun ɗazu take zullumin dawowarsu har kiran Benazir ɗin tayi amma batay picking ba balle har ta samu damar Yin magana da Aneelerh don ta dakatar da ita akan kada ta faɗa mata gaskiyar abun da Ya faru,
"Benazir ba saida nace maki idan kin isa gidan ki kira ni ba? Meyasa bakiyi hakan ba...." a rude Mami ta furta hakan, Cikin shesshekar kuka tace "Nagode ma Allah dana manta ban kira ba, abun da kike 6oye min shi aka faɗa min! Mami meyasa zakiyi min ƙarya akan 6atan mijina da ƴata?" rai a matukar 6ace tay maganar tana kallon cikin idonta,
"Wallahi baku kyauta min ba, kinsan kuwa yadda na ƙwallafa raina akan son ganinsu? Mami why? Why kikai min haka..."
"Dan Allah Kiyi haƙuri Benazir, tayi hakan ne saboda guje ma bacin ranki.." Hajiya Sarah ce ta fara kokarin shawo kanta, Zeenatu dake kuka da gudu ta nufi ɗaki ta shige saboda bata son tashin hankali, Idanunta jawur ta kalli Hajiya Saratu "miye amfanin boyemin da tayi? Bayan dole wata rana zanji awani wuri! Da ace ta faɗamin da yanzu komai ya wuce saboda ba yadda zanyi dole inyi haƙuri ....ni banji daɗi ba Mami wlh baki kyauta min ba...."
Dr shureim Sam Ya kasa magana, tsananin tausayin benazir ne Ya cika sa, baisan Ya akai Aneelerh ta sanar da ita ba,
Kallonshi Benazir tay"Yaya Shureim why? Kaima hada kai aka haɗa baki don 6oye mun gaskiya? Ban ta6a tunanin zakuyi min haka ba..."
"Zanyi maki bayani ki nutsu ki saurare ni...." bai ƙare maganar ba da gudu Benazir ta bar falon ta shige ɗakinta, tana shiga ta maido ƙofa ta datse tabar su atsaye suna kallon kallo,
"Shureim wai wanene Ya faɗa mata? Kuma kana agidan baka dakatar da hakan ba?" cike da damuwa Mami ta faɗa,
"Wallahi Mami bansan komai dangane da wanda Ya faɗa mata ba nasan dai bai wuce Aneelerh, kawai yanzu tun da ta riga ta sani muje mu lallasheta har asamu ashawo kanta,
Babu irin bugun da basuyi ma kofar dakin Benazir ba amma taƙi buɗe masu, tana jiyo sautin muryoyinsu daga waje sunata yi mata magiya akan ta buɗe masu ƙofa,
Tana kuka tace masu dama sun daina wahala saboda bazata bude ba har sai lokacin da ranta yabar gangar jikinta" wannan maganar tay matuƙar ɗaga masu hankali, Mami tun tana lallashinta har takaiga hada mata da ashar amman tayi burus taki buɗewa,
Wuraren ƙarfe tara na dare su Alhaji ubaid suka dawo gidan, nan fa suka tarar da abunda ke faruwa kowa Yayi tsaye kofar ɗakin Benazir in ka cire Alhaji musa wanda tun shigowarsu daya gama sauraran abunda ke faruwa yace su kyaleta in ta gaji zata buɗe kofar, Yana faɗan hakan Ya ƙara gaba abunsa, Babu wanda Yaji dadin maganarsa Hatta Alhaji ubaid yaji zafin Yadda Ya nuna halin ko'in kula akan halin da Benazir ɗin ke ciki, Har wurin ƙarfe 12 na dare ana abu ɗaya don dole suka hakura kowa Ya koma ɗakinshi ransu a jagule ahakan ma babu wanda Ya Iya runtsawa a cikin su..
Dr Shureim Yana Cikin Yin zarya a ɗakinsa kwatsam Ya tuna da shaƙar da ake ma Benazir idan dare Yayi Tabbas Yana ji aranshi za'a Iya kaimata hari duba da halin da take a ciki ba lallai ta iya ta6uka wani abu ba gashi ta datse kofa, Fitowa yai da sauri har Yana tuntu6e garin sauri Ya nufi kofar ɗakin Yay knocking shiru batai magana ba, Cikin sanyin murya yace "Pls idan kina saurarena ki tashi ki kunna karatun alkur'ani kada ki kwana ahaka, Yakamata kiyi hada nafila..." shiru bata tanka masa ba, jikinsa yai mugun sanyi baisan awani hali take a ciki ba, karshe zama yayi a ƙofar ɗakin don baya jin zai iya tafiya yabarta ya ƙwammace ya kwana anan.
____________________________
Sai dare Zahra ta kunna wayarta da Mahboob Ya kawo mata daga wurin gyara, Cike da zumuɗi ta shiga gallery dinta anan taga hotunan da suka ɗauka tare da Unaisah, da sauri ta fito daga ɗakinta ta nufi bedroom ɗin Aneelerh, tana shiga ta sameta a zaune kan prayer mat hannunta ruƙe da cazbaha tana ja yayin da acan ƙasan zuciyarta take tunanin ko ya su Benazir suka isa gida taji shiru bata kirata ba, har kira tay amma ba'ay picking ba,
Jin sallamar Zahra yasa ta ɗago kai ta kalle ta,
"Zahrah me kikeyi har yanzu baki kwanta ba"?
"Taya zan Iya runtsawa bayan ban nuna maki hotunan dinner ba, sai Yanzu na samu damar kunna wayar ma" ta faɗa tare da miƙa mata, Kar6a Aneelerh tayi kafin ta soma bin hotunan da kallo,
Zahra na atsaye tana kallonta, kwatsam taga Aneelerh ta zabura ta miƙe tsaye hannunta na kerma tuni cazbahar ta jima da barin yatsan ta,
A ruɗe ta furta"Zahra wacece wannan Yarinyar da kukai hoto da ita??"
Murmushi Zahra tayi "itace yarinyar da nake baki labari mun haɗu a wurin dinner ɗin, amma ya akai naga kamar hankalinki Ya tashi da ganinta?" Ta faɗa tana kallon fuskarta,
"Zahra taya hankalina bazai tashi ba, ke baki ga fuskarta da kyau ba? wannan yarinyar kamanninta sun 6aci dana Angel ɗinmu...!" Saida Aneelerh tay wannan maganar Zahra tafara tariyo fuskar Yarinyar, haba shiyasa take tayi mata kallon sani,
"Zahra bata fada maki sunanta ba"?
"Tace min sunanta UNAISAH"!
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
Our website uses cookies to improve your experience. Learn more
Accept !
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 26 Complete
by
Novels Elite Admin
July 07, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
Rass Taji gabanta Ya faɗi La66anta na kerma tace"Zahra itama ainihin sunanta Unaisah, Angel da muke kiranta nickname ne da daddynta Ya sanya mata, ɗiyar wacece ne a family din su"?
Hankalin zahra ba karamin tashi yayi ba, ganin yadda aneelerh ta ruɗe ita kanta aruɗen take
"Na manta ban faɗa maki labarin Yaran ba, Kamar Yadda naji daga bakin chief owais, kamar ba su da alaka da su, hasalima a daji suka tsinto su..." tiryan tiryan Zahra ta kwashe duk abunda Ya faru a wurin dinner din dangane da su Unaisah ta sanar da aneelerh
Kusan zaucewa tayi hannunta dafe da kai, ganin tana tangyal tangyal kamar zata faɗi Yasa Zahra Yin saurin ruƙo Aneeelerh ta taimaka mata ta zauna gefen gado
"Wallahi itace, Angel ce, Har abada bazan ta6a mantawa da fuskarta ba, ko shakku banayi wannan Yarinyar ANGEL ce tun da har kika ce tsintar su akai....
Gaba ɗaya rudanine akan fuskokin su,
"Hakan na nufin Junaid Shi Ya fara gane itace?
"Bangane me kike nufi ba yaga hoton ne"!
Jinjina mata kai tay lokacin dana buɗe hoton don in nuna masa da karfi ya kwace wayar daga hannuna Yana fadin Angel Angel..."
"Zai iya yiwuwa saboda Yawan nuna masa hotunanta da nake Yi shiyasa Ya gane ta, Ni dai Yanzu Ki taimaka min zahra! Inason na tabbatar da abun da nake hasashe! Taya zamu Iya ganin ta"❓❓❓
"Auntyna Ganinta ba abune mai sauƙi ba, dama ace bangaren su hajiya saratu suke da zama zaifi min sauki in nemi alfarmar ganinta, amma gaskiya tunkarar chief owais ba abune mai sauƙi ba! Kinsan Yanayin aikin su na jami'an sirri wallahi in ma suka ji maganar zasu Iya tuhumarmu"
"Wallahi zahra In har ban samu ganin Yarinyar nan ba Hankalina bazai ta6a kwanciya ba, ke koda Zasu tuhume ni ne, gobe sai naje estate din nasu..." da kwarin gwiwa tayi maganar
"Ƙwara mu bi komai a sannu, kada mu ce zamuyi gaggawa tun da bamu da tabbacin in itace dagaske...." kafin zahra ta ƙare maganar Aneelerh ta katse ta da cewa"zahra itace! Nifa ba makauniya bace, wallahi unaisah ce Yarinyar nan, tun fa tana jinjirarta muke kula da ita, shayar da ita ne kawai banyi na, tayaya bazan gane fuskarta ba"? Idanunta cike tab da kwalla ta furta maganar
"Ki taimaka min zahra, dan Allah, ko dan saboda Halin da mahaifiyarta take a ciki, wallahi bakiga tashin hankalin data Shiga ba a lokacin dana sanar da ita zancen 6acewar su, ba dan zuciyar imani ba da tuni zuciyarta ta buga...."
Ruƙo hannunta zahra tayi a cikin nata"ki kwantar da hankalinki aunty aneelerh, kada ki bari hawayen dake taruwa a cikin idanunki su zuba, muyi hakuri zuwa gobe inyaso sai muje can estate din nasu watakil adace su barmu mu ganta..." cikin kwantar da murya tayi maganar donta fahimci nema take ta zauce har lokaci bata daina kallon hoton ba
"Mezai hana mu tuntu6i Ziyad? tun da shi yasan da zancen 6acewarsu kuma yana da hotunan Unaisah da na tura masa ko shi zai iya yi mana hanyar haɗuwa da ita"
"Good Idea Auntyna, Yanzu Ki kwanta Ki huta, Gobe saimu ƙarasa maganar"
Jinjina kai tayi"shikenan zahra, Allah yasa zan Iya runtsawa, Bakisan Yadda na ƙagu da son ganin Yarinyar nan ba, fatana Allah Yasa itace ɗin."
"Amma kunyi waya da su aunty Benazir din? Sun isa gida Lafiya?
"Na kira layinta bata ɗaga ba, sai zuwa gobe zan sake jaraba kiran ta.."
Suna Cikin Yin magana Baby Junaid Ya fara mutsu mutsu zai farka daga bacci
"Junaid zai farka, Ki koma gurinsa, ni zan wuce aunty aneelerh,
Miƙa mata wayar tayi"mu kwana lafiya zahra"
Fucewa tayi daga dakin, Aneelerh ta koma kan gado ta janyo junaid on her chest ta rungumesa
Babu alamun zata Iya runtsawa saboda zumudin jiran gobe tayi, abu biyu ne suka tsaya mata aranta, na farko damuwar Benazir, na biyu yarinyar nan mai suna Unaisah...
*HAJJATY*
Can cikin bacci ta soma jin motsi a dakin ta wanda yayi silar farkar da ita, tayi zaton pravin ne Ya shigo shiyasa batai yunkurin tashi ba sai ma ta ƙara gyara kwanciyarta, kwatsam kamar daga sama tajiyo ƙarar faɗuwar wani abun firgigit ta zabura zaune tana faman zare idanunta jikinta Ya hau 6ari ta fara laluban fitila zata kunna hasken ɗakin, akan kunnanta taji takun tafiyar mutun adai dai lokacin ta samu damar kunna light din kamar walkiya taga gifcin mutun Ya lullu6e jikinshi da bargo, wata irin zufa ce ta keto mata numfashinta na hauhawa take kallon ƙofar cike da mamakin wanene Ya shigo? don kwata kwata baiyi kama da pravin ba...
Wurga ido tai akan tsakar dakin bakhhoor burner din da take ajiyewa kan mirror shi ta gani kan floor daga gani kado shi akai
Lamarin Ya ɗaure mata kai, saukowa tay daga kan gadon ta, gaba ɗaya tsoro Ya kamata, dama ƙwarin gwiwarta pravin ne gashi baya nan Yana can dakin Hajiya saratu.
Tayi mamakin ganin bedside drawer dinta a buɗe, zukunna tayi gaban drawer din yatsun hannunta na kerma ta curo album din dake a ciki mai ɗauke da hotunan auransu, cike da tashin hankali take bubbuɗe su ganin ba'a ɗauki hoton Ba Yasa Hankalinta Ya ɗan kwanta, da sauri ta mike taje taja ƙofar ta datse, ta sanya key
Komawa tayi gefe gado ta zauna har time din jikinta bai daina 6ari ba gani take kamar wani mugun abunne zai faru da ita, tun da gashi har an fara kawo mata hari adakin ta, Allah Allah take gari ya waye pravin yazo don ta faɗa masa abun da ya faru
______________________BATOOL✍️
Tsakar dare ta farka sakamakon fitsari da ya matse ta, saukowa tayi daga kan gado
Miƙa tayi kafin ta nufi toilet din tana dab da zata shiga, tajiyo sautin murya ƙasa ƙasa Ana magana har sai da taji gabanta Ya ɗan faɗi da sauri ta kalli gadon su duk a tsammanin ta ummi tana akwance ashe bata nan fululluka ta lullu6e da bargonta sai yai kamar mutun na akan gadon
Kanga kunne tayi don ta ƙara tabbatarwa da kanta muryar waye take ji ƙasa ƙasa kamar ana raɗa
"Kaima kasan bazan ta6a yin kuskuren da wani zaisan ina a tare da kai ba, yanzu haka da nake Yi maka magana ina a cikin toilet saboda bani kaɗai bace a ɗakin, akwai ɗaya daga cikin yaran da muke kula da su, Yarinyar tana sona, a tare muke kwana da ita........"
Ɗagowa batool tayi da kanta, Idanunta aɗan zare babban abun da take jima tsoro da wa aunty ummi take magana a tsakar daren nan kuma acikin toilet? Wanene? Da har take faɗin bata son asan tana waya da shi?
Gaba ɗaya tashiga ruɗani, Ƙara kanga kunnan tay jikin ƙofar
"Bazai yiwu ba, Ni Bazan Iya yakice ta daga gare ni ba, na faɗa maka Yarinyar bata da matsala, she is innocent bayan haka bata da wayon da har za ta sanya min ido..."
"Meyasa baka son kowa Yasan Ina atare dakai? kamar wani mara gaskiya kodai bakasan sunan ka Ya 6aci ne a idon jama'a"?
Ta sake ji ummi ta faɗa, can kuma sai tajiyo tayi wani sauti mai kama da nishi nishi da jan numfashi
Kwatsam tari Ya kubcewa batool waro idanu tayi kafin jiki na 6ari ta watsa aguje ta kashe light din dakin ta haye kan gado ta ja bargo ta lullu6e tana faman sauke ajiyar zuciya
A fujajen Ummi ta fito daga toilet din, yar rigar bacci ce a jikinta shara shara, kai tsaye ta sauke idon ta kan gadon, ganin batool a kwance tana bacci Yasa ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya, juyawa tayi ta koma cikin toilet din taja kofa ta datse
Batool dake a kudundu ne cikin bargo jin alamun ta rufe kofarne Yasa ta ƙara jin hankalinta Ya kwanta, ta kudiri aniyar saita faɗa ma Unaisah maganar da aunty umminsu keyi a toilet, saboda ta tsorata gani take kamar akwai wani abu a ƙasa duk da bata zarginta.
Ga fitsari cike da mararta amma saboda abun da Ya faru Ta hakura da yin shi, ta matse shi kuma cikin ikon Allah wani baccin Ya sake daukarta
____________________UNAISAH ANGEL
Kiraye kirayen sallar asubahin da aka farayi ne Ya farkar da ita, addu'ar tashi daga bacci ta karanta sannan ta miƙe zaune ta ɗan jingina bayanta jikin headboad
Kayan baccine a jikin ta, Milk colour riga da wando masu kyan gaske da alama baccin bai sake ta, sai faman lumshe idanu take Yi
bakomai take tunani ba face Aunty pretty ɗinta, bata ta6a damuwa da ita irin na Yau ba, Wani irin marmarin son jin muryarta take Yi aranta ta ayyana ko awani hali take a yanzu?
Canza akalar tunanin nata tayi akan danish, murmushi tayi tunawa da haukansa na jiya har yanzu inta tuna abun da yai mata sai taji wani irin yanayi atare da ita
Ta ɗau lokaci tana ƴan tunane tunane, kafin ta ware gray eyes din ta, hannu takai ta ɗan bubbuga kafadar deeja dake bacci tana jan minshari
"Sis ki tashi time din salla yayi" cikin magagin bacci deeja tace"Ni ki kyale ni, waike kullum sai munyi sallah ba a hutawa...."
Murmushi unaisah tayi"Pls kada ki wahalar dani..."
Daƙyar ta samu khadeeja ta farka daga bacci, bayan sunyi alwala suka sanya hijabi a jikinsu,
Ko da suka kabbara sallar khaddeeja ba ibadar ce agabanta ba, da zarar unaisah tayi sujjada ko ruku'u sai ta daddage ta ɗuma mata dundu abaya
Baiwar Allah, ahaka ta daure suka kammala sallar, bayanta har wani zogi Yake mata,
Batasan Ya zatai da ita ba, Haris ne Yaja mata shi da ya fara kawota dakin su don ta kwana,
Akan darduma bacci Yai awon gaba da khadeeja
Miƙewa tay da sauri ta dauko wayarta dake ajiye kan mirror cike da zumuɗi ta danna ma aunty pretty call tasan i warhaka ta farka Yin sallar asuba
Almost 3 times wayar tana ringing ba'ay picking ba, duk da haka bata hakuraba ta sake jaraba kira
Cikin sa'a Akai picking batare da anyi mata magana ba
Calmly unaisah tay mata sallama tare da cewa aunty pretty barka da asuba, kin tashi lafiya....." shiru ba alamar za'ay magana
"Naji kinyi shiru bakice komai ba, dan Allah kiyi min magana jiya har mafarkin ki nayi ..." kafin unaisah ta ƙare maganar wata murya ta ratsa ta da cewa"Wacece Ke? Kuma wa kike nema"?
Wani irin shock taji, Har saida gabanta Ya faɗi jin muryar Yarinyar sai taji kamar ta ta6a jinta awani wuri
"I'll hang up if you don't talk!'"
Da sauri tace"sunana unaisah, aunty pretty nake nema"
"Oh ko ke ce kika kira wrong number rannan"?
"Ni ce"
"Okey, me wayar ba ta farka daga bacci ba..".
"Wacece ke"?
"Cousin dinta ce, sunana zeenatu" lokaci ɗaya taji yarinyar ta shiga ranta, ta rasa a ina ta ta6a jin muryarta tabbas akwai wadda ta sani mai irin voice din ta
"Dan Allah, Idan ta farka daga bacci ki faɗa mata na kira,"
"Toh sai anjima" tana fadan hakan tay rejecting call din
Ƙurawa screen din ido Unaisah tayi, yayin da kwakwalwarta ke cigaba da tariyo mata voice din zeenatu.
A bangaren zeenatu bayan sun gama waya da unaisah, mikewa tay daga kan darduma jikinta sanye da dogon hijabi, hannunta ɗaya ruƙe da wayar cikin sauri ta fito ta nufi dakin Benazir
Kamar yadda suka bar shi jiya haka ta same shi a garkame, dr shurem daya kwana awurin kiran sallar asuba ne Ya farkar da shi lokacin da zeenatun tazo baya awurin sun tafi masallaci
Knocking kofar tayi"aunty benazir dan Allah ki buɗe min ƙofa, inason ganinki, jiya na damu da halin da kika shiga, ko baccin kirki bansamu nayi ba..." shiru babu alamun zata buɗe mata.
"Zeenatu ki daina wahalar Yi mata magana ba buɗewa zatay ba, halin ta ne tun tana ƙarama in Ranta Ya 6aci sai munci wahala kafin mu shawo kanta..." hajiya layla ce tay maganar, baiwar Allah daga ganin idanunta ko bacci batay ba sunyi ja idon Ya ƙanƙance
Muryar zeenat kamar zata fashe da kuka tace"tun jiyafa take a daki kulle! Bata magana, Idan wani abu Ya same ta fa..."
Shigowar Su dr shureim ne Yaja hankulansu ga dubansu, Su ukune tare da Alhaji musa da Alhaji ubaid duk sun sanya jallabiya a jikin su.
Zeenatu na ganin daddynta, da gudu ta nufe shi, ta faɗa kan kirjinshi tana kuka take fadin daddy aunty benazir taƙi buɗe ƙofa tun jiya, dan Allah kasa a balle ƙofar, bana so wani abu Ya same ta...'
Fuskarsa babu annuri Yace"meyasa zaki damu kanki akanta? Ba ita ta kulle kan ta ba ne? Ko wani Ya rufe ta ne..." bai kare maganar ba hajiya layla ta katse shi cikin 6acin rai tace"wai kai wani irin bauɗaɗɗan mutun ne? Baka da tausayi ne kwata kwata arayuwarka? Jiya kana ganin halin da ta shiga har faɗa maka akai amma saboda rashin imani sai cewa kai a kyaleta in ta gaji zata buɗe kofar saboda ba yarka bace ko..."?
bata ƙare maganar ba Alhaji ubaid Yai hanzarin katse ta da cewa"dan Allah kiyi hakuri ki daina ɗaga masa murya, jiya agajiye muka dawo gidan shiyasa Yace haka" harara ta wurga masa"kai ay saboda yarkace jiya ka hana idon ka bacci duk da agajiyen ka dawo gida, na tabbata da ace yarsace ke ahalin da benazir take aciki wallahi ba zaka iya runtsawa ba...." tun da tafara magana Alhaji musa Yake bin ta da kallo, arayuwarsa Ya tsani mutumin dake masa faɗa Yana ɗaga masa murya, babu wanda ya ta6a gigin yi masa hakan sai hajiya layla....
Dr shureim Bai tsaya kula su ba, ya juya ya nufi dakinsa zuciyarsa sam bata masa dadi, lamarin Family dinsa Ya fara gundurarsa kwata kwata ba zaman lafiya daga wannan sai wannan
Jinjina kai Alhaji musa Yayi, ba tare daya tanka mata ba, har Ya ɗaga ƙafa zai wuce Hajiya layla ta dakatar da shi ta hanyar shan gaban shi
Da mamaki Ya dago Yana kallon ta
"Wallahi babu inda zakaje! In har bakasa an buɗe kofar dakin benazir ba ni kuma bazan ta6a bari kabar wurin nan ba..." tana huci ta faɗa haɗi da ruƙe qugun ta, wlh a lokaci niyar kwashe ta da mari yayi amma sai Ya fasa Yatsun hannunsa har kerma su ke tsabar 6acin rai, wai shi yau mace zata tari gabansa? Batare da jin shakkarsa ba? Wacece ita? Dame take taƙama ne"?
"Layla ba haka mukai dake ba! Kin manta alkawarin da kikai mun na cewa ba zaki ƙara shiga huruminsa ba"? Azafafe ta kalli Alhaji ubaid"ban manta ba, amma wallahi Yau bazan raga masa ba, ay shi yasan ta yadda zaisa abude kofar, don haka bazan tsaya inaji ina gani in rasa ƴata ba dole yasa aballe kofar can" ta yi maganar tana watsa masa harara...
Fashewa da kuka zeenatu tayi jikin ta har jijjiga yakeyi, cikin shesshekar kuka tace"daddy dan Allah kasa a bude kofar, ni bana son inga kuna samun sa6ani atsakaninku, dan Allah daddy ka taimaka mana..." kukan zeenatu ba karamin tafasa zuciyarsa yakeyi ba
Gauran numfashi Yaja, tare da ɗan jinjina kansa Yana huci kamar mayunwacin zaki ya dubi hajiya layla da tai masa ƙerere kamar zata rufesa da bugu
A fakaice taga Ya sakar mata wani shu'umin murmushi har saida taji gabanta Ya faɗi
Sassauta fushin fuskarsa Yayi"naji zan buɗe ƙofar, ki bani hanya na wuce" matsawa tayi idanunta akan fuskarshi Ya nufi kofar dakin benazir
Yana ƙarasawa bakin ƙofar, Ya ɗaura faffaɗan tafin hannunsa, turata yayi wani iko na Allah sai ga ƙofar ta buɗe
Kallon Juna Alhaji ubaid da Hajiya layla sukai, abun da daure kai tun jiya suke gabzar kofar donta buɗe babu wanda bai jaraba karfinsa ba amma duk abanza ko motsi batayi amma shi daga turawa ta buɗe wani irin ƙarfi ne da shi? Basu tsaya dogon tunani ba, jiki na 6ari suka nufi ɗakin zeenatu da gudu ta rigasu faɗawa a ciki.
Shugarsu keda wuya kowan nan su Yaci burki, Abun da suka gani Yayi matuƙar ɗaga hankulansu, kamar matatta haka suka hangota kwance kan floor rabin jikin ta a cikin toilet dake a buɗe, kamar irin tayi gudu ta kife awurin har kanta Ya daku goshin ta Ya fashe
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji!"un"! hajiya layla ce ta zagba salati tana tafa hannayenta, zeenatu da ta gama ruɗewa agaban benazir ta zube bisa gwiwowinta, takai hannu tana tatta6ata Aunty benazir! Meke damunki dan Allah ki tashi inna lillahi..mami daddy ku ce ta tashi dan Allah....
da sauri Alhaji Ubaid Yaje Ya ɗago da ita, jikinta duk Ya saki ya ɗauko ta da hannu biyu ya kwantar da ita akan gadon ta, sumar kanta duk Ta yamutse
Fita hajiya layla tayi jim kaɗan ta dawo da robar ruwa ta buɗe murfin ta kur6i ruwan tare da furzar da shi kan fuskar benazir
Ruwan na dura tayi wata irin zabura tana ambaton sunan taj ... adai dai lokacin shureim Ya shigo dakin ganin su tsaitsaye bakin gadon ta yasa shi saurin karasawa
Tunkafin yayi magana Hajiya layla tace"shureim ka gani ko? Abun da nake gudu kenan! bansan ya akai ta faɗi kasa daga cikin toilet, kanta Ya bugu..."
Hankalinsa atashe Yake kallon Benazir yatsun hannunta sai kerma suke, ta runtse ido tana sambatu kwata kwata bata acikin hayyacin ta
Zeenatu duk ta damu, Hannunta ruke dana benazir sai faman shesshekar kuka take
"Ya akai kofar ta buɗe"?
"Uncle din ku ne Ya buɗe kofar," ta bashi amsa ataikaice, Alhaji ubaid Tuni Ya fuce Yabi Alhaji musa don Ya fada masa halin da benazir take ciki
A lokacin Har Ya koma Part dinsa, sallamar Alhaji ubaid ce ta katse sa kamar bazai fito ba, don saida Ya ɗau lokaci har sai da hajiya sara tace da shi baiji ana sallama bane? Tukunna Ya mike cikin takun izza Ya fito daga dakin
"Me kuma zanyi bayan na buɗe ƙofar"? A faɗace Ya faɗa Yana ƙanƙance idanunsa
"Dan Allah ka yi hakuri da abun da layla tayi maka, bata jin maganata naja mata kunne taki bansan ya zanyi da ita ba..." ya mutsa fuska Alhaji musa yai"naji, Yanzu awani hali benazir din take a ciki?
Kamar mai jin shakkarsa Alhaji ubaid Ya furta"mun sameta akwance kan floor, rabin jikin ta a toilet, kamar faɗuwa tayi don har kanta Ya daku sosai, ta farka sai dai kamar bata a hayyacin ta shiyasa nazo don na sanar dakai...." ta6e la66ansa yai kafin yace"zanyi magana da likita na, zaizo Ya duba ta" godiya ya yi masa kamar zai masa sujjada, komawa cikin dakin yai hajiya sarah dake a zaune kan darduma ta miƙe tana tambayarshi meya faru ne? Ko benazir ta buɗe kofar ne' amsa mata yai da eh jiki na rawa ta fuce daga dakin don taje dubota...
Gaba ɗaya sun hallara a dakin Benazir kowan nan su Ya shiga hali na damuwa, bada jimawa ba Dr Mark Ya shigo gidan, wani basamuden Likita ne irin african american din nan, yadda kasan Jinin Alhaji musa, Fuskarsa babu fara'a, sumar kansa hada kitson zane, tun da Hajiya layla tayi arba da fuskar dr mark kuma taji cewa Alhaji musa ne Ya kira shi don Ya duba lafiyar benazir, tace wallahi bazai ta6a benazir ba, ai kwata kwata ita baiyi mata kama da likita ba, ta dinga surfa bala'e duk yadda alhaji ubaid Yaso Ya shawo kanta shi da su hajiya sarah akan ta bari aduba ta, amma abun Ya faskara a karshe sai dai Alhaji musa Ya sallami likitan Ya tafi ba tare da ya duba benazir din ba, ran Alhaji musa yai mugun 6aci yace tun da ta hana adubata bazai ƙara sanya hannu a zancen lafiyarta ba....ran kowa saida Ya 6aci da abun da layla tayi Alhaji ubaid har Ya gaji da yi mata faɗa, hajiya sarah ce ta basu shawarar su yi gaggawar kaita asibiti don abinciki laifiyarta, ba su tsaya bata lokaci ba, dr shureim Ya dauko benazir da hannu biyu ya tallabota, suka fito daga falon, A mazaunin baya na motarsa ya shigar da benazir, hajiya layla ta shiga ta rungume ta a jikinta, Alhaji ubaid Ya zauna a front seat tare da shureim, yayin da hajiya sarah ta shiga motarta tare da zeenatu kusan atare motocin suka nufi Gate din gidan, Waɗannan gabza gabzan security officers din suka tari gabansu har sai da suka kira Alhaji musa Ya basu iznin su barsu su fita kafin suka basu hanya
Direct suka nufi Obie International Hospital.
__________________ANEELERH
Wuraren ƙarfe tara, Aneelerh ta kammala shiryawa cikin abaya tayi rolling, gaba ɗaya ta ƙagara su karasa estate din kamar tayi fiffike haka take ji, fitowa tayi daga bedroom dinta ta nufi dakin mami, bayan tayi sallama mami ta amsa mata ta shiga daga ciki ta gaishe da ita
Kallo ɗaya mami tayi mata ta fahimci kamar bata jin dadi
"Aneelerh baki da lafiyane naga idanunki sunyi ja?
Kokarin danne damuwarta tayi"mami lafiyata lou, ban samu isasshen bacci jiya ba..."
"Meyasa? Kar dai ace damuwar abun da Ya faru jiya ne"? Girgiza kai tay"a'a mami na tashi yin nafila ne shiyasa banyi bacci da wuri ba..."
"Kunyi waya da su benazir din? Inataso inji ko sun isa gida lafiya"?
"Tun jiya bayan sun tafi nake ta trying layinta baya shiga, har da safen nan saida na kira ba'a ɗaga ba
"To Allah yasa dai Lafiya, Yanzu ina zakije ne naga kin shirya ko hakanan kikai gayu"?
"Mami wani abun al'ajabi na gani jiya awayar zahra, wanda ya daure min kai shiyasa ma na shigo don in faɗa maki"
"To fa, menene ?
Zaro waya aneelerh tayi daga handbag dinta, ta lalubo layin zahra ta danna mata kira,
Bugu ɗaya tay picking"zahra Kin gama shiryawa?
"Eh yanzu zan fito"
"Okey Ki same ni adakin mami dan Allah kada ki bata lokaci"
Bayan ta katse wayar ta dubi mami"gata nan zuwa, abun da zan nuna maki yana awayarta" amsa mata mami tayi da toh cike da zullumin abun da zata gani
Jim kaɗan zahra ta shigo dakin da sallama, Itama ta shiya cikin abaya maroon colour, ta yi rolling, hannun ta ruƙe da wayarta, a bakin gadon mami ta zukunna"ina kwana mami? Kun tashi lafiya"?
"Lafiyalou zahrana, Ina abun da za'a nuna min"?
danna wayar zahra tayi bayan ta buɗo hoton, ta miƙa ma mami wayar tasa hannu ta ƙarba.
kura ma fuskar unaisah ido tayi kamar ta ɗan ruɗe can dai ta miƙe daga kishigiɗan da take ta ɗan kalli fuskar zahra da aneelerh kafin tace"wannan ay hoton Angel ne ko? Yaushe akai wannan hoton? Amma ya akai naga kamar ta ƙara girma anan..." at same time zahra da aneelerh suka saki murmushi saboda sunji dadin yadda mami itama ta gasgata abunda idanunta suka gane mata tunkafin ma su fada mata wa suke hasashen itace
"Mami wannan yarinyar da kike gani sunanta Unaisah, a wurin dinner din prime minister zahra ta dauko hotonta a dakin taron..." da tsantsar mamaki Mami tace"oh wai da ba Angel din bace? Me kama da itace kenan"!
"Mami itace, abunda muke hasashe kenan, zahra ki bata labarin abun da Ya faru a wurin dinner din...." gyara zama zahra tayi gaba daya ta kwashe abun da Ya faru ta sanar da mami
Lamarin yayi mugun daurewa mami kai
Aneelerh ta ƙara da cewa"yanzu haka can estate din zamuje, don mu tabbatar da abun da muke hasashe akan Yarinyar..." jinjina kai mami tayi ita kanta ta goyi bayan suje saboda kamannin Yarinyar dana Angel sun 6aci, bugu da ƙari da taji cewa Yaran tsintattune watakil su dace
"Aneelerh zaiyi wuya ace yarinyar nan ba ita bace, amma dai kuje kawai, Allah Yasa adace"
"Ameen mami, ki tayamu da addu'a Allah Yasa mu samu ganin ta cikin sauƙi, saboda estate din nasu ba karamin tsarone da shi ba, In har ba wani daga cikin Ahlin su Ya gayyace ka ba to basu bari bakuwar fuska ya shiga....."
"Ita zahra ba suna mutunci da mutanan gidan ba"? Acewar mami
Zahra tace"hajiya saratu ce, nasan indai na tuntu6eta zata taimaka mana, duk da nasan mawuyacin abune tun da yaran a hannun chief owais suke da zama, Ba lallai su bari mu gan su ba.....
Shiru mami tayi kafin tace"to me zai hana ku kira ɗan jaridan nan shima badaga family dinsu Yake ba kuma ay yasan da zancen 6acewar yarinyar tun da har bayanan an tura masa....."
"Har kiran layinsa nayi kwata kwata baya shiga, watakil ko Ya shiga wurin aiki ne..."
Mami ta gyaɗa kai"shikenan Kuje kawai sai ku kira hajiya saratun, sannan dan Allah idan ba abaku damar shiga ba kada ku takura kanku ku dawo gida kawai inyaso sai ayiwa ɗan iya magana tun da shi ya saba hulda da yan siyasa watakil ku samu hanyar shiga ta wurinsa.....
Amsa mata sukai da toh,
Kafin su miƙe mami tay hanzarin dakatar da su"ku jira mahboob Ya shigo gidan, kwara kuje da namiji"
Zama sukai har saida Mahboob Ya dawo Mami ta sanar da shi komai, ay tun da yaji zancen Unaisah ya gaza samun nutsuwarsa dama yajima da burin su gano yarinyar ba dan komai ba sai don jarin da Yake tunanin zai samu da ita shi uban son banza....
Lokacin da Motarsu ta shararo kan titin obie estate Aneelerh ta jinjinama haduwar wurin kasancewar yau ne na farko da suka fara zuwa, bata gama shan mamakin daular ba sai da Mahboob Yayi parking a gaban tankameman gate din estate din, hankalin su ba karamin tashi yai ba ganin Jami'an dake tsaron shi, sojoji da Jami'an Isod
Babu wanda Yayi gigin fitowa daga cikin motar, Mahboob Yace"mun kawo kanmu, zahra ni fa tsoron tunkararsu nake Yi Allah, Sai dai wani daga cikin ku Ya ƙarasa driving din...
Yar dariya zahra tayi"bansan Iya shege mahboob dalla ka ƙarasa mana sai kace ba namiji ba"?
"Indai saina tunkari wadannan masu fuskar shanun zan zama namiji to wlh na kwammace ku kirani da sunan hajara...." dariya suka sanya gaba ɗayansu....
Mahboob Fa Ya dage akan bazai karasa da su ba...."
Kwatsam biyu daga cikin sojojin suka tunkaro motarsu hannayensu ruke da bindigogi tuni zufa ta fara wanke fuskar mahboob ganin Yana kokarin tada motar Yasa zahra yin saurin cafke hannunsa"haba mahboob meye haka? Wai dama haka kake da shegen tsoro? Harara Ya galla mata"nifa ba tsoronsu nake ji ba, tashin hankali ne ke banso ..." daƙyar Ya ƙare maganar ganin har sojojin sun ƙaraso gare su
Kwankwasa window glass din motar, ɗaya daga cikin su Yayi da kakkausar murya Ya furta"Put down the glass!" Aneelerh ce tayi karfin halin sauke glass din windown Ya zukunno da kansa Yana binsu da kallo idanunsa jawur
"Su wanene ku kuma daga Ina?
Murya na rawa zahra tace"wurin Hajiya saratu muka zo...."
"Okey, Ku kirata awaya don ba'a sanar damu zuwanku ba"
jiki na kerma ta amsa mashi da toh, da sauri zahra ta kira Layin hajiya saratu, kusan sau takwas baya shiga, Hankalinsu ba karamin tashi Yayi ba
"Bari na ƙara kiran ziyad watakil shi Ya ɗaga" aneeelrh ta fada yatsun hannunta na kerma ta curo waya ta kira layin ziyad tana ringin baya picking, hankalinsu duk Ya tashi
Ƙasa ƙasa da murya Aneelerh tace"mun shiga uku zahra shima bai ɗaga ba yanzu ya zamuyi"?
Mahboob da ya gama tsorata Yace"mu koma gida kawai shine mafita in ba haka ba wlh wannan mai fuskar shanun tsaf zai Iya bombing motar mu... cikin muryar raɗa yai magana
Zahra tace"wait bari na kira zayn duk da nasan mayucin abune yayi picking..." koda Ta kira layin zayn sau uku baiyi picking ba, A kira na huɗu ne Ya ɗaga muryarsa kamar ta mashayin giya ya furta
"Waye"? Ko sallamarta bai amsa ba
Cike da jin shakkarsa ta furta"zahra ce"
"Wace zahra"? Sarai fa Ya gane muryarta har saving layinta Yana da shi awaya
"Am..zahra wadda mommynka ta haɗa ka da ita, a wurin dinner din prime minister
"Okey nagane, lafiya kika kira"?
"Munzo estate dinkune an hana mu shiga, sojojin sunce dole sai an basu izni kafin su bari mu shiga
Kafin ta kare maganar Zayn yace"kina hauka ne? Ki rasa wa zaki kira saini? Oh tun yanzu raini Ya fara shiga tsakanina dake! Uban me ma Ya kawo ku estate din?
Hatta su Aneelerh sai da sukajiyo masifar da yake zazzaga mata
"Dan Allah ka taimaka mana, bamu da wata mafita ne shiyasa na kira ka, wani abu ne mai mahimmanci Ya kawo mu...." kamar zata sanya kuka
"Look, Ku koma inda ku ka fito tun da baku da wani alaƙa damu" Yana ƙare maganar Ya katse kiran, Tashin sense gasu dai agaban estate an hana su shigaa
"Yanzu menene mafita? acewar Aneelerh
"Aunty aneelerh mu hakura kawai tun da kowa yaki ɗaga kiranmu Inyaso ko zuwa gobe sai mu dawo in ba haka ba wahala zamu sha.."
Gurgiza kai aneerlerh tayi"bana jin zan iya komawa gida, sai dai ku tafi kubarni, Ni kawai zanje na roke su su barmu mu shiga ta fada tare da bude car door din Ta fuce da sauri zahra da mahboob suka bi bayanta
Babu irin magiyar da aneelerh batay masu ba, amma suka dage akan dole sai an basu izni, a karshe ma wani fusatacce daga cikin su Ya tsawatar masu akan su koma inda suka fito
Rai a6ace Aneelerh ta dawo jikin motar ta tsaya fuskarta har ta fara zubda gumi, mahboob da zahra sai rokonta suke akan su hakura su tafi gida, amma ta kafe akan ba inda zataje, su kansu sunyi mamakin taurin kan aneelerh abun da bata ta6a yi ba......
Har mami zahra ta kira tayi mata bayanin halin da suke a ciki, tace su ba aneelerh waya su yi magana bayan ta kar6a mami tace tay hakuri su dawo gida kawai inyaso sai ayi ma uncle dan iya magana.." ta amsa mata da toh bayan sunyi sallama da mami, su zahra har sun fara sauke ajiyar zuciya a tunanin su zata koma akarshe sai cewa tayi"ita fa kawai ta amsa ma mami ne, amma fa ba inda zataje sai taga abun da ya turewa buzu naɗi..." kamar su daura hannu akai suyi ihu haka suka ji, sojojin dake zirga zirga sai kallonsu sukeyi su kansu sunyi mamakin taurin kan matar da basu san wacece ita ba, don ma Taci albarkacin Kyan dake gareta ay da tuni sunyi masu korar kare daga Layin.
babban abun da Yafi damunta dayasa har ta kafe akan sai sun shiga halin Da benazir ta shiga jiya Ya ɗaga hankalinta da ciwon abun ta kwana jiya tasan mawucin abune in wani abu bai faru da ita ba, wanda yasa har bata neme ta ba kuma in ta kira bata samu
Su zahra har sun gaji da tsayuwa tsawon awanni uku har karfe 1 na rana ta buga, kamar zasu sanya mata kuka fuskokin kowannansu sun Yi jawur
Kiran wayane Ya shigo layin Aneelerh a hanzarce ta duba screen ganin sunan benazir ya bayyana ne Yasa tai gaggawar ɗaga kiran hadi da kara wayar a kunne
Muryarta har rawa take wurin furta"benazir ina kika shiga inata kira baya shiga...." cak ta tsaya da maganar jin muryar Dr shureim
"Aneelerh ba ita bace Shureim ne Ina fata kun tashi lafiya..." tun daga kan yanayin sautin muryarsa ta fuskanci babu lafiya
Gabanta na faɗuwa tace"yaya shurem ina benazir din, tun Jiya bayan kun tafi nake ta jaraba kiran layin ta don inji ko kun isa gida lafiya amma ba'a ɗaga wa...
"Aneeelerh! Kunyi magana jiya da benazir akan mijinta ..."
Murya na rawa tace"eh.. munyi"
"Meyasa kika faɗa mata abun da ya faru da su..."
"Yaya shureim wallahi banyi niyar sanar da ita ba, itace ta matsamin..." gaba daya ta faɗa masa maganar da sukai da benazir har rikicewar da tayi
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un..." shine abun da taji Ya furta... Su zahra dake kallon fuskar aneelerh Hankulansu duk sun tashi tunkafin ma suji me suke magana akai
"yaya shureim wani abu Ya faru ne..."
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 27 Complete
by
Novels Elite Admin
July 09, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
___________________________________✍️
❓
"Yaya shurem wani abu ya faru ne"?
Tun daga farkon abun da ya faru bayan komawar su gida ya fara sanar da ita kafin ya ƙara da cewa"Yanzu haka da nakeyi maki magana muna a asibiti, an kwantar da ita, cos She is completely unconscious, sunan mijinta da ƴarta kadai take fadi, kuma dr ya tabbatar mana da cewa she is suffering from depression and panic attacks, sannan in har bata samu abun da take so ba zamu Iya rasa ta...."
kusan suman tsaye Aneelerh tayi jiki asanyaye ta sulale daga jikin motar ta zuƙunna, idanunta cike tab da ƙwalla take ambaton inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un! A kalla ta ambaci hakan yafi sau a kirga, zuciyarta da matsanancin karfi take bugawa kamar zata fasa kirjin ta...
"Aneelerh ku ta yamu da addu'a, benazir taci wahala banaso narasa ƴar uwata.... " cikin rauni na murya yayi maganar
Zuciyarta ce ta raya mata me zai hana ta sanar da shi zancen Yarinyar da suke hasashen unaisah ce ko dan hankalinsu Ya kwanta..
Da sauri tace yaya shurem akwai abunda nakeson sanar dakai, duk da bani da tabbaci...."
Cikin rauni na murya ya furta menene? a tsanake Aneeelerh ta kwashe komai ta sanar da shi
"Yanzu haka muna abakin estate din ba'a kaiga ba mu izinin shiga ciki ba, kaga idan Ya tabbata unaisah ce shikenan Zamu samu maslahar ciwon benazir...."
Tana Iya jiyo Sautin ajiyar zuciyar dr shureim"Aneeelrh baki Ji yadda naji ba, Ubangiji Allah Yasa adace, Dan Allah Duk Yadda ake ciki Ki sanar dani....."
"In sha Allah Yaya Shureim zaka ji daga gareni, awani asibiti ne aka kwantar da ita"?
Yace"Obie International hospital"
"Ubangiji Allah Ya tashi kafadunta, in sha Allah zamuzo dubata, Allah Ya bata lafiya" bayan sunyi sallama hawayene suka wanke fuskar Aneelerh
"Aunty Aneelerh meya faru? Su zahrane suke tambayarta
Cikin shessheƙar kuka ta kwashe komai ta sanar da su, gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi zuciyarsu ta karaya, musamman Aneeleerh wadda tuni ta sulele jikin motar ta zuƙunna tare da kifa kanta tsakanin cinyoyin ta...
_______________________________✍️
Bayan dr shureim Yai sallama da Aneelerh, ɗagowa yayi da idanunsa wadanda suka kaɗa jawur da su shi kadai ne tsaye a corner din da yai wayar, jiya izuwa yau gaba ɗaya ya fita hayyacinsa sam babu nutsuwa a tare da shi, Fatan shi Allah Yasa su Aneelerh suyi nasarar gano yarinyar nan kuma Allah Yasa ƴar benazir din ce da kuwa yafi kowa farin Ciki da hakan.
Wani abu da ya ɗaure masa kai a binciken da likita yai ya bayyana masu cewa akwai wani abu da ya haifar mata da matsanancin tsoro lokaci ɗaya Ya fara tariyo maganar maminsu lokacin daya shiga dakin take fada masa halin da suka samu benazir ta faɗi ƙasa rabin jikin ta a cikin toilet har kanta Ya daku❗
Tuna wannan Ya shi Zare idanunsa, zuciyarsa na harbawa da ƙarfi dama sai da yai fargaban faruwar hakan shiyasa ya kwana abakin ƙofar ɗakin ashe duk da haka sai da aka kai mata hari! Duk da bai da tabbacin abunda Yake zargi Ya yanke shawarar zai jira har zuwa lokacin da benazir zata dawo cikin hayyacinta don Yaji ainihin menene yayi silar faɗuwarta ƙasa❗❓
Cike da rashin kwarin Jiki Ya Nufi Medical room din da aka kwantar da benazir a Emergency depertment tun kafin Ya karasa Ya hango zeenatu abakin door room din tana sharar kwalla, baiwar Allah duk ta fita hayyacinta damuwa ta hanata sukuni
Har ya ƙaraso Bata lura da da shi ba, saboda ta rufe fuskarta ta tafukan hannayenta.
"Zeenat! Ba nace ki daina kuka ba?"? Sanyayyar muryarsa ce ta katse mata kukanta,
Idanunta jawur ta dube shi"yaya shureim hankalina bazai ta6a kwanciya ba in har aunty benazir bata dawo hayyacin ta ba..." ta faɗa tana jan numfashi
"dan Allah Yaya shureim ku nemo mata babynta da mijin ta, ni bana so na rasa ta, ni kawai zan ma daddy magana yasa a nemo mata su nasan zai iya. ..."
Ruƙo hannayenta yai acikin nashi"kiyi hakuri ki daina kukan Ya isa haka! Idan har dagaske kin damu da halin da take a ciki, to kiyi mata addu'a Allah Ya bata lafiya, hakan ne zai tabbatar da kaunar da kike mata.." la66anta na kerma ta fara karanto addu'o'i
"Mu shiga daga ciki" ya faɗa tare da ruƙo hannunta suka shiga room din.
Su Hajiya sarah suna zaune kan kujerun dake fuskantar gadon da benazir ke akwance, babu wani mai kwanciyar hankali a cikin, musamman hajiya layla, fuskarta tayi jawur tsufanta Ya fara bayyana duk ta yamutse kamar itama bata da lafiyan.
Duk sun zuba ido suna kallon benazir wadda tun da likita yayi mata allurar bacci take ta yin shi, har wani firgita take yi kamar mai yin mafarki duk da karfin allurar cikin magagin bacci take ambaton sunan mijinta da yarta saboda sune aranta, baiwar Allah ba karamin jiki taji ba, la66anta sun bushe ƙamas tayi haske kamar ba jini a jikinta, kwarin idanunta sunyi ja da su...
Agaban gadon dr shureim da zeenatu suka tsaya suna kallon ta gwanin ban tausayi, da ace suna da halin da zasu Iya cire mata ciwonta ya dawo jikin su da tuni sunyi hakan...
Wayar hajiya sarah dake a cikin purse ce ta fara ruri da sauri ta curo wayar ta duba sunan mai kiranta My boss wato Alhaji musa.
Picking call din tay ta kara wayar a kunne ko sallamarta bai amsa ba, da kakkausar murya ya ce
"Kin manta Yau kina da aiki a office"? Bata bashi amsa ba, da sauri ta miƙe ta fito daga dakin
Kafin tace"ban manta ba, I'll inform my secretary that I won't be going to work today na ɗauki hutu har sai benazir ta samu lafiya, ay nayi zaton ka kirane don kaji halin da ake ciki game da lafiyarta..." kafin ta ƙare maganar Ya katse da cewa"karki kuskura ki ƙara yi min magana kan benazir! Idan har ba so kike ranki Ya 6aci ba..." ranta Ya 6ace a hasale tace"wai meke damunka ne? Yarinyar nan fa yar yayanka ce, ɗiyarka ce, meyasa kake nuna halin ko'in kula akanta? Sai kace ba jinin ka ba..."? Daƙyar ta ƙare maganar jin wata tsawa da ya daka mata muryarsa da 6acin rai Ya furta"zaki dawo gida ki sameni! Har ni kike ma magana kina ɗaga min murya? Kina cikin hankalin ki kuwa"?yawu ta haɗiya Muryarta adabarbarce ta furta"i'm...so sorry" bata ƙare maganar ba Ya furta"ki faɗawa shurem ya dawo da zeenatu gida, ke kuma zaki zo ki same ni" Duff Yai rejecting call din.
Ya Salam! hankalin ta idan yai dubu toh Ya tashi, bata ta6a hasala shi irin na yau ba, duk tabi tasha jinin jikinta, fargabanta kada taja ma kanta.
_____________________________✍️
Prisoner's shield 👊❤
A hankali Ya ware idanunsa masu ɗauke da bacci da wata irin kasala ya yunkura ya miƙe haɗi da jingina bayan shi jikin pillow, wani irin lalaci yake ji tun karfe 12 bai leƙa ko kofar dakin sa ba, bacci kawai yakeyi, kamar baya jin dadi, short ne kaɗai a jikin shi launin ja, sumar kan shi ta rufe gefen fuskarshi kamar baccin bai ishe shi ba...
Da wani irin kewar unaisah Ya farka, har mafarkinta sai da yayi, sai faman lumshe idanunsa yakeyi, kwatsam hasken ɗakinsa Ya ɗauke ɗuff kamar an kashe switch din dakin Sam bai lura ba ko'ina yayi duhu kamar dare
"Garkuwa namu!...."! cikin kunnansa Yaji wata murya mai kama da ta dattijuwa ta ambaci sunan shi, yayi zaton gizau muryar ke yi masa shiyasa bai mayar da hankali akai ba
"Shield! Shield!! Shield!!! Rass Yaji gabanshi Ya faɗi, A hanzarce Ya buɗe reddish eyes dinsa sosai, a matuƙar ruɗe, sam Ya gaza believing da abun da kunnuwansa suke Jiyo mashi
Durowa yayi daga kan gadon Ya soma bin ceilling din dakin da kallo, a kokarinsa naya gano ta inda sautin muryar ke fitowa.
A hankali Yake bin labulayen ɗakin da kallo farat ɗaya zuciyarsa ta raya masa hanya ɗaya ce zai Iya ganin me Yi masa magana...
A hanzarce Ya juya Ya kalli inda madubin dakinsa Yake, wanda tun da jimawa Unaisah Ta rufe masa shi da towel saboda ta gane baison ganin mirror
Walking slowly Ya nufi gaban madubin Yakai Yatsun Hannunsa dake kerma Ya Yakice Towel din Ya jefar da shi
Kyawawan idanunsa Ya ɗaura akan mirror din duhu ne Ya mamaye cikin sa baka Iya ganin komai....
La66ansa na kerma Ya furta"KHALA❗❓..." sautin dariyarta ne Ya karaɗe ɗakin nashi daga ji tsohuwace tukuf
"Garkuwarmu ko da Yake Yanzu Ka koma Garkuwarsu....' A hankali ta bayyana ta cikin duhun madubin kamar Yana kallon tv tsohuwa ce tukuf ta rufe ko'ina na jikinta da fararen kaya ko fuskarta baka iya gani sai dai idanunta da suka kasance farare ƙyal launin reddish irin nashi
Muryarsa na rawa Ya sake maimaita sunanta Khala
"Bani da isasshen lokaci yin magana!" ta faɗa tana kallon cikin idanunshi
"Inaso nima na bada gudummuwata wurin ganin kunyi nasarar ruguza tarihin kurkukun ƙaddara ...." da tsantsar mamaki yake kallon dattijuwar
Cikin harshensu na matsafa ta soma kora mashi jawabi...." a karshe ta furta"I'm waiting for your attack! Don't take time, the lives of the other prisoners are in danger!" (Ina Jiran farmakin ku! kada ku dauki lokaci, rayuwar sauran fursinonin tana a cikin hatsari)..." har Ya buɗe baki zaiyi magana ɗuff madubin Ya dawo suffarsa ta ainihi, da sauri Ya kawar da idanunsa daga kallon mirror din Ya ɗauko towel din daya jefar Ya lullu6e shi.
Jikin shi har tsuma Yake Yi, numfashin shi da hucin zafi Yake fita, Sam Ya gaza matsawa daga gaban madubin, muryarsa da tsantsar al'ajabi Ya ke maimaita sunan JEREMIAH his childhood friend as the new prison shield gaba ɗaya He was extremely confused, Tashin hankalin da ba'a saka mashi rana har wani tangyal tangyal yayi kamar zai faɗi dakyar ya iya tsayar da kansa bisa kafafunsa abunne Ya daki heart dinsa...❗
A cikin bayanan da dattijtuwar ta sanar da shi hada kwanan watan da za su yi black night ! Shin wacece Khala!?? Baku tunanin tarko ne za'a ɗana masu!? in ba haka ba tayaya matsafiya wadda take rayuwa acikin gidan kurkukun kaddara zata neme sa da sunan bashi gudummuwar tarwatsa kurkukun ƙaddara❓
Knocking kofar room dinsa akai da sauri Ya daidaita nutsuwarsa kamar wani abu bai ta6a faruwa ba...
Yayi zaton unaisah ce sai da yaje gaban kofar ya buɗe karaf idanunsa suka sauka akan chief owais Ya ɗauki wanka cikin shiga ta kakinsa Yayi shirin zuwa Office, from head to toe Ya kalle sa kafin Ya haɗe fuskarsa bakomai Ya tuna ba face unaisah da ya gani adakinsa jiya shiyasa ya ƙarajin haushin mutumin
Chief owais baibi takansa ba Ya nufi cikin dakin hannunsa ruƙe da shopping bag, Ya dire masa ita kan gadon shi
A hankali Ya juyo suka fuskanci Juna
"Ba ka Iya gaisuwa ba ne"? wani ɗan iskan kallo danish Yayi masa
Murmushin gefen fuska chief Yai
"Laifin me na maka kamar baka kaunar gani na"?
Shiru yayi bai tanka masa ba
Da ace chief yasan unaisah ce Silar dayasa danish Yake haɗe masa rai ay da tuni Yayi masa bayanin da zai kwantar masa da hankalinsa don shi A yanzu mace bata agabansa, burinsa ya gano miyagun gidan kurkukun ƙaddara da kuma kawo karshen su shi ne abunda Yasa agaba
kallon shoppin bag din yai alamar yana neman ƙarin bayani yaga bakon abu adakin sa
"It's a gift from Uncle Hateem. Please don't break them they're not toys," he said jokingly. tare da buɗe jakar ya soma fiddo da kayan cikin ta
"suna da amfani, idan ka bani dama zan nuna maka yarda zakai amfani da su" cikin lallami yakeyi mashi magana
Ganin Yayi tsaye Yaki matsowa Ya duba kayan, Yasa chief Tunkararsa Ya ruƙo hannunsa Ya janyo shi har bakin gadon
"Zuwa anjima zan ware mana lokaci in fara koya maka Yadda zakai amfani da su ko baka so"? Yai maganar Yana dubansa sai wani shan mur Yake.
Daurewa kawai cheif yakeyi amma fa ya fara hasala da halin danish kwata kwata baya sakar masa fuska kuma Yaƙi magana da shi, in banda ma Yana neman alfarma awurinsa ay da bai kai matsayin da chief zai kulasa ba
Fucewa yai daga dakin Ya Bar danish a tsaye Ya kasa ta6uka komai, zuciyarsa har yanzu bata daina ambaton sunan jeremiah ba, kalaman tsohuwa Khala sun tsaya masa aransa sai yake ganin kamar amafarki ta bayyana..
zama yayi gefen gadon Ya zubawa kayan ido har cikin rashi Yaji dadin jin cewa Hateem ne Ya bashi kyautarsu, duk da baisan amfaninsu ba amma sunyi mashi kyau, bai ta6a ko ɗaya ba, ya yanke shawarar sai unaisah tazo zasu buɗe su atare
________________________________✍️
*ANEELERH*
"Mu tafi asibitin kawai, bazan Iya jurewa ba...." gani take kamar zata rasa benazir, shiyasa ta hakura da shiga estate din
Su mahoob daman hanyar da zasu tafi suke nema, jiki na 6ari Ya buɗe motar Ya zauna a driver's seat, Aneelerh ta shiga ciki, Zahra na kokarin shiga kwatsam ta hango dankareriyar motar dake tunkaro estate din dakatawa tayi saboda ranta na bata cewar Motar Hajiya saratu ce....
"zahra ke muke jira ki shigo mu tafi" acewar mahboob
"Kaɗan jira, naga kamar motar Hajiya saratu ce ke tunkaro estate din..." jin wannan maganar yasa Aneelerh yin hanzarin fitowa daga motar shima mahboob Ya fito duk suka ƙurawa motar ido cike da sa ran ganin wanene a cikin ta
Lokacin da motar ta kusa ƙarasowa dab da inda suke gudunta ya ragu slowly window glass dinta na back seat Ya zuge hakan Ya basu damar ganin na cikinta
Wata irin nauyayyar ajiyar zuciya zahra ta sauke mai haɗe da annurin farin ciki
Ita kanta Aneelarh ajiyar zuciyar ta sauke haka shima mahboob duk da basu ta6a ganinta ba Yau ne rana ta farko da suka fara ganinta ido da ido
A hakimce take zaune cikin motar, ta ɗauki wankan lafaya, idanunsa na a manne da farin glass ba karamin kyau yayi mata ba
Da alama su take kallo, Umarni ta ba security din dake driving dinta idan sun karasa kusa da motar su zahra yai parking, ya amsa mata da toh
Daga bayan motarsu zahra yayi parking din motar, jiki na 6ari zahra ta nufe ta, a lokacin ta bude car door din ta zuro kafarta ɗaya waje
Sallama tayi mata cikin girmamawa tace"sannu da zuwa mommy, ya gajiyar aiki...."
Fuskarta da fara'a ta furta"lafiyalou daughter, zuwan bazata akai mana? Amma ya akai naganku a waje..."
Zahra kamar zatai mata sujjada tsabar yadda take magana cikin ladabi da biyayya
"Masu tsaron gate din ne suka hana mu shiga sunce dole sai an basu izni, har layinki na kira baya shiga nasan kin shiga busy ne..."
"Eyyah! Na sanya wayar a silent lokacin da zan shiga meeting...' tai maganar tare da kai dubanta ga su aneelerh"su wanene? Ina fata dai lafiya? Ta fada cike da son jin karin bayani
"Auntyna ne da ƙanina mahboob, wani abune mai mahimmanci Ya kawo mu .."
da sauri Aneelerh da mahboob suka karaso bakin motar hajiya saratu cikin girmamawa suka gaishe da ita, fuskarta asake ta amsa masu wato sunci albarkacin zahra shiyasa ta sakar masu fuska
"Pls kuyi hakuri sun shanya ku arana, Yanzu ku shiga motar, mu tafi. " wani irin dadi Ya lullu6e su, da sauri suka nufi motarsu, bayan sun shiga a jere motocin suka nufi cikin estate din babu wanda yayi gigin dakatar da su cikin securities din sai ma gaisuwar da suke mika ma hajiya saratu wadda ko kallo basu ishe ta ba.
Bayan sunyi parking, kowan nan su Ya fito, Aneelerh sai faman satar kallon katafaren estate din takeyi kamar a dubai, Inaga mahboob wanda Yake ta jinjina kai aranshi Yace"Wai dama haka daular obie estate take? Gari guda, Tabɗijan Daga gani anyi almubazzaranci wurin ginasa, Mutane kamar bazasu mutu subar duniya ba? Yo ni Allahna na tuna ko amafarki ban ta6a ganin katon gini irin wannan ba! Kai jama'a..sai faman santi yakeyi acikin ranshi
Gaba hajiya saratu tayi da sauri suka bi bayanta, zahra hada kar6ar handbag dinta ta ruƙe mata ita, irin fadancin nan
Ashe mahbbob baiga komai ba, suna shiga falon kiris Ya rage ya zabga salati saboda ganin makurar kayan alatun da aka baje ta ko'ina...har wani zazzabi yake ji ajikin shi
Ga masu aiki dake kai komo cikin uniform
"Bismillah ku zauna, Ku ɗan bani mintina kaɗan, Yanzu zan fito..' amsa mata sukai da toh, ta nufi daki zahra tabi bayanta don ta kai mata handbag dinta..
Ya rage saura mahboob da Aneelerh, zama sukai akan tamfatsa tamfatsan royal sofa din falon...
"Karshen duniya yazo aunty aneelerh" ya faɗa yana kishingiɗa bayansa jikin sofa, duk da halin damuwar da Aneelerh take aciki sai da ɗan murmusa jin abunda Mahboob Yace, ita kanta ta girgiza da ganin katafaren ginin
"Alhamdulillah Ya Allah.."ta furta aranta"Ya Allah kamar Yadda ka bamu ikon shiga gidan nan lafiya, Ya Allah ka bamu ikon ganin Yarinyar nan cikin sa'a ba tare da mun sha wahala ba" har cikin ranta wani irin sanyi takeji, fatanta Allah Yasa su dace
Kallon mahbbob tayi wanda ke ta bin ko'ina da kallo baki asake kamar lehen sakarai
"Mahboob! Pls kaja aji mana, kada kai mana kauyanci, duk fa abinda suke da shi mu ma muna shi agida...." tashin Farko Ya ce"muna da lifter..? murmushi aneelerh tayi"a'a amma ai akwai stairs ko"?
Girgiza kai yai"ba irin wannan ba duba fa kiga ni har hawa uku, ga yan aiki ta ko'ina..." murmushi tayi tana kallon shi" nifa aunty aneelerh bawai kyawun gidanne Ya ruɗe ni ba, no kawai almubazzarancin da akai wurin ginasa shiyafi komai 6ata min rai, Allah ba karamin mai imani bane zai zauna agidan nan kuma yaci gaba da yin sallah..." yar dariya Aneelerh tayi
Kafin wani Ya ƙara magana sofia ta nufo wurinsu hannunta ruƙe da tray na cool drinks tare da snack ta ajiye masu kan table
"Inayi maku barka da zuwa" amsa mata sukai da yawwa
"Hajiya saratu ce, ta bada umarnin akawo maku drinks, idan akwai abun da kuke bukata ku sanar dani..." har suna haɗa baki furta"a'a mungode,
Bayan ta bar wurin Mahboob Yace"munci darajar Zahra wlh da ko kallo bamu ishi matar can ba, daga ganin ta zatai ji da kai..."
Bayan wasu Ƴan mintuna, Hajiya saratu ta fito har ta canza kayan jikin ta, wata hadaddiyar abayace ta sanya, zahra na abiye da bayanta har suka karaso, zama tayi kan sofa tana fuskantarsu, itama zahra ta zauna.
Ƙara gaisawa sukayi kafin ta ce"Zahra ta faɗa min abune mai mahimmanci Ya kawo ku! ina sauraronku..." cike da dattako tayi maganar.
Gyara zama Aneelerh tayi cikin nutsastsiyar muryarta ta fara kora mata jawabin abun da Ya kawo su...
bayan ta kammala hajiya saratu tayi jimm na ɗan wani lokaci kafin ta dubeta"kun tabbata Yarinyar ce? Shiru sukayi ta kuma cewa" Bana so asamu matsala! Ba ku tunanin ko mai kama da ita ce..."?
Duk da ƙwarjinin da hajiya saratu tay wa aneelerh hakan bai hanata Yin karfin halin furta"muna sa ran itace, saboda ni tamkar uwa nake agareta, Yau shekara shida zuwa bakwai da 6atanta kamar Yadda na fada maki, kuma sunan yarinyar Unasah kamar yadda itama yarinyar da shi owais din yake ruƙo sunanta unaisah, amma muna kiran ta da Angel sunan da daddynta Ya sanya mata..." da kwarin gwiwa Aneelerh tayi maganar don ji take zata iya komai akan yarinyar nan
Numfasawa hajiya saratu tayi abunka ga mace mai izza, bata son abunda zai jawo raini tsakaninta da chief gani take kamar zubda girmane ta nemi alfarma awurinsa shiyasa take jinjinawa lamarin da suka zo mata shi, duk da tana son taimaka masu.
"Ina hoton Yarinyar, Ina son ganin shi" cikin sauri zahra ta buɗe mata hoton awaya ta muƙa mata.
Bayan ta kar6a ta kurawa hoton ido nan take ta gane fuskar yarinyar cikin yaran da owais yazo da su wurin dinner.....
"Ina hoton ita Yarinyar ta wurin ku"? Ta faɗa tana kallon Aneeelerh, yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin saurin curo wayarta daga cikin handbag ta buɗe hoton Angel ta yunkura taje gaban hajiya saratu ta miƙe mata wayar
Bayan ta kar6a ta jera wayar zahra da aneelerh akan table din gabanta, a tsanake take nazarta hotonan ita kanta ta gasgata abunda suke hasashe komai iri ɗaya, banbanci ita yarinyar da uwais Yake ruƙe ta fi angel dinsu girma amma duba da tazarar shekarun da yarinyar ta 6ace zai iya yiwuwa itace taƙara girma...
Gaba daya hankulansu Aneelerh akan hajiya saratu duk sun kagara da son jin me zatace masu..
Bakomai take jinjina mawa ba face ta yadda zata zubda girmanta wurin yiwa owais magana, saboda basa jituwa tun time da ta fahimci bai kaunar mijinta, kuma tana jin haushin Yadda ake nuna wariya tsakanin Twins dinta da shi
"Dan Allah ki taimaka mana kamar yadda Allah Ya taimake ki, wallahi baki ga halin da mahaifiyar yarinyar take a ciki ba, yanzu haka tana agadon asibiti kwata kwata bata a cikin hayyacinta, sunan mijin ta da yarta kadai ta ke Iya ambato..."
muryar Aneelerh ce ta katse mata zancen zucin nata
"Meya same ta ne? Ko kina nufin tsawon lokacin da yarinyar ta 6ace bata a cikin hayyacin ta..." ta jefa mata tambayar cike da sonjin karin bayani
Labari aneelerh tafara bata tun guduwar benazir da kuma dawowarta har izuwa kan abun da Ya faru jiya
Jinjina kai hajiya saratu tayi da alama abun Ya tsuma zuciyarta duk da bata nuna ba.
"Allah ya bata lafiya" suka amsa mata da ameen.
"Zan nema maku alfarmar ganinta, amma kafin nan ina bukatar ku bani zuwa gobe, kunsan yanayin aikinsu na jami'an sirri, kuma yaran kamar suna bincike kan case dinsu ne, ganinsu zaiyi wuya, dole sai na fara yin magana da shi....."
Aneelerh taso ace ta kira chief din awaya sunyi maganar nan take amma dole ta hakura tunda su ne ke nema awurinta dole su yi biyayya
A tare suka haɗa baki wurin yi mata godiya.
har bakin motarsu hajiya saratu ta rakosu ta ƙara jaddada masu gobe zasuji daga gareta
Lokacin da motarsu ta haura kan titi, shiru babu mai magana a cikinsu,
"Wani jinkirin Alkhairi ne, muyi hakuri" zahra ce ta fada ganin damuwa na neman rikita auntynta
"Allah Ya tabbatar mana da alkhairinsa" suka amsa mata da ameen
Dai dai motarsu ta kusa shiga tankameman gate din asibitin saiga motar dr shureim tana fitowa daga ciki, kasancewar window glass din abude Yake da sauri aneelerh ta kwala masa kira Ya shureim...
Ya na ganinsu Ya samu wuri Yai parkin din motarsa, fitowa tayi da sauri ta nufi motar ta ɗan zukunna bakin glass din tana kallonsa
Duk sai taji wani iri ba dadi ganin yadda fuskarsa tayi jawur idanunsa sun kumbura
"Yaya shurem Ya jikin benazir din?
"Da sauƙi, amma har Yanzu bata tashi daga bacci ba...
"Allah Ya bata lafiya
"Ameen..." shiru sukai kafin tace"naga ka fito ko gida zaka koma ne..."
"Bani zan koma gida ba, zeenatu zan maida..." sai da yai maganar idonta Ya hango mata zeenatu dake zaune a backseat ta kifa kanta bisa gwiwowinta yatsun hannunta sai kerma suke daga gani babu nutsuwa atare da ita
"Ina fata badai wani abu Ya same ta ba"!
"Daddynta ne Yace amaida ta gida, shi ne take kuka"
"Allah sarki baiwar Allah...." cikin nuna tausayawa tayi magnar, zeenatu duk tana jinsu saidai bata jin zata iya dagowa saboda gaba daya fuskarta ta ca6e da ruwan hawaye..
"Ya ake ciki game da Yarinyar kun samu ganin ta..."? Ya jafe mata tambayar saboda abun na aransa
Nan Aneelerh ta sanar da shi Yadda sukai da hajiya saratu
Jinjina kai yai"in sha Allah gobe idan ta kiraku awaya tare zamuje estate din....ko su mami ban sanar mawa ba saboda bana so su sanya rai har sai mun tabbatar in itace....
"Shikenan Yaya shureim Allah Ya kaimu lafiya amma zaka dawo ko"?
"Ay dole na dawo aneelerh, Daga na kaita zan juyo..." Allah Ya dawo dakai lafiya
Sallama sukai ma junansu, ta tsaya tana kallon motarshi har ta 6ace ma ganinsa
Komawa tayi cikin motarsu, Mahboob Ya karasa shiga da su ciki tun kafin yayi parking yake ta faman jinjina kai Yana fadin anyi almubazzaranci wurin gina asibitin sai kace ba wurin jinyar marasa lafiya ba, komeye amfanin ƙawata asibiti ...."
yana karasa yin parking suka fito da sauri suka nufi emergency ward sai da suka fara tsayawa wurin nurse's station bayan sun fada masu sunan marar lafiyar da suka zo dubawa, ɗaya daga ciki tayi masu jagora har dakin da aka kwantar da ita, kafin ma su isa suka hango Hajiya layla tare da Alhaji ubaid abakin kofar asitin suna magana atsakaninsu, fuskokin kowan nan su babu annuri sai tsantsar damuwa
Takun tafiyarsu Aneelerh ne Yaja hankulansu ga dubansu
"Aneelerh......" hajiya layla ta fada cike da mamakin ganin ta, ita kanta baza ta iya tuna rana ta karshe da tai tozali da ita ba.
Aneelerh na karasawa ta rungume hajiya layla batasan sa'adda kuka Ya balle mata ba
Shafa kanta hajiya layla tayi tana ɗan rarrashin ta, hakika tayi mamakin ganin yadda ta kara girma rayuwa kenan andade ba'a hadu ba, tun da zumuncin su Ya watse
Tsawon mintuna hajiya layla tana lallashinta, kafin ta dago idanu jawur ta gaishe da Alhaji ubaid fuskarsa da fara'a ya amsa mata har yana ɗan zolayarta
Aneelatu kece kika koma haka? Ƴayanki nawa? Cikin shesshekar kuka tace Yarona dayane Yana a school,
"Allah shi raya shi,
Tace"ameen"
"Ya hakurin abun da ya faru da su Uzair"?
"Mungode Allah"
"Ubangiji Allah Ya bayyanar da su" ta amsa mashi da ameen
Hajiya layla tace"ki shiga ciki," da sauri ta shiga dakin,
Su zahra dake atsaye har suna haɗa baki wurin Gaishe da su ita da mahboob suka kuma yi masu ya mai jiki
"Jikin da sauki bacci take, amma ku yan uwanta ne"?
"Ƴaƴan uncle dinta ne mu"
"Allahu akhbar kamar na ta6a ganinku da jimawa lokacin baku kai haka ba.."
Zahra tace"eh ay muna yawan zuwa joss lokacin baya..."
"Allah sarki ku shiga daga Ciki dan Allah kuyi mata addu'a' amsa mata sukai da toh
Bayan sun shiga, agaban gadon suka iska Aneelerh ta zuƙunna kan gwiwowin ta, kanta akan gadon, hannunta acikin na Benazir, jikinsu duk sai yayi sanyi ganin yadda benazir ta faɗa daga jiya zuwa yau har ta canza...
Har lokacin hajiya sarah na zaune kan kujera sallah kadai ke tada ta..
Gaishe da ita su zahra sukayi tare da yi mata ya mai jiki tace masu da sauki,
"Ubangiji Allah Ya bata lafiya, Allah yasa kaffarane" ta amsa masu da aneen
Gaban gadon suka tsaya kafin suka fara yi mata addu'o'i suna tofe mata jiki da su,.....
Kamar masu zaman makoki haka suka tasa ta agaba suna kallon ta.
Wureran karfe biyu da rabi ta farka kamar mai ta6in hankali haka ta dinga fusge fusge tana ambaton sunan taj da Angel, ta makance bata ji bata gani bata sauraren kowa hauka kawai takeyi masu, haka suka dinga rurruƙe ta don kokari ma take ta sauko daga kan gado, su Aneelerh sun sha kuka ba kamar da ta furta"kada su bari ta mutu bata sanya yarta a idon ta ba, bata son ta mutu bata ganta ba, su taimaka ma rayuwarta....."
babu wanda bai zubar mata da kwalla ba, hatta mahboob Yaji tausayinta
Likitan dake kula da ita ne Ya shiga dakin tare da wasu nurses Ya bukaci su hajiya sarah su fita daga waje
Nan suka fito kowa Ya zauna kan waiting seat suna ta jiran tsammani
Tsawon mintuna ɗuff suka daina jin sautin koke koken benazir, har sun fara fargaban meke faruwane sai ga dr adam Ya fito daga dakin tare da nurses din
Suna ganin shi kowa Ya mike suka nufe shi suna tambayar awani hali take ciki"?
Fuskarsa babu walwala Yace masu suci gaba da yi mata addu'a sannan su yi kokarin samo yarinyar da zata iya pretending amatsayin yarta daga yau zuwa gobe in ba haka ba sakamakon ba lallai Yayi masu dadi ba, don sunyi iyakar bakin kokarinsu amma abun yaci tura, Yanzu haka allurar bacci suka ƙara Yi mata....."
Hankulansu ba karamin tashi Yayi ba, nan fa suka fara shawarar Yadda za su samo Yarinyar dake kama da Angel ƴar fara mai launin ido ruwan toka..
Aneelerh tayi saurin cewa akwai wata yarinya da ta sani mai kama da unaisah, amma ko za'a same ta sai ya kai zuwa gobe...." ta fadi hakanne saboda tana sa ran gobe hajiya saratu zata kirasu inyaso koda yarinyar ba unaisah bace sai su nemi alfarmar abasu ita aro har zuwa time ɗin da benazir zata ji sauki...
Hankalinsu ba karamin kwanciya yayi ba, hajiya layla tsabar zumudi hada cewa me zai hana yarinyar tazo yanzu? In ma da bukatar suje gidan iyayenta neman alfarma sai suje..tace masu ay yarinyar ba'a kusa take ba, suyi hakuri zuwa gobe sai a sanar da iyayenta amsa mata sukai da toh ..........
Bayan komai ya lafa, Aneelerh ta kira mami awaya don ta sanar da ita halin da ake ciki, a lokacin tana a falo zaune zuciyarta cike fal da tunanin kome Ya tsayar da su aneelerh har yanzu basu dawo ba? Ko dai sun samu shiga gidanne? Ita kadai take ta tufka da warwara, kiran na shigowa a hanzarce ta dau wayar dake akan sofa hand, ganin sunan aneelerh yasa tay saurin dagawa
"Aneelerh! Ina fata kuna lafiya? Naji shiru baku dawo ba, ba sai da nace maku in baku samu shiga gidan ba kada ku takura kanku?
On the other hand Aneelerh tace"mun samu shiga mami, amma bamu samu damar yarinyar ba...." a tsanake ta sanar da ita komai ta kara da cewa"tace zuwa gobe zata tuntu6e mu,..."
Mami tace"to kuyi hakuri ku dawo gida, wani jinkirin alkhairi ne..."
"Mami, Yanzu haka muna asibiti, benazir ba lafiya..." tunkafin ta kare maganar mami ta doka salati tana fadin wata benazir din? Meya same ta"? Gaba daya hankalin ta ya tashi
Shigowa ummi tayi falon tana kallon mami dake ta zagba salati tana sauraron Aneelerh dake bata labarin abun da Ya faru bayan komawarsu dr shurem gida,
"Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'i abu baiyi dadi ba, kai jama'a baiwar Allahn nan tana jin jiki, ubangiji Allah Ya tashi kafadunta, Anerlerh gani nan zuwa asibitin, kice wa mahboob kada ya manta da junaid karfe shida Yaje ya daukosa" amsa mata aneelerh tayi da toh
Bayan ta katse kiran, fuska A yamutse ta kalli ummi dake tambayar ta lafiya meya faru taji ta ambaci sunan benzair
Girgiza kai tayi kafin ta kwashe komai ta sanar da ita, hankalin ummi ba karamun tashi yayi ba.
"Yanzu zanje asibitin, ki zauna ke inyaso gobe sai kije kada abar gidan ba kowa, duk da Ana tana nan ba lallai junaid Ya yarda da ita ba kinsan shi da rigima."
Amsa mata ummi tayi da toh, cike da Alhinin abun da Ya faru, da sassarfa mami ta dauko hijabi ta zubla ta fito daga daki, ummi tayi mata adawo lafiy sanna tace agaishe mata da mai jiki, kafin taje goben
Mami na fitowa daga gidan saiga motar abie ta shigo, hakan ba karamin dadi yayi mata ba, dama abun hawa zata tsayar akaita can, sai gashi Allah ya dawo da shi, Agabanta Yayi parking motar bata jira Ya fito ba, ta bude motar ta shige sai da ta zauna yake tambayarta ina zataje yaga kamar bata acikin nutsuwarta, nan ta sanar da shi abun da ya faru na rashin lafiyar benazir, har faɗa sai da yayi akan fada matan da aneelerh tayi mami tace bafa laifin ta bane, itace ta matsa mata, kuskure daine an riga anyi sai dai ayi fatan Allah Ya tashi kafadunta....
Karya kwana yayi da gudu motarsu ta fuce daga gidan kai tsaye suka nufi asibitin.
_________________________________✍️
Slowly motar dr shureim ta kunna kai cikin gidan, bayan yai parking ya dago ya kalli zeenatu da ta kifa kai bisa gwiwa tana ta shesshekar kuka
"Bazan gaji da lallashinki ba, dan Allah ki hakuri ki jure ya shurem bayason ganin hawayen babynsa, na fada maki addu'armu take bukata, kuka ba abunda zaiyi mata...." tun da yafara maganar bata dago dakai ba
Fitowa yai daga motar ya zagaya dayan bangaren da take ya buɗe mata"fito mu shiga" still bata tanka mashi ba, dama dakyar ya rabata da asibitin. Ba karamar badakala suka sha da ita ba. Kuka tadinga yi akan bazata koma gidan ba, dakyar suka lalla6ata.
Ganin zata bata lokaci Yasa shi kai hannayensa ya tuttu6eta kamar yar tsana Yai mata irin daukar da ake ma jariri Ya nufi cikin gidan da ita.
Tana kuka tana fadin yaya shureim bazanje ba ni ka sauke ni, wurin aunty benazir zan koma...bai saurareta ba har ya karasa katafaren falon, Alhaji musa na azaune kan sofa ya daura kafa ɗaya bisa ɗaya, idanunsa na akan laptop dinsa, hada mug din coffee a gefe yana sha babu alamun damuwa akan fuskarsa hankalinsa kwance
Shigowarsu ne Yasa shi dago da ido Ya kallesu Fuskar shureim a daure Ya dira zeenatu, ransa Ya baci da ganin uncle din nasa kamar baisan halin da suke aciki ba.
"Shureim..." har ya kusa Fita ya dakatar da shi waiwayowa yayi babu walwala Ya ke kallonsa, shi kanshi alhaji musan Ya fahimci fushi Yake da shi
"Ya jikin benazir din? Kamar bazai tanka masa ba ya furta"da sauki"
"Menene sakamakon abunda ke damunta"?
Sai da ya ɗanyi jim kafin yace"It's depression and panic attack...." bai kare maganar ba yai hanzarin fucewa daga falon don baya jin zai iya jurar kallon uncle musa tsaf zai Iya gaya masa magana
Har ya kusa fita daga entry hall din kwatsam sautin muryar zeenatu Ya dakatar da shi Ya kasa kunne Yana sauraronta
Cikin muryar kuka take fadin"Wallahi daddy baka da tausayi, kowa ya damu da halin da aunty benazir take aciki ban da kai! Jiya kana gani haka ta kwana akulle kaki taimakawa ka buɗe mata kofa, har sai da ta kwana, why daddy? Baka sonta ne? Ko tayi maka wani laifi ne da yaja har kake nuna halin ko'in kula akan ta, ni wlh ka 6ata min rai daddy tun da har baka damu da rashin lafiyar aunty benazir ba, hankalinka kwance kana agida sai kace ba ɗiyar yayanka ba,....." kamar daga sama dr shureim yaji saukar mari ji kake tasss
A matuƙar furgice ya ware dara daran idanunsa, jikinsa na 6ari a sukwane Ya juya cikin takun sauri Ya nufi falon Har zai shiga wata zuciyar ta gargadesa akan kada Yaje Tsayawa yayi yana sauraron su daga inda yake yana iya hangen zeenatu wadda tunda daddynta ya kwasa mata mari gaba daya ta jirkice ta kife kan hannun sofa, jikinta yadinga bari kusan wannan ne karo na farko daya fara ta6a lafiyar jikin ta....baiwar Allah gaba ɗaya ta furgice ta kasa dagowa ta dinga tsala kuka tana fadin na tsane ka daddy, da kanka ka sa hannu ka buge ni? Daddy ka makance ne? Wlh sai dai ka kashe ni daddy..." masifa ta dinga zazzaga mashi
Zeenatu bata ta6a bashi mamaki ba irin na yau, duk irin shakkarshi da take ji hakan bai hanata fadan ta cikin ta ba, hakan ya tabbatar masa da taji haushin abunda yayi
Yatsun Hannunsa Ya zubawa idanu cike da jin haushin marin ta da yayi,
Duk da ita taja ma kanta, shi fa ba'ay masa fada ana ɗaga masa murya balle ita da take yar cikinsa...
Walking slowly Ya nufi sofa din da take Ya zube kan gwiwowinsa agabanta.
dr shureim dake la6e Yana kallon shi har saida Ya ɗan ware idanunsa cike da mamakin Yadda Alhaji musa Yai kneel down agaban zeentu mutumin da ko uwarsa baya tunanin Ya ta6a zukunna mata, wannan wani irin sone ya ke yi mata?
Kamar zai mata sujjada haka Ya fara magana"i'm really sorry my daughter, kurkurene ba da son raina ba, kece kika fusata ni zeenatu, banso na mareki ba..." yadda yake yi mata magiya ba karamin ɗaure kan dr shureim yayi ba, har tafin hannu yasa ya shafa fuskarsa don Ya tabbatar in ba mafarki Yake Yi ba
Cikin shesshekar kuka take fadin"Dad ..dy dama ka daina bani hakuri, don bayi zanyi ba, ni bana son ganin ka, tun da bakason Aunty benazir dina..." bata kare maganar ba, Yai hanzarin furta"waya fada maki bana sonta? benazir kamar ƴa take awurina..."
To amma meyasa jiya kaki bude mata kofa
"Saboda bani na kulleta ba, itace ta kulle kanta .."
"Daddy ni ban yarda kana sonta ba, tun da kaki zuwa asibiti dubata..."
Hannu yakai tare da janyo zeenatu ya kwantar da kanta saman broad chest dinsa Ya daura tafin hannunsa abayanta yana lallashinta..."ki daina kuka bana so, indai akan benazir ne zanje na dubata hope hakan yayi maki"
Tana faman matse kwalla tace"daddy dr yace in har ba'a bemo mata yarta ba, zuciyarta zata buga ta mutu, dan Allah kasa a nemo mata yar babynta, daddy nasan zaka iya..." yamutsa fuskarsa yai kafin yace"naji zanyi kokarin sanyawa a nemo mata ita, Yanzu ki kwantar da hankalinki, Muje daki ki kwanta ki huta, zan sa tani ta kawo maki abinci nasan kina jin yunwa..." yai maganar tare da mikewa ya ruƙo hannun zeenatu acikin nashi, suka nufi bedroom dinsa
gauran numfashi dr shureim Ya sauke aranshi yana mai al'ajabin irin son da Alhaji musa yake ma zeenatu
Sai dai baiji dadin marin da yayi mata ba, yaji zafi aranshi, saboda yaga shatun yatsunsa sun fito ruɗu ruɗu kan kuncinta yasan dakyar in zazza6i bai kamata ba, saboda zafin hannu gare shi, ya ta6a marin zainab mai aikin gidansu lokacin dayaje joss kawai saboda ta haɗa hanya da shi har ta bangaje shi cikin rashin sani, tun da ya kwasa mata mari sai da tay 1 week tana jinyar fuskarta....
sai dai yasan ba lallai ya bari zeenatu taji jiki ba, tunda yana sonta zai mata maganin abunne
Da wannan tunanin Ya fuce daga gidan Ya shiga mota Yaja Ya nufi asibiti.
______________________EX-PRISONERS
A tsaye suke su biyu suna fuskantar junansu, tunda batool ta sanar da ita game da wayar da tajiyo aunty ummin su, tana yi a tsakar dare cikin toilet, taji hankalinta Ya tashi zuciyarta harta fara raya mata ko dai aunty umminsu da wata muguwar manufar take atare da su?
"Taya za'ay insan dawa take magana"? Ta jefa wa kanta tambayar
"Wai hada cewa ay bani da wayon da zan iya sanya mata ido..." acewar batool
"Anya batool ba zaki daina kwana dakin ta ba?
"Saboda me"?
"Indai zaki cigaba dayi mata la6e duk ranar da ta gano ki, wlh zata Iya hukunta ki, tun da bamusan me take ƙullawa ba!
Girgiza kai batool tayi"ni dai bana Yi mata mummunan zato, kuma bana so na daina kwana dakinta..." fuskarta ayamutse tayi maganar
"Nima ina kyautata mata zato, amma meyasa take abu kamar mara gaskiya? Waya a toilet kuma a tsakar dare? Sannan har tana fadin baki da wayon da zaki iya sanya mata ido?
Ruko hannun batool tayi"bazan hanaki kwana dakinta ba, amma kiyi takatsantsan, kada ki ƙara yi mata la6e kibarta kawai, In sha Allah ba abun da zai faru watakil ma bata son ki farka daga bacci ne shiyasa ta shiga toilet tanayin wayar don kada ta takura maki' jinjina kai batool tayi alamar gamsuwa da maganar unaisah
Kafin wani ya ƙara yin magana a cikin su, suka ji an turo door room din, kusan atare suka dago suna kallon mai shigowa har saida gabansu Ya ɗan fadi ganin matar da suke gulmarta
Tayi gayu abunda cikin riga da wando sun kama jikinta, head din data daura ba karamin kyau yayi mata ba, tuni kamshin turarenta Ya buɗe hancinansu
Ganin yadda suka tsareta da ido ne Yasa tace"lafiya naganku atsaye? Ko dai gulma ta kukeyi ne"?
Har suna hada baki wurin fadin"A'a" kashe masu ido tay tare da sakin murmushi tace"ku fadamin gaskiya ba abunda zanyi maku, meyasa da kuka ga nashigo kukayi shiru? Bayan kafin na shigo naji kuna magana cikin raɗa
"Wlh ba gulmarki mukeyi ba..." ta6e baki tayi"shikenan tun da kunki fadamin gaskiya, Ku zo mu tafi dining, it's lunchtime. Yan uwanku suna jira..."
Amsa mata sukayi da toh, a tare da ita suka fito daga dakin...tunkafin su Isa suka hango su Haris zazzaune kan dining chairs an cika masu table da lafiyyayan abinci
Wuri suka samu kowa Ya zauna har sun fara cin abinci unaisah ta tuna da danish, har ta fara gajiya da halin shi, sam bayason zuwa dining cin abinci sai in taje tay masa magana tukunna Yake fitowa,
Haka da safe lokacin da zasuyi breakfast sai dai Sajeed ne Ya kai masa adakinsa
"Ina ɗan uwanku ne? Na lura baya son zama acikinmu Yaci abinci.." Ummi ce tayi maganar
Naufal Yace"Bari naje na kira shi" yai maganar tare da mikewa, ajiyar zuciya unaisah ta sauke dama neman wanda zaije Ya kirasa Takeyi don batajin zata ƙara zuwa dakinsa gudun kada ya kara yi mata abunda yayi jiya
Dawowa Naufal Yai"yace ki kai masa adakinsa" Ya fada idonsa akan unaisah, Yamitsa fuska tayi"batool ki kai masa pls"
Ummi na murmushi tace"bake Yace kikai masa ba? Ki tashi mana ke Yake son gani"
Maƙe kafaɗa tay alamar bazata je ba,
Mikewa batool tayi"Bari naje na kai masa.." da sauri ummi tace"koma ki zauna ita zataje, tunda ita Yake son ta kai mashi, Ki kasan ko akwai abunda zai faɗa maki...." turbune fuska tayi ranta ajagule kamar an mata dole ta dauki plate da saving spoon ta zuba mashi fried rice ta haɗa mashi da juice, tasan bai cika son cin abinci dayawa ba...
A bakin kofar dakin ta tsaya tare da kai hannu tay knocking, shiru ba'a buɗe ba, daga murya tayi"My man ni ce...." ta fada tana faman haɗe rai
Buɗe kofar yayi, lokacin da ta daura idonta kanshi har saida gabanta Ya faɗi ganin babu riga a jikin shi, zanene kirjinsa Ya ɗan sanya ta jin fargaba
Miƙa masa plate din tay"ga abincin..."
Lumshe idon yai"ki shigo min da shi ciki" make kafaɗa tay"pls ka kar6a kawai ba saina shiga ciki ba,..."
Ya fahimci rigime take ji"wani abu zan nuna maki..."
Harara ta galla masa"salon in shiga ka kara yi min irin abun jiya ko. " sai da tay maganar Ya fahimci abun da take ma fargaba
"Nayi maki alƙawarin bazan ta6a ki ba, tunda bakiso, pls ki shigo ki gani...." yanayin yadda yayi maganr ba karamin sanyaya mata zuciya yayi ba, cikin lallami Ya samu ta shigo Ya mai da kofa...
Akan table ta daura masa plate din tare da juice
Ganin Ya nufi gefen gadonsa yasa takai ido wurin har sai da taɗan ji gaban ta ya faɗi ganin acessories din dake zube kan mattaress dinsa masu kyau da tsada
Da mamaki ta furta"My shield Waya baka wannan"? ta fada tana tunkarar kayan kamar mai jin tsoron su
"Wannan mutumin ne Ya kawo min namanta sunanta, Yace min uncle dinsa hateem ne Yace abani su..."
Waro idanu waje tayi tana Yarfa hannu Ta furta"wayyo Allah daɗi, my man yanzu duka wannan naka ne?amma natayaka murna.... Agaban gadon ta zauna yatsun hannunta har kerma suke Yi ta dauki Apple laptop din ta buɗe ta tana kallon ta.
Ta aje laptop din gefe ɗaya takai hannu ta ɗauki iphone din sak kalar wayarta banbanci su colour ne..
bayan ta ajiyeta ta dauki apple ipad din tana jujuyata faskekiyar gaske...
"Amma dai mutumin nan Yana ji da kai, Allah Ya saka masa da mafificin alkhairi, kamar yadda yake kaunarka nima ina kaunarsa...." abun da bata sani na tun da tafara magana danish Ya nutsu yana kallon duk wani motsin ta, gaba daya ta tafi da imaninsa Yanayin yadda take yaba kayan tana murmushi tare da ɗan zare gray eyes din ta ba karamin kashe mashi jiki tayi ba.....idan ta motsa pink lips dinta kuwa har wani haɗiyar yawu Yake Yi
Duk bata lura ba, Headset ta dauka tana dariya tace"amma dai atare zamu dinga amfani da su ko? Kaga ni bani da wannan.." tay maganar tare da kallon shi ta kashe mashi ido ɗaya tare da daura mashi headset din a kansa ta saita mashi a kunnansa.
"Wow!...." wani Irin kyau yayi mata har bata san sa'adda ta manna masa kiss a cheeks din sa ba, mutumin fa gaba ɗaya ya fara zaucewa wani irin yanayi yake jin kanshi
Cire mashi headset din tayi, ta aje kan mattress din ta janyo eye glss box din tana danna akwatin nan take ya bude jerin hadaddun glass ne na maza ta dauko wani mai walwali launin blue sky ta zura mashi a idanun shi
Tabarakallahu ahsanul khaliqin shine abun da ta furta
Da tafukan hannyenta biyu ta tallabo fuskarsa ta zuba mashi ido tana kallon
Kamar yadda shima yake kallonta ta cikin glass din numfashin su har yana kokarin hadewa dana juna
"Sai naga ka ƙara min kyau my man, bari na canza maka wani" da sauri ta cire na fuskarsa ta dauko wani glass din black colour ta sanya mashi
"Wow kana kashe ni da kyanka...' ta fada tare da cire mashi glass din ta maida shi cikin ɗan akwatin
Ta janyo watchbox ta buɗe shi jerin tsadaddun agogunane ƴan ubansu
ta dauko ɗaya ta kamo hannun shi ta soma kiciniyar sanya mashi a wrist dinshi
"Ka wani kura min ido kana kallona kamar yau ka fara gani na" tayi maganar da zolaya...
Lumshe idonshi yayi ba tare daya furta mata komai ba....
"Wohoho Ina gwanin wani ga nawa..My man wlh kai na musamman ne, komai naka na kece raini ne...Kalli hannunka irin na ƴan gayu wadanda sukaji hutu..." sai faman santin hannunsa take agogon tayi bala'en yi mashi kyau .....
Sam ta manta da abun da ya faru jiya atsakaninsu ta zaƙe sai zuba take yi masa kamar aku
"Kin fara period ne❓Kamar daga sama Taji Ya furta wani bugu zuciyarta tayi mata, a ruɗe ta dago tana kallon shi ido cikin ido suke kallon juna❗❓
*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*
*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*
3196407426
First bank
Bature Hafsat Muhammad,
*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
Our website uses cookies to improve your experience. Learn more
Accept !
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: ____________________Boss Bature✍️
Sam ta manta da abun da ya faru jiya atsakanin su ta zaƙe sai zuba take yi masa kamar aku
"Kin fara period ne❓Kamar daga sama Taji Ya furta, wani bugu zuciyarta tayi mata, a ruɗe ta dago tana kallon shi ido cikin ido suke kallon juna.
har na tsawon mintuna ba tare da sun kyafta ba, gabanta ya soma faɗuwa, gaba ɗaya ta rasa sukuninta, la66anta sai kerma suke.
Sexy voice dinsa ce ta sake ratsa kunnanta"tambayarki nakeyi, ko ba ki ji me nace ba"? Yawu ta haɗiya kutt kafin tayi ƙarfin halin furta"meyasa ka tambayeni"?
Lumshe idanunshi yayi kafin ya ware su akan fuskarta"naga canji a tare da ke....." ɗan zaro ido tayi da tsantsar mamaki take kallon sa, girgiza mashi kai tay ba tare da ta iya furta wani abu ba
"Tell me the truth, have you started menstruating? I want to know. It's something I've been waiting for a long time." rass Taji gabanta Ya ƙara faɗuwa muryarta na rawa ta furta"ni.. Ni ban..ma san kan me kake magana ba..." cikin dabara ta tafara zame jikin ta daga kan gadon, kwatsam Taji Ya damƙi hannunta, Idanu zare ta kalle sa.
"Ki bani amsar tambayar da nayi maki" wani irin ƙwarjini yayi mata kamar ba man dinta ba, kamar mai jin tsoronsa ta furta"na fara, tun ranar da mukaje dinner din prime minister, amma ya ɗauke, a washe garin ranar.. " daƙyar ta ƙara maganar, ganin wani kayataccen murmushi gefen fuska daya bayyana akan kyakkyawar fuskarshi, hatta dimple dinsa sai da ya lotsa...
"Amma tayaya akai kasan alamomin mace idan tafara period? Sannan meyasa naji kace abu ne da ka daɗe kana jira"! Aruɗe ta jefa masa tambayar saboda abun ya ɗaure mata kai.
Matsawa yayi kusa da ita da sauri ta zame hannunta daga ruƙon da yayi mata, taja da baya kamar taga wani mugun abu.
"Kamar yadda na faɗa maki, naga sauyi atare dake..." abun da ya sanyata aruɗani yanayi da tagani atattare da shi, ga wani annurin farin ciki daya wanke fuskarsa.
"My man, Ya kamata na tafi tun da na kawo maka abincin, su aunty ummi suna jirana" adabarbarce tayi maganar jiki na 6ari ta sauko daga kan gadon daƙyar ta saci kallon shi suka haɗa ido"pls kada ka zauna da yunwa, idan ka kammala cin abincin ka yi wanka, ka sanya sutura a jikin ka, sannan pls ka daina kaɗaita kanka aɗaki ka dinga fitowa wurin su Haris...." tana magana tana ja da baya, tana kaiwa bakin kofar da sauri ta buɗe ta fuce daga gudu.
Sai da ta 6ace ma ganin sa, kafin ya kau da idonsa daga kallon ta, kasa cin abincin yayi saboda bashi Yake buƙata ba, akwai wani abu da zuciyarsa take muradi, sai dai yasan ba abune mai sauƙi Ya same shi ba, wata irin kasala ce ta baibaiyeshi cikin sanyin jiki ya kwantar da bayansa kan mattress din, haɗi da lumshe idanunsa.
Nannauyar Ajiyar zuciya Unaisah ta sauke bayan ta sauka downstairs, Hannun ta ɗaya dafe da saifin zuciyarta, bakomai take tunawa ba face kalamansa da suka tsaya mata arai, yayi matuƙar bata mamaki bata ta6a tsammanin Danish Yana da wayau har haka ba, ko tayaya akai yasan alamomin mace idan ta balaga"!? Ta jefa wa kanta tambayar da bata da amsarta..wucewa dinning tayi zuciyarta cike fal da tunanin sa...
_____________________________✍️
Da marece Hajiya saratu tana a gym room na gidan, cikin shiga ta activewear black colour riga da short dai dai gwiwarta, A hankali take running kan threadmill, ta haɗa uban gumi kan fuskarta da jikin ta.
Maganganun da suka tattauna da su zahra ne suka fara dawo mata akanta, Abun Ya tsaya mata aranta, tun bayan tafiyarsu take ta tufka da warwara, tana matuƙar son taimaka masu, but how? Tasan owais mai biyayyane agare ta, komai takeso zaiyi mata, sai dai bata jin girman kanta zai bari ta nemi alfarma agurinsa Kuma bata jin zata iya taka kafarta zuwa gidansa.
"Me ya kamata nayi"? Ta jefa ma kanta tambayar, Farat ɗaya ta tuna da hajiya laurat! Ita kadai ce zata Iya bata shawarar daya dace.
Fitowa tayi daga gym room din ta nufi part din su.
Tana shiga daki, ta nufi toilet ta shiga, within 15 mins, ta fito sanye da bathrobe, ta zauna kan mirror chair, phone dinta ta dauka ta danna ma hajiya laura kira
Sai da kiran ya kusa katsewa kafin hajiya laura tay picking
"Matar yaya barka da marece?ya kike"? Ta faɗa da murmushi akan fuskarta
On the other hand Hajiya laurat tace"Amarya kuma uwargida a wurin praving, lafiya lou, fatan kema haka..."
jinjina kai ta ɗanyi kamar tana agabanta
"naji kinyi shiru? Faɗamin meke damun ki? Don tunda naga kiranki a irin wannan lokacin raina Ya bani wani abu na damunki"
"Shawara nakeso Ki bani...." ta faɗa kamar bata son furta maganar, A hankali ta zayyana mata komai dangane da zuwansu zahra...
"Bansan Ya zanyi ba! Nayi masu alkawarin zuwa gobe zasu ji kirana, nasan sun kwallafa rai, ni kuma Allah bana son in nemi alfarma awurinsa, nasan owais yana da biyayya zaiyi min abun da nakeso amma ina jin nauyin zubda ma kaina mutunci..."
Sautin dariyar Hajiya laurat ne Ya cika kunnanta, nan take ta haɗe rai"bana son iya shege, Oh dariya ma na baki? tun da bazaki bani shawara ba, zan kashe kiran"
Da sauri Hajiya laura tace"Am sorry hajiya, kin bani mamaki ne! Kamar kina jin shakkar tunkararsa, Ki aje wani jin kai gefe ɗaya, Yaron nan ɗan yayanki ne, kuma ɗanki, kina da iko da shi, ba alfarma zaki nema a gurin sa ba! abun da yakamata shine Ki bashi Umarni, kiransa zakiyi awaya kice mashi yazo inda kike Ya same ki, Idan Yazo ki zauna ki faɗa masa komai sannan kice mashi gobe zasu zo ganin yarinyar, baki bukatar wani abu da zai sa girmanki ya zube a idon su...."
tiryan tiryan hajiya laura ta tsara mata komai, tunkafin ta karasa maganar, Hajiya saratu ta fara sakin murmushin gefen fuska, saboda shawarar tayi mata 100% shiyasa take ji da hajiya laurat, matar karshe ce wurin Iya bada shawara..
"I can't thank You enough, Hajiya ta, nagode da shawararki, shiyasa yayana Yake ji dake saboda kin Iya tsara kalami ga iya bada shawara...." sautin dariyar Hajiya laurat ne Ya karade kunnanta
Bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"nima naji dadi da kika dauki shawarata, Yanzu faɗa min Ya ake ciki game da hajjaty? Har yanzu baki gano komai ba"?
Ta6e baki hajiya saratu tayi"Hmm Matar wayon tsiya gareta kamar dila, yarinyar dana sanya tana yi mata leƙen asiri, har yanzu bata gano komai ba, amma tace min tabbas akwai wani abu da take kullawa adakinta, saboda bata son kowa Ya shiga...."
Hajiya laurat tace"munafuka, ay daga ganin ta zatai wayau, kuma wallahi ba wayanta bane akwai wanda ke ɗaurata akan hanya,..."!
"Kamar ya bangane me kike nufi ba.."?
"Ina nufin ba ita kadai take shirya plan ba, akwai wani dake taimaka mata..." da tsantsar mamaki hajiya saratu take sauraronta, tabbas Ta yarda da kalaman hajiya laurat saboda matar tana da kaifin basira...
Sun jima suna tattaunawa akan hajjaty kafin daga bisani su ka yi sallama.
______________________________✍️
Kusan atare motocin su suka kunno kai cikin estate din,
Bayan sunyi parking, Pravin Ya fito cikin shiga, ta suit, Ya jingina bayan shi jikin motar, Idanunsa akan motarsu twins dinsa, fitowa sukayi kowannansu Ya dauki wankan suit, sun kwaso gajiyar aiki sai faman lumshe idanu sukeyi
Tunkarar shi sukayi da sauri shima Ya nufe su, gaba ɗaya ya hadesu Ya rungumesu, tare da daura hannayensa abayansu.
"Yau mun dawo gida atare, ya gajiyar aiki" dagowa sukayi atare suka dube shi
"Daddy Ba dadi, wallahi, na gaji, ni fa kasan bana son wahala.." zayn ne yayi maganar,
Zaid Yace"Alhamdulillah daddy, kaima ya gajiyar naka aikin"?
Murmushi yayi kafin yace"ay ni bana aiki, ina da masu yi min komai, illa Iyaka in karshen wata yayi in kwashi Albashina...." kallon juna sukayi da mamaki akan fuskokin su,
Ko ajikinsa Yaci gaba da fadin"tuntuni naso In wayar maku da kai amma kuka ƙi yarda, Kunfi so ku yi ta wahala akan albashin da bai taka kara ya karya ba, har atm dina na baku don kuyi irin rayuwar da kukeso amma kuka ki kar6a saboda baku yarda dani ba ko.."
Shiru sukayi suna kallonshi, kafin Zayn yai kafin halin cewa"daddy ta yaya zamu kar6i kudinka? Bayan ba halal dinka bane!! Baka aiki kuma kana kwasar albashi, hakan na nufin haramun kake ci, daddy kaji tsoron Allah, ka riga da kasan hukuncin wanda Ya gina kansa haram..." bai ƙare maganar ba, Pravin yayi saurin dakatar da shi ta hanyar ɗaga mashi hannu, da kakkausar murya ya furta"Enough! Don't you dare repeat what you just said to me!! Gidan ubanwa nake cin haram? duk wani kuɗi da nake da su, Hakkina ne ina da goyan bayan waɗanda suka ɗaura ni akan muƙamin da nake da shi. ..." Yana faɗin hakan rai a6ace Ya nufi cikin gidan, da sauri zaid yabi bayanshi tare da shan gaban shi.
"Daddy ka yi hakuri, naga ranka ya 6aci, Dan Allah ka yi hakuri da abun da zayn yace maka! ka yafe masa kada ka ruke sa a zuciyarka..."
Murmushin gefen fuska pravin yayi"kada ka damu my son, komai Ya wuce"
Ajiyar zuciya zaid Ya sauke, Tare da ruko hannun daddyn nasu suka shiga parlour.
Zayn dake kallon su har sai da suka 6ace ma ganin shi, kafin ya jingina bayan shi jikin motarsu, kalaman zahra ya fara tariyowa, a lokacin da ta kira shi Yana a office, ya gama watsewarsa tare da abokiyar aikinsa yana akan network shiyasa Ya zazzaga mata masifa son ranshi aranshi ya ayyana ko sun samu shiga estate din? Ta6e la66ansa Yayi irin bai damu din nan ba, Ya wuce Ya nufi cikin gidan
"CHIEF OWAIS💪💋*
Yana a cikin Katafaren Office dinsa dake a isod Headquater, office ɗin Ya haɗu, an ƙawata shi da high-end supplies komai na cikinsa launin blue sky ne kalar da yafi so, office din Yana da mugun tsaro gaba daya na'urori ne ke sarrafa komai na cikin sa.."
Daddaɗan ƙamshin turarensa Ya gauraya da ni'imtacciyar iskar dake ratsa saƙo da lungu na office din, a yayin da yake azaune kan wata tamfatsetsiyar Excutive chair Ƴar ubansu, Ya ɗaura kafarsa ɗaya bisa ɗaya, daga gaban shi luxury table ne mai ɗauke da High-end computer da sauran kayan amfaninsa dake a baje kan table din
A hankali Ya buɗe idanunsa dake a lumshe, Ya cigaba da operating computer din gabansa,
Adjusting webcam dinsa yayi, kafin ya danna video call Ya dan dakata Yana jira a amsa mashi.
a hankali fuskar commender ta bayyana ta cikin screen din
Murmushi suka sakar ma junansa, Cikin harshen turan ci suka fara magana
"Commander, good to see you, sir," ya faɗa tare da sarah mashi da hannu
"Chief, good to see you too," shima ya sarah mashi.
"What can I do for you?"
Numfasawa chief yai kafin yace"I'm calling to extend an invitation to a high-level meeting in Nigeria, dangane da yaran da kuka damƙa mana case din su" Ya ƙare maganar, Cike da sa ran zai amsa mashi
Jinjina kai commender din Yayi na ɗan wani lokacin Kafin Ya furta" okey, What's the current situation?...bayani ya fara kora masa dangane da halin da ake ciki na binciken prisoners.
Tun da ya fara commender Yake ɗan jinjina kanshi alamar gamsuwa, bayan ya ƙare maganar yace"yanzu wani mataki zaku fara ɗauka"?
Chief yace"That's what we'll discuss during the meeting"
"Tunani mai kyau, zanyi magana da na sama dani, idan har na samu goyan bayan su, zamu halaccin meeting din, yaushe ne kuma a ina za'ayi"?
"Upper week, in Abuja. I'll send over the details. Thank you, Commander..." Ya fada tare da sara ma shi da hannu.. Shima commender din Ya sara mashi
bayan sunyi sallama Ya kwantar da kansa jikin kujerar
"DDG Is coming" Muryar na'ura ce ta ratsa kunnansa, A hankali Yakai idonsa ga duban Glass door ta office dinsa wadda ke kokarin zuge kanta
Big guy ne Ya shigo sanye Cikin kakinsa, Cikin girmamawa Ya sara mashi.
"Sannu da aiki Yalla6ai, Na ji shiru baka fito ba, ko baka lura da time ba ne"? Kallon agogon hannunsa yayi ƙarfe biyar na marece, har time din ta shin sa yayi bai lura ba.
"Have a seat"
Zama big guy yai kan kujerar dake fuskantar chief kamar yadda ya umarce shi
"Munyi waya da commender..." a ƙagare big guy yace"ina fata Ya amsa buƙatarmu"!
Calmly ya zayyana masa tattaunawar da su kai, wani irin farin cikine Ya bayyana akan fuskar shi"Allah Yasa mu ji alkhairi" Ya amsa mashi da ameen
Shiru sukayi na wani lokaci kowa da abunda Yake saƙawa aranshi
"Ya kamata ka tashi muje in kaika gida, burina ka huta..." murmushi chief yayi"nagode da kulawarka agare ni, Ina boss ko har ya tashi aiki"?
"Tun wuraren huɗu ya koma gida, kasan mutun mai Iyali, ba kamar mu da muke tazurai ba..." da zolaya yayi maganar, harara chief Ya dan watsa masa batare daya furta wata kalma ba
Ya miƙe Ya nufi kofar fita, da sauri big guy yabi bayansa a tare suka fito daga office din.
Tsayawa fasalta haduwar isod headquarter bata baki ne, abun sai wanda Ya gani, lifter suka hau ta sauke su down, ta ko'ina ka kalla Jami'an isod ne sanye cikin kakinsu tun daga senior agents dinsu har izuwa jenior agent, duk inda suka bi cikin girmamawa jami'an suke sara masu, Har suka fito daga headquater din, kaitsaye suka nufi katafaren parking space din su, dankara dankaran motocine makil tare da bikes dinsu killace a harabar.
Da sauri wani agent Ya bude masu backseat na motar da zasu shiga, bayan sun shiga kowan nan su Ya zauna, agent din dake jigilar daukar su Ya yi wa motar key cikin ƙwarewa Ya fara driving dinsu zuwa gida.....
Dai dai lokacin da motar su ta kunno kai cikin gidan, Wayarsa ta fara ringing, lokacin da ya duba sunan mai kiransa yayi mamakin ganin aunt saratu, Cos Ya manta when last Yar tahalikar nan ta kira da sunan tayi magana da shi.
Picking call din yayi tare da kara phone din a kunne, Cikin ladabi Ya yi mata sallah tare da gaishe da ita
Ko sallamar shi bata amsa ba ta furta"Owais, bayan sallar magbrib, Ka same ni a pool yard, Ina son yin magana dakai"! Cike da bada umarni ta furta, bata jira amsar shi ba, Ta katse kiran.
Kurawa screen din wayar ido yayi ba tare da ƙyaftawa ba..."
"Yalla6ai, Mun ƙaraso"! Big guy ne Ya fargar da shi, sam bai lura sun karaso ba, Fitowa yayi da sauri Ya nufi Cikin main falo din gidan
Yana shiga bedroom dinsa, Ya rage kayan jikin shi, Ya shiga toilet domin Yin wanka,
*HAJJATY*
Safa da marwa Take Yi atsakar dakinta, tun safe take sa ran zuwan pravin shuru bai leko ba, Hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, gani take kamar wani mugun abunne zai faru da ita, saboda abun da ya faru jiya yayi matuƙar daga mata hankali.
Yanke shawarar fita neman shi tayi, da sauri ta dauko mayafi ta yafa akanta, Tana kokarin fita suka ci karo da juna har saida ta bangaji kirjin shi, da sauri taja da baya tare da dafe gefen kanta da hannu daya
"I'm sorry wifey, Ina zaki je ne"? yayi maganar yayin da yake nufar cikin dakin idanunsa akan fuskarsa
From head to toe Ya kalle ta, farat ɗaya ya gane akwai wani abu dake damunta, da alama ko wanka batayi ba.
"Baki da lafiya ne" ya yi maganar tare da ruƙo hannunta suka zauna gefen gadon ta
"Baki ji ina magana ba? Fashewa tayi da kuka tare da kifa kanta akan kafadarshi
Hankalin shi yayi matuƙar tashi jin kukan hajjaty, yana daga cikin abunda Ya tsana arayuwarshi.....
Cikin shesshekar kuka tace"pravin ina cikin tashin hankali, Saboda akwai mai bibiyar rayuwata, daren jiya bana acikin kwanciyar hankalina, a tsorace na kwana, ko baccin kirki banyi ba, ina ta jira ka dawo shiru baka zo ba..."
Tuni yanayin fuskarshi Ya canza zuwa tsantsar 6acin rai,
"Fada min meya faru dake a daren jiya? Wani ya shigo ne"?....ɗagowa tayi da kanta hawaye na sintiri kan kuncinta ta kwashe komai ta sanar da shi...
Tafukan hannayensa ya daura kan fuskarta,A hankali Ya fara share mata hawayen ta
"Ki yi hakuri, in sha Allah koma wanene ke naman ki da sharri kan shi zai koma, Allah Yana atare dake wani bai isa Ya cutar min dake ba! ...." bai kare maganar ba, tace"bansan ya zanyi ba, wallahi ina jin tsoron ranar da asirinmu zai tonu, pravin bana son abunda zaija mu rasa kimarmu da darajarmu a idon mutanan gidan nan, saboda ina ji araina akwai wanda ke son ya tona mana asiri shiyasa aka fara bibiyana.." ta faɗa tana jan numfashi kafin taci gaba da cewa"saboda fargaban abunda Ya faru daren jiya, ko abinci banci ba tun safe har yau kamar mai azumi, wanka ma nakasa yin shi...."
Ta ƙare maganar, tana kallon cikin idanunshi
"Tuntuni saida naso In siya maki gida daban inda zakiyi rayuwarki cikin kwanciyar hankali, amma sai kika nuna bakison rabuwa da su....abunda nake jiye mana kenan...
"Duk laifinka ne, Abunda kayi min awurin dinner din hateem shine Yaja har wasu suka fara zarginmu, kuma ni gaskiya bazan bar gidan nan ba, kawai ka nema min mafita ..."
Jinjina kanshi yayi tare da ruko hannayenta acikin nashi"zan tambaye ki wani abu" daga mashi kai tai alamar toh
"Idan kika kama 6era adakin ki Yana yi maki 6arna, kuma kinsan zai iya haifar maki da gagarumar matsala wani hukunci zaki masa"?
"Meyasa kayi min wannan tambayar"?
"Kedai ki bani amsa"!
Shiru tayi jim kafin tace"hannayen da yake yin amfani da su wurin yin 6arnar su zan naƙasa, sannan in murje bakin shi ta yadda bazai iya daukar komai da shi ba...." murmushi pravin ya sakar mata"kin kawo shawara mai kyau.." arude tace"bangane me kake nufi ba"
Bai bata amsar tambayarta ba, sai cewa yai muje bathroom In taimaka maki kiyi wankan da kika kasa"
Ajiyar zuciya ta sauke tare da mikewa suka nufi toilet atare almost 18 mins Ya fito dauke da ita a hannunshi, dukansu sun daura towel a waist dinsu,
Taimaka mata yayi ta sanya kaya, shima ya maida nashi
"Tashi ki je kitchen ki shirya mana abinci mu ci atare" amsa mashi tayi da toh,
Bayan fitarta da yan mintuna ta dawo hannunta ruke da try na kayan abinci, ta ajiye masu kan rug, saukowa yayi daga kan gadon suka zauna atare suna ci.....
___________________________✍️
Bayan kammala sallar Magbrib, Owais Ya nufo pool yard din gidan baba obie, Jikin shi sanye da farar jallabiya, tunkafin Ya ƙarasa Ya hango Hajiya saratu zaune kan kujera ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, Hankalin ta na akan wayar hannunta da take dannawa
Cikin kunnanta ta tsinkayi muryarsa"Assalamau alaikum" ba tare da ta kalle shi ba tace"wa'alaikum salam,"
Zukunnawa yayi daga gaban kujerar da take Cikin girmamawa Ya gaishe da ita, Har cikin ranta taji daɗin hakan da yayi mata sai dai bata nuna a fuska ba, wai don kada ya raina ta
"Lafiyalou My son, ina fata Ka wuni lafiya? Ya aiki"?
"Alhamdulillah.."
"Bismilla ka zauna" ta fada tare da nuna masa chair din dake facing dinta, miƙewa yayi bayan ya zauna ya ɗago da ido ya kalle ta, babu alamun zata kalle shi
"Mommy, kince kina son ganin na, zamu yi magana" sai da ta mula ta sha iska kafin tace"eh, magana ce mai mahimmanci, Ina fata zaka bani aron hankalin ka.."
Amsa mata yayi da toh, tsawon mintuna biyar ta shanya shi, kafin ta fara kora mashi jawabi dangane da zuwan su Zahra, da alfarmar da suka nema a wurin ta...." tun da ta fara maganar, Yake dubanta da alamun rudani akan fuskarshi.
"Ita zahran da ta kawo min maganar, tana ɗaya daga cikin interior designers din da suka yi mana aiki aranar dinner din hateem a hall dinne taga yarinyar, sunan yarinyar ta wurinsu Angel amma asalin sunan ta Unaisah, har hotonta sun nuna min, sunyi kama sosai da yarinyar wurin ka,"
Cike da son jin ƙarin bayani yace"ko ta fada maki sunan Baban Yarinyar da sunan mahaifiyar ta"? Shiru tayi tana kokarin tariyo sunan su ....can tace"na tuna, sunan mahaifin yarinyar zaheer tajudeen, mommynta kuma sunanta benazir"
." Bari na kira Daddyn nata, naji idan Ya san su" da mamaki hajiya saratu tace"oh dama mahaifin yarinyar yana atare da ku"?
"Eh," ya bata amsa atakaice, har cikin ranta taji dadin jin hakan....
Phone dinsa Ya curo daga aljihu Ya danna ma Taj Kira, Tana fara ringing Ya saka wayar a handsfree don taji abunda zasu ce
"Yalla6ai barka da marece, Na shigo gidan na taras baka nan.."
"Ina agidan grandpa, zuwa anjima zan shigo"
"Allah ya dawo kai lafiya"
Am so nake na tambaye ka, Wa cece Aneelerh! Kamar na ta6a jin sunan abakin ka"
"Yalla6ai ka kamanta ne halan, matar aminina ce uzair, kamar mahaifiya take awurin Angel ɗina..." murmushi hajiya saratu tasaki jin abun yazo mata cikin sauki
"Zamuyi magana idan na shigo gidan" amsa mashi yayi da toh, bayan yayi rejecting call din Ya ɗago Ya kalli hajiya saratu dake kallon shi
"Yarinyarsa ce..."
"Alhamdulillah, Yanzu gobe da yaushe zasu zo ganin ta? ta tambaya tana kallon shi
"Duk lokacin da yayi miki, su zo kawai" murmushin gefen fuska tasaki, Taji dadin yadda yake bata girma
"Nagode my son, bari nasa akawo mana abun sha" da sauri yace"ina so zan shiga wurin baba"
"Okey, mu tafi tare" mikewa sukayi atare suka jera suna tafiya, abun ba karamin dadi yayi mashi ba, tsawon lokaci basa jituwa da juna, sai gashi silar neman unaisah da yan uwanta sukazo yi Allah Ya haɗa kan su, Har fira ta fara jan shi da ita, a haka har suka karasa dakin baba obie...
Idan muka koma 6angarensu Hajiya Layla dake a asibiti, wuraren ƙarfe 8 na dare, Hospital staff suka fara sallamar mutanan da ke zuwa dubiya, saboda a dokar asibitin karfe takwas na safe visitors suke zuwa da zarar takwas Na marece Yayi kowa zai tafi za'abar majinyaci karkashin kulawar nurses
Hajiya layla tace ita fa ba inda zataje, dole ta kwana don ta kula da yar ta, dr shureim ma ya goyi bayanta, tunawa da barazanar kashe benazir da ake Yi, Idan suka tafi ba lallai nurses su san lokacin da za'a farmake ta ba, duk da akwai cctv camera a kowani daki na marasa lafiya, bayan hakan asibitin Yana da tsaro sosai, kawai dai bai yarda subar benazir ta kwana ba tare da wani nata akusa ba
Hospital staff din basu Yi masu gardama ba, ganin sanannu ne a idon jama'a, kuma da ma ire irensu sunayi masu alfarma, kodan saboda matsayin dake gare su, musamman hajiya Saratu da takasance former firstlady ta kasar, tun da ta sanya baki a maganar suka amince hajiya layla ta kwana tare da ita.
Gaba dayansu sun hallara a harabar ajiye motocin asibitin, Sun fito domin tafiya gidajen su,
Mami da abie suna atsaye, Ga Aneelerh da Zahra da mahboob, Aneeleeh taso abarta tayi jinyar benazir,
"Mu zamu wuce, Ubangiji Allah Ya bata lafiya, Allah Ya tashi kafadunta, in sha Allah zamu cigaba da tayata addu"a" abie ne yai maganar tare da miƙa ma Alhaji ubaid hannu suka yi musabaha
"Mungode sosai, Allah yakaiku gida lafiya,"
Mami tace"dan Allah duk halin da ake ciki game da rashin lafiyarta ayi kokarin sanar damu"
Hajiya sarah tace"in sha Allah zamuyi kokarin hakan"
bayan abie da mami sun shiga mota, Hajiya layla ta ruko Hannun Aneelerh acikin nata fuskarta dauke da matsananciyar damu tace
"Dan Allah kiyi kokari Aneelerh, Zuwa gobe, Ku tuntu6i iyayen yarinyar da kikace tana kama da yarta, ku rokar mana alfarma awurinsu, su ara mana ita, idan ma suna bukatar mu biyasu kudi su faɗi nawa suke so, ko nawa ne zamu biya, wallahi bana so na rasa benazir, ina matuƙar jin tausayinta...." la66anta na kerma ta ƙare maganar, tuni taji hawaye sun wanke fuskarta
Wani irin tausayinta ne Ya kama Aneelerh, bata san sa'adda itama ta fara share kwallar ba, Yau dai sun sha kuka bayin Allah
"Mommy in sha Allah zanyi kokarin ganin sun bamu yarinyar, Indai akan benazir ne wallahi sai inda karfi na ya ƙare...."
"Pls kukan Ya isa haka, Ku yi hakuri, mu cigaba dayi mata addu'a Allah Ya bata lafiya..." acewar hajiya sarah
Dakyar sukayi sallah da juna, bayan sun aneelerh sun shiga motarsu, A jere motocin suka fuce daga asibitin,
"Zan tafi ba dan naso ba, amma In sha Allah, gobe da wuri zan shigo asibitin"
Fuskar hajiya layla a yamutse tace"Sai Allah Ya kaimu.."
"Duk halin da ake ciki, pls ki sanar dani" ta amsa mata da toh,
"Allah Ya bata lafiya" ta amsa mata da ameen, dr shureim ne ya buɗe mata murfin motar, Ta shiga daga ciki, kafin Ya datse mata, akan idonsu motar hajiya sarah ta fuce daga asibitin
Ya rage saura su uku dake atsaye suna kallon juna,
"Shurem muje ko"? Alhaji ubaid ne yayi mashi maganar, Sam baya son tafiya, Gani Yake kamar in ya tafi wani abu zai faru da benazir,
"Toh daddy" Yayi maganar, Tare da ruko hannun hajiya layla
"Mommy, nasan ko ban fada maki ba, zaki kula da ita, amma inaso ki sanya ido sosai, dole sai kin hana idonki bacci in ba haka ba..." bai kare maganar Ba Alhaji ubaid Yace"meyasa kace haka"?
"Daddy akwai wani abu da nake zargi akan benazir, zan sanar daku amma ba yanzu ba, saboda bana son ɗaga maku hankali, kawai abinda nakeso mommy kada kiyi gangancin kula da ita, in ba haka ba za'a iya samun matsala, duk da munsan Allah ke tsare bawansa amma da bukatar muma mu kula"
Hankali atashe Hajiya Layla ke kallon shi, Muryarta na rawa tace"Shureim dan Allah ka fada min meke shirin faruwa da Benazir dina, ni dama najima ina zargin akwai wanda ke bibiyar rayuwarta, so ake akashe min ita, ko faduwar da tayi a toilet sai da raina ya bani wani mugun abunne Ya faru da ita, in ba haka ba taya za'ace ta fita hayyacin ta? Bata gane kowa dake akanta?..." maganganunsu sunso rikita Alhaji ubaid Ya rasa gane inda zancen su Ya dosa
"Dan Allah kuyi min bayani meke faru ne"?
Da ido Hajiya layla tayi ma dr shureim Alamar yayi shiru saboda tana zargin ba hakanan Aka kyale Alhaji ubaid ba, kada su saki baki su sanar da shi zargin da suke Yi Yana iya zuwa ya sanar ma Alhaji musa, tunda Ya zama kamar ubansa komai zaiyi sai ya nemi shawarar shi
Jinjina kai dr shureim yayi alamar Ya fahimce ta,
"Daddy, Muje gida zan sanar da kai komai" Ya faɗa tare da ruko hannun shi, Hajiya layla tayi masu Allah Ya kiyaye hanya, tana atsaye tana kallon motarsu har suka fuce daga hospital din,
Da sauri ta koma ɗakin benazir, tana shiga, ta iske Nurse agaban gadon ga benazir zaune jikin ta sai kerma Yake tana ta sambatu
"Daddy, mommy, ku kira min taj, Ya kawo min babayna dana bar mashi, dan Allah ku bani ƴata, kada na mutu ban ganta ba...." lallashinta hajiya layla ta cigaba da yi sam bata fahimtar komai, sunan ƴarta da mijinta kadai take ambato,
Har abinci nurse ta kawo mata, kwata kwata ta kasa cin shi, duk yadda mami takaiga lallashinta abun Ya faskara, Addu'oi ta koma tana tofa mata, har dare Ya tsala mami tana zaune kan kujera tana kallon ta, Har dr ya shigo ya kara duba jikinta, Ya bata magungunanta dakyar suka samu ta sha, daga bisani bacci Yayi awon gaba da ita, lokacin da aka fara kiraye kirayen sallar ishai'a, mami ta shiga toilet cike da zullumin kada wani ya shigo dakin Ya cutar da benazir, saboda ta razana da jin kalaman dr shureim, jin motsin mutun adakin yasa tayi wuff ta bangaje kofar toilet din ta fito tana haki, Ko alwalar bata karasa ba..
*Daga alkalamin Boss Bature mu haɗu next page✍️*
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Y
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 29 Complete
by
Novels Elite Admin
August 07, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
✍️
Dafe kirji tayi tare da sauke ajiyar zuciya, ganin likitan dake kula da benazir ne
"Are you okey"? Daga mashi kai tayi alamar eh,
Ganin tana mashi kallon kamar bata yarda da shi bane yasa shi cewa"zan tashi daga aikine, Na shigo na kara duba lafiyarta ne, kafin na tafi...." murmushin Yaƙe ta sakar mashi"mungode dr, Allah Ya saka da alkhairi, agaida gida" ya amsa mata da toh, harya fuce daga dakin Yana mai mamakin Hajiya layla, abun ya daure masa kai yadda ta fito daga toilet a haukace anya kuwa tana da lafiya"?
Komawa cikin toilet din tayi, sam babu nutsuwa atare da ita, shaf shaf ta ƙarasa alwalar ta fito da sauri ta nufi closet din dakin ta dauko darduma ta shimfiɗa tare da kabbara sallah.
Da zarar taji motsi adakin sai gabanta Ya faɗi, bayan ta ida sallar, ta zauna tayi addu'o'i ta kai kukanta wurin Allah,
Kafin ta mike ta koma kan chair din dake fuskantar gadon benazir ta zauna tana kallon ta, patient gown din dake ajikinta launin light blue tayi mata kyau, A hankali ta kai hannu ta shafa gefen fuskarta, tuni taji ƙwalla sun cika idanunta.
Idan muka koma bangaren su Aneelerh, bayan komawarsu gida, A falo suka zauna kowa Yana jimamin halin da Benazir take a ciki, Ummi ta fito daga daki hannunta dauke da Baby junaid bawan Allah tunda Mahboob ya dauko shi daga makaranta, Ya dinga kuka Yana ambaton mommynsa, dakyar mami ta samu ta shawo kanshi Har yaci abinci tayi mashi wanka, har bacci Yayi, sauke shi ummi tayi da gudu Ya nufi Aneelerh ya faɗa jikinta Yana kuka, Ta rungune shi tana lallashin shi, dakyar ta shawo kanshi har suka sasanta junansu...
Lokacin da hajiya sara ta shiga falon gidan, kasa yin sallama tayi saboda fargaban hukuncin da Alhaji musa zaiyi mata, Cikin sanɗa ta nufi bedroom din su ko sallama batayi ba, ta shiga ciki,
A kwance ta same shi kan shimfiɗeɗan gadon shi, Ya tada kanshi bisa pillow, zeenatu na arungume da shi, ta daura kanta bisa kirjinsa, daga ita har shi kayan bacci ne a jikin su
Tayi tsammani bacci suke Yi, ajiyar zuciya ta sauke, ta lalla6e ta nufi cikin dakin, ta daura key dinta akan mirror, ta nufi toilet ta shiga, alwala tayo tana kokarin fitowa daga toilet din suka ci karo da shi, wani irin bugu kirjin ta yayi, tuni gumi ya lullu6e fuskarta, la66anta na kerma tace"yanzu na shigo, nayi tunanin bacci kake Yi, fatan na same ka lafiya..." tsare ta da idanunsa yayi masu matukar gigitata, gaba daya yayi mata kwarjini
"Ki faɗa min wani hukunci Ya dace Inyi maki"! Rass taji gabanta Ya fadi, marairaice mashi fuska tayi"am sorry bazan ƙara ba, wallahi bansan na ɗaga maka murya ba, dan Allah Ka yafe min.."
Fuskarshi babu annuri Ya furta"cewa nayi ki fada min wani hukun ci Ya dace nayi maki"?
Shiru tayi batare da ta furta kalma ba, duk tasha jinin jikinta....fargabanta kada Yace zai turata U.s
Saboda bata son duk wani abu da zai rabata da shi, shiyasa take yi mashi biyayya sau da kafa, duk wani abu da tasan zai bata masa rai, tana kokarin ganin tayi takatsantsan da shi
"Daddy kayi mata hakuri tun da ta gane kuskuranta," muryar zeenatu ce ta ratsa kunnuwansu,
"Kinci sa'a, da yau sai kin yaba ma aya zakin ta" nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, har zata wuce ya sake shan gabanta, a rude ta kalle shi
"Ya jikin benazir din?
"Jikin nata yayi tsauri, kwata kwata bata a hayyacin ta, baiwar Allah tana jin jiki"
"Allah Ya bata lafiya, in sha Allah gobe da safe zanje dubata" har cikin ranta taji dadin jin zaije dubata,
"Allah ya kaimu lafiya.."
"Kije kiyi sallar, kafin kin kammala zan kira tani ta shirya maki dinner dinki, nasan kina jin yunwa, kin wuni baki ciki komai ba" ya fada tare dakai hannu Ya shafa flat tommy dinta, aruɗe hajiya sarah take kallon shi, kamar ba Alhaji musa ba,yadda kasan badaga bakinshi kalaman suke fitowa ba,
Kamar sakarya haka ta kura mashi ido tana kallon shi, murmushin gefen fuska ya sakar mata, gaba daya ya nemi zautar da ita, dakyar ta samu nutsuwar sanya hijabi ta kabbara sallah,......"
Sallamar su Alhanji ubaid ce ta karaɗe kunnuwansu, da gudu Zeenatu ta diro daga kan gado ta fuce kamar walkiya, tunkafin ta karaso dr shuriem Ya hangota, murmushi ya saki tare da bude mata hannayenshi ta faɗa kan kirjinshi tana dariya
"Yaya shureim sannu da dawowa, naji dadin ganinka, dama ina ta zullumin kada kaki dawowa gida.." bata ƙare maganarba, Alhani ubaid Yayi mata gyaran murya, waro idanu tayi don gaba daya ta manta da shi awurin cike da jin kunyarshi ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta
Dariya Alhani ubaid Yayi"zeenatu, meya hanaki yin bacci..." muryarta da yar shagwa6a tace"yaya shureim nake jira ya dawo..." kafin ta kare maganar Alhaji musa Ya shigo falon Ya nufe su cikin takun nan nasa na isa
"Sannunku da dawowa, ya mai jikin"?
Alhaji ubaid Yace"da sauki, kafin mu dawo ta farka sai dai bata ahayyacin ta...." cikin nuna tausayawa ya furta"Allah Ya bata lafiya, gobe zanje asibitin, Ina Hajiya laylan ne"?
Dr.shureim yace acan zata kwana" shiru yayi bai ce komai ba.
wani abu daya daurewa dr shureim kai tun da ya dawo gidan zeenatu bata tambaye shi Ya jikin benazir ba, kwata kwata kamar irin ta manta da zancen ta, bayan tafi kowa nuna damuwa akanta, har magana yayi mata banji kin tambayin auntynki benazir ba, sai tayi shiru bata tanka mashi ba kamar bataji me yace ba, kusan sau uku yanayi mata maganar tana share shi, amma idan yayi mata wata maganar daban saita amsa mashi.
Bayan shigar shi daki, kasa runtsawa yayi, har saida Ya kira mommynsu a waya ya tambayeta awani hali suke ciki? Ta tabbatar masa da komai lafiya kafin ya samu nutsuwar Yin bacci.
*EX-PRISONERS*
Around ƙarfe 10 na dare, ummi ta sauko down, har ta shirya cikin kayan baccin ta,
Tunkafin Ta karasa Ta hango wasu daga cikin su kwance ka lallausar carpet din falon suna bacci, tun da zu tabarsu suna ta shan fira atsakaninsu tayi tunanin in sun gama zasuje su kwanta sai kuma ta taras da su kwance suna sharar bacci, wasu asaman sofas wasu akan carpet
Murmushi tasaki haɗi da girgiza kanta, tama rasa tayaya zata fara tada su,duk sun sanya kayan baccin su..., ɗaya bayan ɗaya ta fara farkar da su
"Batool My baby, wake up, Parveen! Hannah ku tashi dan Allah....! Ni bansan ya akai kuka bari bacci Ya dauke ku a falo ba, salon kawai ku wahalar da auntyn naku..." dakyar ta samu batool ta miƙe tana ƴan soshe soshe
"Wuce kije daki" ta amsa mata da toh,
"Praveen ku tashi..." cikin magagin bacci ta buɗe ido bakinta cunkushe da apple din da bata karasa cinyewa ba, bacci yayi awon gaba da ita, miƙa tayi tare da yin hamma ta nufi dakin su, ganin tana tangal tangal kamar zata fadi ne Yasa ummi yin saurin cafko hannunta, a lokacin ta samu hannah ta mike, ta ruko hannayensu a cikin nata har ɗaki takaisu, sai da taga sun kwanta kan gadonsu kafin ta dawo falon
Taci gaba da tada su"sajeed! Naufal ku tashi dan Allah, Mubeen Haris! Javed! Wai baku ji ina magana ne"? da wata irin kasalar bacci kowan nan su Ya mike har kwara mazan da kwarin su, suka nufi bedrooms dinsu
Wurinsu jemimah ta nufa, sun cunkushe kan sofa mai mazaunin mutun biyun yadda kasan kifin gwangwani, hannu biyu tasa ta dauki jemimah, ta daurata a kafadarta, kafin ta sa ɗayan hannun ta ɗago Azeeza, ta daurata a dayar kafadar ta, ahaka ta nufi dakin su, ta kwantar da su kan gadon su, sai da ta kashe masu switch din dakin kafin ta fito ta koma falon,
"Sarah! Wake up, rubina! Hibba! Pls ku tashi! Mana, Yasmin"! Har ta fara gajiya da tada da su, mikewa sukayi kamar babu laka ajikinsu, raka su tayi bayan sun kwanta ta dawo tana kallon waɗanda suka rage, Eve ce kwance kan rug tare da Deeja..Sai unaisah dake a naɗe kan sofa,
"Deejatun haris, Ta shi muje ki kwanta..." cikin magagin bacci ta fara sambatu tana fadin"wai meye haka ne? Ni ku kyaleni wallahi kada wanda Ya ƙara min magana..." Hannu ummi takai da niyar ta dago da ita, aikuwa ta daddage takai mata naushi a gefen bakin ta, tsabar zafin da ummi taji ne Yasa tayi saurin dafe bakin, ta lalla6a ta koma kan sofa ta zauna tana faman yarfa hannunta, ranta ya 6aci taji haushin naushin da khadeeja tayi mata, hakan yasa ta yanke shawarar barin ta a falon ta kwana, gudin kada ta lahantata garin tada ta daga bacci
Mikewa tayi ta nufi hawwa ta dan bubbuga kafafunta, cikin sa'a ta farka
"Ki je daki ki kwanta" amsa wa tayi da toh, bayan tafiyar hawwa ummi ta nufi unaisah
Bata tada ta daga baccin ba, daukarta tayi akan kafadarta, ta nufi bedroom dinsu da ita, tana shiga ta kwantar da ita akan gadonsu, ta kashe mata switch dakin,
Bayan ta fito falon, Ko kallon inda deeja take akwance batayi ba, don ranta Ya 6aci, kaitsaye ta nufi hanyar komawa dakinta, har ta kusa shiga taci karo da Batool kwance kan matattakar benan sai faman sharar baccinta take Yi
da alama zamewa tayi awurin ta faɗi cikin magagin watakil tayi azan gadone shiyasa taci gaba da baccin ta
Ɗaukarta ummi tayi da hannu biyu ta cucci6eta, ta haura da ita upstairs, bayan ta shiga dakin, ta kwantar da ita kan gadon su kafin itama ta haye ta kwanta tare da rungumota a jikin ta....
*❤🩹UNAISAH ANGEL💔*
Around ƙarfe 1:30 na dare, ta farka da matsanancin ciwon mara mai azababben zafi, hannayenta dake kerma ta ɗaura su akan cikinta, sai faman murzarshi take yi, sai faman yin birgima take akan gadon, daƙyar ta buɗe idanunta waɗanda suka kaɗa jawur da su, cikin mawuyacin hali ta kai hannu jikin bedside lamp ta kunna fitilar haske ya gaure zagayen gadon da take, wani irin gumi ke tsastsafowa ta jikin ta, hatta pajama din dake a jikin ta sun manne ma fatarta,
Yunƙurawa tayi daƙyar ta sauko daga kan gado ta shiga toilet, ta haye kan toilet seat, tayi fitsari anan taga jinin da ya dawo mata jawur yana gangarowa ta tsakantsakin cinyoyin ta, runtse idanunta tayi da karfi duk irin ɗaukin da take na son ya dawo mata sai da taji abun ya fita ranta saboda raɗaɗin da mararta ke yi mata
Bayan tayi tsarki ta fito, babu wandon ajikin ta, can ta baro shi a toilet....a gaban drawer chest na wardrobe din kayan su ta zukuna ta buɗe tare da sura hannu ta ɗauko pad daya, ta haɗo da pant, akan mattress ta ɗaura su tana faman sakin nishi kamar mai naƙuda,
"Can I give you a hand ."! kamar daga sama ta tsinkayi muryar mutun a kunnanta, sai tayi tsammanin gizo muryar shi keyi mata...kwatsam hasken ɗakin ya dauke ɗuff duhu ya gauraye ko'ina, a firgice take kallon duhun daya mamaye idanunta, gashi bata ƙarasa sanya pad din ba, cikin duhu tafara laluban gefen gadon don ta kunna fitar, ba zato ba tsammani taji saukar hannun mutun akan mararta, a matuƙar firgice ta zare gray eyes dinta, muryarta na kerma ta furta"de...deeja? deeja? Shiru ba'a amsa mata ba...tasan su biyu suke kwana dakin shiyasa ta ambaci sunanta, tunani tayi kadai batool ce
"Batool ke ce? Shiru ba amsa,"dan Allah wanene? A tsananin tsorace tayi maganar.
"Daddy...." bata kai ga ƙarasa maganar ba, Taji gaba ɗaya anjayota, ta faɗa kan kirjin shi, farat ɗaya ta gane koma wanene namiji ne kuma kakkarfa, Kware baki tayi zata fasa ihu yayi saurin haɗe bakinsu guri guda, jikinta ya fara kerma tafara kiciniyar kwace kanta, kamar yar dambe ta dinga ɗuma masa dundun da hannayenta waɗanda ke abayanshi, tayi kuka tayi haukan ko gizau baiyi ba har gartsa mashi cizo tayi wuri uku a kirjinshi amma babu alamun yaji zafinda zai sake ta
Fashewa tayi da matsanancin kuka"wayyo Allah daddy na, Aunty ummi, my man kana ina? Kana gani za'a cutar dani, na shigo uku wayyo Allah..." da iya karfinta na karshe ta bangaje shi gaba ɗaya ta kife kan floor, bata iya ganin komai da rarrafe tana laluban hanyar fita daga ɗakin, ƙafafunta taji ya ruƙo da hannayensa biyu ya ɗago bai direta a ko'ina ba sai akan gadon ta
Ta yunkura zata gudu Ya hambareta da gwiwar hannunsa, kanta ya daki pillow, kafin tayi yunkuri sake mikewa, mutumin ya toshe mata baki da tafin hannunsa gaba daya ya sakar mata karfi, ta yadda ko yatsan hannunta bazata iya motsawa ba, numfashinta dakyar yake fita, wani iri danshi danshi ta fara ji agabanta kamar ana zuƙe jinin dake fita ta farjin ta, runtse idanunta tay zufa ta fara tsastsafowa ta cikin hudojin gashin jikin ta, ga wani azababen zafi da matsananciyar kasala da suka rufeta a lokaci ɗaya, ta fara jan numfashi tana nishi, hawaye masu ɗumi suka wanke fuskarta, gaba daya ta zauce ta rasa tunaninta, lamarin kamar a amafarki take jin afkurwarsa, ta kasa ta6uka komai, sunan danish dana daddynta da aunty ummi kadai take iya ambato cikin zuciyarta a karshe raci gaba da ambton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un....... ❗
Tashin hankalin da ba'a saka ma shi rana! Shin wanene Yayi ma unaisah wannan aika aikar❓
_____________________________✍️
A zaune Yake kan darduma, Cikin shiga ta farar jallabiya, Hannunsa ruƙe da qur'ani Ya nutsu Yana karanta shi,
"Assalamu alaikum"! Cikin kunnanshi Ya tsinkayi muryar abbansu, sai da yakai aya kafin daura kur'ani kan prayer mat din Ya dago da ita Ya dube shi,
Yana asanye cikin kakin shi, zama yayi daga gefen gadon shi Yana duban fuskar dan nasa dakyau,
"Ina kwana daddy, Kun tashi lafiya"!
"Meke damunka"? Kai tsaye Ya jefa mashi tambayar,
Sunnar dakai kasa yayi kafin ya furta me ka gani daddy"?
"Abubuwa da dama! Na farko kwata kwata baka acikin nutsuwarka, tun zuwanka Nigeria na lura da akwai wani abu dake damun ka! Bayan haka me ya hana ka komawa bakin aikin ka!?
Shiru yayi ba tare sa ya furta kalma ba, baiso daddynsu Ya fahimci halin da yake aciki ba, saboda baya son Ya ɗaga hankalin shi,
"Kada ka 6oye min komai, duk duniya baka da kamata, kasan tsakanina dakai babu sirri, Idan wani abune ke damunka, ka sanar dani, in sha Allah zan taimaka maka mu sami mafita atare..." Ya faɗa cikin nuna kulawa
Bayajin zai iya 6oye mashi damuwar shi,tun da harya riga daya gano da kan shi, kwara kawai ya fada mashi gaskiya,
Cikin sanyin murya ya zayyana mashi komai, tun farkon haduwarsu da Benazir, da irin rayuwar da sukai har izuwa rabuwar su..." dagowa yayi idanunshi jawur cike tab da hawaye ya kalli daddyn nasu
"Daddy ka tayani da addu'a, Allah Ya jarabceni da sonta, ko baccin kirki bana iya yi saboda rashin ta atare dani, bansan awani hali take a ciki ba, nayi jiran hajiya laurat shiru har yau bata neme ni ba..., bana jin zan iya barin kasar nan in har ban hadu da ita ba....."
Tsananin tausayin shi ne Ya kama Daddyn nasa,
"Meyasa baka fada min ba tun farkon zuwan ka"?
"Banyi tunanin yin hakan ba, na bari sai in na hadu da ita sai in sanar dakai..."
Murmushi sir mubarak yayi aranshi yana mai mamakin zaki, mutumin da bai ta6a ganin wata ƴa mace Ya nuna yana son ta ba, Aikinsa kadai Yasa agaba, al'amarin so da girma ya ke...
A hankali Yasa hannu ya zaro wayar shi daga aljihu, ya ɗan daddanata, zaki dake kallon shi bai son me zaiyi ba.
Kara wayar yayi a kunnansa, kafin Ya furta"Assalamu alaikum mutumina, Ina fata kana lafiya"?
On the other hand muryar mutumin ta amsa masa da cewa"wa'alaikum salam! lafiyalou, Ina fata kaima haka"?
"Alhamdulillah, naji muryarka kamar daga bacci ka tashi .."
"No na jima da tashi, ya iyalin naka"?
"Suna nan lafiya lou...Tambaya ce nake so inyi maka..." gaba daya zaki ya nutsu yana kallon sir mubarak, baisan dawa Yake magana
"Ina sauraronka..."
"Yar wurin Yayanka benazir da ta bace, ta dawo gida ko hanyar yanzu ba labarin ta .."?
"Meyasa ka tambaye ni?
"Ka fara bani amsar tambayar da nayi maka..."
"Ta dawo gida..." azabure Zaki Ya miƙe tsaye da alamun rudani yake kallon daddyn nashi
"Nagode mutumina, Idan muka hadu zamuyi magana"
"Okey saina jika" katse kiran yayi, fuskarshi dauke da murmushi Ya kalli zaki, zubewa yayi agaban daddyn nashi, ya dafe gwiwowin kafafunsa da tafukan hanneyansa
"Daddy wanene ka kira a waya.. "?
"Uncle dinta ne Alhaji musa, baka san cewa shi mutumin mu bane, ay da tunfarko ni ka fara tuntu6a da maganar ta, da baka sha wahalar yi ma hajiya laura magana ba..." wani irin annurin farin cikine ya bayyana akan fuskar zaki,
"Idan har kana so In haɗaka da ita, sai ka bani cin hanci" ya fada da zolaya
"Daddy me kakeso na baka? Ka fada min koma menene...." dariya sir mubarak yayi
"Farin cikin ka da kwanciyar hankalin ka nakeso .." dariya zaki yayi
"Ka bani mamaki son, ji bi yadda soyayya ta jigata ka, kamar ba dan sir mubarak ba...." sunnar da kanshi kasa yayi cike da jin kunyar daddynsa
"Ni kamarma na ta6a ganin yarinyar? Halan 6oye ta kake yi idan naje canada don kada na ganta ." girgiza kai yayi"a'a daddy, bana 6oyanta zaka iya saninta, duk wanda yaje gida sai yayi tsammanin yar aiki na ce, shiyasa baku ta6a lura da shakuwar dake atsakanin mu ba..."
"Gaskiya zanso inji meya faru da ita? Meyasa ta gudu tabar Yarta? Amma kaima da laifinka, fisabilillah ina maka kallon uztaz ashe har mace kake 6oyo agidanka, almost 16years haba zakina! Kunyi ma kanku adalci kuwa? Da hankalin ka ka ajiye matar aure kuma kasan guduwa tayi daga gida bakayi yunkurin neman danginta ka fada masu ba!meyasa"?
Ya faɗa fuskarsa adaure alamar baiji dadi ba
"Daddy sonta ne Ya rufe min ido na, nasan na aikata babban kuskure amma nayi nadama, kuma ni harga Allah ban ta6a neman ta ba, abun dayasa ban nemi kowa nata ba saboda ta faɗamin ta tsani danginta, bata son ta dawo Nigeria, nayi kokarin shawo kanta donta amince in dawo da ita amma sai tace idan na matsa mata zata kashe kanta ne, shiyasa na kyale ta, daga baya mijinta ya turo mata sakon saki ta wayarta, daga ganin hakan saina kara samun kwarin gwiwar killace ta agidana saboda in mallake ta........." cikin sanyin murya ya kare maganar yana kallon daddyn nasa,
"Kayi kuskure da baka sanar dani ba, ay da nayi maka hanyar auranta, yanzu koda ka hadu da ita zata iya bijire maka ta koma ma tsohon mijinta...." dafe kanshi yayi da hannu ɗaya"daddy ka tayani da addu'a, Allah yasa rabona ce..."
"In sha Allah zanyi iyakar bakin kokarina don ganin ka samu abunda kakeso.." ajiyar zuciya ya sauke, kafin wani ya kara magana a cikin su,
Sallamar hajiya turai ta katse su, atare suka amsa mata, ta shigo fuskarta dauke da murmushi"i'm sorry na katse maku firarku, my son barka dai, fatan ka tashi lafiya" da fara'a ya amsa mata"lafiyalou mommy,
Kallon sir mubarak tayi"na kammala shirya mana breakfast, ka taso muje kaci kada ka makara" ruko hannun zaki yayi acikin nashi atare suka mike suka nufi dining din
Adai dai lokacin, dr Jazz ya fito sanye cikin black trouser da shirt, Ya daura lapcoat akan kayansa, idanunsa manne da farin glass
"Barka da safiya daddy..."
"Yawwa Son, Harka shirya kenan"
"Eh,"
Ya faɗa tare da samun wuri kan dining chairs suka zauna, turai ta fara yin serving nasu
"Big bro Ina kwana.." murmushi ya sakar mashi kafin yace"lafiyalou, ina fata kaima haka" ya ɗaya masa kai alamar eh,
Har sun fara cin abinci, Ibad Ya fito daga shi sai ɗan short,
"Mommy ni an manta dani, shine ba a kirani inzo inci abincin ba . " ashagwa6e yayi maganar
Turai tace"sorry babyn zaki, Ay nayi zaton zaka jira ne Ya kammala in ya rage sai ka ci.." murmushi sukayi
"Oh wai har yanzu bai daina wannan ɗabi'ar ba"? Sir mubarak ya tambaya yana kallon zaki
"Daddy bai daina, abun nasa kullum ƙara gaba yakeyi, bansan ya zanyi da shi ba, har friends dina sun gane halinsa, Na cin sauran abincin da na rage...."kallon shi sir mubarak yayi da sauri ya juya baya yana faman noke kai
"Daddy pls kada kamin faɗa, ni wlh na saba, kuma nafi jin dadin cin ragowar abincinsa, daɗi Allah" dariya suka sanya gaba dayansu
"Calm down Your mind, kai fa last born ne, shalelan mommy da daddy, ba wanda zaiyi maka faɗa, kayi abunda kakeso" yaji dadin maganar turai,
"Zo ka zauna in zuba maka abinci.." da sauri ya samu guri ya zauna, Yana satar kallon daddyn su da jazz wanda tun ya zauna, hankalin shi baya atare da su, gangar jikinsa ce kadai atare da su ruhinsa yana wurin faryat daya kwallafa rai akai.
"Jazz kaci abinci mana! Salon sai ka makara ko"? Cikin kulawa Sir mubarak yayi masa magana
Kamar baisan cin abincin Ya dauki cuf of tea mai zafi Ya ɗan kur6a
"Daddy dan Allah kace ma yaya zaki mu koma toronto, ko dan saboda karatuna, in ba haka ba zaija amaida ni baya..." da damuwa akan fuskarsa yayi maganar
Harara zaki ya dan watsa mashi"kada na sake ji kayi magana!..."
Sir mubarak ya katse shi da cewa"ba haka yakamata kace mashi ba.." ya faɗa tare da maida dubansa ga ibad wanda Ya haɗe rai.
"Next month zaku tafi, in sha Allah"
Murmushi ibad yayi"yawwa daddy thank you.."
"Wato na lura gudunmu kake Yi ibad..
"No momy wlh saboda school, kuma na manta bibina a gida..." Yana nufi magensa, miƙewa jazz yayi"zan wuce" atare suka haɗa baki wurin yi mashi Allah kiyaye hanya, sai da yabi kowan nan su ya manna masu peck kafin ya tafi......
________________________________✍️
Tun da garin Allah ya waya, Aneeleeh ta rasa kwanciyar hankalin ta, ta kasa tsaye taka zaune kamar mai fama da ta6in hankali, tayi matuƙar kagara ta kosa hajiya Saratu ta kira zahra, duk bayan yan mintuna sai ta leƙa dakin zahra don ta ji ko ta kirata shiru har yanzu babu wani labari, kamar yadda ta matsu haka hajiya layla ta matsu suzo da yarinyar, itace ta fara farkar da ita daga bacci da sanyin safiya ta kira ta awaya, tana kara jaddada mata akan kada ta manta tayi kokari su yi magana da iyayen yarinyar, ta rasa ya zatayi gaba daya ta daura ma kanta damuwa, daren jiya dakyar ta runtsa..
"Aunty Aneelerh"muryar zahrce ta ratsa kunnanta, Jiki na rawa ta juya da sauri ta nufi zahra dake shugowa dakin, tana sanye da hijab, hannunta ruko da wayarta...
"Zahra ta kira? Ko har yanzu"? shiru zahra tayi fuskarta babu walwala.. Hakan ba karamin ɗaga hankalin Aneelerh yayi ba
"Kinyi shiru baki ce komai ba"? fuskarta dauke da matsananciyar damuwa ta furta"muyi hakuri aunty Aneelerh, ta kira tace wai yarinyar ba unaisah ɗinmu bace....."
"Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un..." Hankali atashe Aneelerh ta zabga salati tare da ɗaura hannayenta biyu akanta
"Nashiga uku zahra! Ya zanyi? Ga shi nayi masu alkawarin yau zanzo da yarinyar, dan Allah ki taimaka min zahra, ki nema mana alfarma awurin hajiya saratun su bamu aronta...." gaba daya tabi ta ɗaga hankalin ta...
"Aunty Aneelerh, ki kwantar da hankalin ki, tace muje gida mu same ta yanzu watakil ko zasu ba mu aronta ne.." nauyayyar ajiyar zuciya Aneelerh ta sauke, jiki na 6ari tace"bari na shirya sai mu tafi, mahboob Ya dawo ne"?
"Bai kaiga dawo ba" amsawa tayi da toh, da sauri ta nufi toilet ta shige don tayi wanka
Fitowa zahra tayi daga dakin, jikin ta duk yai sanyi,
Bayan sun kammala shiryawa,sai da suka fara zuwa dakin mami suka sanar da ita kiran da hajiya saratu tayi masu, mami tace Allah Yasa muji alkhairi, idan kun isa komai ake ciki ku kira ku sanar dani,suka amsa mata da toh...
Da matsakaicin gudu motarsu ta haura kan titi, Aneeleerh ce ke driving dinsu, zahara na zaune gefen ta..
"Auntyna ki bi a hankali mana, naga sai zura uban gudu kike kamar zamu tashi sama!
"Ba zaki gane ba Zahra, wallahi ji nake kamar inyi fiffike in karasa estate din, gani nake kamar bana sauri, ni dai burina Allah yasa su taimaka su bamu yarinyar..." zahra ta amsa mata da ameen,
Lokacin da motarsu ta karaso estate din, da sauri Aneelerh ta rage gudun motar, sunyi tsammanin security officers din zasu dakatar da su irin na jiya amma abin mamaki suna isa, da hannu sojojon suka yi masu alamar su wuce, gaba daya suka sauke ajiyar zuciya
Bayan sunyi parking din motar, suka fito daga ciki, adai dai lokacin Hajiya saratu ta fito daga entry hall na gidan, ta dauki wankan leshi, idanunta sanye da farin glass
Cike da zumudi suka nufeta, with respect suka gaishe da ita, fuskarta asake ta amsa masu kafin tace"bismilla muje" ta nuna masu motarta da hannu, su biyu suka shiga back seat, security din da zai yi driving dinsu yana a mazaunin driver, Hajiya saratu na daga gefen shi...
Kaitsaye motar ta nufi cikin estate din
"Kamar yadda nake fada maku, munyi magana da shi jiya, nayi masa bayanin komai dangane da zuwan ku, to a gaskiya yarinyar bata wurin ku ba ce, amma yace zai iya baku ita har zuwa time da ita patient din naku zata ji sauƙi...." fuskarta babu fara'a tayi maganar.
kallon juna zahra da Aneelerh su ka yi jikin su yayi sanyi lakwas...
Cikin karyayyar murya Aneelerh tace"hakan ma yayi mungode sosai..."
___________________________________✍️
Firgigit ta farka daga bacci tana faman zazzare gray eyes dinta tamkar kwayar idanunta zata faɗo kasa, hannun ta ɗaya dafe da goshin ta, numfashin ta na fita da sauri, kwata kwata babu kuzari a jikinta kamar wadda aka zarewa laka, ga wata kasala data baibaye sassan jikin ta, dakyar ta yunkura ta miƙe zaune tare da jingina bayanta jikin pillow, fuskarta ta kumbura suntum, kumatun sunyi jawur, haka la66anta ma sun dan kumbura, idanunta sun ƙanƙance kwarmin idon yayi ja daga gani ta jigata ba kaɗan ba...
Lokaci ɗaya ƙwaƙwalwarta ta fara tariyo mata abunda Ya faru da ita adaren jiya, runtse idanunta tayi sosai kwallar da ta taru acikin su ta fara ƴar tseral kan kuncin ta, ta rasa gane meya faru? Shin mafarki ne ko gaske? Kokwanto ta soma yi saboda zuciyarta tagaza yarda da abun da ya faru, was wasi ta kama yi tana faman tariyo komai daya wakana adaren jiya, babu wata alama da zata tabbatar mata da abun ya faru dagaske, da sauri ta dubi yar rigar jikin ta, tayi uban squeezing kamar an ƙwatota daga bakin kura, da sauri taja rigar ta rufe santala santalan laps dinta, ta sauko daga kan gado tana faman bin dakin da kallo, mirror chair ta gani yashe ta jirkice kan floor
"Ina wandona Yake"? Ta jefa ma kanta tambayar,
Ringing din wayarta ne Ya doki dodon kunnanta, jiki na rawa ta nufi toilet saboda tana tunanin kamar anan ta cire wandon
Tana shuga ciki ta iske shi akan hanger, tunawa tayi da jinin daya dawo mata gadan gadan adaren jira aranta ta ayyana shima dagaske ne ko duk cikin mafarkin ne"? Ta kare maganar tare da buɗe laps dinta ta laluba jikin ta, bata ga komai ba, sai dai wani farin ruwa mai yauƙi yauƙi dake gangarowa...
Gaba ɗaya ta gama rikicewa, tunaninta ya kasu gida biyu, ta jima a toilet din kafin ta fara tunanin yin wankan
Bada jimawa ba, ta fito sanye da rigar wanka, har ta kusa isa gaban mirror tajiyo bugun kofa,
"Wanene"? ta fada tare da kallon ƙofar
"Daddyn ki ne..." sanyi taji ya ratsa zuciyarta, da sauri ta nufi kofar ta buɗe mashi
Tun daga kasa ta fara kallon shi, jallabiya ce a jikin shi maroon colour, sai kamshin turare ke tashi a jikin shi
"Daddy, Ina kwana..." bata ƙare maganarba, ganin yadda yake binta da kallo mai tattare da ruɗani
"Unaisah! Baki da lafiya ne? Meya faru naga fuskarki ta kumbura tayi ja, kamar kinyi kuka..." wani irin mugun bugu kirjinta yayi, babban tashin hankalinta kada ace abunda Ya faru jiya dagaske ne, ba mafarki ba
Muryarta adabarbace ta furta"da.. ddy.. lafiyana lou, meka gani ne."?
girgiza kai taj yayi"no ban yarda ba, fada min ko dai wani ya buge ki ne"?
"Wallahi daddy ba komai, watakil ko dan saboda firar da muka tsaya yi jiyane ban samu isasshen bacci ba shiyasa fuskata ta kumbura..." kwata kwata hankalinsa bai kwanta da yanayin ta ba, janyota yayi tare huggin dinta, ya daura hanneyensa akan bayanta
"Nayi missing dinki my daugher, ina fata kin tashi lafiya.."
"Lafiyalou daddy ..." dago da kanta yayi"baki jin ciwon kai? Ko zazza6i haka"
Ƙaƙaro murmushi tayi akan fuskarta duk don ta kwantar mashi da hankalin shi
"Bana jin komai daddy, ni yau da karfina na tashi..." ajiyar zuciya ya sauke
"Okey, ki shiga ciki ki karasa shiryawa, Chief Yana son ganin ki" waro idanu waje tayi alamar mamaki
"Daddy ni kuma? ɗaga mata gira yai alamar eh
"Ki sanya kaya masu kyau, zan jira ki awaje" cike da mamaki ta amsa mashi da toh,
Bayan fitarshi cikin sauri ta nufi closet dinsu, ta dauko wasu hadaddun riga da wando ƴan pakistan, rigar fara wandon yellow, veil din kayan yellow, ita kanta data sanya kayan saida ta jinjina ma kyan da sukai mata, gaban mirror ta zauna ta fara gyara sumar kanta dakyar take sharce ta da comb, bayan ta kammala gyara gashin, ta shafa powder da lipstick, kafin tayi rolling veil din akanta, takalma ta dauko masu tsini ta zura su a kafafunta,
Komawa tayi gaban mirror ta feshe jikin ta da turare
Har lokacin bata daina tunanin abun da ya faru a daren jiya ba, was wasi take tayi aranta.., kwata kwata bata so ya zamana gaskiyane abun da ya faru da ita....
A hankali ta zura kafarta ta fito daga dakin,
Walking slowly ta nufi daddyn ta dake atsaye yana jiran ta, babu kowa a falon da alama basu kaiga fitowa ba
"Daddy yunwa nake ji, Ciki na babu komai.." ta fada yayin da ta ruko hannunsa acikin nashi
"Kada ki damu, nima banyi breakfast ba, idan munje wurin chief din zamuyi atare da shi..." amsa mashi tayi da toh
Kaitsaye suka nufi walkway bata san ina za su bula ba
"Daddy ba part dinsa zamuje ba"?
"Eh, yace mu same shi a backyard..
Zazzaune suke akan wasu jigunannun sofas ƴan ubansu, backyard din ya Haɗu an ƙawata shi sosai, chief da hajiya saratu suna a zaune kan sofa daya, Aneelerh da zahra suna fuskantar su, tun da suka zauna Aneelerh take ta jinjina ma haduwar gidan da shi kanshi mamallakin gidan wato chief, kallo ɗaya tayi mashi saida gabanta Ya faɗi, ya ɗauki wankan suit navy blue sunyi bala'en yi mashi kyau
Zahra dake satar kallon shi, gani take kamar a mafarki yau gata ga director general na isod, crush ɗinta, mutumin da tayi haukan son shi a lokacin baya..
Round table din dake a tsakiyarsu, cool drinks ne da Snacks asaman hadadden wooden tray
"Idan muka baku aron yarinyar sai yaushe ne zaku dawo mana da ita.."? Hajiya saratuce tayi masu tambayar
"Idan da hali har zuwa lokacin da benazir din zata ji sauƙi, dan Allah ayi mana alfarmar nan..." gyaɗa kai hajiya saratu tayi"okey, amma fa zaku bani tukuici tun da ni nayi maku hanya a wurin chief..." ta faɗa da yar zolaya tana kallon su
Murmushi suka saki zahra tace"bakomai mommy, ay duk abunda kikeso zamu baki.." yar dariya tayi"zolayarku nakeyi..." dariya sukai su kansu sun san tafi karfin tukuici, ta dai faɗi ne don ayi raha...
Kwas kwas sautin takalmanta Ya ratsa kunnuwansu, kusan atare su Aneelerh suka dago tare da kallon inda sautin ke fitowa....❓
*Daga alkalamin Boss Bature mu haɗu next page on monday idan Allah yakaimu da rai da lafiya✍️*
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
Buy bestselling books online
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 30
by
Novels Elite Admin
August 11, 2024
Sponsored Link
Novels Elite English
Kwas! kwas !! sautin takalmanta Ya ratsa kunnuwansu, kusan atare su Aneelerh suka ɗago tare da kallon inda sautin ke fitowa...
Ƙura idanu sukayi suna kallon su, kafin Aneelerh tayi wani irin yunkuri ta miƙe jikin ta na 6ari, zuciyarta na dakan uku uku, gaba ɗaya tabi ta rikice gani take kamar a mafarki take kallon su!! Kokwanto ta farayi anya kuwa sune? Tajudeen da Angel? Ko dai idanunta ne suke nuna mata badai dai ba? Tayaya mutanan da suka 6ace almost 16years yau kwatsam ta gansu, da ransu da lafiyar su, kanta ne ya wani irin sara mata da sauri ta dafe goshin ta, ganin hakan yasa Zahra ta miƙe a matuƙar ruɗe take kallon Aneelerh...
Lokacin da unaisah ta ɗaura kwayar idanunta akan fuskar Aneelerh, Ras taji gabanta Ya faɗi, wani irin burki taci ta dakata da yin tafiyar, idanunta azare take kallon ta, wlh ko amafarki taga fuskar Aneelerh sai ta shaida ta balle kuma azahiri, La66anta na kerma ta furta"Aunty Aneelerh? Daddy! Auntyna ne? Ita ne nake gani azahiri ba mafarki ba? Daddy wallahi itace aunty Aneelerh ce...." kalamanta ne suka dira akan kunnan Aneelerh, baiwar Allah jiki na 6ari ta watso da gudu mayafin ta har yana ƙoƙarin zamewa, da gudu unaisah ta nufe ta, takalman kafarta suka kusa kayar da ita kasa, amma ahaka ta jure don bazata iya jira aunty Aneeleeh ta karaso gareta ba, zubewa Aneelerh tayi akan gwiwowinta tare da ware hannayenta biyu ta rungume unaisah, tayi hugging dinta tightly lokaci ɗaya suka fashe da matsanancin kukan farin ciki mai tsuma zuciya 😖
A hankali taj ya ƙaraso Ya tsaya daga bayansu, tare da goya hannayensa bisa kirjinsa.
A sukwane hajiya saratu da chief suka miƙe tsaye suna kallon su, fuskokin kowan nan su ɗauke da murmushi su kansu da suka sake haɗa wannan zumunci ba karamin dadi suka ji ba, farin cikin da suka gani akan fuskar Aneelerh da unaisah ba zai misaltu ba.
Yadda Aneelerh ta rungume unaisah, kamar zata mayar da ita cikin cikinta, a kalla sun shafe mintuna goma manne da juna, kafin Aneelerh ta raba jikin ta daga na Angel, a lokacin itama ta durƙusa kan gwiwowinta, Aneelerh ta sanya tafukan hannayenta biyu ta tallabo fuskar unaisah da su, itama unaisah ta tallabo fuskar Aneelerh da nata tafukan hannun, suka kurawa juna ido yayin da hawaye ke sintiri kan fuskokinsu, cikin shesshekar kuka Aneeleeh take fadin"Angel dina! Kece nake gani? Dan Allah ki fahimtar dani nagaza yarda da abun da idanuna suke gane min! Wayyo Allahana.." ta fada tana jan numfashi.
"inna lillahi Ya Allah Idan Mafarki nake kada ku tada ni, kubarni kawai inci gaba da yin shi, Ya ilahi Angel dina ce..Ina kika shiga? Kika bar auntynki da ciwon rashin ki? Angel wayyo Allah...duk tabi ta susuce
Cikin muryar kuka unaisah tace"Aunty Aneeleeh, ni ce Angel dinki, ƴarki, Aunty Aneeleehna, ba mafarki kike Yi ba, ni ce dagaske, Angel dinki abokiyar firarki, mai sanyaki nishadi..." ƙara rungumeta Aneeleerh tayi.
Gyaran murya taj yayi cikin karayar zuciya ya firta"Aneelerh!.." kamar jira take yayi magana, a zabure ta mike ta tsaya agabanshi idanunta jawur ta furta"taj! kasan irin haukan rashin ku da nayi? Me nayi maka dana tsantsanci haka daga gareka?..." kwalar rigarshi ta damƙa da hannayenta biyu ta jijjiga shi kamar zata rufe shi da bugu taci gaba da fadin"taj meyasa kayi min haka? Meyasa ka gudu da unaisah kuka barni da kewarku? Taj kasan irin kunci da radadin dana naji a lokacin dana farka naga babu ku"?
Kalamanta sun karya zuciyarshi baisan sa'adda hawaye suka wanke fuskar shi ba, Zahra dake kallon su tuni hawaye sun wanke fuskarta ga wani farin ciki da ya lullu6e ta na ganin Unaisah, Jikin chief owais yayi sanyi lakwas tsantsar tausayinsu ne ya kama shi, ba shi ba hatta Hajiya saratu sai da taji tausayinsu duk da bakomai ta sani ba dangane da rayuwar su ba.
"Taj Ina mijina? Ina uzair! nasan Yana atare ku? Ka faɗa min taj meyasa kuka gudu daga gida? Tsawon shekara da shekaru baku ta6a waiwayena ba? Laifin me nayi maku taj? Idan wani abu ne yasa kuka gudu meyasa baku sanar dani ba? Harga Allah bakuyi min adalci ba taj! dai dai da rana ɗaya baku ta6a nema na ba ko da awaya ne...." Daƙyar ta ƙare maganar, Lokaci ɗaya ta yanke jiki zata faɗi da sauri taj ya tarota ta faɗo kan kirjinsa.
Da sauri zahra ta karaso gabansu tana kuka, zuƙunnawa taj yayi a hankali ya kwantar da kanta bisa laps din sa, har lokacin Angel tana a durkushe kan gwiwowinta da karfi take furta"Aunty aneelerh ki tashi! Dan Allah ki tashi wayyo Allahna daddy ka ce mata ta tashi" duk tabi ta rude zahra ma kukan take tana ambaton sunanta, Hajiya saratu ta kasa furta komai, lamarin ne da ta6a zuciya..
robar ruwa mai sanyi chief ya dauko daga kan table, Ya nufo wurinsu Ya buɗe murfin tare da mika ma Taj, Hannunsa na kerma Ya kar6a Ya tarfa ruwan a tafin hannu Ya watsa mata kan fuskarta, nan take taja mumfashi tare da furzar da shi...
Cikin karyayyar murya ya furta"Anila! dan Allah ki saurareni, wallahi bada son ranmu muka gudu ba, mummunar ƙaddara ce ta afka mana wadda tayi silar barinmu gida..., na rasa komai nawa Aneeleeh..." ya faɗa yana kallon cikin idanunta, dakyar take kallon shi, wani irin azababben ciwon kaine Ya far mata, ita kadai tasan halin da take a ciki.
"Nasan zaki fahimce ni Aneeleerh, har abada kinsan bazan Iya gudunki hakanan ba tare da wani ƙwaƙƙwaran dalili ba, dukan mu babu wanda baiyi kewar rashinki ba, kuma ko bayan da muka gudu kina aranmu bamu manta dake ba....."
"Taj ina mijina...."! Gabansa ba karamin faduwa yayi ba, kallon chief yayi da sauri ya girgiza mashi kai alamar kada Ya faɗa mata, saboda a halin da take ciki muddin suka sanar da ita tsaf zata iya zaucewa.
"Aneelerh, bansan Ina uzair Yake ba! Idan ba zaki manta ba, ba atare muka bar gida ba, adaren ranar da abun ya faru kinzo har gida kin same ni kina kuka kika ce uzair bai dawo ba, har na kwantar maki da hankali, tun daga wannan lokacin ban ƙara sanya uzair a idona na, amma muna nan muna bincike akanshi, in sha Allah shima zamu gano shi.
zuciyarta ba karamar karaya tayi ba, tuni ta sake fashewa da wani sabon kukan.
Kafin wani ya sake magana a cikin su, wayar Hajiya saratu ta fara ringing, da sauri ta zaro wayar daga cikin handbag dinta, ta duba mai kiran ta, p.a din tace, picking call din tayi"Okey, Gani nan zuwa yanzu nan.." ta faɗa tare da katse kiran ta dago ta dubi chief.
"My son yakamata na tafi, naso in tsaya amma kirane na gaggawa, duk halin da ake ciki pls ka sanar da ni..." ta fada cikin saurin murya, kafin ta dubi su Zahra.
"Zahra, Ni zan wuce, in sha Allah idan na samu time zanzo asibitin in duba mara lafiyan..." tayi masu fatan Alkhairi, godiya suka dinga yi mata, Har bakin mota chief tare da zahra suka rakata, akan idonsu motar ta fice daga gidan.
Dawowa sukai wurinsu Taj dake a durkushe ƙasa.
"Taj baka fadamin meyasa kuka gudu ba..."? Cikin jin ƙunar rai ta jefa mashi tambayar.
Atakaice ya labarta mata abun da ya faru da su, tun farkon da suka fara yi ma Alhazawan nan leƙen asiri da kuma farmakin da suka kawo mashi atsakar dare harya gudu da Angel....."
sai dai bai sanar da ita wayar da uzair ya kira shi ba ya dai ce shi baisan meya faru da uzair ba, har yau suna neman shi ba su gan shi ba, hankalinta yayi mugun tashi jin wannan musifar data afka masu, hatta zahra tayi matuƙar firgita jikin ta sai tsuma yake abun ya bata tsoro...
"Shiyasa bamu neme ki ba, saboda rayuwarmu tana a cikin hatsari, idan har miyagun suka san muna raye ba za su kyale mu ba, don dole muka killace ce kanmu kafin Allah ya tona asirin su"
"Inna lillahi wa'inna ilaihirraji! taj wannan wani irin tashin hankaline! Ni dama saida raina ya bani ba hakanan kuka gudu ba, Allah Yasa basu kashe uzair ba, nama san mawuyacin abune uzair ya rayu watakil sun kashe min shi...." bai bari ta ƙare maganar ba, Ya fara lallashin ta dakyar Ya shawo kan ta....
Zafafan hawayene suka cigaba da wanke kuncin ta,
"Boss!" chief ne Ya kira sunan shi
"Na'am yalla6ai"
"Ina son magana daku, ban da unaisah"
A hankali Ya ɗago da Aneeleeh, da sauri zahra ta zuƙunna tare da tallabo ta don gaba ɗaya jikin ta ba kwari dakyar ta samu ta miƙe.
Unaisah dake kallon su ta shiga ruɗani tunda chief Yace Yana son ganin su ban da ita...
Ruƙo hannunta taj yayi, suka nufi sofas din wuri ya zaunar da ita
"Daddy meya faru"?
"Kada ki damu, magana ce mai mahimmanci zamuyi, Idan muka gama zamu sanar dake, cike da gamsuwa tace toh
"ɗazu Kin faɗa min kina jin yunwa, ga snacks nan da juice ki sha kafin mu gama magana" yatsun hannunta har kerma suke wurin daukar burger ta fara cin ta.
idanunta akan su Aneelerh dake tafiya suna nufar can nesa da ita, zuciyarta cike fal da farin ciki, kamar wadda akaiwa albishir da gidan Aljanna, bakinta yaki rufuwa sai faman tariyo fuskar aunty aneeleeh takeyi, burinta su gama maganar don ta tambayeta ina ƙanin ta da daddynta ya bata labari ta haifa mata....
Bayan kowan nan su ya zauna kan kujeru suka nutsu suna jiran jin me chief zai sanar da su
"Inaso ku faɗa masa abun da ya kawo ku neman ƴar sa"! Ya faɗa batare da ya ɗago ya kalli waninsu ba, aɗan ruɗe Taj Ya kalli su Aneeelerh.
Baiwar Allah tama rasa ta ina zata fara, saboda tasan ba lallai Ya amince masu ba.
"Aneelerh kinyi shiru! Faɗa min meyasa ku ka zo neman Angel? Tun jiya chief yayi min bayanin zuwan ku amma bansan cewa ku bane, nayi mamakin ganin ku! Tayaya har kuka gano inda mu ke!? Ya fada cike da son jin ƙarin bayani.
Cike da fargaba Aneeleeh ta fara zayyana masa abun da ya faru na bayyanar benazir, bata 6oye mashi komai.
tunkafin ta ƙarasa maganar yanayin fuskar taj ya canza zuwa tsantsar 6acin rai, kwata kwata baiji dadin bayyanar benazir ba, saboda tafi ta aransa baya buƙatarta arayuwar shi, wani irin ɗaci yaji aran shi, Aneeelerh ta fama mashi tsohon raunin dake a zuciyar shi.
ko sunan ta baison ji, aranshi ya arayyana da ranta da lafiyarta tsawon shekara da shekaru bata ta6a neman su ba? Idan har shi bata neme shi ba ay yakamata ko yarta ta nema baisan wata irin zuciya bace a kirjin benazir ya riga da yasan halinta domin kuwa ba zai ta6a manta irin rayuwar auran da sukai da ita ba, macace mara kunya batasan darajar aure ba, ta azabtar da shi da soyayyarta.
gaba ɗaya sun lura da yanayin shi, kamar baya atare da su, Aneeleerh duk tasha jinin jikin ta, dafa kafadarsa chief yayi a hankali ya kallesa idanunshi sun kaɗa jawu"dan Allah kada kace inyi hakuri, saboda bana jin zan iya yafewa benazir, hasalima ban yarda cewa dagaske ta damu da mu har haka ba, Allah kadai kasan manufar da take da ita akan mu, ba zan ta6a yarda da benazir ba, matar da ta tafi tabar yarta a kwamin wanka, taje can tana yawon biɗiɗin ta tsawon shekaru bata ta6a neman mu sai yanzu"? Hawayen dake taruwa a cikin idanunsa tuni sun wanke fuskarshi hakan ba karamin ɗaga hankalin zahra da Aneeerh yayi ba..
Shi kadai yasan ƙunar da zuciyar shi take yi mashi
Shiru chief yayi sam ya kasa furta magana,
Cikin karyayyar murya Aneelerh tace"dan Allah taj kayi hakuri mu manta da abun da ya wuce, Benazir tayi nadama, neman ku take ruwa ajallo don ta nemi yafiyarku, wallahi taj ta riga ta gane kuskurenta" tana magana tana marairaice mashi fuska don ya tausaya masu"ka dubi girman Allah ka kuma duba darajar yarinyar dake atsakaninku ko dan saboda ita yakamata ka sassauta mata, Allah ma muna yi mashi laifi ya yafe mana balle mu da muke ƴan adama, taj ita kanta bada son ranta ta gudu ba kamar yadda na faɗa maka asiri akayi mata, yakamata kayi nazari kada ka yanke hukunci cikin fushi, nasan Benazir bata kyauta maku ba, amma ka duba pls, tana fa sonku shiga akayi tsakaninku saboda babu yadda za'ay uwa ta haifi ɗan sunna tayi watsi da shi......"
babu alamun taj zai fahimci maganar ta, idanunsa sun kaɗa jawur bakomai yake tunano ba face lokacin da ta ɗauki cikin unaisah hauka ne kadai batayi ba saboda ta tsani ciki, har fadi take zai bata mata shape din jikin ta, bayan haka tasha yin yunƙurin zubda shi Allah bai nufa ba.
"Pls, koda bazaka yafe mata ba, dan Allah ka amince Unaisah ta gana da mahaifiyarta..." kafin ta ƙare maganar yace
"Aneelerh kin riga da kinsan ƙiyayyar da unaisah take ma benazir, tunkafin ta mallaki hankalin ta, unaisah bata buƙatar mamanta, Nima kuma bana bukatarta...." hankalinsu ba karamin tashi yayi ba, Ga samu ga rashi, kallon chief Aneelerh tayi ya kasa kunne yana sauraron su.
"Dan Allah ka taimaka mana ka sanya baki a maganar nan!...." ta fada hawaye na bin fuskarta.
Duk yadda taj yaso hana chief magana sai da ya sanya baki
"Taj, I won't come between you and your ex-wife, Unaisah ita ce damuwata! Bana so ta rasa gatan da uwa take ba ɗan ta! duk irin tsanar da tayi mata wlh tana bukatar soyayyar mahaifiyarta fiye da taka!" ya ɗan dakata da maganar yana kallon taj, wanda ya nutsu yana sauraron shi.
"kai kanka ba zaka so unaisah ta rasa albarkar mahaifiyarta ba, shin zaka so unaisah tabar duniya ba tare data gana da mahaifiyarta ba? Ya jefa mashi tambayar cikin tausasa harshe shiru taj yayi
"Zaka so ne ta mutu da bakin cikin mahaifiyarta? Taj Ka riga da kasan mahimmanci uwa a addinance, ko da kuwa ta banza ce, bana so mahaifiyar yarinyar nan ta mutu a sanadin rashin ganin yarta da batai ba, kuma bana so unaisah ta rasa soyayyar mahaifiyarta, ba zakai mata kwaɗayin ta samu ladar dake a cikin kyautatama iyaye ba? Ka gama da iyayen ka lafiya ita bakaso ta gama da nata iyayen lafiya ne"?
cikin kwantar da murya chief ya cigaba dayi mashi nasiha, su Aneelerh duk sun nutsu sun kasa kunne suna sauraron shi, mutumin Ya kara shiga ransu, yadda yake magana cikin hikma da ilmi ba karamin sace mashi zuciya yai ba.
Jikin shi yayi sanyi sosai, kalaman chief sun ratsa zuciyar shi, aranshi yana ji koda bazai yafewa Benazir ba, zai yi kokarin haɗa Unaisah da maman ta, Benazir taci albarkacin chief wlh da ko kallo bata ishe su ba. Koda kuwa zuciyarta zata buga ta mutu ne....."
Gyaɗa kai yayi cikin sanyin murya yace"Na amince, wallahi taci albarkacinku, bazan iya watsa maku ƙasa a ido ba, Ina matuƙar ganin ƙimarku da darajarku, kuma bana fata Allah Ya nuna min ranar da zan bijire ma bukatarku..." ya faɗa yana kallon chief da Aneelerh, har cikin ran su sunji dadin maganar shi.
Hanky chief Ya zaro daga pocket dinsa Ya miƙa ma taj don ya share hawayen shi, da sauri Ya kar6a yai masa godiya kafin ya share fuskarshi
"Yanzu za'a iya bamu aronta muje da ita asibitin"?
"Ban amince a fita da ita daga gidan nan ba, sai dai Idan mara lafiyar za'a kawo nan ta zauna"! Acewar chief, yarfa hannu Aneelerh tayi, tuni murnar da suke ta koma ciki, muryar ta kamar zata fashe da kuka tace"dan Allah ka taimaka mana! Ka dubi girman Allah ku bamu ita, mu kai ma mamanta, Benazir ba zata iya zuwa nan ba..." saukowa tayi daga kan kujerar ta zukunna kan gwiwowin ta, da sauri ta yace tashi ta zauna, jiki asanyaye ta koma ta zauna.
"Aneelerh kina ganin unaisah zata yarda idan taji cewa wurin mahaifiyarta zaku kaita? kin riga da kinsan irin tsanar da tayi mata, tun kafin ta mallaki hankalin ta...." dafe kai Aneelerh tayi, sam ta manta da wannan zancen ita dai burinta kawai Angel taga mamanta
"Ya zamuyi taj? Wallahi nasan mawuyacin abune Unaisah ta bamu hadin kai"
Taj yace"ko nayi rantsuwa ba zanyi kaffara ba, Unaisah ba zata amince da ita ba don ta yanzu..."
"Kana nufin ta san komai game da yadda mahaifiyarta ta gudu bayan ta haife ta?"
"Ta sani yalla6ai"!
"Ya salam, kunyi babban kuskure da kuka sanar da ita, saboda kun dasa mata ƙiyayyar mahaifiyarta, tun da kuruciyarta, kuma yaro yana da ruƙon abu a zuciya....."
Shiru taj yayi shi kanshi yasan yayi kuskuren sanar da Angel, duk da ba a hayyacinsa ya faɗa mata ba, a lokacin da take cikin azabtar da shi da rashin jinta, har ya taushe mata fuska da pillow, aranar ne ya sanar da ita, don ta tausaya mashi tasan cewa shi kadai ne gatan da take da shi......."
Shiru sukayi tsit na wani lokaci, Kowa da abunda Yake saƙawa aran shi
Unaisah dake zaune tana shan lemu sai kallon su take Yi, ta rasa me suke tattaunawa, tsawon lokacin nan basu gama ba, gashi ta ƙosa ta sake huggin din auntyn ta.
"Ko da zan baku unaisah! Zan gindaya maku sharudda, saboda a halin Yanzu bincike mukeyi kan case dinsu, Rayuwarsu tana a cikin hatsari, babu buƙatar kowa yasan suna araye, daga ita har taj din!" hankali atashe zahra da Aneelerh suka kalli fuskar chief da yayi maganar.
"Dalilin dayasa tun farko na kira ku gefe ɗaya, don in gargaɗe ku akan kada ku kuskura kuyi gangancin da wani zaisan suna araye!!...." babu wasa akan fuskarshi yayi maganar.
"Idan har kukai kuskuran da wani Ya sani, ku kuka da kanku! zaifi kuyi takatsantsan yadda mukai maganar anan to mu binne komai anan"!
ya faɗa tare da kwankwasa table din gabansa.
Zahra ba karamin tsorata tayi ba, Jikin ta har ya fara kerma, dama da biyu chief ya tsoratar da su don su dauki maganar serious kada su 6ata masu dokar aikin su.
Murya na rawa Aneelerh tace"in sha Allah ba zamu bari wani ya sani ba,..." la66an zahra na kerma tace"wallahi nima bazan yi kuskuran sanarma wani ba, nayi maku alkawari..." Aneelerh tace"zahra bata da matsala, zata rufa mana asiri, ba zata bari wani ya sani ba, amma ni damuwana tayaya zamuje da unaisah asibitin"?
"Unaisah ba zata bamu matsala ba, Zan ja mata kunne akan kada ta fadama kowa ina araye! Ita ma kuma kada ta bayyana kanta koda wani ya nuna ya santa! abun da yakamata shine zaku je da ita amatsayin yarinyar da kuka ce zaku kawo masu, kada abari kowa yasan itace yarta ta ainihi!"
gaba ɗaya sunyi amanna da maganar Taj,
"Itama unaisah za'a fada mata cewa zataje duba mara lafiyane wadda yarta ta 6ace mai kama da ita, ta hakane kadai zamu samu yardarta, inyaso daga baya idan suka shaƙu da juna ta yadda ba zata iya jurar rashinta ba, sai afaɗa mata gaskiya" sai da taj yakai Aya Aneelerh tace"amma anya ba za'a samu matsala ba? Benazir idan tana sambatu sunanka dana Angel take fadi saboda mun riga mun fada mata sunan yarta, bayan haka Alhaji ubaid yasan unaisah, itama tasan shi! Kana ganin idan ta ganshi bazata nuna ta sanshi ba? Ko ta tambayi meye alakarshi da mara lafiyar....."
Calmly chief yace"wannan ba matsala bane, idan har zamu bada unaisah dole asibitin ya kasance a karkashin kulawar jami'an mu, zamuyi magana da likitocin dake kula da mommyn nata, zamu sa ahana kowa shiga dakinta, daga ita Unaisah din sai grandma dinta, ko itama tasan ta ne"?
Girgiza kai tay yai"a'a hajiya layla bata san angel ba, bana tunanin ko a hoto ta ta6a sanin ta, saboda babu zumunci atsakanin ta da taj...."
Taj yace"abun zaizo mana da sauki saboda kaf dangin Benazir ba wanda yasan Angel sai kakanta, bayan haka bana tunanin sambatun da maman nata takeyi zai tona asirin wacece ita, duk da Angel tana da kaifin basira but zata ruɗe ne saboda tasan ba ita kadai bace mai suna angel after that koda ta furta sunan taj ba lallai tai tunanin ni take nufi ba"! ajiyar zuciya Aneeelerh da zahra suka sauke a lokaci ɗaya.
"Amma da zarar ta dawo hayyacin ta, Aneelerh ki sanar da ita cewa yarta ce, sannan kiyi kokarin jan kunnanta akan kada tace zata furta wata kalma da zaisa unaisah ta gane itace mahaifiyarta...." amsawa sukayi da toh
Chief ya ɗaura da cewa"Ko da zamu baku ita, ba yanzu ba, sai zuwa dare zansa akawo ta asibitin, She will be under the care of our officers because we won't be careless with her life..." cike da gamsuwa suka amsa mashi da toh, sunjima suna tattaunawa, a karshe taj shi Ya ce zai yi magana da unaisah dangane da zancen zuwanta asibitin bayan haka sun yanke shawarar canza mata suna duk dan kada a gane itace.
Godiya su Aneelerh suka dinga yiwa chief kamar zasuyi mashi sujjada, har saida taj yace su daina baison ana yi mashi godiya kafin suka dakata har cikin ransu sunji dadin hadin kan da suka samu a wurin shi........"
Unaisah kamar jira take su kammala maganar, tana ganin sun nufo wurin ta, jiki na 6ari ta miƙe ta nufesu, murmushin farin ciki suka saki, da sauri Aneeelerh ta ɗauketa kamar karamar yarinya ta rungumeta a jikin ta, zahra sai jin dadi take yau gata ga yarinyar data kwallafa rai akai.
Su uku suka zauna kan sofas din, taj da chief suna zaune can inda suka baro.
Aneelerh ta kasa janye idanunta daga kan Angel, tayi mamakin girman ta, ga wata madarar kyau da tayi komai nata ya canza mata, sai faman sakar ma juna murmushi suke yi.
"Aunty aneelerh, daddy Ya faɗa min kin haifa min baby boy, Yana Ina?
"Angel, ƙanin ki junaid Yana a school, bawan Allah, Kullum burinshi yaga Angel, Yana matukar sonki Angel, tun yana jariri nake nuna mashi hotunanki, Yasan komai dangane dake ganinki ne kadai bai ta6a yi ba...." marairaice fuska tay kamar zata fashe da kuka
"Ina son ganin shi..." da sauri zahra ta lalubo hoton junaid awayarta ta mika ma Unaisah, yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin karbar wayar, ta kura mashi ido tana kallon ɗan kyakkyawan yaron aunty aneenerh, wani irin farin cikine Ya bayyana akan fuskarta, hada videos dinsa ta kalla.
"Aunty Aneelerh, fuskarshi kamar anyi photo copy din fuskarki, dake yake kama, Wallahi harna ƙosa mu haɗu da ɗan ƙanina, In rungume shi a jikina in ji ɗumin shi, Ya Allah nagode maka da ka nuna min wannan ranar, ga ni ga aunty na, ga ɗan kanina da zan gani wayyo dadi...." zahara dake kallon ta ji take kamar ta rungumeta, Yarinyar tajima da sace zuciyarta, tun ranar da suka hadu awurin dinner din hateem ashe da rabon su sake haduwa matsayin yar uwar mijin auntynta......
"Angel ga zahra, itace ta ɗauko min hotonki awurin dinner, ɗiyar uncle dina ce..." sai lokacin Angel ta dubi zahra dakyau, nan take ta gane fuskarta, da sauri taje ta rungume zahra, fuskar kowan nan su da murmushi....
"Angel ina tayaki murnar ganin auntynki, Nima nayi murnar ganinki, wallah ba zan iya misalta farin cikin da nake a ciki ba, naji dadi dana zama silar haduwarku...." ta ƙare maganr tare da raba jikinta daga na Unaisah, share mata hawaye tayi da tafukan hannayenta"ki daina kuka kinji, Allah yakamata muyiwa godiya daya sake hadaku, naga ma kamar baki da lafiya, fuskarki ta kumbura, Jikinki da zafi..." cikin kulawa da nuna tausayawa tayi mata maganr
Cikin sanyin murya tace"lafiyana lou, babu abunda ke damuna, farin cikin ganin auntyna ne" ta fada tare da kallon Aneelerh dake kallon ta.
Wayar Aneeleerh ce ta fara ringing, ta ɗauko bag din data bari kasan sofa ta zaro wayar
"Tun bayan da chief ya kiraku wayarki take ta ringing, banaso na katse maku tattaunawarku shiyasa ban kawo maki ita ba..." murmushi aneelerh tayi aranta ta ayyana har yanzu tana nan da wayonta, ga hankali
Ko da ta duba screen din wayar missed calls ta gani sunkai ashirin, daga wurin mutun uku hajiya layla da dr shurem dana mami din su..
Unaisah zan amsa kira" amsa wa tay da toh, mikewa aneelerh tayi ta nufi gefe ɗaya, tabar zahra zaune tare da Unaisah kamar wasu kawaye haka suka fara fira
Hajiya layla ta fara danna wa kira, bayan sun gaisa hajiya layla tace"Aneelerh ya ake ciki? Naji shiru baki kirani ba, ko dai iyayen yarinyar basu bamu ita bane? Wallahi jiya ko baccin kirki Benazir batayi ba, tana ta sambatu tana ambaton sunan yarta .."
"Ki cigaba da kwantar mata da hankali, nayi magana da iyayen yarinyar sun bamu ita, amma sai zuwa anjima zata zo asibitin"
Muryar Hajiya layla da alamun farin ciki ta furta"Alhamdulillah!....wallahi naji dadi Aneenerh, dan Allah kuyi mana godiya wurin iyayanta..."
Murmushi Aneelerh tayi"in sha Allah zanyi masu" sallama sukai da juna, ta sauke ajiyar zuciya, idanunta akan su unaisah, wani irin sonta ne ke kara baibaye zuciyarta,
Layin mami ta kira, ko sallama Aneelerh bata kaiga yi ba, mami ta katse ta da cewe"Aneelerh sai yanzu zaki kirani? Baki ga missed call dina bane? Kunsa inata zullumi, na kasa tsaye na kasa zaune..."
"Allah sarki mami, Yanzu na dauko wayar, banga call din ki ba"
"Toh ya ake ciki ne"?
"Mami, mun ga yarinyar, dagaske ba unaisah bace, zahra tayi kuskuren fada mata sunan ta, ashe ita wannan sunanta Azeezaty, suna bala'en kama da unaisah, amma iyayen yarinyar sun bamu aron ta har zuwa time da benazir zataji sauƙi"
"Toh Aneelerh, har naji sanyi wlh, yanzu zakuje asibitin ne"?
"Mu zamu tafi, ita kuma yarinyar sai zuwa anjima da dare za'a kaita"
"Allah yakaimu lafiya" ameen mami, daga haka sukai sallama da juna, komawa tayi wurin su unaisah suka cigaba da yin firar yaushe rabo, chief tuni ya shige gidan saboda yana son ya fita office, zama taj yai a wurinsu suka dinga sanya juna nishadi, ana tuna rayuwar baya, har wuraren ƙarfe 9 na safe kafin su Aneelerh suka mike zasu tafi, Angel kamar tay masu kuka taso su shiga ciki suka ce a'a sai zuwa na gaba suna sauri ne, dakyar taj ya lallashe ta yace ta koma gida, zaije ya rakasu, tana ji tana gani ya tafi da su aneelerh, a motarshi yakaisu cikin estate din inda suka bar motarsu, sai da ya tabbatar sun tafi kafin ya dawo.
________________________________✍️
Fitowa dr shureim yayi daga bedroom dinsa, Ya kimtsa tsaf cikin shigar su ta larabawa, hannun sa ruke da wayarshi, har ya fara tafiya kiran Aneelerh ya katse mashi hanzarin shi, da sauri yai picking tare da kara wayar a kunnansa
"Assalamu alaikum Aneelerh, barka da safiya, fatan kun wayi gari lafiya"
On the other hand Aneelerh tace"lafiyalou Alhamdulillah, Ya shureim.."
"Tun ɗazu nake ta kiran layin ki don inji Ya ake ciki game da yarinyar an dace ko kuwa"?
"Yaya shureim, mu hadu asibitin zanyi maka bayanin komai" amsa mata yayi da toh, kafin sukai sallama, a tsanake Ya nufi falo, tunkafin Ya isa ya hango mutanan gidan a dining sun hallara sunayin breakfast,
"Shureim har ka kammala shiryawa"? alhaji ubaid ne yai masa maganar
"Eh daddy..." ya faɗa tare da gaishe da su, Alhaji musa yace"ba zakayi breakfast din bane"?
"Idan naje can zanyi..."
"Okey,
Hajiya sarah tace"in sha Allah idan na taso daga office zanbiyo asibitin.."
"Allah ya kawo ku lafiya..." satar kallon zeenatu yayi, hannunta ruke da cup tana shan tea, murmushi ta sakar mashi tare da kashe mashi ido ɗaya...lamarinta ya fara bashi tsoro yarinya kamar mai iskokai?
"Zeenatu ba zaki bini mu tafi ba"?
"Ina zamuje"?
"Asibiti wurin auntynki benazir.." maƙe mashi kafada tayi"bana jin dadi, bazan iya zuwa ba, ka tafi kawai..." da mamaki hajiya sarah take kallon ta
"Zeenatu! Kin kuwa saurari abun da yace maki dakyau? Asibitinne ke bazaki je ba? Dallah tashi ki bi shi ku tafi, idan kika zauna gidan me zaki yi ke kadai? Daddynki ma fita zaiyi..." bata kare maganar ba, Alhaji musa ya katse ta da cewa"ba ki ji tace bata da lafiya ba?
Rai a6ace hajiya sarah tace"amma ay lafiyarta qalou, ni banga wani alamun rashin lafiya atare da ita ba..."
Alhaji ubaid yace"shureim ka tafi kawai, Kada ku takura mata, tun da ba koshin lafiya gare ta ba, ni bana so ma taje asibitin taita kuka kamar jiya da mukai ta fama da ita...." jiki asanyaye dr shureim Ya miƙe idanunsa akan fuskar zeenatu, itama kallon nashi take Yi, ji take kamar ta tashi tabi shi sai dai ta kasa kamar ana ruke kafafunta, a hankali Ya juya yana tafiya kamar babu kuzari a jikin shi, bakomai yake tariyowa ba face kalamanta! Meyasa zeenatu ta canza daga jiya zuwa yau? Ya jefawa kansa tambayar da baida amsarta!!
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe chapter 31 by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
August 27, 2024
Takun Ƙarshe
Bayan komawar Unaisah cikin parlour, a dining room ta hango ƴan uwan ta, har sun fara yin breakfast sunyi neman ta har sun gaji ba su ganta ba, suna jin takun tafiyarta gaba ɗaya suka dago suna kallon ta.....
"Sister! Ina kika shiga muna ta neman ki"? Batool ce tayi mata maganar, bata tanka masu ba, sai faman sakin murmushi takeyi kamar wadda akayiwa albishir da gidan Allah, yau ranta fari fess, cike da zumudi taja kujera ta zauna tana kallon su ɗaya bayan ɗaya, tasan in har ta sanar da su Azeeza game da zuwan auntyn ta aneelerh ba karamin dadi zasu ji ba saboda tasha basu labarinta agidan kurkukun ƙaddara,
abunda bata sani ba tun da ta zauna suke ta kallon ta
"Aunty ummi Ina kwana.. " wani kallo ummi tabi ta da shi, har saida tasha jinin jikin ta
Kafin ummi ta furta kalma Sajeed Ya riga ta cewa"Sister baki da lafiya ne? ko kinyi kuka ne"? lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya canza! Kwata kwata ta manta da abun da ya faru daren jiya, saboda murnar zuwan Aunty Anila, maganar sajeed ce ta tuna mata, tuni murnar da take yi ta koma ciki.
"Sister kinyi shiru baki ce komai ba? Meke damunki"? Cike da tashin hankali batool tayi maganar, su Parveen duk sun kura mata ido suna kallonta, jemimah tace"le6enki ma ya kumbura kamar yankan tumatur"
"Unaisah! Lafiyarki kuwa"? Acewar ummi ta faɗa tana kare mata kallon ƙurulla
Adabarbace ta furta"am.. Umm.." sam ta kasa ƙarasa maganar, idanunta azazzare take kallon su.
gani take kamar sun san komai daya faru da ita adaren jiya, da sauri ta miƙe jikinta na kerma tace" aunty ummi babu komai, ba abunda ke damuna, lafiyana lou..." bata ƙare maganar ba, kamar mara gaskiya ta nufi hanyar fita daga dining room din zuciyarta cike fal da tashin hankali
Gaba daya sun lura da tashin hankalin dake akan fuskarta
Deeja na dariya tace"wallahi Allah kumatunta sun kumbura suntum kamar alkubus, wama ya sani ko bugun tsiya akai mata..." bata kare maganar ba, Haris ya toshe bakin ta..
Miƙewa ummi tayi sam hankalin ta bai kwanta da yanayin unaisah ba, miƙewa batool tayi da niyar tabi bayansu, da sauri ummi ta dakatar da ita"ki zauna ku karasa cin abincin, zanji da ita" jiki asanyaye ta amsa mata da toh..
Da sauri ummi ta nufi dakin su Unaisah, tana shiga tajiyo sautin kakarin amanta a toilet kamar zata fasa makoshin ta.
Knocking ƙofar toilet din tay"unaisah ina son magana dake"
Fitowa tayi fuskarta sharkaf da hawaye, hannun ta ruke da ɗan pant din ta.
"Meke damunki ne"? tana faman jan numfashi tace"bakomai aunty ummi..." katse ta ummi tayi"kada kiyi min karya, yanayinki ya riga ya nuna baki da koshin lafiya, kawai ki fadamin meke damunki! Idan ba haka ba hankalina ba zai kwanta ba..." cikin nuna damuwa tayi maganar, shiru tayi jim tana tunanin ko dai ta fada mata watakil ta taimaka mata....
Miƙa mata pant din hannunta tayi, waro ido ummi tayi"me zanyi da shi" matse shi tayi, tana faman noƙe kai tace"jiya da tsakar dare na tashi da matsanancin ciwon mara, kamar bazan rayu ba, bayan na shigo toilet na duba sai naga jini ne ya dawo min"
cike da jin tausayinta ummi ta ruko hannunta suka zauna gefen gadon.
"Sannu unaisah, wallahi daga gani kin ji jiki ba kaɗan ba, meyasa a daren baki neme ni ba? Ay da na taimaka maki, halan ko magani baki sha ba"?
"Ban shaba ba aunty ummi, saboda naji saukin ciwon, kuma lokacin dana farka da safe banga jinin ba ya dauke! Aunty ummi dama Yana haka"? ɗaga mata kai ummi tay alamar eh"kada hakan ya dameki, nima sometimes yana yi min haka yaje ya dawo, in har bai wuce kwanaki goma shabiyar ba, to still jinin ne, amma da zarar kinji ya dauke duf babu shi sai kiyi wankan tsarki ki cigaba da sallah" ajiyar zuciya unaisah ta sauke, sam tagaza fada mata abun da ya faru jiya.
"Me kike son nuna min a jikin pant din . " cike da jin kunyarta tace"wani abune da nake gani kamar kunu gayanan kyankyamin shi nake ji .."
kiris Ya rage ummi ta fashe da dariya ganin yadda ta kwa6e fuska tana gwale la66anta.
"Nuna min in gani .." buɗe mata pant din tayi.
Shiru ummi tayi jim alamar tana nazartar abunda ta gani, tabbas sperm ne amma meya kawo shi? Cos Bata tunanin unaisah ta fara feelings...rayawa tayi aranta watakil ba abun da take tunani ba ne
"Unaisah, dole fa sai kinyi takatsantsan, kamar yadda nayi maki bayani zan ƙara jan kunnanki, daga yanzu kada ki kuskura ki ƙara ba wani namiji damar da zai ta6a jikin ki, ko da ruƙe hannunki ne! In ba haka ba ke zakija ma kanki zunubi, saboda duk wasu hukunce hukunce na musulunci sun hauki, Idan kika aikata mai kyau za'a rubutaki, haka zalika idan kika aikata zunubi za'a rubuta maki. .."nan dai tayi mata takaitaccen bayanin dalilin dake kawo hakan dallah dallah yadda tasan zata fahimta, hankalin unaisah ba karamin tashi yayi ba.
"Kuma idan kika bari Namiji yana wasa dake yana tattabaki, you can get pregnant, a yadda kike ƙaramar nan har ranki zaki iya rasa wa...." ummi bata kare maganar ba Unaisah ta daura hannayenta biyu akai la66anta na kerma ta furta inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un...." da biyu ummi ta fadi hakan saboda taja mata kunne.
Tayi mamakin ganin Yadda jikinta ke kerma, da gudu ta fada toilet taja kofa ta datse.. " lamarin ya daurewa ummi kai, arude ta mike tana kwala mata kira"unaisah! Unaisah? Lafiyarki kuwa? Meya faru? ko dai maganar dana fada ce? To meye na damuwa"? Shiru bata amsa ba, bugun kofar ummi ta dinga yi kamar zata balle ta"ki bude min kofa, keda baki jira kin karasa jin me zance ba, meye na tada hankali kamar baki da gaskiya"? Ta faɗa tana kumshe dariya a bakinta saboda ta bata dariya.
"Unaisah, ki fito muyi magana, watakil baki fahimci me nake nufi ba, zan yi maki bayani..." cikin disasshiyar murya ta furta"aunty ummi ki tafi dan Allah, cikina ne Ya katsa, idan na gama zan same ki a daki muyi magana" ajiyar zuciya ta sauke"shikenan zan jiraki"
Sai da taji alamun ummi ta fita daga dakin, kafin ta fito fuskarta sharkaf da hawaye baiwar Allah, hankalinta yayi matuƙar tashi, ta raza da jin kalaman ummi, fargabanta kada ta samu ciki!
Wani irin ciwon kaine Ya farmata, ga wani bacci da ta fara ji mai hade da kasala, Pant din da ta bari kan floor ta ɗauko ta koma toilet din,
Wankan tsarki tayi tare da alwala, daga bisani ta fito sanye da towel, da wata irin kasala ta dauko wasu kayan tasa tare da hijab ta zura a jikin ta.
Bayan ta kammala sallah ta zauna kan darduma ta ɗaga hannayenta tana addu'a hawaye na sintiri kan kuncinta, ko da ta gama bata motsa daga kan dardumar ba.
Bakomai ne Ya faɗo mata aranta ba face Danish, ko ya ci abin ci? taga bata ganshi a dining ba, har cikin ranta ta damu da shi, bata son yana ke6e kan shi a ɗaki, batasan meke damunshi ba...
"Sister dina!" muryar batool ce ta katse zancen zucinta, da sauri ta mike tare da juyawa ta kalle ta.., sam babu walwala atare da ita, duk ta damu da yar uwartata
"Dan Allah ki fadamin meke damunki" ƙaƙaro murmushi tayi akan fuskarta
"Calm down your mind! Ni Ba abunda ke damuna, lafiyana lou, ciwon ciki nayi jira da daddare naci wahala sister, amma yanzu da sauki jikin nawa..." huggin dinta Batool tayi sai taji wani sanyi ya ratsa zuciyarta.
"Ni kadai na kwana jiya adaki"
tausayinta ne Ya kara kama Batool
"Da na sani jiya na tayaki kwana, amma kodan saboda ke zan dawo kwana dakin nan"
Murmushi unaisah tayi"kada ki damu, ay naji sauki ma"
Kallon dakin Batool tayi"duk yayi datti bari na taimaka maki"
"Nagode sister," ta fada tare da zama kan mirror chair tana jiran batool ta kammala gyaran.
"Sister an kaiwa danish abinci a dakin sa"?
"Eh, Haris Ya kai ma shi, ni bansan meke damun shi ba, kema kin lura da yanayin shi naƙin shiga cikin mu"? Ta faɗa a yayin da takai hannu tajanyo zanin gadon da yayi uban squeezing kamar an ƙwatoshi daga bakin kura.
"Batool na lura, abun yana damu na, nayi masa faɗa yaƙi dainawa to ya zanyi da shi? ta faɗa da damuwa akan fuskarta"ko da yake halinsa ne ko a prison bai fiye shiga cikin mu ba, yafi son yaganshi kwance kan gado" daurewa kawai takeyi sam bata son batool ta fahimci halin da take a ciki.
Adai dai lokacin Batool ta fara kakka6e zanin gadon, Kwatsam ba zato ba tsammani unaisah ta hango zoben da ya faɗo ta cikin bedsheet din..saukowa tayi daga kan kujerar, ta nufi inda Yake ta zuƙunna tana kallon shi, zoben azurfa ne sai kyalli yake a hankali tasa yatsanta daya ta ɗago da zoben, hankalin batool kwata kwata baya akanta, sai surutu takeyi mata....
Ƙura ido tayi sosai akan zoben, was wasi ta fara yi kamar wanda prime minister ya ba danish❗
Anya kuwa shi ne?❓ kokwanto ta shiga yi, tayaya akai zoben ya shigo dakin su idan na shi ne ...? yunkurawa tayi a sukwane ta mike, batare da sanin batool ba, ta fuce daga dakin.
"Sister jiya kafin mu kwanta aunty ummi ta kunna min kallo a laptop din ta...." dakatawa tayi da yin maganar ganin babu kowa adakin.
"Unaisah! Unaisah! "ranta ne Ya bata kodai ta shiga toilet, hakan yasa taci gaba da gyara mata dakin......."
________________________________✍️
Prisoners shield💔
Fitowa yai daga toilet, jikinshi a sanye da bathrobe, baijima da tashi daga bacci ba Ya shiga wanka, yayi wani fresh dashi, sumar kanshi ta lullu6e bayan shi.
Walking slowly Ya nufi dressing mirror, zuciyarshi cike fal da tunanin Angel dinsa, yayi maraicin ganin ta idanunsa sun kwaɗaita da son ganin ta, tun safe baici komai ba, abincin da haris ya kawo mashi yana nan ajiye kan table ko buɗesa baiyi ba.
Har ya yunkura zai zauna kan mirror chair, sautin knocking din kofar Ya dakatar da shi . ....
Cike da zumudi Ya nufi kofar, fatan shi Allah Yasa Angel dinsa ce,
Buɗe ƙofar yayi a hankali, tun daga kasa Ya fara kallon ta, ko takalma babu a kafarta kamar an korota,
Gown din jikinta tayi mashi kyau sauke idanunsa yayi akan fuskarta har saida gaban shi Ya faɗi, ganin yadda ta kumbura gashi babu fara'a ko kaɗan ta haɗe rai, ido cikin ido suke kallon juna har na tsawon mintuna biyar kafin sanyayyar muryarshi ta katse mata shirun ta
"Mu shiga ciki" yayi mamakin ganin batayi mashi musu ba, ta nufi ciki da sauri yabi bayanta, a tsakiyar dakin suka dakata
"Meke damunki? Idanunki sun kumbura kamar kinyi kuka, faɗamin waya ta6a min ke"
Lumshe idanunta tayi kafin ta buɗe su a hankali.
Takawa tayi har zuwa gabanshi ta tsaya suka fuskanci juna
"My man, Ina zoben da prime minister Ya baka"? Cike da fargaba Ta furta maganar ita kanta tsoron amsar da zai bata take ji saboda bata son zargin da take yi ya tabbata.
da sauri Danish Ya ɗago da yatsun hannun shi Ya kallesu kwata kwata babu zobe
aruɗe ya furta"ban gan shi ba, bansan a ina ya faɗi ba, bari na duba toilet watakil na manta shi a ciki"
Juyawa yayi da sauri ya nufi toilet ya shige ciki.
tana atsaye cikin jin kunar rai, take kallon shi har ya 6ace ma ganinta, wani irin kululun bakin ciki ne Ya tokare makoshinta, hankalin ta yayi mugun tashi, zuciyarta ta karaya jikinta yayi sanyi, ta gaza yarda da abunda take zargi!!
dagaske danish ne ya aikata mata rashin imanin nan? babu tausayi babu imani Yana ganin tana fama da azabar radadin ciwo ahaka Yayi abun da yakeso yayi? Tunawa tayi da lokacin daya wurgar da ita kan gado, Ya sa hannu Ya hambareta har kanta Ya daki pillow, abun ya tsaya mata aranta.
Fitowa yayi daga toilet din, ya ɗago suka hada ido, wani irin faduwa gaban shi yayi ganin kallon tuhuman da take jefa mashi, tuni yasha jinin jikin shi
"My man, kaga zoben"? La66anta na kerma ta furta maganar
Girgiza mata kai yayi"ban gan shi ba, bansan a ina Ya faɗi ba..."
Murmushin takaici ta sakar mashi, kafin tace"Ni na ganshi"! da mamaki Ya kalle ta, hannu ta zura cikin aljihun gown din, ta zaro zoben ta miƙa mashi
"A ina kika gan shi"? ya faɗa tare da matsowa kusa da ita, ya miƙa hannu zai karba, daddagewa tayi da iya karfinta na karshe ta ware yatsu biyar ta wanka mashi zazzafan mari kan kun cin shi, tashin hankalin da ba asaka mashi rana! lamarin ya gigita shi da sauri ya dafe kun shi, jikinsa na 6ari ya ɗago amatuƙar ruɗe ya kalli fuskarta...la66ansa na kerma ya furta"my.. Angel? Kina cikin hayyacin ki kuwa? Ni kika mara"?
Harara ta watsa mashi da kakkausar murya ta furta"idan akwai abun da yafi mari zanyi maka shi! Mugu Azzalumi, fasiki ɗan iska... " waro idanunshi waje yayi tamkar kwayar zata fado ƙasa He was completely confused
"Danish me nayi maka dana cancanci haka daga gareka? Danish kaida kanka? Sai yanzu na gane dalilin dayasa ka tsareni jiya akan in faɗa maka idan na fara period, dama abunda kake jira kenan, Ina fata yanzu hankalin ka Ya kwanta, tunda ka samu abunda kakeso ...." rushewa tayi da matsanancin kuka mai cin rai, bawan Allah Yama rasa bakin magana, har yanzu baisan kan me take magana ba, ko kaɗan baiji zafin marin da tayi mashi na, babban tashin hankalin shi miya faru da ita a daren jiya❓
"Kiyi min bayanin meya faru dake"? Tsawa ta daka mashi kamar zata rufe shi da bugu tace"kana nufin kamanta abunda kayi min? Saboda ba damuwarka bace in rayu ko in mutu ko"? Ta fada tana cije la66anta da hawaye suka jiƙa su.
"Idan ka manta bari na tuna maka, jiya ka shiga dakinmu da daddare...." zayyana mashi komai tayi tunkafin ta karasa gabansa yayi wani irin mugun bugu na tashin hankali, miƙa mashi zoben tayi"a jikin zanin gadonmu na tsince shi, ina fata yanzu ka tuna komai....."
Runtse idanunshi yayi, wani irin ƙunci yaji aran shi, jikin shi ya hau yin kakarwa kamar wanda Sanyi ya kama . shirun da yayi ne ya ƙara tabbatar mata da zarginta akanshi.....amsar shi kawai take jira.. Duk da bata bukatar wannan
"Bani bane! Bazan Iya cutar dake ba Angel! bansan ya akai zobe na Yaje dakin ku ba..."
wasu zafafan hawayene suka wanke fuskarshi, wlh yafi ta jin radadin abunda akai mata, yaji zafi kamar ya fasa ihu! Wai Angel dinsa ce wani yayi ma wannan aika aikar?
"Danish baka ta6a min karya ba sai yau, baka da wata hujja da zaka kare kanka awurina, zoben ka ba ƙafa gare shi ba, balle kace shi yakai kan shi dakina...Danish meyasa kayi min haka? Ko amafarki ban ta6a tunanin zakai min haka ba? A zato na kai garkuwane agareni mai bani kariya a duk lokacin da wani yayi yunkurin cutar dani sai gashi kai da kanka ka cutar dani, saboda idonka Ya makance burinka kawai ka samu abunda kake so ko"?
Dafe kanshi yayi da hannu ɗaya saboda wani irin sara masa da yai, ƙafafunsa sungaza daukarsa baisan sa'adda Ya zube kan gwiwowinsa ba.
Ya rurruƙe ƙafafunta da hannayen shi, hawaye na fita ya furta"Unaish ki yarda dani! Ban ta6a maki karya ba, bani bane! Bansan wanene yayi maki aika aikar nan ba! Garkuwarki bazai ta6a cutar dake ba, ni aikina shine baki kariya kamar yadda kika faɗa" ya faɗa yana fitar da huci mai zafin gaske
"ki tausayama rayuwata, kada ki yanke min hukunci akan laifin da bani na aikata ba! nayi maki alkawarin zan gano koma wanene yayi miki hakan ..." cikin rauni na murya ya ƙare maganar, yana kallon cikin idanunta.
cike da jin tsanar shi ta sa kafa ta buge hannayenshi daya ruke kafarta da su, ta soma ja da baya tana fadin"wallahi bana son ganinka! Ka fita araina Danish! Na tsaneka! Ka 6ata komai, kullum burina in faranta maka rai ashe kai ba haka bane awurinka, abin da baka sani ba ni nema nake na nema mana hanyar da zamu mallaki juna na har iya tsawon rayuwarmu, sai dai kash gajen hakurin ka da son zuciyarka sun ja maka
wurga mashi zoben tayi kan kirjin shi, da gudu ta juya ta fuce daga dakin.
Jiki amace ya kwanta kan floor, hawaye suka cigaba da sintiri kan kuncinshi, ga wani azababben ciwon kai da yake ji, tuni zazza6i Ya lullu6e jikin shi, ɗaukar zoben yayi a hannunshi Ya kura mashi ido yana kallon shi, ya rasa ya akai zoben yaje dakin su?wa ya kai shi? Wanene Ya cutar mashi da Angel dinsa?
sambatu ya fara yi"bani bane! Bazan iya cutar dake ba! Ni garkuwa ne agareki mai baki kariya, kada ki juya min baya, bana jin zan iya rayuwa batare dake ba, Angel kada ki fushi dani bani bane❗❗❗
Gaba ɗaya kalamansa acikin kunnanta, tana a durkushe bakin kofar dakinsa tana kuka kamar ranta zai fita, ganin lamarin take kamar a mafarki! wai Danish dinta ne yayi mata haka? Wlh ya karya mata zuciya! Ya kunsa mata kiyayyarshi, duk irin burin da taci na son ganin sun rayu a karkashin inuwa ɗaya ya ruguza komai....
Jin motsin mutun yasa tayi saurin share hawayen ta, jiki ba kwari ta miƙe daddynta ta hango yana shigowa, da alama Ita Yake nema...
Sai da ta fara daidaita nutsuwarta kafin ta sauko down ta nufe shi, sam baiji takun tafiyarta ba, sai dai Yaji ta faɗa kan bayan shi ta rungumeshi, bata san sa'adda ta sake fashewa da wani kukan ba, duk yadda taso ta shanye shi takasa har saida Taj yaji, gaba daya yabi ya rikice, kafin yayi yunkurin ruko ta da gudu tabar jikin shi, ta nufi dakinsu ta shiga, a lokacin Batool ta jima da fita, kan gado ta haye ta kifa kanta jikin pillow ta cigaba da kuka kamar ranta zai fita.
da gudu Taj Ya faɗo dakin, Ya hau har saman gadon, jikin shi har kerma yakeyi tsabar rudu da tashin hankali, janyota yayi da karfi ya rungumeta sosai a kirjin shi, muryar shi na rawa ya furta
"Unaisah! my Angel! Meya faru? Waya ta6a mun ke? baki da lafiya ne?
fuskarta tayi sharkaf da hawaye, hatta temperature din jikinta ya dauki zafi rau.
"My Angel meke damunki? Dan Allah kiyi min bayani? Ko baki da lafiyane?" sai da tayi kukan mai isarta kafin ta raba jikinta daga nashi ta sauko daga kan gadon, ta nufi toilet ta shige, jim kaɗan ta fito da alamun ruwa akan fuskarta...tsayawa tayi nesa da shi tana faman sauke ajiyar zuciya.
"Zonan Unaisah" Ya kirata fuskarshi babu walwala, kamar babu laka a jikin ta ta karasa tare da zukunnawa ta zauna kasan gadon, saukowa yayi ya zauna suka fuskanci juna
Ya ruko hannayenta a cikin nashi"fada min meke damunki? Meyasa kike kuka?
Shiru tayi jimm har cikin ranta bata jin zata iya tona mashi asiri, koda zuciyarta zata buga saboda bakin cikinsa, ta ƙwammace tabar abun aranta.
"daddy dan Allah kada ka tambayeni meke damuna, ka tayani da addu'a, in sha Allah zanji sauƙi.."
ta faɗa tare kwantar da kanta saman kafadarshi, ɗaura hannun shi yayi akan bayanta yana dan shafa shi cikin sigar lallashi yace"kiyi hakuri duk da bansan meke damunki ba, tun da kin nuna bakison in tambayeki dole in hakura, amma dan Allah kada ki sanya damuwa aranki! Ki kai kukan ki wurin Allah, Nima zan tayaki da addu'a in sha Allah.." lumshe idanunta tayi har yanzu bata daina jin kukan ba...
"Daddy, Inaso nayi nesa da gidan nan, na wani lokaci..." tun da yaji wannan maganar Ya fahimci akwai wanda Ya 6ata mata rai, a sannu zai gano koma wanene.
dagowa tayi a hankali suka kalli juna, idanunta sun ƙanƙance sun kaɗa jawur saboda kukan da ta sha..
"Daddy, Ka kaini part dinka, in zauna gurin Aunty danejo, ko kuma ka kaini wurin aunty Aneelerh dan Allah" marairaice mashi fuska tayi kamar zata fashe da kuka, kallonta kawai yakeyi gwanin bantausayi, arayuwarshi yatsani duk wani abu da zai ta6a lafiyar yarsa, bai son damuwarta.
"Daddy kayi shiru bakace komai ba"?
Numfasawa yayi kafin Ya furta"magana nakeso nayi dake, shiyasa na shigo gidan nan, sai kuma na taras da abunda Ya 6ata min raina..."
"Ka yi hakuri daddy, na daina kukan ay, ba zan kara sanya damuwa araina ba..." ta faɗa tare da ƙaƙaro murmushi akan fuskarta.
Kwantar da ita ya kuma yi ajikin shi don ta samu relief din abunda ke damun ta..
Calmly ya fara zayyana mata maganar da suka tattauna da su chief
"Ita mara lafiyan yar uwarsa ce, kuma kawar auntynki Aneelerh, tana a kwance gadon asibiti kwata kwata bata acikin hayyacinta tun lokacin data rasa yarta da mijin ta, likita yace idan har ba asamo yarinyar da zata iya acting kamar yartaba, to zata rasa ranta ne..." ɗagowa Unaisah tayi a hankali ta kalle shi da alama taji tausayin matar.
"Muna so kije a matsayinta Unaisah, nasan zaki Iya!"
"Daddy na amince muje asibitin, dama najima ina neman hanyar da zan kyautatama chief, na ji dadi data kasance yar uwar shi, Allah yasa in zama silar samun warakarta .." murmushi taj yayi
"Ameen, amma akwai abunda nakeso in ja maki kunne akai! Idan har muka kaiki asibitin kada ki kuskura ki faɗa ma wani ina raye! Ko ki bayyana wacece ke! Saboda har yanzu rayuwarmu tana acikin hatsari akwai masu bibiyarmu unaisah! Waɗanda suka kashe uzair zasu iya kashe ni idan sukaji ina raye!" cikin matsananciyar damuwa yayi mata maganar donta dauki abun serious...girgiza kai tayi"daddy bazan bari kowa ya sani ba, saboda bana so na rasa ka"
"Koda wani ya nuna ya sanki ki ce bake bace, kinji"? Ɗaga mashi kai tayi...
"Ko kinsan mutun kika ganshi kada ki tanka mashi ko ki nuna kin sanshi, tun da haryanzu bamu san wanene ya sadaukar dake ba!"
Gefen fuskarta yashafa da hannun shi, ki fara shiri zuwa anjima da daddare zamu tafi" ta amsa mashi da toh, jan ta da fira ya farayi duk don ya faranta mata rai ko ta manta damuwar da take a ciki.......
______________________________✍️
wuraren ƙarfe biyar, A jere motocin su Alhaji musa suka kunno kai cikin asibitin, A parking space suka dakata, da sauri body guard din dake driving din sa ya fito ya bude mashi mota, gently ya fito, ya ɗauki wankan shadda mai ɗaukar ido, fuskarsa na sanye da mask, Iya idanunsa ne kadai zaka Iya gani, fitowa Alhaji ubaid Yayi daga motar, a tare suka nufi ciki, wani irin farin jini ne da shi duk inda ya gifta satar kallon shi ake, daga nurses har drs din kai harma da visitors.
Duk da ya 6oye fuskarsa hakan bai hana wasu gane shi ba, cikin girmamawa likitoci ke gaishe da shi wasu kamar zasu durkusa ƙasa, cikin isa Yake ɗaga masu hannu batare daya furta magana ba....
Kafin su karasa ga medical room din, suka hango dr shureim tare da Aneelerh da zahra atsaye suna tattaunawa....
"Shureim"! Alhaji ubaid ne Ya kira sunan shi, kusan atare zahra da Aneelerh suka dago tare da kallon su...Rass Aneeleeh taji gabanta ya faɗi ba ita ba hatta zahra saida taji wannan yanayin datayi tozali da Alhaji musa, Yayi matukar jan hankulansu...
Ƙura mashi ido Anila tayi, a lokacin dr shureim Ya karasa wurin su, kamar taso ta gane wanene, sai ta ga kamar uncle din benazir, bazata ta6a mantawa da ɗan tahalikin nan ba, saboda kyautatawar da yayi masu tun da kuruciyarsu, kafin daga baya lokacin daya taka matsayi mai girma gaba ɗaya suka daina jin duriyarshi.
"Aunty Aneelerh wanene wannan"?
"Kamar uncle din benazir, banga fuskar dakyau ba amma inaji araina shi ne. ." bata ƙare maganar ba, su Alhaji ubaid suka karaso wurinsu, atare suka haɗa baki wurin gaishe da su
Alhaji ubaid ne kadai Ya amsa masu, da fara'a Yace"Aneelerh sannunku da kokari, Ya mai jikin"? Ita yake yi ma magana amma hankalin ta na akan Alhaji musa ya wani kau da ido kamar bai gan su ba.
"Alhamdulillah daddy, Jikin nata da sauki ba kamar jiya ba"
"Aneelerh ga Uncle musa ku gaisa ko baki gane shi ba..." dr shureim ne ya faɗa
Murmushin yake ta saki"ina wuni..." ƙasa ƙasa da murya ya furta"lafiya..." zahra na gaishe shi ko kallo bata ishe shi ba, Ya wuce Ya nufi dakin Alhaji ubaid yabi bayan shi.
jinjina kai zahra tayi aranta ta ayyana wannan wani irin mutunne? daga gani Yana da girman kai da izza.
"Shureim ko dai Ya manta dani ne? Naga kamar bai gane ni ba, duk sai naji ba dadi..."
Shiru shureim yayi har cikin ranshi baiji dadin halin ko'in kulan da alhaji musa Ya nuna ma Aneelerh ba bayan ya santa farin sani...
Murmushi ya ɗanyi kafin Yace"bana tunanin ya ganeki"
Ajiyar zuciya taɗan sauke kafin suka cigaba da magana game da yarinyar da suke jiran zuwanta anjima...
Lokacin da su Alhaji musa suka shiga dakin, Hajiya layla tana azaune kan prayer mat, hannunta ruƙe da cazbaha, kamshin turaren Alhaji musa ne Ya fara dakar hancinta kafin sallamarsu ta ja hankalin ta ga duban su, kamar taga wani mugun abu haka ta zabura ta mike tana kallon shi cike da mamakin ganin shi, saboda bata tsammanci zaizo ba tun da bai damu da benazir ba....
Tunda ya shigo idonshi na akan Benazir wadda ke kwance ta lumshe idanunta sai sambatu takeyi ƙasa ƙasa, kai tsaye ya nufi gaban gadon Ya zauna kan chair din dake fuskantarta
"Sannu daughter, Ya jikin naki"? Ya faɗa tare dakai hannu Ya shafa goshin ta, a firgice ta bude ido tana kallon shi, la66anta na kerma ta furta"Uncle! Daddy! ina babyna? Ina Angel dina, dan Allah ku nemo min taj ya kawo min babyna"
Lumshe ido Alhaji musa yai kafin a hankali Ya furta"calm down your mind, zansa a nemo maki ita, but ki fara kwantar da hankalin ki" rurruke hannunshi tayi acikin nata"dan Allah ku kawo min ƴata da mijina, uncle ku taimaka min kada na mutu ban gansu ba...."
tun shigowar shi bai dago Ya kalli hajiya layla ba, kamar babu ita adakin, wato yafi karfin yayi mata magana.
Ita ko tayi tsaye tana kallon ikon Allah, sam batayi farin cikin zuwan shi ba, gani take kamar ba alkhairi ne Ya kawo shi ba...
Gyaran murya Alhaji ubaid yayi mata
"Layla ya jikin nata"?
"Da sauki, mun samu taci abinci har wanka na taimaka mata tayi"
"Ya ake ciki game da yarinyar da Aneelerh zata kawo"?
"Sai zuwa dare zata zo asibitin"
"Allah Ya kawota lafiya, amma iyayenta ba su nemi komai ba"?
"Sai dai sunzo zamuji"
ajiyar zuciya yadan sauke
"Ba kiga musa ba ne? Naga baku gaisa ba" ya fada tare da nuna shi da hannu...
Harara ta watsa mashi kafin tace"ay shi yakamata ya fara yi min magana bani ba, sai kace dai Nina tursasa mashi yazo asibitin"?
gaba daya maganganun da suke tattaunawa akan kunnansa ko ajikinsa.
Sun ɗan jima kafin ya miƙe Alhaji ubaid Yabi bayansa suka fito daga dakin
Sai da suka fara zuwa office din likitan dake kula da ita don jin karin bayani dangane da lafiyarta, kafin suka fuce daga asibitin.
_________________________________✍️
Wunin ranar Danish bai leƙo ko kofar dakin sa ba, babu wanda Yasan halin da yake a ciki, kamar yadda ita ma ta killace kanta adaki, wuni tayi kudundune cikin bargo lokacin sallah kaɗai ke tada ta, tuni zazza6i ya lullu6eta jikin ta har kerma yakeyi kamar zatai hauka saboda azabar raɗaɗin da zuciyarta keyi mata, tayi kukan har ta gaji ta gode ma Allah, danish ya dasa mata tsanar shi a zuciyarta, ko sunan shi bata son ambato, hauka tadinga tana bubbuga mattress da hannayenta kamar yar dambe duk ta hargitse dakin a karshe ta fashe da kuka tana fadin"ka karya min zuciya my man, na tsane ka! Bana son ka! Bana son ganin ka! Ban ta6a tsammanin zaka iya cutar da rayuwata ba! Meyasa kayi min haka? ..." tajima tana haukanta ita kadai kamar zata zauce.
Wuraren ƙarfe takwas na dare, taj ya kirata awaya yace ta shirya ta same su a parking spot, jiki na rawa na shiga toilet, dama a kagare take data bar gidan kodan ta nisanta da shi, watakil ta samu relief din radadin da heart dinta keyi mata.
Bayan ta fito shaf shaf ta shirya cikin abaya, ta dauko kaya kala uku ta cusa a backpack dinta, ta goya jakar abayanta, ta zura takalmanta kafin ta dauki wayarta, babu wanda Yasan da zancen tafiyarta, harta fuce daga gidan.....
Cikin sauri take tafiya kamar zatayi tuntu6e, a parking space ta hango daddynta tsaye, ya sanya face mask a fuskarshi
Kallo ɗaya yayi mata ya fahimci har yanzu akwai sauran damuwa atattare da ita
Baisan ya zaiyi da ita ba, taki fada masa damuwarta, buɗe mata murfin motar yayi, wani sanyayyan kamshin turarene Ya daki hancinta, nan take ta gane kamshin wanene da sauri ta dago ta kalli daddyn nata
Murmushi ya sakar mata kafin yace"ki shiga mana"
"Wanene a ciki"? Ta jafe mashi tambayar
"Chief ne, tare da shi zamu tafi" jim ta ɗanyi kafin ta kutsa kai ciki, har saida gabanta ya dan fadi lokacin da ta sauke idonta a kanshi, yana daga zaune ya ɗauki wankan shadda blue sky tayi bala'en yi mashi kyau, laptop dinsa ce akan laps dinsa, ya dan lumshe idanunshi....
Bata san ya akai ta tsinci kanta da jin wani irin sanyi acikin zuciyarta.
Sai da ta zauna gefen shi kafin ta samu kwarin gwiwar yi mashi sallama tare da gaishe da shi...
Calmly ya amsa mata...
Nutsuwa tayi idon akan glass din motar da bai karasa rufewa ba, tana iya hangen filin gidan....
"Zamu Iya tafiya" chief ne Ya faɗa, security din dake zaune a driver seat Ya tada motar, A hankali Ya fara driving dinsu, motarsu big guy tana abiye da bayansu su biyu aciki tare da daddynta, sai motar jami'ansu dake abiye da su....
Lokacin da motocin suka haura kan titi, ajiyar zuciya ta sauke tare da kwantar da kanta, ta lumshe idanunta, bakomai take tariyowa ba face abunda Ya faru tsakanin ta da danish, tayi fatan ace mafarkine ba gaske ba..........bata san sa'adda hawaye suka gangaro takan kuncin ta ba, kwata kwata ta manta da chief acikin motar,
Ranta ne ya bata ana kallonta, a hankali ta buɗe idanunta waɗanda suka kaɗa jawur, karaf idanunsu suka shiga cikin na juna.....
Daga ita har shi sun kasa sarrafa kansu, wani irin kallo suke bin juna da shi mai wuyar fassaruwa
Ƙamshin turarenshi ba karamin kashe mata jiki yayi ba..."
Tsananin tausayinta ne Ya kama shi, har yau yana mai mamakin kananun shekarunta da kuma irin wahalhalun rayuwar da ta fuskanta, shi tunda yataso rayuwarsa baisan menene wahala ko rashi ba.
"I don't want to see your tears..."
*✊DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE✍️*
*Mu haɗu Jibi, Idan Allah yakaimu da rai da lafiya, Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe chapter 32 by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
August 28, 2024
Sponsored Link
Takun Ƙarshe
lumshe ido tayi ya nutsu yana kallon eye lashes dinta da suka jiƙe da ruwan hawaye ita kaɗai ta san me take ji, zaro hanky yai daga pocket dinsa a hankali ya soma share mata tears ɗinta, jin saukar hannunsa akan fuskarta yasa ta yi saurin buɗe idanunta ƙiris ya rage karan hancinsu ya gogi na juna, hatta numfashin su kokawar haɗewa yake.
Kasancewar chief na bala'en kama da Danish sai ta dinga ganin kamar shi ne a tare da ita, shima haka yake nuna damuwa akanta ya bata kulawa amma sai gashi rana ɗaya ya karya mata zuciya, duk irin burin da taci akan shi na son ganin sun mallaki juna.
Tuna wannan yasa ta fashe da kuka duk yadda taso ta haɗiye kukan ta kasa, da sauri chief ya kwanto da ita kan kirjin shi, hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba, hatta agent din dake driving ɗinsu saida yaji sautin kukanta...."
"Sir meke faruwa ne?" Ya faɗa tare da satar kallon su ta mirror, wani shock yaji cos bai ta6a ganin chief yayi hugging ɗin macen da ba muharramarsa ba.
Bakomai ya jawo hakan ba face tausayinta daya rufe shi gani yake kamar kanwarsa ce Hindu take kuka...
A hankali ya zagayo da hannayansa ta bayanta, cikin sigar lallashi yake ɗan shafa shi, wani irin relief taji tuni ta nemi kukan da ta ke yi ta rasa, nutsuwa tayi akan chest dinsa ta lumshe idanunta, tana jin wani irin yanayi da bata ta6a jinsa ba, at same time heart dinsu take beating rapidly, tsit kake ji babu mai magana a cikinsu, Cheif bai ta6a tsintar kanshi a irin wannan yanayin ba yana jin wani irin feelings a tare da shi,
daƙyar ya samu ƙwarin gwiwar, raba jikin shi daga nata
ya tallabo gefen fuskarta da hannun shi, sam ta kasa buɗe idanunta wani irin nauyin shi da kunyarshi take ji.
Sexy voice dinsa ce ta ratsa kunnanta"Tell me, meke damun ki? Me yasa kike kuka" la66anta na kerma ta ce"ba abunda ke damuna, lafiyana lou" ta rasa ya akai take jin muryarshi kamar ta Danish hakan ba ƙaramin karya mata zuciya yake yi ba,
"Ban yarda ba, kuka baya zuwa saida dalili! Faɗa min ko dai baki son zuwa asibitin ne? Daddynki ne Ya tursasa maki"? da sauri ta ce "ina son zuwa, ba shi ya tursasa min ba, kawai bana jin dadin jikina ne, bansan meke damuna ba...." gaba ɗaya idanunsa na akan pinkish lips ɗinta sun jiƙa da hawaye sunyi taushi...
Ya fahimci akwai abunda ke damunta, bata son faɗa masa ne, kuma bai son ya takura mata hakan yasa shi furta "Okey, ki daina kuka, Idan muka isa asibitin, zanyi magana da likita ya duba min lafiyarki..." wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta, still bata buɗe idanunta ba ta amsa mashi da toh, gyara zamanshi ya yi zuciyarshi cike fal da tausayinta ya maida hankalinsa akan laptop ɗinsa, yayin da Unaisah ta ƙurawa glass din motar ido tana kallon motocin dake zarya kan titi, ƙoƙari take ta kauda tunanin Danish a ranta amma abun ya faskara.....💔
_________________________✍️
Su Aneleerh suna zaune a hospital courtyard kan kujeru su uku ita da Zahra tare da Dr. Shureim sun ƙi tafiya gida kowan nansu ya ƙwallafa rai da son ganin haɗuwar Unaisah da mamanta, duk bayan ɗan lokaci sai a
Anila ta duba agogon hannunta,
Zahra harta fara gyangyaɗin bacci..
"Anila anya zasu zo? Naji shiru har yanzu.." Dr. Shureim ne ya yi maganar, fuskar shi ayamutse daga gani ya gaji ba kaɗan ba,
"In sha Allah zasu so, mu ɗan ƙara hakuri, ina ji araina sun kusa ƙarasowa..." ta faɗa tare da kallon zahra dake gyangyaɗi
Da zolaya ta ce, "Zahra kada fa kiyi mana bacci anan, kinsan dai ba iya ɗaukarki zanyi ba, sai dai ko Dr. Shureim ya taimaka mini" murmushi ya yi tare da kallon ta, idanunta sunyi ja muryarta da kasala tace "na gaji ne, ga yunwa ina ji, ga bacci..."
"Ki zo na sauke ki a gida." girgiza kai tayi, "a'a Ya Shureim kaima nasan ka gaji, bana son ma na tafi, hankalina bazai kwanta ba, in har banga haɗuwar Aunty Benazir da Azeezaty ba.." har cikin ranshi yaji dadin yadda suke nuna damuwarsu akan yar uwarsa....
Kafin wani ya ƙara furta kalma a cikin su, sautin horn Ya karaɗe kunnuwansu, kusan atare suka kai dubansu ga enterance gate din asibitin, a jere motocin suka kunno kai da matsakaicin gudu suka nufi parking space....
"Ina tunanin sune suka ƙaraso" a cewar Anila, miƙewa sukayi tsaye suna kallon su cike da sa ran ganin sune.
Tun kafin motocin su ƙarasa yin parking, Md Dr.Jidenna ya fito daga cikin asitin babban mutunne ya fara manyanta, gashin kanshi duk hurhura, Dr. Jazz na abiye da shi, already sun san da zuwan Chief, shiyasa suka fito don su tarbe shi....
Da sauri Jami'an Isod suka fara durowo daga kan motarsu sanye cikin kakinsu, qugunansu na a soke da kananun bindigu,
Cikin zafin nama suka buɗe masu murfin motar, A hankali chief ya fito kafin Unaisah ta fito idanunta akan katafaren asibitin, a ranta ta jinjina ma haɗuwar shi, su Aneleerh na ganinta farin ciki ya lullu6e su kasancewar akwai bulbs light daya mamaye ko'ina tamkar da rana..
"Yaya Shureim sune muje mu tarbo su" Anila ce ta faɗa da sauri suka nufi gurinsu, tunkan su ƙaraso Unaisah ta hango su wani irin farin ciki ne ya lullu6eta da sauri ta nufo su, kafin ta ƙaraso Anila ta buɗe mata hannu suka rungume juna, Dr Shureim tun da ya kafe ta da ido ya kasa ƙyaftawa wani irin faɗuwar gaba ne ya dirarsa masa, ya ƙura mata ido kamar zai lashe ta, ita ko ta ƙanƙame Aunty Anila kamar karta saketa,
"Sannu da zuwa my Azeezaty, tun ɗazu muke sa ran ganin ku..." Anila ta faɗa tare da ɗago da fuskar unaisah, "Ga Yaya Shureim ku gaisa, ɗan uwan mara lafiyan ne" sai lokacin ta lura da shi ita kanta da ta kalle shi saida taji gabanta ya ɗan faɗi, cikin sanyin murya ta ce "ina wuni? Ya mai jiki?"
Murmushi ya sakar mata, "Mai jiki Alhamdulillah, Malama Azeezaty, ina fata bamu takura maki ba, zamu ɗaura maki ɗawainiyar jinya," murmushi tayi "Babu takura, ni naji zan iya, kuma ni abun farin ciki na ne, fatana Allah ya bata lafiya" ba ƙaramin burge shi tayi ba, yarinyar ta shiga ran shi lokaci guda sai yaji inama ace yarinyar Benazir ɗinsu ce da sai yafi kowa farin ciki.
"Aunty Zahra" miƙa mata hannu Unaisah tayi suka gaisa da juna, Zahra na murmushi ta ce "Na ji dadin sake ganinki, Azeezaty tamu, mai mutunci" murmushi kowan nans u yayi.
Taj dake a zaune cikin motarsu Ya nutsu Yana kallonsu Aneelerh, fuskar shi kwata kwata babu walwala.
"Pls ka tashi mu fita mana" girgiza kai ya yi ba tare da ya kalli Big guy ba yace "ba inda zanje, tunda na bada Unaisah babu buƙatar in shiga ciki, ka tafi zan jira ku anan",
"Wai duk akan me kake fushin nan? Saboda baka son ganin ex-wife ɗin ka?" Banza yayi dashi bai tanka mashi ba,
"Meye na damuwa? Matar da bata acikin hayyacinta, kuma in banda abunka wazai san kaine? Mu da zamu 6adda kama da face mask"?
A takure ya ce"Don Allah ka kyale ni! Nace ba zan je ba, ka tafi mana..."
gyaɗa kai Big guy ya yi, yasa hannu ya gyara mask din fuskarsa ya fito daga cikin motar, ya nufi wurin su Chief dake atsaitsaye suna gaisawa da su Dr Jidenna.
Ɗaya bayan ɗaya ya miƙa masu hannu sukayi musabaha kafin ya ɗan russina saitin kunnan Chief cikin muryar raɗa yace"Sir taj yace bazai shiga ciki ba!" juyawa Chief yayi har zuwa bakin window glass din motar yayi kncoking din ta,
"Taj, ka sauke glass" zuge shi yayi,
Duƙowa chief yayi suka haɗa ido da shi "Haba mutumina, mun riga da munzo asibitin shiga ciki ne zai gagare ka uhuym?"
Fuskarshi a yamutse ya ce "Sir pls, bana son shiga ne, nafiso kubarni anan..."
"No taj, ban amince ba," ba don ya so ba, ya ɗauko backpack din Unaisah da ya kar6a a wurinta, ya sargafo hannun jakar a kafaɗarshi, kafin ya fito daga motar,
Ruƙo hannun shi Chief ya yi suka nufi su Dr Jazz atare suka haɗu suka dunguma zuwa cikin asibitin, su Anila suna a biye da bayansu ta ruƙe hannun Unaisah a cikin nata, kamar wani yace zai ƙwace mata ita.
Corridor din da zai sada su da emergency ward suka nufa, cikin girmamawa Nurses da Docs suke gaishe da Chief...
Sau ɗaya Taj ya saci kallon Dr. shureim, ba su ta6a haɗuwa da juna ba, lokacin daya auri Benazir Dr shureim ɗin ba ya a ƙasar ya koma Egypt da zama, sau ɗaya suka ta6a gaisawa a waya lokacin da ya kira ya damƙa mashi amanar ƴar uwarshi..."
Lokacin da suka ƙaraso gaban Medical room ɗin da Benazir take sai kowannansu Ya dakata da yin tafiya.
Kasancewar kofar ta glass ce suna Iya hangen Benazir dake a kwance tana bacci, Dr Adam Yana a tsaye bakin gadon Yana ƙara duba ta,
Knocking kofar Dr. Jazz ya yi, da sauri Dr Adam Ya juyo ya dube su, aiko da ganin su Chief jiki na 6ari ya fito cikin girmamawa ya miƙa masu hannu suka gaisa..
Fitowa hajiya Layla tayi daga dakin jikinta a sanye da hijabi bakinta washe ta fara gaishe da su, suka yi mata ya mai jiki ta amsa masu.
tunda Taj Ya kalleta sau ɗaya ya kau da idon shi gefe, ba zai ta6a mantawa da irin wulaƙancin da Hajiya Layla tayi mashi ba, hakanan ta ɗaura mashi karan tsana saboda yana son yarta, har faɗi take in banda haɗama irin na ɗan talaka ina shi ina Benazir? waye ubansa a kasar? Da aikin Jarida zai ciyar da ita? "Wama ya sani ko asiri kayi mata shiyasa ta nace saita aureka .." murmushin takaici ya saki ta cikin face mask ɗinsa...,
Dr Adam Ya ce, "ina yarinyar ne?" da yake basu lura da ita ba duk ta takure bayan Anila kamar tana jin tsoron wani abu,
"Azeezaty, zo nan mana" Biy guy ne ya kira sunanta, fitowa tayi idanunta na kallon ƙasa ta tsaya a tsakiyar su, gaba ɗaya ta tsargu da kallon da su ke yi mata, Hajiya Layla ta kasa rufe bakin ta saboda mamakin ganin yarinyar, sai taga kamar sunyi kama da Benazir ɗinta, sai lokacin Dr Jazz ya lura da ita sun ɗan ruɗe da kyawunta, musamman Dr. Adam har dai ya gaza jurewa ya ce "Tabarakallahu ahsanul khalikin..." bai ƙare maganar ba, Dr jazz ya yi saurin yi mashi raɗa a kunne"kallon ya isa haka! Future wife ɗin babban yayanmu ce, wlh ka shiga taitayinka" da sauri Dr Adam ya rufe bakin shi da tafin hannu.
"Azeezaty, ina fata anyi maki bayanin abunda ya kawo ki nan?" ɗaga mashi kai tayi alamar eh,
"Okey, abunda muke so kaitsaye ki shiga ɗakin wurin patient ɗin, ki yi hugging ɗin ta sannan ki kirata da sunan Mommynki" amsa mashi tayi da toh, kafin slowly ta juya ta nufi ɗakin zuciyarta na dakan uku uku wani irin faɗuwar gaba take ji, gaba ɗaya sun nutsu suna kallon ta...
Duk taku ɗaya idan tayi sai gaban ta ya faɗi rass, ta rasa gane dalilin shigarta yanayin da take a ciki.
Tunda ta zura ƙafarta a ɗakin idanunta suka sauka akan mara lafiyan dake a kwance tana bacci, walking slowly ta ƙarasa ta tsaya daga bakin gadon tana kallon ta, tun daga kan fararen kafafuwanta har zuwa kan fuskarta, sumar kanta ta lullu6e gefen fuskarta daga gani ba ƙaramin hauka tayi ba kafin a samu ta runtsa.
Wata irin kasala ce ta baibaye Unaisah gaba ɗaya ta kasa ta6uka komai sai kallonta takeyi kamar zata haɗiyeta.....
"Ki rungumeta mana, ke muke jira" ƙasa ƙasa da murya Dr Adam ya furta maganar,
Numfashi ta ja kafin ta daidaita nutsuwarta, a hankali ta zauna daga gefen gadon kafin ta faɗa kan ƙirjinta tare da lumshe idanunta lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka me sautin gaske ita kanta batasan kukan Ya kubce mata ba, hankalinsu ba ƙaramin tashi ya yi ba amma sai suka yi zaton tayi ne don abun ya tafi dai dai..
Sautin kukanta ne Ya daki kunnan Benazir, cikin magagin bacci ta fara sambatu tana faɗin "Babyna, wayyo Allah mami! ina babyna naji sautin kukan ta, don Allah ku kawo mini ita..." yatsun hannunta na kerma ta ɗaura su kan bayan Unaisah, da dukan hannayenta biyu ta fara shafa bayanta taji mutun akan cikin ta, hakan yasa ta fara kokarin buɗe idanunta, daƙyar ta buɗe su sun kaɗa jawur saboda bacci,
Daga can waje Dr Adam ya ce "Nayi mamakin farkawarta, because bana tunanin allurar da nayi mata ta isa ta saketa..."
Su Anila duk sun ƙagara Benazir ta karasa farkawa, gaba ɗaya jikinsu sai tsuma yake yi ga wani irin annurin farin ciki da ya wanke zukatansu,
Mayafin kan Unaisah tuni ya jima da zamewa, hakan yaba Benazir damar cusa hannayenta acikin sumar kanta ta cigaba da sambatu tana faɗin "Babyna ne? Mami daddy kuna ina? Wanene Ya kawo min babyna? meyasa take kuka?" Sosai Unaisah ta ƙanƙameta, ta ƙara cusa kanta a kirjin Benazir babu alamun zata saketa, Allah sarki jini ɗaya ba wasa ba, wannan unconditional love ɗin dake atsakanin uwa da ɗanta shine yayi tasiri a zukatansu, a karo na farko da ta fara jin ɗumin mahaifiyarta ba tare da sanin itace ba, aruɗe Benazir ta zabura ta ɗago da fuskarta ta ƙura mata ido tana kallonta, baiwar Allah Angel fuskarta tayi jawur da ita ruwan hawaye ya wanketa tass, da ƙyar take buɗe idanu tana kallon cikin idon Benazir, kallon kallo suka fara jefawa junansu duk hawayen Unaisah sun wanke fuskar Benazir, la66anta na kerma ƙirjinta na bugawa ta furta "Mamana! Ni ce babyn ki, meyasa kika tafi kika barni? kin manta dani a rayuwarki? Nayi kukan rashin ki atare dani mamana!"
Shigowa ɗakin Hajiya Layla tayi daga bakin gadon ta tsaya tana kallonsu, ƙwalla sun taru acikin idanunta,
"Mommy ki faɗamin? Da gaske babyna ne nake gani ba mafarki nake ba? Angel ɗina ne?" Kwata-kwata Angel bata fahimci sambatun Benazir ba saboda ita kanta ta ɗan shiga ruɗanin halin da ta tsinci kanta game da matar,
"Benazir, yarinyar ki ce Angel, ki rungume ta a jikin ki, " Hajiya layla ta faɗa da murmushi akan fuskarta, fashewa da kuka Benazir tayi, da sauri ta kwantar da Unaisah kan kirjinta ta rungumeta sosai kamar zata mayar da ita cikin cikin ta.
Cikin shesshekar kuka take lallashin ta"kiyi shiru ki daina kuka, bana son ji, nasan nice na 6ata maki rai, kiyi hakuri ki yafe min bazan ƙara tafiya in barki ba, nayi maki alkawarin zan baki kulawa babyna, kinji my Angel"? Sambatu taci gaba da yi taƙi bari Unaisah ta ɗago da kanta ta ƙanƙame abun ta kamar wani yace zai kwace mata ita.....
Jikin Taj ba ƙaramin sanyi yayi ba, da sauri ya duƙar da kan shi hawaye sun cika idanunshi, sai yaji inama ace zai iya zuwa ya haɗa su duka a kirjinshi ya rungumesu,
Zahra sarkin tausayi tuni ta fara matse ƙwalla, ita kanta Aneleerh kukan ne ya kusa kubce mata, da hannu biyu ta toshe bakin ta don bata son ayi zargin ko yarta ce ta gaske,
Lumshe ido Chief ya yi a yayin da yake kallon su, ya jima baiga abun farin cikin da ya sanyaya zuciyarshi ba irin na yau! abun ya ta6a zuciyar shi....
Hatta Docs ɗin dake a tare da su saida suka ji tsananin tausayinsu, A hankali Dr shureim Ya zaro hanky daga aljihu Ya share kwallar da suka tarar masa, yana ji aransa da wuya yarinyar in ba jinin su bace!!
Dr Adam ne ya sauke yar ajiyar zuciya ya ce "in sha Allah zata samu sauƙi, naga alamun nasara tun kan aje ko'ina, Yarinyar ba ƙaramin wayau ne da ita ba, ta iya acting,..." kallon shi kawai Anila tayi su da suka san meke atsakanin su..
Dr jazz ma ya ce "Ubangiji Allah Ya bata lafiya, Allah yasa yarinyar nan ta zama silar warakarta" gaba ɗaya suka amsa mashi da ameen....
"Yalla6ai, muje office mu ƙarasa magana" Dr. Jidenna ne Yayi maganar, atare da Chief suka nufi katafaren office dinsa.Tattaunawa suka yi dangane da Unaisah, Chief ya ce masa baya son kowa ya sake shiga ɗakin mara lafiyan daga grandma ɗinta sai Unaisah, bayan haka Yana so a canza mata ɗaki su maida ta private room saboda Unaisah ta samu damar sakewa wurin yin jinyarta, ya ɗaura da faɗin "Bana buƙatar wani likita ya shiga dakin ta in ba Dr Jazz ba, shi nake so ya cigaba da kula da mara lafiyan" Dr Jidenna ya ce "Consider it done sir, in sha Allah a cikin daren nan zamu aiwatar da komai" sun jima suna tattaunawa a office din kafin daga bisani suka fito a tare, har lokacin su Shureim suna a tsaye bakin kofar dakin suna kallon su Benazir,
Bayan sun dawo wurinsu chief Yaja hannun Dr Jazz suka ke6e wuri ɗaya dama shi mutuminsa ne, Yana jin dadin aiki da jazz yaron yana da hankali,
"Jazz, nayi magana da Md, kaine zaka cigaba da kula da mara lafiyan! Pls bana so asamu matsala!" murmushi jazz yayi "In sha Allah babban yaya zanyi kokari sosai gurin basu kulawa,"
"Good, sannan inaso ka duba jikin yarinyar, ta faɗamun bata jin dadi, pls inaso ka bata kulawa ta musamman, bana so ta nemi wani abu ta rasa! Kayi kokarin kwantar mata da hankalinta kamar akwai abunda ke damunta"
Jinjina kai jazz ya yi "In sha Allah My Boss, kasan bana wasa da duk wani abu da ya shafe ka" harara Chief ya ɗan watsa mashi, ya sunnar dakai ƙasa yana murmushi...
Ruƙo hannunsa chief yayi suka koma wurinsu Taj,
Duba agogo big guy ya yi "Yakamata mu tafi dare yayi, almost 12,"
Da sauri Anila ta ce "pls muna son muyi mata bankwana kafin mu tafi"
Dr Adam ya furta "Okey, bari na kira maku ita" shiga dakin yayi,
"Azeezaty yan uwanki suna son ganinki zasu tafi, ki fito kuyi sallama" shiru yaji bata amsa mashi ba, leƙa fuskokinsu yayi abun mamaki bacci ne ya ɗaukesu rungume da juna bayan sun gama shan kukan, gaba daya Unaisah tana kwance kan jikin Benazir shiyasa gadon ya dauke su....
Fitowa Dr Adam ya yi fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce "sai dai kuyi hakuri bacci suke yi, ba zamu iya tada su ba"
"Dr ga backpack ɗin kayanta, ka shigar mata da ita ciki" sauke jakar Taj ya yi tare da miƙa ma Dr Adam ya shiga da ita ciki ya ɗaurata kan kujerar gaban gadon.
Kamar kar su tafi haka suka dinga kallon su ta cikin door glass ɗin, kafin daga bisani suka kama hanyar barin asibitin, har bakin parking space Hajiya Layla ta rakasu tana ta faman yi masu godiya kamar zata duƙa ƙasa, shima Dr. Shureim godiya sosai ya yi masu tare da fatan alkhairi, sallama sukayi wa junansu Zahra da Anila suka shiga motarsu, Taj da Big guy suka shiga tasu motar, kafin Chief ya shiga motarshi, saida Hajiya Layla ta ƙara yi masu Anila godiya saboda halaccin da su ka yi masu kafin motocin suka fuce a jere da matsakaicin gudu, ya rage saura Hajiya layla da Dr Shureim, su jazz tuni sun koma cikin asibitin..
"Shureim ka ga wani ikon Allah? Yarinyar nan tana kama da Benazir, bansani ba ko idanuna ne suke nuna min hakan"
Murmushi shureim ya yi "ba idanunki bane, nima naga kamanceceniyarsu, wlh Mommy naji dadin ganin yadda Benazir ta rungumi yarinyar ajikinta, sai naji inama ace yarta ce, saboda ta kwanta mun araina..."
Hajiya layla ta ce "ba kai kadai ba shureim, nima yarinyar ta burgeni, ga wayau daga gani tana da kaifin basira, iyayenta sunyi mana hallaci kuma basu nemi komai daga gurin mu ba, ko da yake naga yarinyar ma ƴar masu arziki ce...."
Dr shureim ya ce "Mommy zan wuce gida dare yana ƙara yi, pls ki kula da yarinyar nan, kinga dai yadda yan'uwanta suka damƙa mana amanarta, bana so asamu matsala..."
"In sha Allah Shureim, ay bazan yi sakaci da rayuwarta ba, dole inyi takatsantsan tun da naga ɗiyar manya ce, hada fa jami'ai cikin waɗanda suka kawo ta"
Ƙara tattaunawa suka yi kafin ya yi mata sallama ya buɗe motar shi ya shiga ciki, akan idon ta motar ta fuce daga asibitin, ajiyar zuciya ta sauke kafin ta juya ta nufi ciki cike da zumudin son ganin yarinyar..
______________________________✍️
Bayan su taj sun rako chief part dinsa, saida suka ga shigarshi cikin bedroom dinsa kafin suka sauko falo, har sun kusa fita suka tsinkayi muryar ummi daga bayan su
"Boss sannun ku da zuwa"! Atare suka juyo tare da kallonta, sleeping gown ce a jikinta, ta yafa mayafi akanta, da alama ta fara bacci ta farka
"Yawwa Ummi, me kike yi har yanzu bakiyi bacci ba"?
Fuskarta ayamutsa tace"na kasa bacci saboda damuwar rashin unaisah, tun wuraren karfe takwas da rabi muke ta nemanta saboda muyi dinner shiru babu ita, ko'ina mun duba, ƴan uwanta ma dakyar na kwantar masu da hankali har su ka yi bacci, nayi zaton ko taje part din ka ne" Tay maganr tare da nuna taj
Big guy dake kallon ta from head toe gaba daya ta jefa shi ayanayi, saboda kayan baccin jikinta sun bayyana surarta,
"Ummi, unaisah ba agida zata kwana ba, taje asibiti" bai ƙare maganr ba, ummi ta zaro ido tare da dafe kirjin cike da tashin hankali tace"inna lillahi meke damunta? Bata da lafiya ne"? abun da yasa ta ruɗe saboda halin data ganta dazu a daki, abun ya tsaya mata arai, har jiran zuwanta tayi kamar yadda tace mata zata zo amma shiru bata neme ta ba...
Kwantar mata da hankali taj yai"lafiyarta ƙalou ba ita ce ke bata da lafiya ba, yar uwar chief ce...." bayani yayi mata dalla dalla, lokaci daya ta sauke ajiyar zuciya,
"Hankalina har ya kwanta, amma banji dadin tafiya da tayi batare data yi mana sallama ba, yanzu sai yaushe zata dawo gida"?
"Bani da masaniya, amma bana tunanin zata dauki lokaci, pls ki kwantar ma yan uwanta da hankalli banaso su sanya damuwa aransu"
"In sha Allah, mu kwana lafiya boss, agaida min da madam" ya amsa mata da toh, satar kallon big guy tay ya wani tsareta da ido, harara ta dan watsa mashi haɗi da yin murmushi ta juya ta nufi ciki, harta bace ma ganinsa bai kauda idonsa ba, sai da taj ya bugi kafadarsa kafin ya juya suka fuce kowa ya nufi part dinsa..
______________________________✍️
Prisoners Shield💔
Bawan Allah, kwata kwata baya acikin hayyacinshi, Yasha bakar wahalar radadin da zuciyarshi keyi mashi, tun safe har kawo iyanzu da dare ya ratsa ko ruwa bai gifta makoshin shi ba, saboda tashin hankalin da yake a ciki, yayi haukan yayi kukan amma babu abunda Ya canza nadaga kuncin da yake ji, babu wanda yayi tunanin ya leko dakinsa yaga awani hali yake ciki, saboda su kansu yan uwan nashi yanzu mantawa su ke yi da shi tun da suka fahimci bayason shiga cikin su kuma baya son kowa ya ra6e shi, a fahimtarsu, unaisah ita kadaice ta damu da shi, bata iya wuni batare da ta leko dakinsa ba, ta damu da shi fiye da yadda ta damu da kanta, itace farin cikinsa kuma gatansa, baya jin zai iya rayuwa batare da ita ba, Unaisah kaddararsa ce! Bugun zuciyarsa ce.
Cikin ikon Allah bacci mai nauyi ya ɗauke shi, hakan ba karamin relief ya sama mashi ba, yayi bacci sosai har na tsawon awanni, gab da za'a fara kiran sallar asuba, ya fara mutsu mutsu, yatsun hannayensa dana kafarsa suka fara kerma....."
Farat ɗaya ya buɗe idanunsa waɗanda suka kaɗa jawur tamkar garwashin wuta, Gaba ɗaya rasa ƙwarin gwiwarshi, kamar matacce Sam ya kasa motsawa daga kan floor, ko yatsansa Ya gaza ɗagawa, wani irin gumi ne Ya wanke jikinshi kamar wanda aka tsamo daga cikin teku, ta ko'ina zufa ke tsatsafo mashi, ga wani azababben zafi da jikin shi ya ɗauka.
shatun jijiyoyin goshinsa sun fito rudu rudu kan fatarsa,a kalla ya shafe mintuna yana kokarin sarrafa zuciyarsa gudun kada evil heart dinsa ta motsa, bakomai idanunse ka hango mashi ba face fuskar Unaisah.
Dakyar ya samu kwarin gwiwar motsa gabban jikinsa, Ya lalla6a Ya miƙe tsaye kan ƙafafunsa, jansu ya dinga yi saboda wani nauyi da sukai mashi dakyar yakai kan shi toilet ya faɗa ciki yana jan numfashi, agaban sink ya tsaya yana faman sauke ajiyar zuciya.
Sannu a hankali brain dinsa ta fara tariyo mashi abunda Ya faru daren jiya atsakaninsu, yaga komai a mafarkinsa.
ɗago da hannayensa yayi tare da saita su saitin fuskarshi Ya ƙura ma tafukansa ido Yana kallon su ....da sauri ya girgiza la66ansa na kerma ya furta"bani bane! Bada son raina ba, bansan na akaita ba, bana a cikin hayyacina!...." dafe kansa yai da hannu ɗaya ya cusa yatsunsa acikin sumar kanshi, ya cigaba da cakuɗata gaba daya ya haukata gashin kanshi, duk ya rikice saboda ya gane shine da kafafuwansa Yaje dakinta adaren jiya har yayi mata aika aikar nan sai dai yayi imanin bayin kanshi bane❗ cije la66ansa yayi har saida suka fashe jini ya fara ɗiɗɗigowa, wani irin tsanar kanshi ne Ya kama shi, kamar ya kashe kanshi haka Yake ji, da karfi ya buga forehead dinsa jikin sink nan take fatar wurin tayi jawur kamar zata fashe, buga kanshi yacigaba dayi yana sambatu yana fadin Ni ne da kaina na cutar da Angel dina? tana kuka tana rokona dan in taimaka mata amma nagaza share mata hawayenta, bani da tausayi, ni mugune, na tsani kaina..." jinine ya fara gangarowa ta kofofin hancin shi, wani irin jiri ya fara kokarin kwasarshi, ya fara tangal tangal zai kife kasa kwatsam ba zato ba tsammani Yaji hannu mutun akan damtsensa, gaba daya ya janyo shi tare da rungume shi akan broad chest dinsa, ya zagayo da hannayensa akan bayan shi, bawan Allah baya gane komai, idanunsa sun makance, ji yake tamkar angel dinsa ce ta rungume shi, hakan ya shi ƙara ƙanƙame mutumin da ya rungumeshi duk ya 6ata mashi gaban Rigarshi da jininsa, hakan baidame shi ba, babban tashin hankalin shi halin da yaron yake aciki! Ya tsorata da ganin yadda yake kokarin kashe kan shi ❗lamarin yayi matukar gigita shi..
"Ki yafe min Angel, ba yin kaina bane, bazan iya cutar dake ba, sharri akaimin, ba halina bane, ki tausayama rayuwata, ke kadai ce farin cikin da nake da shi a duniyar nan, bani da gata daya wuce ke...." gaba ɗaya sambatunsa acikin kunnan sa, Ya nutsu Yana sauraron shi, har lokacin bai ɗago da kan shi ba, balle har yasan wanene Ya rungume shi.
___________________________________✍️
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*
Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US
OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.
Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job
LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe chapter 33 Complete
by
Novels Elite Admin
August 29, 2024
Takun Ƙarshe
✍️
Table of Contents